← Book details Jawaheer Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 23 OF 45

Sashe 23

Jawaheer Part 1 Complete Hausa Novel · about 4 min read

Jawaheer kam bata Jin komai na abunda dr yake fada mata, shima kaman ya lura da hakan yasa yace mata bari ya barta yaga kaman ta gaji, hakan ya mata dadi yace ta bashi number dinta, bashi tayi sannan ya bata ledoji manya guda biyu daya kawo mata, amsa tayi tare dayi mishi godiya sannan ta fita tayi gida, a falo ta tarar da adda tana cin danwake, zama tayi kusa da adda tace adda samir yazo naga bai dade ba ya fita, adda tace hmm aini yau yaban mamaki, kinji hausa gaidani yayi da hausa harda cemin saida safe, jawaheer kam shuru tayi tana tunanin mai yasa ya tafi bai bari ta shigo ba, jin adda tayi ta katse mata tunani da fadin nasan ya ganki keda wani koh? Tace eh adda wannan dr din nanne yazo dubani, kinga yanda ya sakar min harara nan taba adda labarin abunda ya faru, adda tayi murmushi tace jawaheer inaso ki nutsu ki bama wannan dr din lokacinki dan ki nuna ma m samir kema fah akwai masu sonki, jawaheer tace adda shifa dr gaidani yazo yi ba sona yace yakeyi ba, adda tace aida haka zai fada miki, kedai kawai kiyi abunda nace..... Sallaman mum ne ya katse musu firan da sukeyi, jawaheer da fara'a tace mum har kun dawo sannu da zuwa, mum ta amsa tare da fadin dad dinki yace kije yana waje, tashi tayi ta fita ta sami dad a mota, dad yace jawaheer gobe ni zan koma ko akwai abunda kike bukata? Tace a'a dad babu komai sai dai ina son ka canza masu adda gida inda hali, dad yayi murmushi yace naso nayi hakan amma m samir ya rigani dan dazu abubakar yake fadamin fitan da sukayi gida yaje ya siyan musu cikin adamawa, abubakar yace gidan babba ne akwai komai da komai domin gidan wani barawon gwamnati ne wanda ya saci kudi shine gwamnati ta kama gidan ta saida, jawaheer tace kai Allah ya saka mishi da alkhairi, dad ya amsa da ameen, sannan yace an fara biyan kudin aikin haji, zan biya musu sai yasa zan koma ma gobe, sannan ina aiyuka, jawaheer tace Allah ya saka maka da alkhairi dad, murmushi yayi tare da kara son yar tashi ba ita yama abu ba amma tana ta godiya, kudi ya dauko ya bata ta amsa tare da fadin dad nida transfer kamin ma da yafi, dad yace toh riqe wannan din bari in miki transfer din ma, nan ya mata transfer tace kai dad kudin yayi yawa, yace jawaheer kudin da nayi ta sanadinki ne in baki ciba wa zaici, sannan million dari din da mum dinki ta bani lokacin data miqa mana ke, dasu na fara sana'a har nayi mugun arziki inada kalan kudin wajan sau million, na ware miki million dari na ajiye duk sanda naga mahaifiyarki zan bata kudin, wani hawaye ne ya zubo ma jawaheer tare da fadin dad idan na tuna baku kuka haifeni ba ina shiga cikin wani hali, wlh dad zuciya na yana zafi inna tuna hakan dan Allah dad kubar tunamin, ta karasa zancen cikin kuka, ya janyota jikinshi yana bata hakuri tare da fadin jawaheer ke yata ce har gobe, murmushi tayi tare da fadin ngd dad, yace bari inzo in tafi bacci nake ji, tace toh saida safe dad, gida ta koma inda ta sami adda ta fiffito da kayan da dr ya kawo kayan tea ne manyan gwangwani dasu milo sugar kwali dasu biscuit chocolate, mum tace ashe dr yazo dubaki? Tace eh mum, mum tace wannan hidima haka Allah dai ya saka mai, adda ta amsa da ameen, jawaheer kam haushin kayan ma taji tana yi, dan me yasa zai kawo mata suma, tashi tayi ta nufi daki, bata dade da shiga ba mum ta shigo, tace mum ashe samir ya siyama su adda gida? Mum tace eh wlh gobe zamu gidan ma muga in akwai abunda yake bugata duk da abubakar yace basai ansa komai ba, amma gobe zamu mu gani, jawaheer tace Allah ya kaimu, jawaheer ta kasa bacci babu abunda take son ji sai muryan m samir tashi tayi ta fita ta kira number dinshi amma taji ance switch off, tsaki tayi ta koma daki ta kwanta sai juyi take tayi.
Chapter 23 · 0% Book details