← Book details Gwajin Dafi Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 70 OF 74

Sashe 70

Gwajin Dafi Complete Hausa Novel · about 8 min read

Tad'anyi murmushi"zuwa kai amma kabari muyi sallar Isha'i.Yasaki labulan yak'arasa shiga cikin d'akin yamik'a mata wata babbar waya samfurin Samsung"to ga wannan idan kun gama you shoud let me know zani Fadiyan Guga ne.Takar6i wayar ranta ba dad'i, a daren litini yashigo da manyan wayoyi sunfi hamsin,da su na'ura me kwakwalwa wai duk tsintar yayi a cikin gari da tarin kud'ad'e a cikin buhu"lallai wata shari'ar sai dai a lahira wallahi!.

Washe gari da sassafe sukayi sallama da kowa suka d'auki hanyar garin gwamma,ko a hanya basu samu wata matsala da jami'an tsaro ba dan kowa ya san abinda yafaru a Zonkwa, idan musulmai ne su jajanta tarebda addu'ar"ALLAH yasa kaffarace,idan kuma arna ne suji dad'in ganin mutanan da suke kwance cikin mawuyacin hali,da da dama da sun k'arasa su da bindiga,wanima gallama Alhajin Salim harara yayi"to wad'annan dai ai kuna 6atama kanku lokaci me wajen kaisu asibiti"repetitive strain injury ne dasu fa ko baku gani bane?Mun gani sai yaya?Alhaji Salim ya tambayeshi.Yamotsa kafad'a yana ta6e baki"they are in coma I don't think they will survive. Alhaji Salim yaja motar ba yare da yace kome ba.

Motarsu tana tsayawa a harabar gidan sauran yaran suka fito da gudu" oyoyo Abbanmu... oyoyo Yaya Umminmu,suka ringume juna cikin farin ciki.Hajiya Bara'atu farar mace,jaruma me k'ok'arin adalci da gaskiya a duk al'amuranta tak'arasa saukowa daga matattakalar benen,fuskarya d'auke da murmushi, Ummi tasaki k'annanta ta rungumeta "Mamanmu nayi kewarki,kullum sai na yi mafarkinki. Tarik'e hannunta suka zauna"nima haka,toh ya fargaba?Ummi takad'a kai"Mamanmu al'amarin ba kyan gani sai ma kinga wad'anda muka kai asibiti mutum a raye amma ya fara ru6ewa tsutsotsi suna fitowa a jikinshi!takama goshinta da hannun dama kwallah sun ciko idanunta "kai! Mamanmu arna basu da imani kona sisin kwabo kuma...sallamar Alhaji Salim daya tsaya gaisawa da mak'otanshi da katseta daga abinda zata fad'a.

"Sannu da zuwa Alhaji.Ya zauna"yauwa sannu da gida ya akaji da yara?Tayi murmushi kawai wanna ta tambayi ya masu jikin?Toh godiyar Ubangiji a kowani hali da yanayi,yakad'a kai amma abin kam ba gyan gani.

Hajiya Bara'atu tama mijin na ta wani kallo dasu biyun suka san ma'anarshi duk da yana cikin damuwa sai da yayi dariya,sauran k'annin Ummi suka shiga tayashi darawa duk da basu san abinda yasashi dariya ba,Ummi ce kawai taga abinda yafaru tace musu "to kiyi shiru Ku fa a wasu lokutan baku da wayau,dan kawai kunga ana dariya sai kuma ku fara?Yaran suka kalleshi"kaima Abbanmu ALLAH sai kayi shiru.Toh nayi shiru ya daina dariyar,sai suma sukayi shiru.

Ummi tamik'e"Mamanmu barinje in watsa ruwa,kuma kuzo muje daga nan kowa yabani labarin abin dad'in da Mamanmu tabashi da bama nan.Suka mik'e Yehhh...wallahi munji dad'i,munje kasuwar baje koli,munje gidan dabbobin daji har munyi selfie da 6auna da giwa da d'awisu kuma hotunan suna wayar Mamanmu tace dama zata nuna muku.Suka bisu da kallo cikin so da k'auna irin ta Iyaye da babu kamarta a wajen kowa sai su d'in har suke shige d'akin Ummi,sai tasama k'ofar mukulli dan kar wani yafito"toh duk ku zauna sai na fito daga wanka zan baku tsarabar dana siyo muku ta d'auko wayarta ta kunna musu wak'ar"Adam wa Hauwa na Ihab Taufiq nan da nan suka fara bin wak'ar.

Mutane goma Alhaji Salim yad'ibo daga Zonkwa tare da d'aukar nauyin kome nasu na magani har zuwa sanda zasu samu sauk'i,sai dai a cikin watanni biyu da zuwan su"44 Nigerian Army Hospital"mutum d'ayane"Julaibib Abdullahi D'ansarai shine ya zama ZAKARAN GWAJIN DAFI.

Sai dai shima a watanni biyun nan sau d'aya rakkin-rak ya farfad'o daga dogon suman da yayi yana kuka da sambatun kiran Bilkisuna,Innarmu, Musaddiq, Zaujatiii... Walida,Sudaida,da sauran sunayen yan'uwa amma wad'annan su yafi kira ko a cikin baccin shi.

Sai kuma yau da yasake farfad'owa sai dai Alhamdulillahi wannan karan cikin hankali yadawo hayyacinshi,a hankali ya bud'e idanunshi yana bin d'akin da kallo,ya gane a gadon asibiti yake kwance, duk in da yasamu karaya an gyara,na hannayen shima sun warke sai dai k'afarce har yanzu da saura, ya maida idanunshi kan Ummi da take zaune nesa dashi tana magana a waya.

Wacece wannan?Ya tambayi kanshi yana kuma k'ok'arin tunano a in da yata6a ganinta sai dai bangaren tunani da adana bayanai na kwakwalwarshi sun bashi tabbacin bai san taba,bai kuma ta6a ganin taba sai yau d'in,abu d'aya da zai iya tunawa shine wata ma'aikaciyar jinya tace zata taimakesu bayan nan kuma k'irjinshi yafara mishi suya sai jin wani abu kamar allura yana tsikarin jikinshi daga nan kuma ya numfashin shi ya d'auke.Idanunshi suka sake kad'awa jawur,yanzu ne yake jin asalin ciwo a jikinshi ko ina yayi tsami.

Kwanakinshi hud'u kenan da dawowa daga hayyacinshi,amma ba wanda yasani saboda yana jin alamar za a shigo zai maida idanunshi ya rufe, yauma jin za a shigo da yamaida idanunshi ya rufe a haka har baccin gaske ya d'auke shi.Sai farkawa yayi yafara jin sheshshek'an kuka ana magana a hankali"kiyi hak'uri Ummi ki bar kukan nan dan banga amfaninshi ba,kar yajawo miki matsala".

Mamanmu ni tausayi yake bani,duk wanda muka zo dasu sun mutu sai shi kad'ai yarage, sannan yanzu duk azabar da yasha an sake karya k'afar wai bata zauna a saiti ba?Takalleta cikin natsuwa"ba kina wajen akayi hoton k'afar ba? Kuma ai kinji bayajin da likitan yayi dan haka ba kome Ummi, ai gwamma ayi abinda ya dace a lokacin da yadace tunda ko an bar k'afar haka to daga baya dolen-dole dai sai an dawo an gyara"ayi agama ai yafi gobe adawo.

Da wannan yawan kukan da kike yi ai gwamma ki dinga mishi addu'a"ALLAH yatashi kafad'a, yasa kaffarace wannnan wahalhalun rayuwar da yake ciki ko?Tagyad'a kai"to amin Mamanmu. Hajiya Bara'atu tayi murmushi"barinje wajen A'isha mu gama maganar kayan danace takawo min sai in zo mu wuce gida yamma na yi.Julaibib yasake tambayar kanshi"su wad'annan su wanene?Sune dai suka kawo shi asibiti suna cigaba da kula dashi ko shakka babu,kullum addu'arshi a garesu"ALLAH yasaka musu da mafificin sakamakonshi ya sanya hakan a mizanin kyawawan ayyukanshi.

"This is my hijab...I will never remove.

Wak'ar Ahmad Bukhatir data sa a matsayin ringtone d'inta tafara tashi,abinda yasa Julaibib yazabura tare da bud'e idanunshi yana kallanta.Itama abin ya bata mamaki,tabbasss da k'afarshi ba a sagale take ba,ba abinda zai hanashi mik'ewa.

Tad'aga wayar da sallama,jikin Julaibib ya dad'a yin sanyi saboda ringtone d'in Sudaida kenan tun saninshi da ita da waya bata ta6a canja waba, haka kuma idan tana cikin nishad'i wak'ar da zaiji tanayi kenan,wanda a wasu lokutan shima ba zato sai yaji yana wak'ar,har rannan yakalleta "Zaujatiii...bakya gajiya da wannan wak'ar,ta masa"eh Yaya D'ansarai ai kalmomin cikin wak'ar ne babu na yarwa,ni duk wak'ok'in Ahmad Bukhatir ina sansu tunda ba harigido, gaskiya da gaskiyace kawai.

Yamaida idanunshi ga kallanta. Tagyad'a kai"na'am Insha-ALLAH,tayi jimmm...tana sauraron abinda ake fad'a daga d'ayan bangaren,wani d'an lallausan murmushi ya su6uce mata gefe da gefenta fuskarta suka lotsa ciki sosai(dimple)sannan tace"fi amanillah...Ilal-liqaa.Tacire wayar a kunnanta tana kallan d'an siririn farin agogon dake d'aure a hannun damarta,tayi rubutu a wayar sannan tasata a jaka.

Tamatsa kusa da gadan da yake kwance tana farin ciki da farkawarshi,cikin muryarta ta natsuwa tace mishi"sannu...ya jikin?Sai kawai idanunta suka kawo ruwa saboda tuno ranar data fara d'ora k'wayar idanunta a kanshi"yana kwance magashiyan wasu sassan jikinshi inda akwai sara da suka naman wajen yayi kore yana fitar da wani ruwa me wari,tsutsotsi yammm...sunata fitowa ta wajen, sai dai yanzu Alhamdulillahi yanata samun sauk'i,ta sauke idanunta akan k'aton d'inkin da aka mishi a kai da kafad'unshi duk sun d'auko warkewa.

Tasake kallan fuskarshi sai taji irin abinda taji a ranar farko ruguzowar wani abu kamar gini a k'ahon zuciyarta,ta kauda kai da sauri,shigowar wasu ma'aikatan jinya guda biyu sanye da kakin soja ya bata tabbacin lokacin bada magani yayi.Tad'an sara musu dan suna aikin su yadda yakamata"aikinku yana kyau"bravo.Sukayi murmushi"Thank you. Tagyad'a kai"you're well come,tajuya tafita a d'akin tare da rufo musu k'ofar a hankali.

Makonni uku bayan nan Julaibib yayi kyan gani fiye da zato saboda yana samun kulawa ta musamman da kuma cimar abinci me inganci da gina jiki,k'afar da aka dad'a gyarawa itama yana d'anyi tattaki da ita amma da taimokon sandunan da yake dogara jikinshi(crotch)a gajiye yashigo d'akin ya had'a zufa kashirban saboda d'an tafiyar da yayi,ya yar da sandunar yana goge zufan fuskarshi,tunani barkatai sun cika k'wak'walwarshi na abubuwan da suka faru, yanajin d'acin mutuwar kamar yanzu yafaru.

Aka turo k'ofar tare da yin sallama. Yad'ago idanunshi da suka kad'a jawur ya amsa sallamar,bai kuma cewa kome ba har Alhaji Salim ya zauna yanata kallan Julaibib d'in cikin tausayi yana ayyane-ayyane a zuci,yasauke numfashi"Qadarullahi wamasha'a fa'al.

Julaibib sai hak'uri dan ALLAH mahaliccinmu ya fika sanin halin da kake ciki,idan ka dogara gareshi zai samar maka da mafita a ragowar rayuwar da zakayi ga kuma tarin lada na maida al'amura gareshi.Nagode Alhaji, kuma bani da bakin da zan gode muku sai dai Ubangiji yasaka muku da irin sakamakon shi,dama kuma ina son sanin kud'ad'en da ka kashe min a asibiti nan.Alhaji Salim yagirgiza kai"ni duk abinda na maka na yi shine dan girman zatin ALLAH a matsayinka na d'an uwana musulmi me buk'atar taimako,ba wai na yi shine idan ka warke ka biyani ba,ni a wajen ALLAH nake neman ladana.

Yagyad'a na sani Alhaji ban kuma man taba,kuma har abadan duniya bazan ta6a mantawa da wannan karamcin na kaba,to amma ina da kud'ad'e da yawa a asusun ajiyata ta gidan kud'i... idanunshi suka sake kad'awa jawur bani da kowa... idan ban baka kud'in ba to me ma zanyi dasune?Wa zan ba?Iyaye da Iyali da sauran yan'uwa ko? Toh duk sun rigamu gidan gaskiya, yakad'a kai cikin alhini da tsananin tausayin kai.

Zuri'ata tatafi abadan,babu me dawowa har a nad'e doron duniya!!!Yad'aga hannayenshi"Ya Ubangijina!ka jikansu, ka gafarta musu!kasasu a cikin shahidan bayinka wad'anda zasu tashi ranar alkiyama jinin jikinsu da aka zubar yana k'amshin turaren almiski.Alhaji Salim yana tayashi da amsawa da"amin amin ya rabbi.
Chapter 70 · 0% Book details