Sashe 36
Gwajin Dafi Complete Hausa Novel · about 8 min read
"YA ALLAH!KA GAFARTA MATA!YA ALLAH KABA TA TABBATA!
Suka juya zuwa cikin gari jikinsu a sanyaye,zuciyoyin su cike da alhini da d'acin mutuwa.
Malama Lamid'o da iyalinshi suka fito za su tafi.Julaibib yana tsugune a gabansu ya sunkwui da kai,kukan shar6e yake yi hawayen suna ambaliya a fuskar shi, ganin haka yasa Tukur yarik'o hannun Inna da take matsar kwallah zuwa mota"Inna zauna.Cikin dauriya Malam Lamid'o shima yatsuguna yadafa kafad'arshi"kayi hak'uri Julaibib hak'ik'a wannan mutuwar babu wanda ta dake su kamarmu iyayanta da kai,to duk mu d'auki hak'uri kowa zaman jiranta yake yi,tabbasss da ina da wata 'yar bayan Bilkisu to dana ba ka, amma zan cigaba da maka addu'a"ALLAH yaba ka wacce tafi Bilkisu,yayita rarrashin shi sannan sukayi sallama dasu Baba.Tukur yaja mota suka tafi. Julaibib yabi bayan motar da kallo har tasha kwana ta6ace ma ganin shi sharrr...sharrr...wasu zafafan hawaye suka zubo mishi. Yakad'a kai cikin maimaita Istirja'i.
Bayan sallar magriba Inna ta kawo mishi kunun tsamiya da kosai.Julaibib daga dawowa daga masallaci sai kuma ka kwanta? Tashi kayi bud'a baki mana.Yamik'e zaune dak'yar dan kanshi na wani sarawa "Inna bana jin yunwa cikina ya cunkushe kamar na ci abinci"Tajijjiga kai"na sani D'ansarai to amma dai ai ka san an umarce mu da gaggauta bud'a baki,azumi fa kayi daure kaci dabino kaji... yakar6i guda d'aya haka dai yaci amma wallahi baiji d'and'anon shi ba dakyar ya had'iye.
Malam Abdullahi yashigo shima yazauna yadafa kafad'ar shi"Malam D'ansarai ai wannan lokacin yana d'aya daga cikin lokutan amsa addu'a,to ba sai kayi amfani da wannan damar wajan rok'ama Magado gafara dama kai kanka ba?Duk da yana cikin damuwa amma sai da yad'anyi yake ganin yadda suke ta rarrashin shi Inna wai ita sai ta bashi kunnun ma abaki wallahi kuma yau a d'akin baccin ta za su kwana tare "Karki damu Inna zan sha amma sai zuwa anjima kin san ba sosai nake cin abinci daga shan ruwa ba.Eh haka ne ,tamik'e ta barshi da Baba.
Washe gari su Julaibib da iyayan su motoci guda uku sukayi dan zuwa Matsirga ta'aziyya sun tafi da manyan kololin shake tam da abinci ,kullum sai sunje har sai da akayi addu'ar uku.
Yana rik'e da agogon da aka cire a hannun Bilkisu lokacin da za'a mata wanka sai jujjuya shi yakeyi,tunaninta da irin hirarra kinsu ya cika k'wak'walwar shi"Bilkisu a very meek damsel ta tafi ta barshi,burin su na zama ma'aurata bai cika ba.
"Sai na kira...
kalmar da suka fad'a ma juna ta k'arshe shi da ita kenan,sai sak'on muryar data turo mishi,yasake kunna sak'on muryar yana sauraro a karo na barkatai sau shurin masaki,ya kad'a kai"uh uhun mutuwa rigar kowa...
Sudaida tashigo tana kallanshi cikin zancen zuci"shi ko wani irin so yakema wannan Bilkisun?Kullum taganshi sai taga ya dad'a ramewa,tausayinshi yamamayeta dan ba ta jin dadin ganin shi a haka,itama tayi nadamar abinda tadinga ma Bilkisu wanda ita Bilkisun ko a fuska bata ta6a nuna ta ji haushi ba"Yaya Julaibib dan Allah kayi hak'uri,kaga yadda kake ta ramewa? Yad'an kalleta"to nagode.Ta ajiye rediyon tafita. Inna tafio daga D'akin-girki tana kallanta tana sa takalmi"ba dai tafiya za kiyi ba?Tafiya zan yi Inna dan zanyi rubutun allo yau akwai darasu,amma idan nagama zan dawo in sha fate na.To shikenan, ALLAH yamuku albarka"Amin Innarmu.
Malam Lamid'o yana zaune a d'akin zaure yajiyo sallamar Julaibib.Yafito da sauri kaine haka?To maraba yashiga suka gaisa.Malam Lamid'o yace ikon ALLAH dama Tukur nake jira yadawo anjima za muzo wajan na ku.Ya amsa cikin girmamawa"Malam shi yasa ma nazo dan Baba yafad'a min yadda kukayi ta waya"Indai za kuzo ne dan kawo wani abu game da kayan auran Megado to kubari.
Malam Lamid'o yagirgiza kai"sam-sam baza ayi haka ba.Ya amsa cikin ladabi"wallahi Malam kome da aka kawo saboda Bilkisu na bar muku har abadan duniya arabama yan'uwa da abokan arziki bazan kar6a ba.Malam Lamid'o yayi shiru cikin jinjina wannan al'amari,sai kawai yad'auki wayar shi yakira Alhaji Abdullahi yafad'a mishi abinda Julaibib yace"Baba yayi murmushi "haba Malam dan D'ansarai ya ce haka har sai ka kira?Tunda yace ya bari to ya bari d'in ne,kutaya mu addu'a kawai Allah yabashi macen alheri.Ya ajiye wayar cikin sanyin jiki.Karka damu Malam Julaibib yafad'a."Julaibib ALLAH yamaka albarka,ALLAH yasa kagama da duniya lafiya, ALLAH yaba ka wacce tafi Bilkisu.
Yamishi jagora zuwa cikin gidan. Innan Bilkisu tana ganin shi tafara kuka,ya sunkwui da kai cikin wani irin yanayi,ga tausayin ganin yadda Innar Bilkisu ta zabge,tayi bak'i, idanun ta sun k'ank'ance saboda yawan kuka"Inna kiyi hak'uri Bikkisu ba kuka take buk'ata a wajan muba,addu'a tafi buk'ata.Inna takad'a kai cikin hawaye "kaiya d'an nan ba kukan rabuwa da Bilkisu nake yi har yanzu ba,ina kuka ne saboda wata rana za a manta da Bilkisu wajan yi mata addu'a kaasatan(a ke6e) saboda bata bar baya ba,dama Ya'ya sune duk rintsi baza su gaji dama mahaifa addu'a ba,har sai ranar da suma suka koma ga Ubangiji.Yajijjiga kai haka ne,to amma Inna ya zamuyi da hukuncin Ubanguji?ALLAH bai k'addari za tayi aure ba, bare har ta haifi Ya'ya,Inna duk hukuncin Ubangiji akan bawan shi adalcine,duk da bata haihu ba to ai akwai sadakatul-jariya,sadaka me gudana kamar mutum yana raye adoron duniya ni zan je cikin k'auye inda duke wuyar ruwa zan gina mata rijiya...Malam Lamid'o yatari numfashin shi"a ah basai ka sake kashe kud'in kaba kabari kawai tunda kabar mana kome to zan gina mata da kud'in sadakinta...Inna tafashe da kuka ALLAH yabaka wacce tafi Bilkisu d'an nan, hakika kai masoyin Bilkisu na gaskene dan ka nuna mana haka duk da bata cikin doron duniya.
Idanun shi suka kad'a jawur"ni gobe zan koma wajan bautar k'asa dama sallama nazo muyi sai an kwana biyu,suna sallama Bello yashigo da gudu yana haki yana dariya"Yaya D'ansarai ina dabinon ajwa na da inibi na?Suka zuba mishi idanu ba abinda yadame shi sai tsallan shi yakeyi"k'uruci dangin hauka.Yamik'a mishi ledar daya shigo da ita a hannunshi.Yakar6a cikin tsallan murna"Yaya D'ansarai nagode ya k'ank'ame ledar akirjin shi"to yaushe zaka dawo? Yakalleshi da kulawa"zan dad'e ban dawo ba. Bello yad'an zaro idanu"kaiii kaima irin tafiyar da Adda tayi za kayi?Inna fa tafad'a min wai ita baza ta sake dawo wa ba sai dai muje mu same ta,ni fa shi yasa baza ni ba,kai ai za ka dawo ko?Insha-ALLAH Bello... Idanun Julaibib suka sake kad'awa jawur ya tuno da Bilkisu da take cewa gobe fa zan dawo Insh-ALLAH... Cikin wani irin yanayi suka yi sallama yaja motar shi yatafi,ya dad'e a Water-fall d'in Matsirga yana kallan ruwan yadda yake gudu cikin Qudirar Ubangiji ba dare ba rana shekara aru-aru.
Sagir yafito da gudu yana kiran shi" Yaya Julaibib wai katsaya.Inji wa?Yana hakin gudun da yayi yace"inji Yaya Sudaida.To ya shiga mota ya zauna yad'aura belt,k'afarshi d'aya tana waje.Tak'arsso wajan yana waya,wucewar wasu dak'ik'u sannan yagama wayar ya ajiye a gafenshi sannan yad'an kalleta kince in tsaya me zaki bani? Tabud'e gidan baya ta ajiye mishi wata madaidaiciyar leda ruwan hoda"Donut na maka, tarufe murfin tadawo wajanshi,wallahi tausayi yake ba ta duk yayi sanyi dama shi bame san hayani bane"sai yaushe zaka dawo?Ba rana sai dai kun ganni.Idanun ta suka cika da kwallah"dan ALLAH Yaya D'ansarai ka dinga cin abinci kaga yadda kazama kuwa?Ina cin abinci mana Sudaida ai d'an Adam bazai rayu ba abinci ba.Tad'an marariraice"to amma dai d'an tsakura ka keyi, kadinga ci dayawa,yamaida k'afarshi cikin motar tarufe murfin.Nagode Sudaida.kadinga cin abinci kaji?Tasake fad'a.To ya fad'a a tak'aice. Tasunkuyo"Allah ya kaika lafiya.amin Sudaida yaja motar tabi bayan motar da kallo har yayi nisa ya6ace ma ganinta,wani abu na mata kai-kawo a zuci,tasauke numfashi tabaki ta hanci sannan tajiya zuwa cikin gida ran ta ba dad'i.
A sanda hantsi yadubi ludayi na safiyar alhamis suna cikin hutun makarantar boko na ranar yara(Children's day)kuma yau ba makarantar allo ba Islamiyya kowa yana abinda yake so ne, dan duk sun gama ayyukan gida.Tana kwance ranta ba dad'i tunda Julaibib yatafi sau uku kawai sukayi waya yauma takira shi sama-sama suka gaisa yakatse,tasake kira yad'aga da sallama"Yaya Julaibib na maka laifine? A ah baki min kome ba.To me yasa kike min wani iri? Yad'anyi murmushi"Sudaida kenan ni ban miki wani iri ba fa zan shiga aji ya katse wayar...Tayi lamooo a gadan,tunani barkatai ya cika k'wak'walwarta ta rasa na za6a tayi.
Nasmat suka shigo suna hayaniyarsu kamar yadda suka sa ba,suka kalleta suka kwashe da dariya"Sudaida uwar tafakkuri (tunani)me kuma yafaru?Khausar ta ta6e baki tabud'e wadrobe ta d'auki kayan da zata goge a D'akin-shak'atawa tafita...Bata basu amsar tambayar su ba,takalli Zainab"ya maganar bikin saukar mu?Ta zauna a gefan gadan"ai Malam yayi tafiya sai ranar asabar zai dawo.A'isha tamik'e "barinje muk'arasa kallan mu dan yau bazan dad'e ba,angona Hashim anjima yana hanya.Nasmat tad'an daki kafad'arta"to gaggawa hannu hagu a romo mutumin da ko tasowa bai yiba.suka mik'e ita da Zainab.Nasmat tabi da Sudaida da kallo "dan ALLAH me yake damun kine?Tamaida kanta saman matashi"na fad'a miki ba abinda yake damuna to ki rabu dani mana.Sudaida na damu dake shi yasa nadamu da halin dakike ciki. Tamaida idanun ta tarufe...Nasmat ki kyaleni bana san hayaniya fa.Tamik'e ALLAH yabaki hak'uri, amma ina zargin wani abu koda yake...sai tad'an motsa kafad'a shikenan can da yawarki yarinya.
Sai da aka cinye zangon karatu d'aya sannan Julaibib yazo gida.Yau alhamis ranar da ake bikin saukar Alqur'ani me girma nasu Sudaida,kome an shirya shi cikin mutunci, bangaran maza daban na mata daban Liman yabud'e taran da addu'a yama daliban addu'a Allah yasa suyi amfani da abinda aka koya musu a kowani irin hali da yanayi suka shiga na rayuwa...aka biyama d'aliban allunan su sannan aka cigaba da wa'azi da fad'akarwa akan neman ilmi dan shine yake sanya rayuwa tayi kyau tayi albarka.
Bayan angama kome sannan aka shiga yin hotuna da rabama d'alibai kyaututtuka aka rufe taro da addu'a,Sudaida tasunkwui da kai abinda yaba mak'alallun k'wallan cikin idanun ta damar zubowa k'asa sharrr... wannan taran me tarin albarka mutane da yawa sun halacceshi amma banda Sinan,to me ya hanashi zuwa tunda ya sani?Tayi kwafa wallahi za mu had'u ne.
Suka juya zuwa cikin gari jikinsu a sanyaye,zuciyoyin su cike da alhini da d'acin mutuwa.
Malama Lamid'o da iyalinshi suka fito za su tafi.Julaibib yana tsugune a gabansu ya sunkwui da kai,kukan shar6e yake yi hawayen suna ambaliya a fuskar shi, ganin haka yasa Tukur yarik'o hannun Inna da take matsar kwallah zuwa mota"Inna zauna.Cikin dauriya Malam Lamid'o shima yatsuguna yadafa kafad'arshi"kayi hak'uri Julaibib hak'ik'a wannan mutuwar babu wanda ta dake su kamarmu iyayanta da kai,to duk mu d'auki hak'uri kowa zaman jiranta yake yi,tabbasss da ina da wata 'yar bayan Bilkisu to dana ba ka, amma zan cigaba da maka addu'a"ALLAH yaba ka wacce tafi Bilkisu,yayita rarrashin shi sannan sukayi sallama dasu Baba.Tukur yaja mota suka tafi. Julaibib yabi bayan motar da kallo har tasha kwana ta6ace ma ganin shi sharrr...sharrr...wasu zafafan hawaye suka zubo mishi. Yakad'a kai cikin maimaita Istirja'i.
Bayan sallar magriba Inna ta kawo mishi kunun tsamiya da kosai.Julaibib daga dawowa daga masallaci sai kuma ka kwanta? Tashi kayi bud'a baki mana.Yamik'e zaune dak'yar dan kanshi na wani sarawa "Inna bana jin yunwa cikina ya cunkushe kamar na ci abinci"Tajijjiga kai"na sani D'ansarai to amma dai ai ka san an umarce mu da gaggauta bud'a baki,azumi fa kayi daure kaci dabino kaji... yakar6i guda d'aya haka dai yaci amma wallahi baiji d'and'anon shi ba dakyar ya had'iye.
Malam Abdullahi yashigo shima yazauna yadafa kafad'ar shi"Malam D'ansarai ai wannan lokacin yana d'aya daga cikin lokutan amsa addu'a,to ba sai kayi amfani da wannan damar wajan rok'ama Magado gafara dama kai kanka ba?Duk da yana cikin damuwa amma sai da yad'anyi yake ganin yadda suke ta rarrashin shi Inna wai ita sai ta bashi kunnun ma abaki wallahi kuma yau a d'akin baccin ta za su kwana tare "Karki damu Inna zan sha amma sai zuwa anjima kin san ba sosai nake cin abinci daga shan ruwa ba.Eh haka ne ,tamik'e ta barshi da Baba.
Washe gari su Julaibib da iyayan su motoci guda uku sukayi dan zuwa Matsirga ta'aziyya sun tafi da manyan kololin shake tam da abinci ,kullum sai sunje har sai da akayi addu'ar uku.
Yana rik'e da agogon da aka cire a hannun Bilkisu lokacin da za'a mata wanka sai jujjuya shi yakeyi,tunaninta da irin hirarra kinsu ya cika k'wak'walwar shi"Bilkisu a very meek damsel ta tafi ta barshi,burin su na zama ma'aurata bai cika ba.
"Sai na kira...
kalmar da suka fad'a ma juna ta k'arshe shi da ita kenan,sai sak'on muryar data turo mishi,yasake kunna sak'on muryar yana sauraro a karo na barkatai sau shurin masaki,ya kad'a kai"uh uhun mutuwa rigar kowa...
Sudaida tashigo tana kallanshi cikin zancen zuci"shi ko wani irin so yakema wannan Bilkisun?Kullum taganshi sai taga ya dad'a ramewa,tausayinshi yamamayeta dan ba ta jin dadin ganin shi a haka,itama tayi nadamar abinda tadinga ma Bilkisu wanda ita Bilkisun ko a fuska bata ta6a nuna ta ji haushi ba"Yaya Julaibib dan Allah kayi hak'uri,kaga yadda kake ta ramewa? Yad'an kalleta"to nagode.Ta ajiye rediyon tafita. Inna tafio daga D'akin-girki tana kallanta tana sa takalmi"ba dai tafiya za kiyi ba?Tafiya zan yi Inna dan zanyi rubutun allo yau akwai darasu,amma idan nagama zan dawo in sha fate na.To shikenan, ALLAH yamuku albarka"Amin Innarmu.
Malam Lamid'o yana zaune a d'akin zaure yajiyo sallamar Julaibib.Yafito da sauri kaine haka?To maraba yashiga suka gaisa.Malam Lamid'o yace ikon ALLAH dama Tukur nake jira yadawo anjima za muzo wajan na ku.Ya amsa cikin girmamawa"Malam shi yasa ma nazo dan Baba yafad'a min yadda kukayi ta waya"Indai za kuzo ne dan kawo wani abu game da kayan auran Megado to kubari.
Malam Lamid'o yagirgiza kai"sam-sam baza ayi haka ba.Ya amsa cikin ladabi"wallahi Malam kome da aka kawo saboda Bilkisu na bar muku har abadan duniya arabama yan'uwa da abokan arziki bazan kar6a ba.Malam Lamid'o yayi shiru cikin jinjina wannan al'amari,sai kawai yad'auki wayar shi yakira Alhaji Abdullahi yafad'a mishi abinda Julaibib yace"Baba yayi murmushi "haba Malam dan D'ansarai ya ce haka har sai ka kira?Tunda yace ya bari to ya bari d'in ne,kutaya mu addu'a kawai Allah yabashi macen alheri.Ya ajiye wayar cikin sanyin jiki.Karka damu Malam Julaibib yafad'a."Julaibib ALLAH yamaka albarka,ALLAH yasa kagama da duniya lafiya, ALLAH yaba ka wacce tafi Bilkisu.
Yamishi jagora zuwa cikin gidan. Innan Bilkisu tana ganin shi tafara kuka,ya sunkwui da kai cikin wani irin yanayi,ga tausayin ganin yadda Innar Bilkisu ta zabge,tayi bak'i, idanun ta sun k'ank'ance saboda yawan kuka"Inna kiyi hak'uri Bikkisu ba kuka take buk'ata a wajan muba,addu'a tafi buk'ata.Inna takad'a kai cikin hawaye "kaiya d'an nan ba kukan rabuwa da Bilkisu nake yi har yanzu ba,ina kuka ne saboda wata rana za a manta da Bilkisu wajan yi mata addu'a kaasatan(a ke6e) saboda bata bar baya ba,dama Ya'ya sune duk rintsi baza su gaji dama mahaifa addu'a ba,har sai ranar da suma suka koma ga Ubangiji.Yajijjiga kai haka ne,to amma Inna ya zamuyi da hukuncin Ubanguji?ALLAH bai k'addari za tayi aure ba, bare har ta haifi Ya'ya,Inna duk hukuncin Ubangiji akan bawan shi adalcine,duk da bata haihu ba to ai akwai sadakatul-jariya,sadaka me gudana kamar mutum yana raye adoron duniya ni zan je cikin k'auye inda duke wuyar ruwa zan gina mata rijiya...Malam Lamid'o yatari numfashin shi"a ah basai ka sake kashe kud'in kaba kabari kawai tunda kabar mana kome to zan gina mata da kud'in sadakinta...Inna tafashe da kuka ALLAH yabaka wacce tafi Bilkisu d'an nan, hakika kai masoyin Bilkisu na gaskene dan ka nuna mana haka duk da bata cikin doron duniya.
Idanun shi suka kad'a jawur"ni gobe zan koma wajan bautar k'asa dama sallama nazo muyi sai an kwana biyu,suna sallama Bello yashigo da gudu yana haki yana dariya"Yaya D'ansarai ina dabinon ajwa na da inibi na?Suka zuba mishi idanu ba abinda yadame shi sai tsallan shi yakeyi"k'uruci dangin hauka.Yamik'a mishi ledar daya shigo da ita a hannunshi.Yakar6a cikin tsallan murna"Yaya D'ansarai nagode ya k'ank'ame ledar akirjin shi"to yaushe zaka dawo? Yakalleshi da kulawa"zan dad'e ban dawo ba. Bello yad'an zaro idanu"kaiii kaima irin tafiyar da Adda tayi za kayi?Inna fa tafad'a min wai ita baza ta sake dawo wa ba sai dai muje mu same ta,ni fa shi yasa baza ni ba,kai ai za ka dawo ko?Insha-ALLAH Bello... Idanun Julaibib suka sake kad'awa jawur ya tuno da Bilkisu da take cewa gobe fa zan dawo Insh-ALLAH... Cikin wani irin yanayi suka yi sallama yaja motar shi yatafi,ya dad'e a Water-fall d'in Matsirga yana kallan ruwan yadda yake gudu cikin Qudirar Ubangiji ba dare ba rana shekara aru-aru.
Sagir yafito da gudu yana kiran shi" Yaya Julaibib wai katsaya.Inji wa?Yana hakin gudun da yayi yace"inji Yaya Sudaida.To ya shiga mota ya zauna yad'aura belt,k'afarshi d'aya tana waje.Tak'arsso wajan yana waya,wucewar wasu dak'ik'u sannan yagama wayar ya ajiye a gafenshi sannan yad'an kalleta kince in tsaya me zaki bani? Tabud'e gidan baya ta ajiye mishi wata madaidaiciyar leda ruwan hoda"Donut na maka, tarufe murfin tadawo wajanshi,wallahi tausayi yake ba ta duk yayi sanyi dama shi bame san hayani bane"sai yaushe zaka dawo?Ba rana sai dai kun ganni.Idanun ta suka cika da kwallah"dan ALLAH Yaya D'ansarai ka dinga cin abinci kaga yadda kazama kuwa?Ina cin abinci mana Sudaida ai d'an Adam bazai rayu ba abinci ba.Tad'an marariraice"to amma dai d'an tsakura ka keyi, kadinga ci dayawa,yamaida k'afarshi cikin motar tarufe murfin.Nagode Sudaida.kadinga cin abinci kaji?Tasake fad'a.To ya fad'a a tak'aice. Tasunkuyo"Allah ya kaika lafiya.amin Sudaida yaja motar tabi bayan motar da kallo har yayi nisa ya6ace ma ganinta,wani abu na mata kai-kawo a zuci,tasauke numfashi tabaki ta hanci sannan tajiya zuwa cikin gida ran ta ba dad'i.
A sanda hantsi yadubi ludayi na safiyar alhamis suna cikin hutun makarantar boko na ranar yara(Children's day)kuma yau ba makarantar allo ba Islamiyya kowa yana abinda yake so ne, dan duk sun gama ayyukan gida.Tana kwance ranta ba dad'i tunda Julaibib yatafi sau uku kawai sukayi waya yauma takira shi sama-sama suka gaisa yakatse,tasake kira yad'aga da sallama"Yaya Julaibib na maka laifine? A ah baki min kome ba.To me yasa kike min wani iri? Yad'anyi murmushi"Sudaida kenan ni ban miki wani iri ba fa zan shiga aji ya katse wayar...Tayi lamooo a gadan,tunani barkatai ya cika k'wak'walwarta ta rasa na za6a tayi.
Nasmat suka shigo suna hayaniyarsu kamar yadda suka sa ba,suka kalleta suka kwashe da dariya"Sudaida uwar tafakkuri (tunani)me kuma yafaru?Khausar ta ta6e baki tabud'e wadrobe ta d'auki kayan da zata goge a D'akin-shak'atawa tafita...Bata basu amsar tambayar su ba,takalli Zainab"ya maganar bikin saukar mu?Ta zauna a gefan gadan"ai Malam yayi tafiya sai ranar asabar zai dawo.A'isha tamik'e "barinje muk'arasa kallan mu dan yau bazan dad'e ba,angona Hashim anjima yana hanya.Nasmat tad'an daki kafad'arta"to gaggawa hannu hagu a romo mutumin da ko tasowa bai yiba.suka mik'e ita da Zainab.Nasmat tabi da Sudaida da kallo "dan ALLAH me yake damun kine?Tamaida kanta saman matashi"na fad'a miki ba abinda yake damuna to ki rabu dani mana.Sudaida na damu dake shi yasa nadamu da halin dakike ciki. Tamaida idanun ta tarufe...Nasmat ki kyaleni bana san hayaniya fa.Tamik'e ALLAH yabaki hak'uri, amma ina zargin wani abu koda yake...sai tad'an motsa kafad'a shikenan can da yawarki yarinya.
Sai da aka cinye zangon karatu d'aya sannan Julaibib yazo gida.Yau alhamis ranar da ake bikin saukar Alqur'ani me girma nasu Sudaida,kome an shirya shi cikin mutunci, bangaran maza daban na mata daban Liman yabud'e taran da addu'a yama daliban addu'a Allah yasa suyi amfani da abinda aka koya musu a kowani irin hali da yanayi suka shiga na rayuwa...aka biyama d'aliban allunan su sannan aka cigaba da wa'azi da fad'akarwa akan neman ilmi dan shine yake sanya rayuwa tayi kyau tayi albarka.
Bayan angama kome sannan aka shiga yin hotuna da rabama d'alibai kyaututtuka aka rufe taro da addu'a,Sudaida tasunkwui da kai abinda yaba mak'alallun k'wallan cikin idanun ta damar zubowa k'asa sharrr... wannan taran me tarin albarka mutane da yawa sun halacceshi amma banda Sinan,to me ya hanashi zuwa tunda ya sani?Tayi kwafa wallahi za mu had'u ne.