Sashe 39
Gwajin Dafi Complete Hausa Novel · about 8 min read
D'an gajeran sak'on Sinan daya shigo wayar ta kenan,tayi murmushi.Tazauna tana kiran A'isha dan Kafanchan ta tafi wajan Kaka acan tayi sallah. Tad'aga da sallama,Sudaida ta amsa sannan tad'ora"zakara ya ja kaza kinyi sallah lafiya?Ta amsa"a ah mantawa kikayi takalmi ne yaja k'afa.Sudaida taja tsaki "ai wallahi sa a ma kika ci dana kira ki,keda za kiyi zaman ki shi Hashim d'in yazo nan yayi sallar wai sai kawai kika wani bishi...A'isha ta tari numfashi" ke dakata haka malama karki d'oramin jakar tsaba kisa kaji sudinga bina,wannan sallar nafara zuwa Kafanchan?Ni ba wajen shi naje ba wajan Kaka naje.Tasake jan tsaki"ba cinya ba k'afar baya. Itama ta amsa"a ah ALLAH yasa k'afar kafad'a ce, ke kika sani,ba Khausar wayar.Yaya Khausar gida tawuce ni ina gidan Hajiya.Tam barin kirata sukayi sallama. Asama taji Hajiya tana fadin"to na samo maka matar aure.Matar aure wace iri kamar yaya? Yatambayeta cikin rashin fahimta.Takalleshi"au ka manta yadda mukayi dakai cikin azumi?Ba ka ce in samo maka bane?Yakama kai"Innalillahi,Hajiya ni fa wasa nake miki.Tawatsa hannaye "kai kajiyo, amma dai aikin gama ya gama duk dai ban fad'a ma kowa ba sai yarinyar,to amma tunda kaima na fad'a maka to zan fad'a ma Iyayan na ku kowa yaji yakuma sani.Wacece ita?Tagirgiza kai"uh uh ba yanzuba ina so ne tad'an kara girma da hankali lokacin an kawar da Yayyinta.
Shi da Sudaida suka kai juna.Yakauda kai cikin rashin sanin abun fad'a,yasauke numfashi,d'an madaidaicin kofin hannun shi ya ajiye a saman tebur."akara maka ne?Yakalli Hajiya kamar be ji abinda tafad'a ba na'am, a ah Alhamdulillah wannan d'inma ban shanye dukaba, yad'auki murfin yarufe kofin.Yad'an karkace kad'an yaciro rafar yan naira ashirin guda d'aya ya'ajiye agabanta"Hajiya ga nawa goron sallar ba yawa. Tayi murmushi"Julaibibi me yawan kenan ALLAH yayi albarka nagode madallah.Sai ga Nasmat ta shigo da babban foodflask cike tam da tuwon sallah"godiyar me wannan tsohuwar take yi?
Idanun ta yasauka akan kud'in takama ha6a wai wai wai sai ta zauna"Hajiya lillahi warasulihi keda mutuwa tafara k'wank'wansa miki k'ofa me za kiyi da sababbin kud'i?Tamik'a mata hannu kawo su kawai,to ke me ma za ki siya ne? Hajiya ta d'auki kud'in ta"zancen ki dutse,zan kuma rasa ba ki, ki zauna jiran gawon shanu kinji ko?Takalli Julaibib"Autan Inna yau take sallah fa.Yamata wannan rikitaccen kallan na shi yayi-yayi tadaina kiranshi da wannan sunan amma tak'i "yan mata kyau da sallah idan tawuce sun zama jakai.
Tagalla mishi harara"wallahi ALLAH yasauwak'e ai kaima ka san ba ma cikin irin wad'annan kucankan 'yan matan. Adai fad'ama wanda bai sani ba"ai kaima ka sani kana kuma gani ganin idanunka.Yad'an kalleta"uh ke dai abar tuna ba ya kawai wai gyartai ya ci sarauta,yajefa mata rafar 'yan naira biyar guda d'aya"ga shinan gaba d'aya 'yan matan dake zuri'ar Hajiya za ku raba,kowacce ki tabbata kin ba ta dan ba wacce zan kuma ba sisin kwabo na, yanuna Sudaida sai ki fara da ita.Tasa kud'in a jaka tabbb... Wannan shine tazo muji ta tawuce ta bayan kunni wannan nawane ni kad'ai kai dasu wallahi...bai saurare taba yama Hajiya sallama yatashi yatafi.
Yaya Julaibib tabishi zaure.Yajuyo "na'am.Dan ALLAH rake za ka siyo min idan za ka dawo anjima.Yakalleta cikin natsuwa"Sudaida a ina zan samu rake yau sallah fa ai basa fitowa. Tad'an marairaice "ALLAH bayan sallar la'asar za a samu wanda yafito.Yad'an motsa kafad'a"idan an samu to.Nasmat da Sudaida su suka gyara naman suka soya ma Hajiya,dan dama sun iya kome an horasu da aiki.
Yadda yake juyi a kan gadon cikin sulusin dare dan ba ya jin bacci,haka yake juya kalaman Hajiya"to na samo maka matar aure...amma dai aikin gama ya gama...yagyara rufa yana dad'a d'ora kanshi a saman matashin "hummm...wacece matar?Wacece ita? Yakad'a kai cikin sauke numfashi"ALLAH yajik'anki Megado... Wani tunani yad'arsu a zuciyar shi game da Sudaida,sai kuma yagirgiza kai"abun dakamar wuya...toh yanzu da Hajiya take wannan maganar "idan yarinyar bata mishi ba fa?Yana jinjina irin zaman da za ayi na har k'arshen numfashi ne fa, yagyad'a kai"abu mafi sauk'i suyi magana da Hajiya tafad'a mishi ko wacece,idan bata mishi ba toh a canja mishi da wata tun kafin Iyaye suji maganar.
Daga masallaci sallar asubahi yaje yasa mu Hajiya da maganar amma fau-fau tak'i yadda suyi ta"wai ai yarinyar da d'an sauran ta,za ta fad'a mishi a lokacin daya da ce,kuma ba ta dawani makusa dole ma ya so ta tunda itama macece.Dole ya hak'ura yatattara yakoma inda yafi wayau...Ko hutunan da suka d'auka dasu Hajiya bai tsaya ya kar6a ba,dan Hajiya tace bata san wani hoto a waya,dole suka kira Misbahu me hoto ya d'auke su na kati,bai ma yi sallama da yan'uwa kamar yadda yasa ba ba.
Tana wanke kayan makaranta Asma'u takawo mata waya"ga shi ya damemu da kira.Waye?Bata yi magana ba ta ajiye wayar a gefen ta,tajuya tayi tafiyarta. Aka sake kira tad'aga tana d'an turo baki kamar yana ganin ta"ni dai ALLAH na yi fushi.Shi yasa nake ta kira kika k'i d'agawa?A ah wayar tana d'aki na sa ta a caji,ni kuma ina tsakar gida ina wanki,ALLAH da gaske Yaya D'ansarai naji haushi dana je gida neman ka Inna tace wai asubanci kayi.To kiyi hak'uri. Nayi. Yauwa nagode ALLAH yamiki albarka. Amin. Sudaida...yakira ta. "Na'am.Baki fad'amin hotunan da mukayi a masallacin Idi sunyi kyau ko basu yi ba?Tayi yar dariya"sunyi kyau musamman wanda muka yi da Hajiya.To d'an turo min ta whatsapp"tabbb...ai kawai kayi hak'uri idan kadawo ka gani ganin idanun ka.Yayi murmushi "wato kin rama ko?To shikenan ki ajiye min,nima a makon nan zan shigo,kin ko ajiye min dambun naman ko duka kika ba wannan yaron?Ta gane wanda yake nufi amma sai tace"Yaya Julaibib wani yaro zan ba dambun nama har da na ka? Saurayin ki...yafad'a a dak'ile.Kai dan ALLAH Sinan d'in ne yaro?To dame kwad'o yafi gaya?Zak'i. Yabata amsa a tak'aice kafin tace wani abu ya katse wayar.
Julaibib Abdullahi D'ansarai...Yana gama degree d'in shi na farko ya d'ora degree na biyu(masters) a dai Islamic Studies baya wani samun zama kullum cikin zirga-zirga tsakanin Zonkwa da Zari'a har ya kammala kome sai karatu da za a fara ba kama hannun yaro yazo gida yayi mako d'aya sannan ya tattara yakoma dan cigaba daka inda aka tsaya,shi dai Musaddiq bai cigaba ba sai harkar kasuwancin su ya keyi,yana kuma yin kome tsakani da ALLAH,kome a rubuce yake sai Julaibib ya zo ya nuna mishi.
Sudaida tana zaune a tsakar gidan su Swachet wata yar ajin su ce ta je kar6o takaddun WAEC na shekara uku da suka wuce wanda Yayan ita Swachet d'in ya rubuta,tana so tad'anyi nazarin su,tana zaune zaman jiran Swachet takwaso matasu a d'aki.Tayi tsai...na wucewar wasu dak'ik'u da tunanin waye to da wannan aikin?Karo na uku kenan ana lek'owa ana komawa,to mutanan da suke shiga gida kai tsaye ko macece ko namijine indai ba mara gaskiya ba wazai yi haka?
Tamik'e cikin sand'a dan san ganin ko waye.Caraf idanun su yahad'u,tabud'e idanu cikin mad'aukakin mamaki da tsoro, tanuna shi da yatsa"Sinan kaine kake lek'e?Me kazo yi anan unguwar? Ya sosa kai yana mata d'an murmushi" wai dama kece?me kika zo yi anan?Tayi jimmm... tana mishi kallan nazari kamar ba shi da gaskiya sai waige-waige yake yi"kar mu maimaita tambaya ba amsa mana. Yasake sosa kai yana murmushi "Sudaida sarauniya ta... wallahi na fito shan iskane kawai, sai kuma naga wata kamar ke shine nake lek'awa,yakalli agogon dake d:aure a hannunshi "kai jama'a lokaci fa ba wuya,kin san yau akwai wa'azin maza a gidan bak'i, muje mana,yad'ago yana kallanta har yanzu itama shi take kallo "lafiya kuwa Sudaida?Tagirgiza kai"ni mamaki kake bani wai duk girman cikin gari karasa inda za kaje kasha iska har sai ka shigo nan daba bahaushe ko musulmi me sallah ko d'aya? Ni fa wallahi Sinan ba na ga ne ma wasu al'amuran na kafa gaskiya.Anya Sinan...?Yatare da sauri cikin dad'in baki da rantsuwar ba abinda yakawo shi,har sukayi sallama yajuya da sauri yabar unguwar. Takama ha6a "Sinan fa kamar ba shi da gaskiya tajijjiga kai akwai lauje cikin nad'i.
"Hey Ibrahim...
Swachet ta dafa ta,me kika fito yi a waje? Sudaida tajuyo cikin sauke numfashi,sannan tasa hannu tazame hannun Swachet daga kafad'arta"na sha fad'a miki mu addinin mu na musulunci yaba Iyaye girma na alk'adari akan Ya'yan su, mu kome sunan mahaifin kane ba ka kiran sunan shi kai tsaye ba dan ya haife kaba sai dai dan yaci darajar sunan mahaifin ka ko mahaifiyar ka,ni sunana Sudaida to banga dalilin da zai sa ke kuma kidinga kirana da sunan mahaifi na ba,wannan al'adar turawar ba da Sudaida ba gad'a da fatalwa.
Swachet tawatsa hannaye cikin halin-ko-inkula"ni banga wani abu ba fa.Takar6i takaddun tana gyad'a kai "tunda baki gane me nace miki ba ko?Tad'an ta6e baki tana yar dariya"Sudaida kin cika shagwaba tun muna JSS Class idan an miki abu sometimes sai kin turo d'an k'aramin bakin nan naki kamar gidan tsutsa gashi har yanzu as a matual baki bari ba haka zaki haifi Ya'ya idan sun baki haushi kidinga musu? Takai mata duka. Sukayi dariya.Muje in taka miki amma ba da yawa ba, dan akwai wanda nake jira.Sudaida takalleta da sauri"waye shi?Ko kema kin fara zuwa kwanan gidan ne.Tayi d'as da yan yatsunta"God forbid bad things ni da zan zama sister,ni bani da saurayi ma, sak'o kawai zai kawo min in kaima budurwar ta shi.
Tibishi yatare shi"wai har ka dawo sai kace akan k'aya kake?Yafad'a kujera tare da lumshe idanun shi na wucewar wasu yan dak'ik'u sannan ya bud'e su"ai ban ma k'arasaba na had'u da Sudaida.Yacire kofin bommi(ruwan kwakwa) dayake shirin kaiwa bakin shi,yana mishi kallan uku ahu"to me kake nufi?Ya ajiye kofin a saman tebur yahad'a hannayan shi waje d'aya yad'ora ha6arshi akai"wai tsoron yarinyar nan kakeji?Har yanzu baice kome ba,ya daiyi tagumi yana zancen zuci"zan bar abinda nafara kawai tun kafin wankin hula yakaini ga dare,kwata-kwata bani da kwanciyar hankali.Tibishi yaja dogon tsaki sannnan yamik'e yabar d'akin yana zagin Sudaida, Sinan,hausawa dama duk wani wanda yake sallah harda Katafawa yan'uwanshi a jinsi da d'aukacin masu sallah na doron duniya gaba d'aya.
Shi da Sudaida suka kai juna.Yakauda kai cikin rashin sanin abun fad'a,yasauke numfashi,d'an madaidaicin kofin hannun shi ya ajiye a saman tebur."akara maka ne?Yakalli Hajiya kamar be ji abinda tafad'a ba na'am, a ah Alhamdulillah wannan d'inma ban shanye dukaba, yad'auki murfin yarufe kofin.Yad'an karkace kad'an yaciro rafar yan naira ashirin guda d'aya ya'ajiye agabanta"Hajiya ga nawa goron sallar ba yawa. Tayi murmushi"Julaibibi me yawan kenan ALLAH yayi albarka nagode madallah.Sai ga Nasmat ta shigo da babban foodflask cike tam da tuwon sallah"godiyar me wannan tsohuwar take yi?
Idanun ta yasauka akan kud'in takama ha6a wai wai wai sai ta zauna"Hajiya lillahi warasulihi keda mutuwa tafara k'wank'wansa miki k'ofa me za kiyi da sababbin kud'i?Tamik'a mata hannu kawo su kawai,to ke me ma za ki siya ne? Hajiya ta d'auki kud'in ta"zancen ki dutse,zan kuma rasa ba ki, ki zauna jiran gawon shanu kinji ko?Takalli Julaibib"Autan Inna yau take sallah fa.Yamata wannan rikitaccen kallan na shi yayi-yayi tadaina kiranshi da wannan sunan amma tak'i "yan mata kyau da sallah idan tawuce sun zama jakai.
Tagalla mishi harara"wallahi ALLAH yasauwak'e ai kaima ka san ba ma cikin irin wad'annan kucankan 'yan matan. Adai fad'ama wanda bai sani ba"ai kaima ka sani kana kuma gani ganin idanunka.Yad'an kalleta"uh ke dai abar tuna ba ya kawai wai gyartai ya ci sarauta,yajefa mata rafar 'yan naira biyar guda d'aya"ga shinan gaba d'aya 'yan matan dake zuri'ar Hajiya za ku raba,kowacce ki tabbata kin ba ta dan ba wacce zan kuma ba sisin kwabo na, yanuna Sudaida sai ki fara da ita.Tasa kud'in a jaka tabbb... Wannan shine tazo muji ta tawuce ta bayan kunni wannan nawane ni kad'ai kai dasu wallahi...bai saurare taba yama Hajiya sallama yatashi yatafi.
Yaya Julaibib tabishi zaure.Yajuyo "na'am.Dan ALLAH rake za ka siyo min idan za ka dawo anjima.Yakalleta cikin natsuwa"Sudaida a ina zan samu rake yau sallah fa ai basa fitowa. Tad'an marairaice "ALLAH bayan sallar la'asar za a samu wanda yafito.Yad'an motsa kafad'a"idan an samu to.Nasmat da Sudaida su suka gyara naman suka soya ma Hajiya,dan dama sun iya kome an horasu da aiki.
Yadda yake juyi a kan gadon cikin sulusin dare dan ba ya jin bacci,haka yake juya kalaman Hajiya"to na samo maka matar aure...amma dai aikin gama ya gama...yagyara rufa yana dad'a d'ora kanshi a saman matashin "hummm...wacece matar?Wacece ita? Yakad'a kai cikin sauke numfashi"ALLAH yajik'anki Megado... Wani tunani yad'arsu a zuciyar shi game da Sudaida,sai kuma yagirgiza kai"abun dakamar wuya...toh yanzu da Hajiya take wannan maganar "idan yarinyar bata mishi ba fa?Yana jinjina irin zaman da za ayi na har k'arshen numfashi ne fa, yagyad'a kai"abu mafi sauk'i suyi magana da Hajiya tafad'a mishi ko wacece,idan bata mishi ba toh a canja mishi da wata tun kafin Iyaye suji maganar.
Daga masallaci sallar asubahi yaje yasa mu Hajiya da maganar amma fau-fau tak'i yadda suyi ta"wai ai yarinyar da d'an sauran ta,za ta fad'a mishi a lokacin daya da ce,kuma ba ta dawani makusa dole ma ya so ta tunda itama macece.Dole ya hak'ura yatattara yakoma inda yafi wayau...Ko hutunan da suka d'auka dasu Hajiya bai tsaya ya kar6a ba,dan Hajiya tace bata san wani hoto a waya,dole suka kira Misbahu me hoto ya d'auke su na kati,bai ma yi sallama da yan'uwa kamar yadda yasa ba ba.
Tana wanke kayan makaranta Asma'u takawo mata waya"ga shi ya damemu da kira.Waye?Bata yi magana ba ta ajiye wayar a gefen ta,tajuya tayi tafiyarta. Aka sake kira tad'aga tana d'an turo baki kamar yana ganin ta"ni dai ALLAH na yi fushi.Shi yasa nake ta kira kika k'i d'agawa?A ah wayar tana d'aki na sa ta a caji,ni kuma ina tsakar gida ina wanki,ALLAH da gaske Yaya D'ansarai naji haushi dana je gida neman ka Inna tace wai asubanci kayi.To kiyi hak'uri. Nayi. Yauwa nagode ALLAH yamiki albarka. Amin. Sudaida...yakira ta. "Na'am.Baki fad'amin hotunan da mukayi a masallacin Idi sunyi kyau ko basu yi ba?Tayi yar dariya"sunyi kyau musamman wanda muka yi da Hajiya.To d'an turo min ta whatsapp"tabbb...ai kawai kayi hak'uri idan kadawo ka gani ganin idanun ka.Yayi murmushi "wato kin rama ko?To shikenan ki ajiye min,nima a makon nan zan shigo,kin ko ajiye min dambun naman ko duka kika ba wannan yaron?Ta gane wanda yake nufi amma sai tace"Yaya Julaibib wani yaro zan ba dambun nama har da na ka? Saurayin ki...yafad'a a dak'ile.Kai dan ALLAH Sinan d'in ne yaro?To dame kwad'o yafi gaya?Zak'i. Yabata amsa a tak'aice kafin tace wani abu ya katse wayar.
Julaibib Abdullahi D'ansarai...Yana gama degree d'in shi na farko ya d'ora degree na biyu(masters) a dai Islamic Studies baya wani samun zama kullum cikin zirga-zirga tsakanin Zonkwa da Zari'a har ya kammala kome sai karatu da za a fara ba kama hannun yaro yazo gida yayi mako d'aya sannan ya tattara yakoma dan cigaba daka inda aka tsaya,shi dai Musaddiq bai cigaba ba sai harkar kasuwancin su ya keyi,yana kuma yin kome tsakani da ALLAH,kome a rubuce yake sai Julaibib ya zo ya nuna mishi.
Sudaida tana zaune a tsakar gidan su Swachet wata yar ajin su ce ta je kar6o takaddun WAEC na shekara uku da suka wuce wanda Yayan ita Swachet d'in ya rubuta,tana so tad'anyi nazarin su,tana zaune zaman jiran Swachet takwaso matasu a d'aki.Tayi tsai...na wucewar wasu dak'ik'u da tunanin waye to da wannan aikin?Karo na uku kenan ana lek'owa ana komawa,to mutanan da suke shiga gida kai tsaye ko macece ko namijine indai ba mara gaskiya ba wazai yi haka?
Tamik'e cikin sand'a dan san ganin ko waye.Caraf idanun su yahad'u,tabud'e idanu cikin mad'aukakin mamaki da tsoro, tanuna shi da yatsa"Sinan kaine kake lek'e?Me kazo yi anan unguwar? Ya sosa kai yana mata d'an murmushi" wai dama kece?me kika zo yi anan?Tayi jimmm... tana mishi kallan nazari kamar ba shi da gaskiya sai waige-waige yake yi"kar mu maimaita tambaya ba amsa mana. Yasake sosa kai yana murmushi "Sudaida sarauniya ta... wallahi na fito shan iskane kawai, sai kuma naga wata kamar ke shine nake lek'awa,yakalli agogon dake d:aure a hannunshi "kai jama'a lokaci fa ba wuya,kin san yau akwai wa'azin maza a gidan bak'i, muje mana,yad'ago yana kallanta har yanzu itama shi take kallo "lafiya kuwa Sudaida?Tagirgiza kai"ni mamaki kake bani wai duk girman cikin gari karasa inda za kaje kasha iska har sai ka shigo nan daba bahaushe ko musulmi me sallah ko d'aya? Ni fa wallahi Sinan ba na ga ne ma wasu al'amuran na kafa gaskiya.Anya Sinan...?Yatare da sauri cikin dad'in baki da rantsuwar ba abinda yakawo shi,har sukayi sallama yajuya da sauri yabar unguwar. Takama ha6a "Sinan fa kamar ba shi da gaskiya tajijjiga kai akwai lauje cikin nad'i.
"Hey Ibrahim...
Swachet ta dafa ta,me kika fito yi a waje? Sudaida tajuyo cikin sauke numfashi,sannan tasa hannu tazame hannun Swachet daga kafad'arta"na sha fad'a miki mu addinin mu na musulunci yaba Iyaye girma na alk'adari akan Ya'yan su, mu kome sunan mahaifin kane ba ka kiran sunan shi kai tsaye ba dan ya haife kaba sai dai dan yaci darajar sunan mahaifin ka ko mahaifiyar ka,ni sunana Sudaida to banga dalilin da zai sa ke kuma kidinga kirana da sunan mahaifi na ba,wannan al'adar turawar ba da Sudaida ba gad'a da fatalwa.
Swachet tawatsa hannaye cikin halin-ko-inkula"ni banga wani abu ba fa.Takar6i takaddun tana gyad'a kai "tunda baki gane me nace miki ba ko?Tad'an ta6e baki tana yar dariya"Sudaida kin cika shagwaba tun muna JSS Class idan an miki abu sometimes sai kin turo d'an k'aramin bakin nan naki kamar gidan tsutsa gashi har yanzu as a matual baki bari ba haka zaki haifi Ya'ya idan sun baki haushi kidinga musu? Takai mata duka. Sukayi dariya.Muje in taka miki amma ba da yawa ba, dan akwai wanda nake jira.Sudaida takalleta da sauri"waye shi?Ko kema kin fara zuwa kwanan gidan ne.Tayi d'as da yan yatsunta"God forbid bad things ni da zan zama sister,ni bani da saurayi ma, sak'o kawai zai kawo min in kaima budurwar ta shi.
Tibishi yatare shi"wai har ka dawo sai kace akan k'aya kake?Yafad'a kujera tare da lumshe idanun shi na wucewar wasu yan dak'ik'u sannan ya bud'e su"ai ban ma k'arasaba na had'u da Sudaida.Yacire kofin bommi(ruwan kwakwa) dayake shirin kaiwa bakin shi,yana mishi kallan uku ahu"to me kake nufi?Ya ajiye kofin a saman tebur yahad'a hannayan shi waje d'aya yad'ora ha6arshi akai"wai tsoron yarinyar nan kakeji?Har yanzu baice kome ba,ya daiyi tagumi yana zancen zuci"zan bar abinda nafara kawai tun kafin wankin hula yakaini ga dare,kwata-kwata bani da kwanciyar hankali.Tibishi yaja dogon tsaki sannnan yamik'e yabar d'akin yana zagin Sudaida, Sinan,hausawa dama duk wani wanda yake sallah harda Katafawa yan'uwanshi a jinsi da d'aukacin masu sallah na doron duniya gaba d'aya.