Sashe 63
Gwajin Dafi Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bilkisu tagigice dan taji dukan yadda yakamata tak'ara fashewa da kuka kamar zata shid'e, ya d'auketa ya zubama wajen data shaud'a mata idanu,cajar ta fito rad'am da kwanciyar jini a wajen toh jikin hutu ko ina lukwui-lukwui da tsoka ga kuma farar fata,yakalleta fuskar shi ba wal-wala"Sudaida baki da hankali kasheta kike so kiyi? Dan tace ga kayan da take so sai yazama laifin da har sai kin mata wannan dukan?An siyo kayan dan ayi meye dasu?Ya rufeta da fad'a kamar zai daketa,Sudaida tayi shiru tana zancen zuci"wai ita ce za ta kashe mishi 'ya saboda ta daketa sau d'aya.
Tashi ki d'auko mata rigar.Takalleshi cikin idanu"na rantse da girman ALLAH ba zan d'auko ba!Yashare ma Bilkisu hawaye"to fad'a min in da take in d'auko...Cikin fushi tace"wannan rigar haramiyar ta har abadan duniya wallahi.Shima cikin fushi yajuya rungume da Bilkisu"kar ki d'auko ki dafa kici...
Sharrr...sharrr wasu hawaye masu d'umi suka zubo mata akan Bilkisu suke wannan ja-in-jar da Yaya D'ansarai?Ranta in yayi dubu ya 6aci wai shi wani irin so yake ma wannna yarinyar da har zai ga laifin ta amma yakasa tsawatar mata?Wannan makauniyar soyayyace wacce daga k'arshe baza ta haifar da d'a me idanu ba wai Zaujiii...Shine yake mata wannan hayagagar...za ta kashe mishi 'ya... tadafa rigar taci tunda baza ta bata ba...taci kukan ta ta k'oshi tayi shiru tunani barkatai ya cika k'wak'walwarta...yawa-yawan Ya'yan da suke samun matsala a rayuwar su to hakan yana samo asaline daga irin mugun gatan da ake nuna musu tun zamanin k'uruciya.
Sai da hantsi yadubi ludayi sannan Walida tashigo d'akin cikin wata shiga ta daban riga da wando da k'aramin hijab yan kanti...ran Sudaida ya kuma 6aci wato fitan da yayi sababbin kaya yayafi ya siyo musu kenan? Walida takalleta"kingani Baba ya siyo mana wasu kayan?Tagyad'a kai"na gani Walida. Mama kuma na ce mishi ALLAH amfana... tad'an shafa kanta"yauwa Innarmu ALLAH yamiki albarka haka ake so duk wanda yabaki abu kisa hannu biyu ki kar6a kuma kiyi godiya...tayi yar dariya"wanda yagode sai ALLAH yak'ara mishi haka kika fad'a min ko? Eh Innarmu ashe baki manta ba.To nagode da kike rik'e duk abinda nake fad'a miki. Tad'anyi jimmm...sannan ta kalli Sudaida"Mama ita Yaya Bilkisu fa da Baba yakawo sai tace wai basu da wani kyau sai da yahad'a mata lemun tuffa da karas sannan ta yadda tasa...wai ita dai na Umrah nan take so,shine yace sai ya koma wata Umrah,damu zai tafi muje can muza6a irin wanda muke so da kanmu...
Walida... Suka jiyo muryar shi daga D'akin-shak'atawa yana kiranta,sai ta d'an bud'e idanu "Mama...Baba ne yace wai kizo mutafi na manta... tafita da gudu tana amsa kiran na shi.Takoma tayi kwanciyarta"da bata hak'ura ba baza suyi tafiyar ba kenan kome?Tayi k'wafa"wallahi abu d'aya zai sa tabisu dan tafad'a ma su Baba abinda yake yi, da ba in da za taje,gwamma ayi ma tufkar hanci,ai gabama da gabanta aljani ya taka wuta,ita baza ta iya cigaba da ganin kayan takaicin nan ba nama na jan kare.
Ko kallanta bai yiba,to itama a cikin fushi take dan haka ba wanda yakula wani har suka isa Zonkwa. Inna taji dad'in ganinsu sai ina za a saka ina za a aje takeyi da jikokinta haka suka yi wunin farin ciki.Bayan sallar magriba Sagir k'aninta daya yazama matashin saurayi takira yaraka ta wajen gyaran gashi har Julaibib yadawo basu dawo ba shima yazauna ana ta hira,Bilkisu Megadon Zinare an samu abinda ake so dafadukar cus-cus me nama da kayan lambu take ci,ga Baba ya kawo mata yoghurt tana taci tana sha cikin jin dad'i da kwanciyar hankali.
Sai wajen takwas da rabi suka shigo Sagir yasake gaishe dasu Baba sannan yamusu sai da safe,ita kuma taje tayi sallar Isha'i ta zubo abinci tanaci;yad'an saci kallanta tayi kyau sosai amma ko nahiyar da yake bata kallaba har tagama ci takai farantin D'akin-girki sannan ta dawo ta zauna tad'an kalli yaran"kutafi D'akin-shak'atawa ku kalli wannan shirin na Balarabe da bai iya gaza gurasa ba...Suka mik'e da Sauri"ehhh kuwan Mama...
Tad'an sunkwui da kai cikin ladabi"Baba ina son magana da ku.Yagyad'a kai"to Sudaida... Julaibib yayi wani huci"me wannan yarinyar take nufi? K'arar shi za ta kawo wajen su Baba?Ina jinki Sudaida me yafaru?Muryar ta tafara rawa alamar zuciyarta ta karye"ni dai Dan ALLAH Bilkisu zata dawo gidan nan da zama zan had'o kayanta... Inna tace"ashsha to me yayi zafi idanu za suci wuta har haka Sudaida?Inna kusan kullum sai mun samu sa6ani da Yaya D'ansarai a kan ta,wai d'azu da safe har yana fad'a min zan kashe mishi 'ya saboda na daketa,kuma agaban idanunta ya rufeni da fad'a kamar zai dakeni,Lillahi warasulihi Inna ace kamar Bilkisu sai abinda take so za a dinga yi a cikin gidan nan?Sannan ita ba ta laifi, ba ta kuskure kome tayi dai-dai be a wajen shi, wannnan abinda yake yi ya dace da tsarin ingantacciyar tarbiyya!?
Ni dai ta zauna a wajenku kawai.Inna ta numfasa to me yakawo dukan?Sudaida duka ai baya ba da tarbiyya sai dai yakangarar,ni ma ba na son duka.Wani haushi yamamaye ta wallahi mantawa tayi kuka takawo gidan mutuwa"ai kamar yadda Bilkisu take hantar Yaya D'ansarai to haka abun yake a wajen Inna son ta take kamar me,shi yasa ba gidan da take son zuwa kamar nan dan Inna tana biye mata ne,yanzu ma abincin daren ta daban tadafa mata.
Tasa hannu ta share hawaye"shikenan Insha-ALLAH daga yau ba ruwana da duk abinda Bilkisu za tayi ai ALLAH yagani bani da wani k'arfi ne dan haka zan kyamaci kome a zuciyata.Auna had'a idanu ya gallamata harara"ai dukan yayi yawa ne har ciwo kika ji mata to me zaisa bazanyi fad'a ba.
Baba yayi tsaiii...yana nazarin kalamansu d'aya bayan d'aya,yakad'a kai"Maimunatu wannan hukuncin na ki na adalci ne kuwa?Tsakani da ALLAH Sudaida ta fiku gaskiya;kar k'aunar yarinyar nan tarufe idanunku fa,idan an ciza to yakamata a hura...yanuna Julaibib"Malam D'ansarai da ilminka da girmanka amma kana irin wannan abun?Kiwo aka ba ka game da sha'anin Iyalinka fa,shi itace tun yana d'anye ake tank'warashi...kana nunama Bilkisu tsananin gata amma ba kwa6a to an yi ba ayiba kenan...an 6ata goma biyar bata samu ba,dan me za tayi laifi ba za a hukunta taba?Mahaifiyar tace fa idan ba a nuna mata abinda takeyi kuskure ne tun yanzu ba,to a gaba ma cigaba dayi za tayi,kuma duk fad'an da zaka ma Sudaida to na rok'eka da girman ALLAH kadaina yi a gaban Ya'yanku,hakan yana gur6ata tarbiyyarsu,dan ALLAH Malam D'ansarai idan rai ya 6aci to bai kamata hankali yagusheba kaji ko?
Yanuna ta"ke kuma Sudaida ba ke za ki yanke hukunci na rad'in kan ki ba kome ya miki,tunda shine ubansu shine a hakku a kansu dan shine shugabanku ke da yaran gaba d'aya.Ubangiji ya muku albarka,sannan duk yadda ranki ya6aci kiyi hak'uri dasu kinga banji dad'in furucinki akan Bilkisu ba,ke uwace bakinki amsashshene akan ta,dan haka ki janye wad'annan kalaman na ba babu ruwanki da duk abinda za tayi,ai kece kuwa me ruwa da tsaki yaushe za ki biye ta wani D'ansarai Ya'yanki kadararki su shiga garari,duk abinda ya kumayi ki bugo waya ni dake ki fad'a min zai sha mamakin yadda zanyi wallahi ALLAH kinji na rantse ko?
Kalaman Baba sun tausashi zuciyarta"to Baba nagode ALLAH ya k'ara girma.Inna ma tajijjiga kai toh na gano kuskure na kiyi hak'uri Sudaida ALLAH yamuku albarka,ku tashi kitafi gida dare yana dad'a yi,ta lek'a D'akin-shak'atawa duk sun yi bacci Inna tace suyi tafiyarsu kawai.
Suna zuwa gida taje tayi wanka tayi kwanciyarta shi kuma yatafi D'akin-girki zai dafa shayin na shi na fama taja tsaki sai kaje kayita sha...takwanta cikin tunanin tsohuwar soyayyar su..ita dai ta san da son Julaibib ta girma kuma ba tajin da wani abu dazai rage k'aunarshi a sararin zuciyarta,to amma wannan yawan sa6anin da saka fara samu ita tata k'arfin k'aunar ta zuciyarshi ce ta koma kan Bilkisu da kuma kud'in da yakeji yayi?Ko kuma giyar Ilmi da dukiyace tafara bugar dashi...!?
Tad'auki wayarta takira"Umma kiyi hak'uri na kiraki da daddaren nan wata magana nake so muyi.Ba kome me yafaru ne?Hawaye suka zubo mata"Umma ni da Yaya D'ansarai ne...sai kawai tafara kuka,Umma bata hanata kukan taba sai da taci ta k'oshi tabari dan kan ta...Umma tasauke numfashi "Sudaida kiyi hak'uri ni bazan shiga tsakanin ki da D'ansarai ba ai kunfi kusa,kuma ai ba a ta6a zaman tare ace wani bazai sa6a ma wani ba...fuskantar matsalolin aure irin wannan ai dole ne dan haka ki k'ara hak'uri kuma ki yawaita addu'a kome yayi farko yana da k'arshe...kuma in dai akan Bilkisu ne to fa dole sai kin kawar da kai...ba kome za ki nuna ya dame ki ba...ki dai kiyi k'ok'ari ki jata ajiki kinga ai tafi shak'uwa dashi ko? Eh Umma...to ko ni nan a yanzu nagano wasu kura-kurai danayi game da tarbiyyarku to amma har kwanan gobe ina godema ALLAH ina godema Mama wacce ba dan ita ba da kuma kun samu tasgaro dan haka ki natsu ki san abinda kike yi game da sha'anin tarbiyyarsu...
haba Sudaidan D'ansarai kika juya shi yayi wasu abubuwan da bai so ba sai kuma wannan za ki fara raki? Ki bi dashi ta siyasar rayuwa ko bai daina wasu abubuwan ba to amma ai za ki samu sauk'in wasu,Umma tad'anyi murmushi"taurin kan Bilkisu da kafiya kema fa haka da kike k'arama kinyishi,shi yasa bana miki da wasa...ita kuma sai abun yahad'u mata da gata...
Julaibib yashigo lokacin suna sallama da Umma.Yakar6e wayar"k'arata kika sake kaiwa,me kika fad'a mata?Abinda kunnuwanka sukaji.Yayi murmushi"ALLAH ko?Tajijiga kai"bawai...yashiga rarrashi"kiyi hak'uri Sudaidan D'ansarai ni ma na gane kuskure na,bai kamata ace Bilkisu ce zata shiga tsakanin muba,ai tare tazo ta ganmu,lallai ke macen albarka ce dakika jajirce dan ganin na dawo kan hanya nagode Zaujatiii...ALLAH yamiki albarka ya saukeki lafiya.Sai taji zuciyarta ta yi wasai"ta marairaice Zaujiii..to idan banyi hak'uri ba me zanyi bayan mun zama k'arfe da mayen k'arfe,mutu karaba takalmin kaza...?Hummm fushin masoya hutuhhh...
Rawa da k'afa d'aya sai gwani.
Da ba 'yan koyo da gwanaye sun k'are...
5 Rajab 1441
28 February 2020
We Ibrahim's Daughters👇
Asdilat KD...2geda with Ra'ibs.
DANGIN NONO WRITERS ASSOCIATION
{Da Inganci Mukayi Fintinkau}
Bismillahi wabihi nasta'in
...GWAJIN DAFI💔
Almost true story
Daga alk'alamin🖊
Ya'yan Ibrahim
Saudat A.Baba (Asdilat KD)
Da
Bara'atu Ibrahim (Ra'ibs)
Shafi na ashirin da hud'u.
Tashi ki d'auko mata rigar.Takalleshi cikin idanu"na rantse da girman ALLAH ba zan d'auko ba!Yashare ma Bilkisu hawaye"to fad'a min in da take in d'auko...Cikin fushi tace"wannan rigar haramiyar ta har abadan duniya wallahi.Shima cikin fushi yajuya rungume da Bilkisu"kar ki d'auko ki dafa kici...
Sharrr...sharrr wasu hawaye masu d'umi suka zubo mata akan Bilkisu suke wannan ja-in-jar da Yaya D'ansarai?Ranta in yayi dubu ya 6aci wai shi wani irin so yake ma wannna yarinyar da har zai ga laifin ta amma yakasa tsawatar mata?Wannan makauniyar soyayyace wacce daga k'arshe baza ta haifar da d'a me idanu ba wai Zaujiii...Shine yake mata wannan hayagagar...za ta kashe mishi 'ya... tadafa rigar taci tunda baza ta bata ba...taci kukan ta ta k'oshi tayi shiru tunani barkatai ya cika k'wak'walwarta...yawa-yawan Ya'yan da suke samun matsala a rayuwar su to hakan yana samo asaline daga irin mugun gatan da ake nuna musu tun zamanin k'uruciya.
Sai da hantsi yadubi ludayi sannan Walida tashigo d'akin cikin wata shiga ta daban riga da wando da k'aramin hijab yan kanti...ran Sudaida ya kuma 6aci wato fitan da yayi sababbin kaya yayafi ya siyo musu kenan? Walida takalleta"kingani Baba ya siyo mana wasu kayan?Tagyad'a kai"na gani Walida. Mama kuma na ce mishi ALLAH amfana... tad'an shafa kanta"yauwa Innarmu ALLAH yamiki albarka haka ake so duk wanda yabaki abu kisa hannu biyu ki kar6a kuma kiyi godiya...tayi yar dariya"wanda yagode sai ALLAH yak'ara mishi haka kika fad'a min ko? Eh Innarmu ashe baki manta ba.To nagode da kike rik'e duk abinda nake fad'a miki. Tad'anyi jimmm...sannan ta kalli Sudaida"Mama ita Yaya Bilkisu fa da Baba yakawo sai tace wai basu da wani kyau sai da yahad'a mata lemun tuffa da karas sannan ta yadda tasa...wai ita dai na Umrah nan take so,shine yace sai ya koma wata Umrah,damu zai tafi muje can muza6a irin wanda muke so da kanmu...
Walida... Suka jiyo muryar shi daga D'akin-shak'atawa yana kiranta,sai ta d'an bud'e idanu "Mama...Baba ne yace wai kizo mutafi na manta... tafita da gudu tana amsa kiran na shi.Takoma tayi kwanciyarta"da bata hak'ura ba baza suyi tafiyar ba kenan kome?Tayi k'wafa"wallahi abu d'aya zai sa tabisu dan tafad'a ma su Baba abinda yake yi, da ba in da za taje,gwamma ayi ma tufkar hanci,ai gabama da gabanta aljani ya taka wuta,ita baza ta iya cigaba da ganin kayan takaicin nan ba nama na jan kare.
Ko kallanta bai yiba,to itama a cikin fushi take dan haka ba wanda yakula wani har suka isa Zonkwa. Inna taji dad'in ganinsu sai ina za a saka ina za a aje takeyi da jikokinta haka suka yi wunin farin ciki.Bayan sallar magriba Sagir k'aninta daya yazama matashin saurayi takira yaraka ta wajen gyaran gashi har Julaibib yadawo basu dawo ba shima yazauna ana ta hira,Bilkisu Megadon Zinare an samu abinda ake so dafadukar cus-cus me nama da kayan lambu take ci,ga Baba ya kawo mata yoghurt tana taci tana sha cikin jin dad'i da kwanciyar hankali.
Sai wajen takwas da rabi suka shigo Sagir yasake gaishe dasu Baba sannan yamusu sai da safe,ita kuma taje tayi sallar Isha'i ta zubo abinci tanaci;yad'an saci kallanta tayi kyau sosai amma ko nahiyar da yake bata kallaba har tagama ci takai farantin D'akin-girki sannan ta dawo ta zauna tad'an kalli yaran"kutafi D'akin-shak'atawa ku kalli wannan shirin na Balarabe da bai iya gaza gurasa ba...Suka mik'e da Sauri"ehhh kuwan Mama...
Tad'an sunkwui da kai cikin ladabi"Baba ina son magana da ku.Yagyad'a kai"to Sudaida... Julaibib yayi wani huci"me wannan yarinyar take nufi? K'arar shi za ta kawo wajen su Baba?Ina jinki Sudaida me yafaru?Muryar ta tafara rawa alamar zuciyarta ta karye"ni dai Dan ALLAH Bilkisu zata dawo gidan nan da zama zan had'o kayanta... Inna tace"ashsha to me yayi zafi idanu za suci wuta har haka Sudaida?Inna kusan kullum sai mun samu sa6ani da Yaya D'ansarai a kan ta,wai d'azu da safe har yana fad'a min zan kashe mishi 'ya saboda na daketa,kuma agaban idanunta ya rufeni da fad'a kamar zai dakeni,Lillahi warasulihi Inna ace kamar Bilkisu sai abinda take so za a dinga yi a cikin gidan nan?Sannan ita ba ta laifi, ba ta kuskure kome tayi dai-dai be a wajen shi, wannnan abinda yake yi ya dace da tsarin ingantacciyar tarbiyya!?
Ni dai ta zauna a wajenku kawai.Inna ta numfasa to me yakawo dukan?Sudaida duka ai baya ba da tarbiyya sai dai yakangarar,ni ma ba na son duka.Wani haushi yamamaye ta wallahi mantawa tayi kuka takawo gidan mutuwa"ai kamar yadda Bilkisu take hantar Yaya D'ansarai to haka abun yake a wajen Inna son ta take kamar me,shi yasa ba gidan da take son zuwa kamar nan dan Inna tana biye mata ne,yanzu ma abincin daren ta daban tadafa mata.
Tasa hannu ta share hawaye"shikenan Insha-ALLAH daga yau ba ruwana da duk abinda Bilkisu za tayi ai ALLAH yagani bani da wani k'arfi ne dan haka zan kyamaci kome a zuciyata.Auna had'a idanu ya gallamata harara"ai dukan yayi yawa ne har ciwo kika ji mata to me zaisa bazanyi fad'a ba.
Baba yayi tsaiii...yana nazarin kalamansu d'aya bayan d'aya,yakad'a kai"Maimunatu wannan hukuncin na ki na adalci ne kuwa?Tsakani da ALLAH Sudaida ta fiku gaskiya;kar k'aunar yarinyar nan tarufe idanunku fa,idan an ciza to yakamata a hura...yanuna Julaibib"Malam D'ansarai da ilminka da girmanka amma kana irin wannan abun?Kiwo aka ba ka game da sha'anin Iyalinka fa,shi itace tun yana d'anye ake tank'warashi...kana nunama Bilkisu tsananin gata amma ba kwa6a to an yi ba ayiba kenan...an 6ata goma biyar bata samu ba,dan me za tayi laifi ba za a hukunta taba?Mahaifiyar tace fa idan ba a nuna mata abinda takeyi kuskure ne tun yanzu ba,to a gaba ma cigaba dayi za tayi,kuma duk fad'an da zaka ma Sudaida to na rok'eka da girman ALLAH kadaina yi a gaban Ya'yanku,hakan yana gur6ata tarbiyyarsu,dan ALLAH Malam D'ansarai idan rai ya 6aci to bai kamata hankali yagusheba kaji ko?
Yanuna ta"ke kuma Sudaida ba ke za ki yanke hukunci na rad'in kan ki ba kome ya miki,tunda shine ubansu shine a hakku a kansu dan shine shugabanku ke da yaran gaba d'aya.Ubangiji ya muku albarka,sannan duk yadda ranki ya6aci kiyi hak'uri dasu kinga banji dad'in furucinki akan Bilkisu ba,ke uwace bakinki amsashshene akan ta,dan haka ki janye wad'annan kalaman na ba babu ruwanki da duk abinda za tayi,ai kece kuwa me ruwa da tsaki yaushe za ki biye ta wani D'ansarai Ya'yanki kadararki su shiga garari,duk abinda ya kumayi ki bugo waya ni dake ki fad'a min zai sha mamakin yadda zanyi wallahi ALLAH kinji na rantse ko?
Kalaman Baba sun tausashi zuciyarta"to Baba nagode ALLAH ya k'ara girma.Inna ma tajijjiga kai toh na gano kuskure na kiyi hak'uri Sudaida ALLAH yamuku albarka,ku tashi kitafi gida dare yana dad'a yi,ta lek'a D'akin-shak'atawa duk sun yi bacci Inna tace suyi tafiyarsu kawai.
Suna zuwa gida taje tayi wanka tayi kwanciyarta shi kuma yatafi D'akin-girki zai dafa shayin na shi na fama taja tsaki sai kaje kayita sha...takwanta cikin tunanin tsohuwar soyayyar su..ita dai ta san da son Julaibib ta girma kuma ba tajin da wani abu dazai rage k'aunarshi a sararin zuciyarta,to amma wannan yawan sa6anin da saka fara samu ita tata k'arfin k'aunar ta zuciyarshi ce ta koma kan Bilkisu da kuma kud'in da yakeji yayi?Ko kuma giyar Ilmi da dukiyace tafara bugar dashi...!?
Tad'auki wayarta takira"Umma kiyi hak'uri na kiraki da daddaren nan wata magana nake so muyi.Ba kome me yafaru ne?Hawaye suka zubo mata"Umma ni da Yaya D'ansarai ne...sai kawai tafara kuka,Umma bata hanata kukan taba sai da taci ta k'oshi tabari dan kan ta...Umma tasauke numfashi "Sudaida kiyi hak'uri ni bazan shiga tsakanin ki da D'ansarai ba ai kunfi kusa,kuma ai ba a ta6a zaman tare ace wani bazai sa6a ma wani ba...fuskantar matsalolin aure irin wannan ai dole ne dan haka ki k'ara hak'uri kuma ki yawaita addu'a kome yayi farko yana da k'arshe...kuma in dai akan Bilkisu ne to fa dole sai kin kawar da kai...ba kome za ki nuna ya dame ki ba...ki dai kiyi k'ok'ari ki jata ajiki kinga ai tafi shak'uwa dashi ko? Eh Umma...to ko ni nan a yanzu nagano wasu kura-kurai danayi game da tarbiyyarku to amma har kwanan gobe ina godema ALLAH ina godema Mama wacce ba dan ita ba da kuma kun samu tasgaro dan haka ki natsu ki san abinda kike yi game da sha'anin tarbiyyarsu...
haba Sudaidan D'ansarai kika juya shi yayi wasu abubuwan da bai so ba sai kuma wannan za ki fara raki? Ki bi dashi ta siyasar rayuwa ko bai daina wasu abubuwan ba to amma ai za ki samu sauk'in wasu,Umma tad'anyi murmushi"taurin kan Bilkisu da kafiya kema fa haka da kike k'arama kinyishi,shi yasa bana miki da wasa...ita kuma sai abun yahad'u mata da gata...
Julaibib yashigo lokacin suna sallama da Umma.Yakar6e wayar"k'arata kika sake kaiwa,me kika fad'a mata?Abinda kunnuwanka sukaji.Yayi murmushi"ALLAH ko?Tajijiga kai"bawai...yashiga rarrashi"kiyi hak'uri Sudaidan D'ansarai ni ma na gane kuskure na,bai kamata ace Bilkisu ce zata shiga tsakanin muba,ai tare tazo ta ganmu,lallai ke macen albarka ce dakika jajirce dan ganin na dawo kan hanya nagode Zaujatiii...ALLAH yamiki albarka ya saukeki lafiya.Sai taji zuciyarta ta yi wasai"ta marairaice Zaujiii..to idan banyi hak'uri ba me zanyi bayan mun zama k'arfe da mayen k'arfe,mutu karaba takalmin kaza...?Hummm fushin masoya hutuhhh...
Rawa da k'afa d'aya sai gwani.
Da ba 'yan koyo da gwanaye sun k'are...
5 Rajab 1441
28 February 2020
We Ibrahim's Daughters👇
Asdilat KD...2geda with Ra'ibs.
DANGIN NONO WRITERS ASSOCIATION
{Da Inganci Mukayi Fintinkau}
Bismillahi wabihi nasta'in
...GWAJIN DAFI💔
Almost true story
Daga alk'alamin🖊
Ya'yan Ibrahim
Saudat A.Baba (Asdilat KD)
Da
Bara'atu Ibrahim (Ra'ibs)
Shafi na ashirin da hud'u.