Sashe 23
Gwajin Dafi Complete Hausa Novel · about 8 min read
Fuska a sake tashiga gida. Maman Hasan tace"Yaya dai Sumayya?Sai ta zauna a kujera tana yar dariya wallahi haka kawai take jin nishad'i,rabon data tsinci kanta a irin wannan yanayin tun ranar da D'an Sarai yamata nasiha data daina k'arama sama hazo(shan taba) Maman Hasan ta tayata da murmushi"a Alhamdulilla labarin zuciya a tambayi fuska.
Da safe tana shan shayin na'ana'a, kalla,kanumfari,da ya'yan algarib sai tiriri yake yi da k'amshi me dad'in dake k'ara mishi armashin da ko bakayi niyyar sha ba idan aka baka sai ka sha.Hafsa tashigo da waya d'akin baccin su dan yau bata fita D'akin-shak'atawa ba,anan ta zauna tana karyawa tana nazarce-nazarcenta.
Tamik'a mata wayar"ga shi ana magana"takar6a takai kunnan ta da sallama,ya amsa sallamar yana tambayar ta ya gida ya karatu?A takaice ta amsa"Lafiya...Alhamdulillah. Sukayi shiru na wucewar wasu dak'ik'u"wake magana?Takatse shirun.
"Salim ne.
Salim... Salim...
Tafad'a ta maimaita cikin tunanin ga no wa ye haka?Sai yatari numfashin ta,a d'an marairaice"Innalillahi...Ina zan sa kaina...? Mummuna ya ga mata.Kar dai ace baki gane Salim d'in ba?Haba Sumayya to Salim d'in kine fa. Ta d'an bud'e idanu"Oh...Ya Rahman afwan Salim ka san bani da lambar ka.Yayi yar dariya"na sani nima jiya ne na kar6i ta ki lambar a wajan Alhaji,yana nufin Alhaji Hafiz.Kin san ranar dana zo k'aunar ki ta mamaye k'wak'walwa ta har natafi ban baki ba,nima ban kar6i ta kiba.Suka gaisa a mutunce"Sumayya da yammacin yau nake san zuwa wajen ki shin kina da lokacina?
Tad'anyi murmushi"haba Salim girman ka ya wuce haka,ai ko ba lokacin ka to dole a k'irk'iroshi bare ma a kwai,amma I'm really sorry to say...ka san yanayin karatu,yau k'arfe goma na safiyar nan zan tafi makaranta kuma gaskiya sai biyar da rabi za mu gama lectures sai dai gobe.Yagyada kai"ba damuwa da yau da goben duk d'aya ne.Kad'an suka ta6a hira sukayi sallama.
Sumayya da Salim k'ank'anin lokaci suka aminta da juna.Sumayya har ranta take jin ta samu abokin rayuwa,saboda Salim mutum ne me sauk'in kai,bai cika d'aukar al'amura da zafi ba.Dariya takeyi saboda kalaman shi,yabita da kallo cikin zancan zuci,wallahi kome na ta akwai tsabta,hak'oranta farare tas kamar ba dasu take tauna duk abinda yake shiga cikin cikin taba.
"Sumayya dawani man goge baki kike amfani ne?Takatse dariyar"man goge baki kuma?Yajijjiga kai eh dan na ga hak'oranki sun bambanta dana mutane da yawa cikinsu kuwa har da ni d'in nan yanuna kanshi,kamar bakya 6a tasu da abinci sai d'aukar idanu suke yi.
Kana so kasan sirrin?Sosai kuwa.To ka zama me yawan aswaki ba sai lokacin alwala kad'ai ba, kuma musamman kasa mu aswakin al'araq,wannan shine sirrin ga shi kuma sunnane.Kuma ka san ko masana a harkar bincike na yanzu da suke ganin sune tushen ilimin kome,to sunyi bincike kuma sun ga no sun kuma tabbatar yin aswaki goge hak'ora da chewing-stick magogi,ba brush ba yana k'ara k'arfin dasashi. ALLAU-AKBAR tsarki ya tabbata ga ALLAH. Manzan ALLAH sai da yace ba dan kar ya takura ma al'umma ba da ya farlanta mana yin aswaki. Salim ya jijjiga kai gaskiya kin tunatar dani abinda na manta,nagode miki Sumayya lallai tunatarwa tana amfanar da mumini.
Sumayya ki bani dama in tura Iyayena,ai mun d'an fahimci juna,yanzu mun san wasu daga cikin halayan junan mu ko? Duk da dai ba a sanin maci tuwo dole sai miya ta k'are. Takalleshi cikin natsuwa"Salim a da zuciya ta, tana rayamin inyi musulunci saboda Julaibib ne, kuma koda na kar6i musulunci na kar6a ne saboda shi,amma cikin k'udirar Ubangiji sai zuciya ta,tacanja daga wancan tunanani da niyar.A yanzu na yadda saboda zatin ALLAH nake musulunci,da taimakon su Uncle ta fuskar nasiha da zuwa Islamiyya da sauraran wa'azi daga bakunan manyan malamai mabambanta duk su suka cusa min yin abu saboda ALLAH,na san na rasa D'an Sarai amma zuciya ta bata aminta da barin musulunci ba,dan na gamsu addinin musulunci shine addinin gaskiya,ina zaune kwatsam sai Uncle yazo min da maganar ka,a lokacin na amsa mishi ne saboda kawai tsakani na da Uncle ba musu har abadan duniya,wallahi kome rashin jin dad'in abu in dai yabani umarni inyi ko in bari zan yi,dan na san soyayya ce a tsakanin mu,har fa zuciyata ta fara min sak'a da mugun zare amma ban biye mata ba,nayi ta addu'a ina neman rok'on Ubangijin mu yakawo min agaji kar in biye ma sharrin ta.
Amma a ranar da idanuna suka fara yin tozali da kai,kalamanka da kome naka sai suka burgeni, zuciya ta tayi wasai...A ranar na kar6e ka kamaye gurbin Julaibib,tad'an sake kallanshi cikin natsuwa Salim har yanzu ina jin wani abu game da D'ansarai amma ba soyayya ba,saboda sanadiyar shi nabar kowa da kome, harkar da nake yi nabin maza da tara abinda duniya daga garesu yabar zuciya ta,fatana kawai in mallake shi,to sai nagane a yadda yake me natsuwa da kamewa hak'ata bazata tadda ruwa ba, sai na bijiro mishi da maganar aure, na sadak'ar zanyi sallah ba dan kome ba sai dan kawai na k'wallafa rai shi d'in kawai nake san mallaka,manyan idanunta masu maik'o suka cika da kwalla.Ubangijin mu alhakimu ne,sai gashi ya canja min da wani daban kuma zuciya ta ta aminta da shi,dan haka Salim kai nake so soyayyar da ba ka da abokin tarayya.Julaibib dai yana da lada a wajan ALlAH saboda halayan shi masu kyau da tsabta wanda addinin musuluncine yazo dasu da kuma karatun addinin da yayi shine ya siffantu da siffofin,nima sai yanzu nagane wasu halayanshi da, a da nake mugun mamakin me yasa shi baya kaza?Me yasa yake kaza? Tad'aga hannayen ta sama ALLAH kahad'ashi da macen albarka,kamilalliya me addini.ALLAH kasamu daga cikin wad'anda ta sanadiyyar mu wasu za su samu haske irin na addinin ka.Ubangiji ka kara mana lafiya ka kara inganta mana Imanin mu.Yanata kallanta cikin so da k'auna,sai yadad'a aminta da ita dan Alhaji Hafiz ya mishi bayanin kome dalla-dalla ba jibge.
Sumayya...
Bata amsa ba tad'ago a hankali suka kalli juna"Sumayya yau rana ce ta musamman a wajan mu ko?Tasunkwui da kai daga kallan da yake mata tana murmushi.
Sai da a ka tsaida ranar auran Salim da Sumayya,Miqdad da budurwar shi Zainab sannan Alhaji Hafiz yatashi Miqdad d'in musamman dan zuwa k'auyan su Madauci wajan d'an uwanshi,bai ta6a zuwa garin ba amma da tambaya sai gashi a k'ofar gidan.Yanata sallama yaji shiru ba a amsaba,zuwa can sai yatuna to su ina ruwansu da wata sallama?Sai yakai hannu yafara rank'washin k'ofar.Yana gyangyad'i kamar a sama yaji ana buga k'ofar yamik'e dasauri yana fad'in"kai wanene haka daba zai shigo ba,bayan k'ofar ba kulle ta akayi ba amma yatsaya awaje?Sukayi kallan kallo na wucewar wasu dak'ik'u sannan ya matsa mishi yashigo,suka zauna a fararan kujerun robar tsakar gidan har yanzu kallan juna sukeyi "daga ina haka d'an Samari?Kantiok ya tambaye shi.Miqdad yayi murmushi daga Kaduna nake.Ai yana jin haka sai yamik'e ya rungumeshi yana dariyar murna"haba no wonder naji a jikina kamar na san ka to sai dai a ina?
Kai yaran Shedrak ne ko?Ina Kasham? Ya baku zo tare ba?Su ma suna nan zuwa.Yasaki Miqdad yafita dasauri,lemun kwali Don Simon,ruwa da kofi yakawo mishi gashi nan kasha barin kar6o maka abinci... ya tareshi da saurin"a ah kabar shi kawai.Yaja yatsaya yana kallanshi"Kazo gidana amma baza ka ci abincin mu ba saboda me?Yad'an shafa fuskar shi"Kayi hak'uri Kawu ina azumi ne amma da ba abinda zai hana ni ci.Yadawo yazauna to kai saboda ALLAH za kayi tafiya ba sai kabar azumin ba?Ya amsa mishi cikin girmamawa"Kawu azumin yana da muhimmancine.
Suna ta hira kamar sun saba. Miqdad yabashi sak'on da aka aiko shi wasik'a ce Alhaji Hafiz d'in yake sanar dashi"Kasham tana wajan shi tana kuma sallah,yanzu kuma ta samu mijin aure,dan haka zai aurar da ita,amma bayan bikinza suzo Insha-ALLAH,sai takardan kud'i (cheque)an rubuta mak'udan kaud'ad'e an sa hannu sai zuwa gidan kud'in(Bank)a Kar6a "Hallelujah..yafad'a saboda mamakin adadin kud'in daya gani a rubuce,gaskiya shi har yagama aiki bai ta6a kar6an rabin-rabin wannan ba,yana ta dariyar murna,shi kuma Miqdad tasbihi yakeyi a zuciyar shi"ALLAH buwayi gagara misali hatta wushiryar shi irin ta mahaifin shine,sunyi kama sosai sai dai wannan fari ne, mahaifanshi kuma baki ne.
Kiran wayar ta tashigo yad'aga da sallama"Yaya Miqdad ya hanya ka sauka lafiya ko? Yagyad'a kai"na sauka lafiya Sumayya gani ga Kawu na ganshi ganin idanuna.Tayi yar dariya."to masha-ALLAH ba shi wayar.Yamik'a mishi.Yana jin muryarta yayi dariyar jin dad'i "Kasham sai kuma yajuya harshe zuwa yarensu na Bajju,sun dad'e suna hira sannan yafara gyad'a kai da alama wata magana me mahimmanci take fad'a mishi yake gyad'a kan cikin gamsuwa"amin Kasham nagode ALLAH yamiki albarka.Miqdad yakad'a kai"wato kowa dai ya san akwai ALLAH yadda da shine dai ba kowa yayi ba.
Yana shirin tafiya yace ni har zan tafi banga Maman Sumayya baWai Kasham ce ta koma Sumayya?Eh kawu"Yayi murmushi kawai, Maman Kasham ta tafi kasuwa gashi kuma sai yamma za ta dawo,to ka kwana mana.Yayi yar dariya"Kawu ina da ayyukan da zanyi da yawa amma zan zo na musammma idan nasamu sarari zan kwana in ga sauran yan uwan mu.To shikenan ALLAH yakaimu"yarakoshi har inda ya ajiye motar shi yana bashin tabbacin zaizo ayi d'aurin auran su dashi.To Kawu aiko za muji dad'i ba kad'an ba,yad'auko rafar kud'i yan naira ashirin guda d'aya yabashi,sai yagirgiza kai,haba My Son ni ban ba ka kome ba ai kuma bazan kar6e na kaba, kabarshi kawai nagode,ga cheque na kud'i me yawa da zan kar6a.Miqdad yakalleshi cikin natsuwa"Kawu ai wancan d'an uwan kane yabaka,wannan kuma d'an kane yabaka,tashi kyautar daban,tawa ma daban,sai dai ban sani ba d'an uwa ya fi d'ane a wajanka?Yasake mik'a mishi sai yakar6a yanata mishi godiya,sukayi sallama cikin farin ciki.Yad'aga hannu yana mishi adabo tare da addu'ar ALLAH yatsare ya kiyaye mishi hanya,har motar tasha kwana ta6ace ma ganin shi, sannan ya juya,yak'are ma gidan kallo lallai gyara yazo tunda kud'i sun samu.
Da safe tana shan shayin na'ana'a, kalla,kanumfari,da ya'yan algarib sai tiriri yake yi da k'amshi me dad'in dake k'ara mishi armashin da ko bakayi niyyar sha ba idan aka baka sai ka sha.Hafsa tashigo da waya d'akin baccin su dan yau bata fita D'akin-shak'atawa ba,anan ta zauna tana karyawa tana nazarce-nazarcenta.
Tamik'a mata wayar"ga shi ana magana"takar6a takai kunnan ta da sallama,ya amsa sallamar yana tambayar ta ya gida ya karatu?A takaice ta amsa"Lafiya...Alhamdulillah. Sukayi shiru na wucewar wasu dak'ik'u"wake magana?Takatse shirun.
"Salim ne.
Salim... Salim...
Tafad'a ta maimaita cikin tunanin ga no wa ye haka?Sai yatari numfashin ta,a d'an marairaice"Innalillahi...Ina zan sa kaina...? Mummuna ya ga mata.Kar dai ace baki gane Salim d'in ba?Haba Sumayya to Salim d'in kine fa. Ta d'an bud'e idanu"Oh...Ya Rahman afwan Salim ka san bani da lambar ka.Yayi yar dariya"na sani nima jiya ne na kar6i ta ki lambar a wajan Alhaji,yana nufin Alhaji Hafiz.Kin san ranar dana zo k'aunar ki ta mamaye k'wak'walwa ta har natafi ban baki ba,nima ban kar6i ta kiba.Suka gaisa a mutunce"Sumayya da yammacin yau nake san zuwa wajen ki shin kina da lokacina?
Tad'anyi murmushi"haba Salim girman ka ya wuce haka,ai ko ba lokacin ka to dole a k'irk'iroshi bare ma a kwai,amma I'm really sorry to say...ka san yanayin karatu,yau k'arfe goma na safiyar nan zan tafi makaranta kuma gaskiya sai biyar da rabi za mu gama lectures sai dai gobe.Yagyada kai"ba damuwa da yau da goben duk d'aya ne.Kad'an suka ta6a hira sukayi sallama.
Sumayya da Salim k'ank'anin lokaci suka aminta da juna.Sumayya har ranta take jin ta samu abokin rayuwa,saboda Salim mutum ne me sauk'in kai,bai cika d'aukar al'amura da zafi ba.Dariya takeyi saboda kalaman shi,yabita da kallo cikin zancan zuci,wallahi kome na ta akwai tsabta,hak'oranta farare tas kamar ba dasu take tauna duk abinda yake shiga cikin cikin taba.
"Sumayya dawani man goge baki kike amfani ne?Takatse dariyar"man goge baki kuma?Yajijjiga kai eh dan na ga hak'oranki sun bambanta dana mutane da yawa cikinsu kuwa har da ni d'in nan yanuna kanshi,kamar bakya 6a tasu da abinci sai d'aukar idanu suke yi.
Kana so kasan sirrin?Sosai kuwa.To ka zama me yawan aswaki ba sai lokacin alwala kad'ai ba, kuma musamman kasa mu aswakin al'araq,wannan shine sirrin ga shi kuma sunnane.Kuma ka san ko masana a harkar bincike na yanzu da suke ganin sune tushen ilimin kome,to sunyi bincike kuma sun ga no sun kuma tabbatar yin aswaki goge hak'ora da chewing-stick magogi,ba brush ba yana k'ara k'arfin dasashi. ALLAU-AKBAR tsarki ya tabbata ga ALLAH. Manzan ALLAH sai da yace ba dan kar ya takura ma al'umma ba da ya farlanta mana yin aswaki. Salim ya jijjiga kai gaskiya kin tunatar dani abinda na manta,nagode miki Sumayya lallai tunatarwa tana amfanar da mumini.
Sumayya ki bani dama in tura Iyayena,ai mun d'an fahimci juna,yanzu mun san wasu daga cikin halayan junan mu ko? Duk da dai ba a sanin maci tuwo dole sai miya ta k'are. Takalleshi cikin natsuwa"Salim a da zuciya ta, tana rayamin inyi musulunci saboda Julaibib ne, kuma koda na kar6i musulunci na kar6a ne saboda shi,amma cikin k'udirar Ubangiji sai zuciya ta,tacanja daga wancan tunanani da niyar.A yanzu na yadda saboda zatin ALLAH nake musulunci,da taimakon su Uncle ta fuskar nasiha da zuwa Islamiyya da sauraran wa'azi daga bakunan manyan malamai mabambanta duk su suka cusa min yin abu saboda ALLAH,na san na rasa D'an Sarai amma zuciya ta bata aminta da barin musulunci ba,dan na gamsu addinin musulunci shine addinin gaskiya,ina zaune kwatsam sai Uncle yazo min da maganar ka,a lokacin na amsa mishi ne saboda kawai tsakani na da Uncle ba musu har abadan duniya,wallahi kome rashin jin dad'in abu in dai yabani umarni inyi ko in bari zan yi,dan na san soyayya ce a tsakanin mu,har fa zuciyata ta fara min sak'a da mugun zare amma ban biye mata ba,nayi ta addu'a ina neman rok'on Ubangijin mu yakawo min agaji kar in biye ma sharrin ta.
Amma a ranar da idanuna suka fara yin tozali da kai,kalamanka da kome naka sai suka burgeni, zuciya ta tayi wasai...A ranar na kar6e ka kamaye gurbin Julaibib,tad'an sake kallanshi cikin natsuwa Salim har yanzu ina jin wani abu game da D'ansarai amma ba soyayya ba,saboda sanadiyar shi nabar kowa da kome, harkar da nake yi nabin maza da tara abinda duniya daga garesu yabar zuciya ta,fatana kawai in mallake shi,to sai nagane a yadda yake me natsuwa da kamewa hak'ata bazata tadda ruwa ba, sai na bijiro mishi da maganar aure, na sadak'ar zanyi sallah ba dan kome ba sai dan kawai na k'wallafa rai shi d'in kawai nake san mallaka,manyan idanunta masu maik'o suka cika da kwalla.Ubangijin mu alhakimu ne,sai gashi ya canja min da wani daban kuma zuciya ta ta aminta da shi,dan haka Salim kai nake so soyayyar da ba ka da abokin tarayya.Julaibib dai yana da lada a wajan ALlAH saboda halayan shi masu kyau da tsabta wanda addinin musuluncine yazo dasu da kuma karatun addinin da yayi shine ya siffantu da siffofin,nima sai yanzu nagane wasu halayanshi da, a da nake mugun mamakin me yasa shi baya kaza?Me yasa yake kaza? Tad'aga hannayen ta sama ALLAH kahad'ashi da macen albarka,kamilalliya me addini.ALLAH kasamu daga cikin wad'anda ta sanadiyyar mu wasu za su samu haske irin na addinin ka.Ubangiji ka kara mana lafiya ka kara inganta mana Imanin mu.Yanata kallanta cikin so da k'auna,sai yadad'a aminta da ita dan Alhaji Hafiz ya mishi bayanin kome dalla-dalla ba jibge.
Sumayya...
Bata amsa ba tad'ago a hankali suka kalli juna"Sumayya yau rana ce ta musamman a wajan mu ko?Tasunkwui da kai daga kallan da yake mata tana murmushi.
Sai da a ka tsaida ranar auran Salim da Sumayya,Miqdad da budurwar shi Zainab sannan Alhaji Hafiz yatashi Miqdad d'in musamman dan zuwa k'auyan su Madauci wajan d'an uwanshi,bai ta6a zuwa garin ba amma da tambaya sai gashi a k'ofar gidan.Yanata sallama yaji shiru ba a amsaba,zuwa can sai yatuna to su ina ruwansu da wata sallama?Sai yakai hannu yafara rank'washin k'ofar.Yana gyangyad'i kamar a sama yaji ana buga k'ofar yamik'e dasauri yana fad'in"kai wanene haka daba zai shigo ba,bayan k'ofar ba kulle ta akayi ba amma yatsaya awaje?Sukayi kallan kallo na wucewar wasu dak'ik'u sannan ya matsa mishi yashigo,suka zauna a fararan kujerun robar tsakar gidan har yanzu kallan juna sukeyi "daga ina haka d'an Samari?Kantiok ya tambaye shi.Miqdad yayi murmushi daga Kaduna nake.Ai yana jin haka sai yamik'e ya rungumeshi yana dariyar murna"haba no wonder naji a jikina kamar na san ka to sai dai a ina?
Kai yaran Shedrak ne ko?Ina Kasham? Ya baku zo tare ba?Su ma suna nan zuwa.Yasaki Miqdad yafita dasauri,lemun kwali Don Simon,ruwa da kofi yakawo mishi gashi nan kasha barin kar6o maka abinci... ya tareshi da saurin"a ah kabar shi kawai.Yaja yatsaya yana kallanshi"Kazo gidana amma baza ka ci abincin mu ba saboda me?Yad'an shafa fuskar shi"Kayi hak'uri Kawu ina azumi ne amma da ba abinda zai hana ni ci.Yadawo yazauna to kai saboda ALLAH za kayi tafiya ba sai kabar azumin ba?Ya amsa mishi cikin girmamawa"Kawu azumin yana da muhimmancine.
Suna ta hira kamar sun saba. Miqdad yabashi sak'on da aka aiko shi wasik'a ce Alhaji Hafiz d'in yake sanar dashi"Kasham tana wajan shi tana kuma sallah,yanzu kuma ta samu mijin aure,dan haka zai aurar da ita,amma bayan bikinza suzo Insha-ALLAH,sai takardan kud'i (cheque)an rubuta mak'udan kaud'ad'e an sa hannu sai zuwa gidan kud'in(Bank)a Kar6a "Hallelujah..yafad'a saboda mamakin adadin kud'in daya gani a rubuce,gaskiya shi har yagama aiki bai ta6a kar6an rabin-rabin wannan ba,yana ta dariyar murna,shi kuma Miqdad tasbihi yakeyi a zuciyar shi"ALLAH buwayi gagara misali hatta wushiryar shi irin ta mahaifin shine,sunyi kama sosai sai dai wannan fari ne, mahaifanshi kuma baki ne.
Kiran wayar ta tashigo yad'aga da sallama"Yaya Miqdad ya hanya ka sauka lafiya ko? Yagyad'a kai"na sauka lafiya Sumayya gani ga Kawu na ganshi ganin idanuna.Tayi yar dariya."to masha-ALLAH ba shi wayar.Yamik'a mishi.Yana jin muryarta yayi dariyar jin dad'i "Kasham sai kuma yajuya harshe zuwa yarensu na Bajju,sun dad'e suna hira sannan yafara gyad'a kai da alama wata magana me mahimmanci take fad'a mishi yake gyad'a kan cikin gamsuwa"amin Kasham nagode ALLAH yamiki albarka.Miqdad yakad'a kai"wato kowa dai ya san akwai ALLAH yadda da shine dai ba kowa yayi ba.
Yana shirin tafiya yace ni har zan tafi banga Maman Sumayya baWai Kasham ce ta koma Sumayya?Eh kawu"Yayi murmushi kawai, Maman Kasham ta tafi kasuwa gashi kuma sai yamma za ta dawo,to ka kwana mana.Yayi yar dariya"Kawu ina da ayyukan da zanyi da yawa amma zan zo na musammma idan nasamu sarari zan kwana in ga sauran yan uwan mu.To shikenan ALLAH yakaimu"yarakoshi har inda ya ajiye motar shi yana bashin tabbacin zaizo ayi d'aurin auran su dashi.To Kawu aiko za muji dad'i ba kad'an ba,yad'auko rafar kud'i yan naira ashirin guda d'aya yabashi,sai yagirgiza kai,haba My Son ni ban ba ka kome ba ai kuma bazan kar6e na kaba, kabarshi kawai nagode,ga cheque na kud'i me yawa da zan kar6a.Miqdad yakalleshi cikin natsuwa"Kawu ai wancan d'an uwan kane yabaka,wannan kuma d'an kane yabaka,tashi kyautar daban,tawa ma daban,sai dai ban sani ba d'an uwa ya fi d'ane a wajanka?Yasake mik'a mishi sai yakar6a yanata mishi godiya,sukayi sallama cikin farin ciki.Yad'aga hannu yana mishi adabo tare da addu'ar ALLAH yatsare ya kiyaye mishi hanya,har motar tasha kwana ta6ace ma ganin shi, sannan ya juya,yak'are ma gidan kallo lallai gyara yazo tunda kud'i sun samu.