Sashe 42
Gwajin Dafi Complete Hausa Novel · about 8 min read
Luuu tatafi kamar za ta fad'i saboda jirin daya fara d'iban ta,a hankali takoma ta zauna,tasa duka tafukan hannayenta tarufe fuskarta tana k'ank'ame jiki dan bata daina jin sanyin ba."Sannu Sudaida jiri ko? Tagyad'a kai. Sudaida yakira ta.Tacire tafukan hannayenta a fuska sannan takalle shi,yamik'a mata Farm-pride yoghort d'in hannun shi"ki daure kisha.Tawani marairaice"Yaya Julaibib bazan iya sha ba,amai zanyi.Yazauna a gefen ta sannan yayi k'asa da murya cikin rarrashi"haba Sudaida kiyi hak'uri kisha zai miki magani,rashin cin abincin ki ya dame ni,Sagir ya fad'amin kinfi mako d'aya a haka,kullum sai Umma ta tasa ki a gaba kike cin d'an kad'an,yabud'e mata "d'an daure kisha kinji ko?
Yaya Julaibib amai zanyi zuciyata tana ta tashi fa.Yagirgiza kai"uh uh kar6i kisha baza kiyi amai ba rashin cin abincin ne yasa miki ta shin zuciyar.Tasa hannu biyu takar6a,kad'an ta kur6a tamik'a mishi, yagirgiza kai"d'an kara...da haka har sai da tasha rabi,yakar6a yarufe yamik'a mata anjima kidaure kishanye zai miki amfani,kinga yadda kika zama kuwa Sudaida?Takaryar da kai gefen dama"kai baza ka shaba? Uh kisha kawai. Tamik'a mishi hannu"d'an ban dabino... baya rasa dabino a aljihu yasa hannu ya d'ibosu"guda uku suka rage.Tasa hannu biyu takar6a tana ci.
A mashayar"Beer Parlour"suka had'u da Zigwai.Yaja kujera ya zauna yana kallan ta tana shafama faratanta jan farce ja,tad'ago takalle shi"daga ina kake tun d'azu ka shanya ni?Daga cikin gari mana,na je samo kud'in kashewa ne tunda ke muguwa ce fiance d'inki ba shi da kud'i amma baza ki iya taimaka mishi ba.Tagalla mishi harara"in taimaka maka fa kace?Kai bakaji kunya ba kura da shan duka gardi da kar6e kud'i? Yamotsa kafad'a"a very stingy woman,ba wata kunya dana ji,kin san da ina dashi bazan tambaye kiba,tare ma zamu kashe su.
Tagama shafe faratan ta sannan tasa nailpolish d'in a jaka,tabi wajan da kallo ya cika dank'am da mutane maza da mata ga hasken disco light kore,ruwan bula da ja,wasu na shaye-shaye,wasu suna bin wakar da aka kunna a k'atuwar rediyon,tamaida kallan ta ga Tibishi "birthday party na bazai yiwu a ranar lahadi ba,na maida shi ranar juma'a.To saboda me?Tad'ora duka hannayen ta a saman tebur d'in"dole ranar juma'a zan yi shi saboda ranar juma'ace d'aurin auran Sinan ka gane manufa ta?Yajijjiga kai"na ga ne,kinyi tunani me kyau,amma fa a tsorace nake kar kwa6armu tayi ruwa.Yaba ta k'warin gwiwa "hey just chill up"kwa6armu baza tayi ruwa ba,duk abinda zai faru indai munci gari ba damuwa,ai ranar biyan buk'ata rai ba a bakin kome yake ba inji k'uda.
Da yammacin ranar laraba,rana tayi sanyi Hajiya takira layin Julaibib yad'aga da sallama yana yar dariya"Oh Hajiyar mu na yi kewar kifa"taja tsaki"kai tafi can kaba ni waje,ka yi kewa ta amma tunda kasa k'afa kabar garin nan kaka sa kirana?Ayya Hajiya ta ke kad'ai,kin san d'an makaranta yana fama da geron Sunday(garin kwaki\rogo)ba ta siyan katin waya nake yi ba.Yadda yayi maganar cikin jimami da tausayin kai yasa Hajiya tayi dariya"Julaibibi kana dani amma katsaya fatarar katin waya?To bari yanzu za kaji alert..Yauwa Hajiya ta nagode miki ba kad'an ba Ubangiji yak'ara girma.Amin Julaibibi. Hajiya ina cikin damuwa,na ka sa samun natsuwa.Ashsha me yake damun ka Julaibibi?Tun ranar dakika fad'amin kin samo min matar aure,Dan ALLAH Hajiya ba wai butulci zan yi da za6in ki ba,dan na san baza kimin za6en tumun dare ba,to amma alfarma d'aya nake nema kifad'amin wacece ita?Taja tsaki"na d'auka wata lalura ce ke damun ka?To yar gidan Kawun kace.Wane Kawun nawa?A ah to kuma nan d'aya ni dai nafad'a maka sai ta k'ara girma,yo data isa aure tare za a had'a dana su Sudaida ta k'arasa karatun a gidan ka.Yar karama ce kenan,ajin ta nawa?A ji d'aya take a ka'aramar Secondary idan kuma kana so ayi bikin ta girma a d'akinta to,kayi rainon ta yadda kake so.Yayi shiru kamar baiji abinda tafad'a.Hajiya tayi dariya"Julaibibi na to sai anjima ta katse wayar.Yahura iskar bakin shi bayan ya maida wayar shi aljihu,yayi tsai...cikin tunani Kawun nan na shi ai suna da yawa,kuma kowanne yana da tarin ya'ya mata,yayi iya tunanin shi amma bai canko ko wacece ba, yarik'e kugu yana bin d'akin na shi da kallo...
Sinan yana tsaye da mahaifin shi yana ba shi sak'on wasu kayayyaki da zai siyo mishi a Kaduna,Zigwai tak'araso wajan,tana sanye da matsatstsun riga da buje na material ruwan d'orawa an mishi d'inkin rashin mutunci da rashin sanin kimar kai,tantirancinta ya bayyana, tana rataye da bakar jaka,takalmanta masu rufi da tsinin diddige bak'ak'e"Sannu Alhaji tad'an rusuna tana gaishe da mahaifin shi,wani abu yadaki zuciyar Sinan, yad'auke kai daga kallan k'urullan da take mishi.Alhaji yakalle shi sai ya sunkwui da kai.Zigwai tayi wata yar dariya irin ta yan duniya"Malam Sinan angon Sudaida.Yad'ago yana murmushin yak'e,sai ta mik'a mishi envelop "sak'o nakawo maka.Yak'ar6a yana mata kallan tuhuma.
Tajuya tayi tafiyarta tana murmushi"za ka gane da gero ake koko, Sinan ai sai dai muyi biyu babu. Suka kalli juna shi da mahaifinshi "yadafa kafad'arshi,Sinan ba girma a ganka kana mu'amala da irin wad'annan k'adangarun barikin, ka san shaid'an baya raina k'ofa.Yagyad'a kai "Baba baka yadda dani bane?Sinan ba rashin yadda ce tasa na fad'a maka haka ba,illah gyara kayan ka...ai kai ba k'aramin yaro bane,sai dai tunatarwa tana amfanar da mumini,ai mun ba ka tarbiyya gwargwadon iyawarmu,idan kaje kayi wani abu sa6anin wanda muka d'oraka a kai,to ai ALLAH yana ji yana kuma gani wannan tsakanin ka dashi ne,bazai kama mu da sakaci ba,ni dai idan za kayi sara to kadinga duba bakin gatarin ka, kasan da irin mutanan da za ka dinga mu'amala, ina jiye maka kaidin irin wad'annan da suke ji kamar su juwo mutum ta k'arfin tsiya ya dilmiya. Jikin shi yayi sanyi,yayi nadamar abinda yafara "nagode Baba.Alhaji Kamal yashige motar shi yatafi. Yazauna a wajan cikin damuwa"to wai ma me yakai shi k'ulla mu'amala da Zigwai?
Sun gama jarabawa anyi speech and prize giving day anyi angama lafiya,kowa ya koma gida zaman jiran sakamakon girbe abinda aka shuka.Maganar biki ya dad'a kankama anata shirye-shirye,amare ana shan gyara Umma ce a wannan harkar dan kunsan ita bata d'aukar raini kona sisin kwabo ko ba dan ALLAH ba kowa sai ya bi.
Jajibarin auren su Sinan kai ya d'auki zafi baya samun zama,yana sa takalmi Tibishi yashigo yana kallan shi"maganar birthday party na Zigwai zan tuna maka fa.Yakalle shi rai a 6ace"Tibishi karabu dani,dan ba wannan ne a gabana ba.Yajijjiga kai"nima na sani to amma karka manta alk'awari kad'auka.Yagama sa takalmi yamik'e "Tibishi ta shi katafi akwai inda za ni,suka fito Sinan yakulle d'aki kowa yayi hanyar shi.
Bai dawo ba sai kwanciyar bacci a na ta dad'a gyara gidan amarya,sai da ya tabbatar kome ya kammala sannan hankalin shi ya kwanta, sai lokacin yasamu damar kiran Sudaida.Tana ganin kiran shi tad'an harari wayar tana k'unk'uni, sai da yakira sau uku sannan tad'aga"Sudaida sarauniyata...tatari numfashin shi"ni ba wata sarauniyar ka tunda tun safe baka nemi ni ba,na kira ka na jita a kashe,ni fa kana 6ata min rai. Wayyo ni Sinan to kiyi hak'uri ina can ina hidimta ma muhalllin kine,amma ko ina naje to tabbaci hak'ik'a kina cikin zuciya ta, ina son ki Sudaida... Tace hum...yacigaba'irin soyayyar da baza ta fad'uba,yayi yar dariya ALLAH dai yakai damo ga harawa ko baici ba yayi burgima,gobe war haka kin zama sarauniyar Sinan ta hak'ik'a,farin cikina zai fara daga gobe ne...yayita maganganun shi batace kome,basu wani dad'e yamata sallama dan zai kwanta ya gaji lik'is.
Farar rana me kyakkyawar suna, wato juma'a.Yan'uwa da abokan arziki cike da gidajan biki an karkasa ayyukan shi yasa nan da nan akayi aka gama.K'arfe sha biyu da rabi Julaibib yasamu isowa garin.Yashiga D'akin-shak'atawar Inna ana gaisawa.Yaya Karima takalle shi"ai na d'auka baza kazo ba.Yad'an shafa kwantaccen bak'in gashin kanshi"Yaya Karima yanayin karatun ne sai a hankali.
To ALLAH yataimaka.Amin.Yawuce d'akin shi dan shirin masallaci.Yana sanye da babbar riga,'yar ciki da wando na farar shadda getzner,hular shi k'ube da aikin babbar rigar shi ruwan toka da ratsin fari da bak'i, takalmishi sau ciki fari,agogo da zoben shi na farin azurfa sai d'aukar idanu sukeyi saboda hasken su, k'amshin arabian perfume d'inshi me dad'in shaka,ya cika wajan.Duk suka bishi da kallo.Yaya Karima tace "gaskiya autan Inna kayi sharrr...dakai kamar wani ango,Yayi murmushi kawai"kice ma Inna na tafi masallaci.
Yau gaba d'aya hud'ubar akan aure da ma'aurata akayi,bayan an idar da sallah anyi addu'o'i an shafa,auran Hashim da Aisha aka fara daurawa,sai Muhammad da Zainab,Abdullahi da Maryam,Abdulkarim da Nasmat,Huzaifa da Khausar...sai na Sinan da Sudaida da ake shirin d'aurawa,to amma wani wawan burki da aka taka sai da yatshi hankali jama'a,wasu suka fito daga masallacin dan ganin abinda yake faruwa.
Sinan ne yafito daga cikin motar yana sambatu da tam6elen mashayar...Su...Sud... Sudai...damata...ta..taceba...wanda...zai...raba ni da ita... alk'...wari...ba karyawa mutu ka raba takal...min kaza. Ciki da wajan masallaci kowa yayi d'ifff...ya cika da mad'aukakin mamaki na ganin Sinan a wannan yanayin, a hankali k'ananan surutai yafara ta shi.
Alhaji Kamal sai da numfashin shi yad'auke na wucin gadi yayi mutuwar zaune,dan abun ya kad'a shi"Innalillahi Wa'inna Ilaihi raji'un yake maimaitawa, Liman yakalle shi"dama ka san d'an ka yana shan giya? Yakad'a kai cikin damuwa "Liman bazan maka k'arya ba wallahil-azim ban sani ba,ban san kome game da Sinan ba sai halaye masu kyau.
Sinan d'in aka fitar daga masallacin dan yafara kakarin amai.Liman yakalli mahaifin Sudaida meye abin yi? Kafin yayi magana Alhaji Kamal ya amsa"ba za a d'aura ma Sudaida d'an giya ba,irin wannnan hukuncin zan zartar ko 'ya tace wallahi,dan haka ina rok'on alfarma a d'aura auran nan da k'anin Sinan,yanuna Hamidan dake zaune a gefen shi cikin 6acin ran abinda Sinan yayi.Liman yabi sauran jama'ar da kallo,yasauke numfashi"k'warai zan so haka,to amma wani hanzari ba gudu ba idan aka had'asu aure Sinan bazai barsu suyi zaman lafiya ba, zumuncin dake tsakanin su na shak'ik'an juna zai samu tasgaro, indai ba tsananin sa a a kaci Sinan d'in me hange nesa da maida al'amura ga ALLAH bane.Alhaji Kamalu kayi hak'uri,ni na san da wanda zan had'a auran nan yanzu da izinin ALLAH gida bai k'oshi ba ai baza a ba dawaba. Yaciro dubu ashirin d'in da kaba bashi zakkarsu dazai taho masallaci "yanzun nan zan d'aura auran Julaibib da Sudaida akan sadaki naira dubu ashirin lak'anan(lakadan) Masallaci yad'auki kabbara.
Yaya Julaibib amai zanyi zuciyata tana ta tashi fa.Yagirgiza kai"uh uh kar6i kisha baza kiyi amai ba rashin cin abincin ne yasa miki ta shin zuciyar.Tasa hannu biyu takar6a,kad'an ta kur6a tamik'a mishi, yagirgiza kai"d'an kara...da haka har sai da tasha rabi,yakar6a yarufe yamik'a mata anjima kidaure kishanye zai miki amfani,kinga yadda kika zama kuwa Sudaida?Takaryar da kai gefen dama"kai baza ka shaba? Uh kisha kawai. Tamik'a mishi hannu"d'an ban dabino... baya rasa dabino a aljihu yasa hannu ya d'ibosu"guda uku suka rage.Tasa hannu biyu takar6a tana ci.
A mashayar"Beer Parlour"suka had'u da Zigwai.Yaja kujera ya zauna yana kallan ta tana shafama faratanta jan farce ja,tad'ago takalle shi"daga ina kake tun d'azu ka shanya ni?Daga cikin gari mana,na je samo kud'in kashewa ne tunda ke muguwa ce fiance d'inki ba shi da kud'i amma baza ki iya taimaka mishi ba.Tagalla mishi harara"in taimaka maka fa kace?Kai bakaji kunya ba kura da shan duka gardi da kar6e kud'i? Yamotsa kafad'a"a very stingy woman,ba wata kunya dana ji,kin san da ina dashi bazan tambaye kiba,tare ma zamu kashe su.
Tagama shafe faratan ta sannan tasa nailpolish d'in a jaka,tabi wajan da kallo ya cika dank'am da mutane maza da mata ga hasken disco light kore,ruwan bula da ja,wasu na shaye-shaye,wasu suna bin wakar da aka kunna a k'atuwar rediyon,tamaida kallan ta ga Tibishi "birthday party na bazai yiwu a ranar lahadi ba,na maida shi ranar juma'a.To saboda me?Tad'ora duka hannayen ta a saman tebur d'in"dole ranar juma'a zan yi shi saboda ranar juma'ace d'aurin auran Sinan ka gane manufa ta?Yajijjiga kai"na ga ne,kinyi tunani me kyau,amma fa a tsorace nake kar kwa6armu tayi ruwa.Yaba ta k'warin gwiwa "hey just chill up"kwa6armu baza tayi ruwa ba,duk abinda zai faru indai munci gari ba damuwa,ai ranar biyan buk'ata rai ba a bakin kome yake ba inji k'uda.
Da yammacin ranar laraba,rana tayi sanyi Hajiya takira layin Julaibib yad'aga da sallama yana yar dariya"Oh Hajiyar mu na yi kewar kifa"taja tsaki"kai tafi can kaba ni waje,ka yi kewa ta amma tunda kasa k'afa kabar garin nan kaka sa kirana?Ayya Hajiya ta ke kad'ai,kin san d'an makaranta yana fama da geron Sunday(garin kwaki\rogo)ba ta siyan katin waya nake yi ba.Yadda yayi maganar cikin jimami da tausayin kai yasa Hajiya tayi dariya"Julaibibi kana dani amma katsaya fatarar katin waya?To bari yanzu za kaji alert..Yauwa Hajiya ta nagode miki ba kad'an ba Ubangiji yak'ara girma.Amin Julaibibi. Hajiya ina cikin damuwa,na ka sa samun natsuwa.Ashsha me yake damun ka Julaibibi?Tun ranar dakika fad'amin kin samo min matar aure,Dan ALLAH Hajiya ba wai butulci zan yi da za6in ki ba,dan na san baza kimin za6en tumun dare ba,to amma alfarma d'aya nake nema kifad'amin wacece ita?Taja tsaki"na d'auka wata lalura ce ke damun ka?To yar gidan Kawun kace.Wane Kawun nawa?A ah to kuma nan d'aya ni dai nafad'a maka sai ta k'ara girma,yo data isa aure tare za a had'a dana su Sudaida ta k'arasa karatun a gidan ka.Yar karama ce kenan,ajin ta nawa?A ji d'aya take a ka'aramar Secondary idan kuma kana so ayi bikin ta girma a d'akinta to,kayi rainon ta yadda kake so.Yayi shiru kamar baiji abinda tafad'a.Hajiya tayi dariya"Julaibibi na to sai anjima ta katse wayar.Yahura iskar bakin shi bayan ya maida wayar shi aljihu,yayi tsai...cikin tunani Kawun nan na shi ai suna da yawa,kuma kowanne yana da tarin ya'ya mata,yayi iya tunanin shi amma bai canko ko wacece ba, yarik'e kugu yana bin d'akin na shi da kallo...
Sinan yana tsaye da mahaifin shi yana ba shi sak'on wasu kayayyaki da zai siyo mishi a Kaduna,Zigwai tak'araso wajan,tana sanye da matsatstsun riga da buje na material ruwan d'orawa an mishi d'inkin rashin mutunci da rashin sanin kimar kai,tantirancinta ya bayyana, tana rataye da bakar jaka,takalmanta masu rufi da tsinin diddige bak'ak'e"Sannu Alhaji tad'an rusuna tana gaishe da mahaifin shi,wani abu yadaki zuciyar Sinan, yad'auke kai daga kallan k'urullan da take mishi.Alhaji yakalle shi sai ya sunkwui da kai.Zigwai tayi wata yar dariya irin ta yan duniya"Malam Sinan angon Sudaida.Yad'ago yana murmushin yak'e,sai ta mik'a mishi envelop "sak'o nakawo maka.Yak'ar6a yana mata kallan tuhuma.
Tajuya tayi tafiyarta tana murmushi"za ka gane da gero ake koko, Sinan ai sai dai muyi biyu babu. Suka kalli juna shi da mahaifinshi "yadafa kafad'arshi,Sinan ba girma a ganka kana mu'amala da irin wad'annan k'adangarun barikin, ka san shaid'an baya raina k'ofa.Yagyad'a kai "Baba baka yadda dani bane?Sinan ba rashin yadda ce tasa na fad'a maka haka ba,illah gyara kayan ka...ai kai ba k'aramin yaro bane,sai dai tunatarwa tana amfanar da mumini,ai mun ba ka tarbiyya gwargwadon iyawarmu,idan kaje kayi wani abu sa6anin wanda muka d'oraka a kai,to ai ALLAH yana ji yana kuma gani wannan tsakanin ka dashi ne,bazai kama mu da sakaci ba,ni dai idan za kayi sara to kadinga duba bakin gatarin ka, kasan da irin mutanan da za ka dinga mu'amala, ina jiye maka kaidin irin wad'annan da suke ji kamar su juwo mutum ta k'arfin tsiya ya dilmiya. Jikin shi yayi sanyi,yayi nadamar abinda yafara "nagode Baba.Alhaji Kamal yashige motar shi yatafi. Yazauna a wajan cikin damuwa"to wai ma me yakai shi k'ulla mu'amala da Zigwai?
Sun gama jarabawa anyi speech and prize giving day anyi angama lafiya,kowa ya koma gida zaman jiran sakamakon girbe abinda aka shuka.Maganar biki ya dad'a kankama anata shirye-shirye,amare ana shan gyara Umma ce a wannan harkar dan kunsan ita bata d'aukar raini kona sisin kwabo ko ba dan ALLAH ba kowa sai ya bi.
Jajibarin auren su Sinan kai ya d'auki zafi baya samun zama,yana sa takalmi Tibishi yashigo yana kallan shi"maganar birthday party na Zigwai zan tuna maka fa.Yakalle shi rai a 6ace"Tibishi karabu dani,dan ba wannan ne a gabana ba.Yajijjiga kai"nima na sani to amma karka manta alk'awari kad'auka.Yagama sa takalmi yamik'e "Tibishi ta shi katafi akwai inda za ni,suka fito Sinan yakulle d'aki kowa yayi hanyar shi.
Bai dawo ba sai kwanciyar bacci a na ta dad'a gyara gidan amarya,sai da ya tabbatar kome ya kammala sannan hankalin shi ya kwanta, sai lokacin yasamu damar kiran Sudaida.Tana ganin kiran shi tad'an harari wayar tana k'unk'uni, sai da yakira sau uku sannan tad'aga"Sudaida sarauniyata...tatari numfashin shi"ni ba wata sarauniyar ka tunda tun safe baka nemi ni ba,na kira ka na jita a kashe,ni fa kana 6ata min rai. Wayyo ni Sinan to kiyi hak'uri ina can ina hidimta ma muhalllin kine,amma ko ina naje to tabbaci hak'ik'a kina cikin zuciya ta, ina son ki Sudaida... Tace hum...yacigaba'irin soyayyar da baza ta fad'uba,yayi yar dariya ALLAH dai yakai damo ga harawa ko baici ba yayi burgima,gobe war haka kin zama sarauniyar Sinan ta hak'ik'a,farin cikina zai fara daga gobe ne...yayita maganganun shi batace kome,basu wani dad'e yamata sallama dan zai kwanta ya gaji lik'is.
Farar rana me kyakkyawar suna, wato juma'a.Yan'uwa da abokan arziki cike da gidajan biki an karkasa ayyukan shi yasa nan da nan akayi aka gama.K'arfe sha biyu da rabi Julaibib yasamu isowa garin.Yashiga D'akin-shak'atawar Inna ana gaisawa.Yaya Karima takalle shi"ai na d'auka baza kazo ba.Yad'an shafa kwantaccen bak'in gashin kanshi"Yaya Karima yanayin karatun ne sai a hankali.
To ALLAH yataimaka.Amin.Yawuce d'akin shi dan shirin masallaci.Yana sanye da babbar riga,'yar ciki da wando na farar shadda getzner,hular shi k'ube da aikin babbar rigar shi ruwan toka da ratsin fari da bak'i, takalmishi sau ciki fari,agogo da zoben shi na farin azurfa sai d'aukar idanu sukeyi saboda hasken su, k'amshin arabian perfume d'inshi me dad'in shaka,ya cika wajan.Duk suka bishi da kallo.Yaya Karima tace "gaskiya autan Inna kayi sharrr...dakai kamar wani ango,Yayi murmushi kawai"kice ma Inna na tafi masallaci.
Yau gaba d'aya hud'ubar akan aure da ma'aurata akayi,bayan an idar da sallah anyi addu'o'i an shafa,auran Hashim da Aisha aka fara daurawa,sai Muhammad da Zainab,Abdullahi da Maryam,Abdulkarim da Nasmat,Huzaifa da Khausar...sai na Sinan da Sudaida da ake shirin d'aurawa,to amma wani wawan burki da aka taka sai da yatshi hankali jama'a,wasu suka fito daga masallacin dan ganin abinda yake faruwa.
Sinan ne yafito daga cikin motar yana sambatu da tam6elen mashayar...Su...Sud... Sudai...damata...ta..taceba...wanda...zai...raba ni da ita... alk'...wari...ba karyawa mutu ka raba takal...min kaza. Ciki da wajan masallaci kowa yayi d'ifff...ya cika da mad'aukakin mamaki na ganin Sinan a wannan yanayin, a hankali k'ananan surutai yafara ta shi.
Alhaji Kamal sai da numfashin shi yad'auke na wucin gadi yayi mutuwar zaune,dan abun ya kad'a shi"Innalillahi Wa'inna Ilaihi raji'un yake maimaitawa, Liman yakalle shi"dama ka san d'an ka yana shan giya? Yakad'a kai cikin damuwa "Liman bazan maka k'arya ba wallahil-azim ban sani ba,ban san kome game da Sinan ba sai halaye masu kyau.
Sinan d'in aka fitar daga masallacin dan yafara kakarin amai.Liman yakalli mahaifin Sudaida meye abin yi? Kafin yayi magana Alhaji Kamal ya amsa"ba za a d'aura ma Sudaida d'an giya ba,irin wannnan hukuncin zan zartar ko 'ya tace wallahi,dan haka ina rok'on alfarma a d'aura auran nan da k'anin Sinan,yanuna Hamidan dake zaune a gefen shi cikin 6acin ran abinda Sinan yayi.Liman yabi sauran jama'ar da kallo,yasauke numfashi"k'warai zan so haka,to amma wani hanzari ba gudu ba idan aka had'asu aure Sinan bazai barsu suyi zaman lafiya ba, zumuncin dake tsakanin su na shak'ik'an juna zai samu tasgaro, indai ba tsananin sa a a kaci Sinan d'in me hange nesa da maida al'amura ga ALLAH bane.Alhaji Kamalu kayi hak'uri,ni na san da wanda zan had'a auran nan yanzu da izinin ALLAH gida bai k'oshi ba ai baza a ba dawaba. Yaciro dubu ashirin d'in da kaba bashi zakkarsu dazai taho masallaci "yanzun nan zan d'aura auran Julaibib da Sudaida akan sadaki naira dubu ashirin lak'anan(lakadan) Masallaci yad'auki kabbara.