← Book details Gwajin Dafi Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 38 OF 74

Sashe 38

Gwajin Dafi Complete Hausa Novel · about 8 min read

Bayan sallar asham Julaibib yawuce gidan Hajiya anan yatarar dawasu daga cikin jikokinta maza anata hira da ciye-ciye.Yajawo kaskon data cika da garwashi gaban shi, Musadduq yaja tsaki"Lillahi warasulihi yauma karasa abinda za ka kawo mana sai bushashshen masara?Kai ALLAH yasauwake.Ya amsa da amin "dan ka kawo mata bushasshen nama wai shi kilishi ba shi zai hanata cin gashashshiyar masara ba.Musaddiq yagirgiza kai"kai Malam ai yanzu ba lokacin cin kilishi bane,watan ramadan muke gasassun yan shila nakawo mata me ruwa-ruwa da yajin tafarnuwa ya ji kayan lambu.Yaturama Julaibib k'unshin duba kagani.Yayi kamar ba dashi yake magana ba yafara gasa masararshi yana tambayar Hajiya ta saurari tafsir na karfe uku da yammacin yau?

Kwanci tashi har anyi azumi takwas, agida tasame shi yana shirin komawa Azare "tazauna tana kallan shi"Yaya D'an Sarai tafiya ba sallama?Yacigaba da shirya kayan shi a jaka ba tare daya d'ago ya kalle taba"ai naje gidan akace kin tafi Hayin-Dogo"haka ne to yaushe za ka dawo? Yarufe jakar yad'auki agogo yana d'aurawa a hannun damar shi"sai ALLAH ya kaimu sallah idan muna raye,ta taya shi kwashe kaya zuwa mota yayi sallama da Inna suka fito,tajingina da motar tana kallan shi cikin kissima wani abu a zuci yana zuba ruwa a lagireto har yagama yashiga mota yazauna yana d'aura belt.

Yad'anyi murmushi"duk kinyi wata iri ko za ki bini ne?Ta turo baki gaba"da inada wannan damar ai da ba haka ba wallahi.Baiyi magana ba,yabata wasu kud'i"bayawa.Tasa hannu biyu takar6a"nagode Yaya D'ansarai ALLAH yak'ara bud'i,suka d'aga hannu suna ma juna adabo.

Sun dawo makaranta suka tarar da Asma'u kanwar Sudaida ta ci kuka ta gode ALLAH idanun ta sun kumbura sun kad'a jawur"lafiya Asma'u? A tare suka tambaye ta,sai tasake jin wani sabon kukan ya kufce mata tafi minti goma sannan tafara rage sauti tana ta jera ajiyar zuciya"ke wai kukan me kike yi ana tambayar ki kin ma mutane shiru wacece sa'ar ki anan? Khausar ta tambaye ta.Taja majina tana hura iskar bakin ta"labarin zuciya a tamabayi fuska ranta in yayi dubu ya 6aci,cikin hawaye tafara magana"wai arasa wanda za a bani a matsayin mijin aure sai Yaya D'ansarai...wasu hawaye masu d'umi suka sake zubowa sharrr...sharrr...Sudaida tamik'e zaune da sauri kamar za ta hantsila,duk suka bita da kallo ganin yadda tayi sai kuma ta koma ta kwanta batayi magana ba dan ta ma rasa abinda za ta fad'a wallahi.

Asma'u tacigaba bayan kowa ya san Alk'asim nake so amma ance a ah wai shi yaro ne ko Secondary bai gama ba,takad'a kai cikin takaici"saboda ALLAH wai Yaya D'ansarai. Khausar takalleta cikin natsuwa"bakya san shine? Dasauri tace"eh mana me zanyi dashi bak'ink'irin dashi kamar bak'in gashin kanshi...bata gama rufe baki ba taji saukar mari hagu da dama"Yaya D'ansarai kike za gi?To dame kwad'o yafi gaya?Ba gwamma shi bak'i kyakkyawa bane.Asma'u tamik'e cikin hawaye"amma wannan rashin 'yanci da yawa yake,ga mari ga tsinka jaka?Takalle ta "wallahi Yaya Sudaida bana san shi,tafita a d'akin da gudu cikin shashshekan kuka.

Tadunk'ule hannu ta naushi iska"da kin tsaya k'aramar mara kunya da kinga yadda zan yi dake.Khausar takalle ta"ai baki isa ki kuma dukan taba akan me? Dan tace ba ta san shi shine ya zama laifi?Yaya Julaibib d'in?Kwarai kuwa shi wanene da kowa sai ya so shi so?Wa kika ta6a gani ko jin labari kowa na doron duniya ya so shi? Ko wanda yayi mu an samu wanda basa san shi ta hanyar k'in yadda da duk abinda yace ayi,da wanda yace abari,bare wani Julaibib ordinary human being,ai dama na dad'e ina zargin wani abu bani da tabbasss shiyasa naja bakina nayi shiru; to amma yau na samu yak'ini san Julaibib d'in nan ki keyi,to dake dashi d'in duk sai kuje kuji da manufurcin ku,ai shima ina lura da takunshi akanki.Yaya Khausar daza kice haka shi kuma Sinan d'in ina zan kai shi?Tawatsa hannu"ke kika sani...

Cikin bugun zuciya tafara harhad'a littafan data barbaza a kan gado da niyyar yin nazarin su,ta tsuke baki tana yamutsa fuska Khausar tayi yar dariya tana rage kayan jikinta za ta shiga wanka Asma'u ta D'ansarai bak'ak'e biyu kila za su iya samar da wankan tarwad'a ko fari ko sarauniyar Sinan?Bata kula taba tamak'alama wayar ta earphone tana k'ok'arin toshe kunnuwan ta dashi. Khausar ta fizge"ke malama kirufa mana asiri karki zama kanwar kurma,so nawa ni da ke munajin bayanan da likitoci k'wararru a bangaran kunne,mak'ogwara da hanci(E N T) sukeyi,yawan amfani da earphone yana kawo matsala a bangaran ji"tagyad'a kai "naji bani wayata.Tamik'a mata, kita shi kisan abinda za ki d'ora tunda su Mama basa nan ko miyar shuwaka za ki mana mun kwana biyu bamu ciba wallahi,ta san Sudaida bata so dan tayi tsokana tafad'a. Yaya Khausar"ai bazan hana kiyi idan kina so ba"kuturu da kud'in shi alkaki ba sai na k'asan kwano ba?Gaskiya ne to d'anje kifara wanke min shuwakar kafin in fito wanka.

Kwana biyu da maganar ranan Asma'u ce da aiki tasame ta a D'akin-girki tana kad'a miya sai ta kar6i maburgin barin taya ki,Asma'u tad'anyi murmushi "Yaya Sudaida saboda ALLAH ko kuma cin tuwon kishiya...?Duka biyun.Sukayi dariya, Asma'u tana zuba mata garin kuka tana cigaba da burgawa har suka gama, tad'an jefa kanwa kad'an wucewar wasu yan dak'ik'u tasauke to d'orama Yaya Aminu ruwan da zata dama mishi custard aranta tana mita"gaskiya Siddika ta shiga uku da shan kunu,ga fa kunun tsamiya can Inna ta aiko mai dashi amma duk da haka wai dole-dole sai ta dama mishi custard,ruwan yana tafasa ta dama tajuye mishi a flask.

Tamatsa gefe tana cema Asma'u ai dai na taya ki,dan haka zo ki dora ruwan tuwon ki. Takalli Asma'u da natsuwa bayan tad'ora ruwan "waye yace za a ba ki Julaibib a matsayin mijin aure?Tayi d'an tsaki"na manta.Kin manta?Eh,to ban sa a ka ba inji 6arawon tagiya,sai kuma tayi kwafa"ba Hajiya ce da wannan neman maganar ba,haka kawai ga wanda zuciyata take marari... Tad'auki flask batace kome ba tajuya tafita. Asma'u tabita da kallo"yauma kinji haushi dan na ce ba shi nake so ba ko?Tad'an motsa kafad'a,sai dai kiyita jin haushin me zanyi dashi?Tad'auko garin dawa za tayi talge dan har ruwan ya tafasa.

Littafan tane a saman tebur ta barbaza, nazarin su take so tayi d'aya bayan d'aya saboda ranar Litini za su fara jarabawa,tad'auki littafin lissafi tana dad'ayin nazari akan darasin da aka musu wancan makon Simultenous Equation sai dai ko dak'ik'u goma bata had'a ba taji ta gaji,ta kasa fahimtar kome duk da kuwa a wajan lissafi babbar k'waruwace,ita dai azumi yana ba ta wahala da mutum zai iya biya a mishi aikin ibada to ita dai azumi za ta dinga biya,kome a wahale takeyi,ta ture littafin gefe idan ba haka ba yanzun nan kanta zai fara ciwo kuma yau itace da aikin abin bud'a baki,a hankali taza me takwanta a doguwar kujera gwamma tad'an rintsa kafin lokacin aiki yayi,tad'anyi tsaki tun yanzu jikinta ya mutu murusss... ALLAH dai yasa Umma karta ba ta aiki me wahala.

Kamar a mafarki tashak'o k'amshin arabi'an perfume tare da sallama.Dasauri tabud'e idanunta da suka canja kala dan bacci ya fara awon gaba da ita,yana jingine da k'ofar shigowa yayi sharrr...sharrr dashi cikin farin yadi me k'ananan huji-huji kana hango farar singilet d'inshi, bak'in gashin kanshi ya sha gyara yanata kyallin hair fruits,ba laifi yafara maida jikinshi sai taji dad'i a ranta.

Tamik'e zaune cikin mamaki"Yaya D'ansarai?Yabar duba wayar hannun shi yad'ago yana kallanta "na'am,ina ta sallama baki amsa ba szumin tun yanzu ya fara duka kenan.Tayi murmushi"tad'anyi tsaki kai dai bari kawai, wai ba ka ce sai sallah za kazo ba?Yak'arasa shiga D'akin-shak'atawar"eh,yau da safe nazo anjima kad'an zan koma na manta wasu muhimman takaddune abinda yadawo dani kenan,yad'aga kiran daya shigo wayar shi, baiyi magana ba bayan sallamar da yayi,sauraro yakeyi... zuwa wasu yan dak'ik'u ya amsa da"nagode Maimun musha ruwa lafiya.Yasa wayar a aljihu,yana d'ago kai caraf idanunsu yahad'u yakauda kai...daga can tsakar gidan suka fara jiyo Asma'u cikin nishad'in ta,tana rera wasu baiti daga cikin baitocin wakar Sadi Sidi Sharifai da Maryam A.Baba(Sangandale)suka rera...tana tafe tana tafa hannaye.

🎶🎵Taho malam,taho gani nan da soyayya nafito daga gida🎵🎶

🎶🎵Ina shaidama a yau ne nasamu sak'onka, ina zaune a gida sai naji shi begen ka🎵🎶

🎶🎵Shine nafito in duba ko zan ganka🎵🎶

🎶🎵Amsar sak'onka na yarda in zam matar kazamo megidahhh...🎵🎶

Tana shigowa suka bita da kallo.Kunya da haushin shi suka rufe ta,tayi jimmm...fuska a yamutse tagaishe shi,bata jira amsawar shi ba ta d'auki abinda yashigo da ita"tin-opener"a saman tebur tajuya.Asma'u yakira ta.Sai tayi kunnan uwar shegu tak'ara sauri.A k'ofa sukayi kaci6is da Mama,takalleta da kulawa"saboda ALLAH Asma'u a wannnan gwalagwalan kwanakin nagoman k'arshe kika tsaya rera wak'a...?Tayarfe hannu "dan ALLAH Mama kiyi hak'uri kar Umma tajiyo ki, yanzu tashigo gidan daqowarta daga unguwa. Astagfirullah...Mama tayi murmushi"ALLAH yadad'a shirya ku.

Sudaida tabishi da kallo bata ga wani yanayi a fuskar shi ba,yakalli agogon dake d'aure a hannunshi na dama,lokaci ya ja gashi har Matsirga yake so yaje kafin yawuce. Yad'an kalle ta"ke na wuce.Ta taka mishi har k'ofar gida inda ya ajiye mota"Yaya Julaibib ALLAH yatsare hanya, musha ruwa lafiya.Amin Sudaida nagode.Tajuya zuwa cikin gida tana zancen zuci"Yaya Julaibib bai san da maganar Hajiya akan an ba shi Asma'u ba. Asma'un kawai Hajiya tafad'a ma.

Yau take sallah...kowa kagani yayi sharrr dashi dashiga ta burgewa ya kure adaka.Bayan an sakko daga sallar Idi Hajiya da wasu daga cikin jikokin ta suka mata rakiya zuwa gida.Me musu fid'an ragon sallah har yazo na Hajiya yake fara gyarawa kafin yawuce sauran gidajan, suna d'an hira da Sudaida tana kallan yadda yake yi cikin sauri da k'warewa.

Julaibib yashigo da sallama,yana sanye da babbar riga,'yar ciki da wando na farin voil,takalminshi sau ciki da hular dara bak'a, k'amshin arabi'an perfume d'inshi ya cika tsakar gidan kamar lokacin yake fesawa, gyaran fuskar dayayi sai yak'ara mishi kyau"har ka cire kwalliyar sallar?Ba dole ba autan Inna,zanyi aikin fid'a da farar shadda ne?Zai shiga d'akin Hajiya yace "ka daiyi sauri kagama dan ga na Inna can yana jiranka.Tabi bayan shi zuwa d'akin.

"Happy Eid-eel Fitr sarauniyar Sinan.
Chapter 38 · 0% Book details