Sashe 50
Gwajin Dafi Complete Hausa Novel · about 8 min read
Gajiyace da samun waje wai kuturu da gad'a,bayan ta gama shan raken bacci yafara kawoma idanun ta ziyara.Hajiya tatashe ta,tamik'e zaune tana mitstsik'e idanu"Hajiya lafiya?Tagyad'a kai"lafiya k'alau,kishiga d'aki ki kwanta a gado mana.Takalli agogon dayake d'aure a hannunta nadama tad'an yi tsaki"lokaci ya ja sosai,sai tamik'e tanasa hijab,tad'auki jakarta tara taya "Hajiya gwamma in tafi gida yamma tayi sosai. Hajiya tace shikenan sauka lafiya,sukayi sallama tatafi.
Bayan sallar Isha'i tana zaune tana nazarin littafan data barbaza akan daddumar datayi sallah, hankalinta yayi nisa akan karatun kamar a sama taji an maida k'ofar D'akin-shak'atawa an rufe,ba tare dataji motsin shigowa ba,tamik'e dasauri kamar za ta hantsila littafin hannunta yafad'i k'asa,tarintse idanun ta tana Istirja'i zuciyarta tana bugawa da k'arfi saboda tsoro, d'akin yayi tsit ba motsin kome sai karar agogon bango tik tik tik...Tasake kasa kunne,nan ma shiru bataji kome ba,sai tabud'e idanun ta wato kawai tsorata tayi?Takad'a kai"wallahi mutum rahama ne,yanzu ma dan dare yayi ne amma da gidan Inna za ta tafi,ALLAH yakaimu gobe na daina kwana ni kad'ai.Caraf idanun su yahad'u,yana tsaye nad'e da hannayenshi a k'irji, kafad'ar shi tadama rataye da jakar matafiya ruwan toka,yayi sharrr...dashi cikin farin yadi da farar hula zita.Tanunashi da yatsa"Yaya D'ansarai kaine da gaske ko kuma gizo ne?Yak'arasa kujera yazauna "matsoraciya kawai,to da gaske ni d'inne.
Tasauke numfashi"wai ALLAH to sannu da zuwa,sai kuma tad'an turo baki gaba"amma gaskiya ka tsora tani,kuma d'azu munyi waya amma baka fad'amin yau zaka dawo ba?Nasamu sarari ne shi yasa nace yau kome dare sai nazo na ga Zaujatiii...Takawo mishi ruwa da lemu,yad'auki ruwan yanasha yana mata kallan nazari ta dad'a ramewa.Ya ajiye kofin yarik'ota"Zaujatiii...me yake damun kine? Tad'ago kai takalleshi kamar bata ji ba"na'am me kace?Sai kuma tagirgiza kai"ni ba abinda yake damuna,tamik'e barin maka abinci me sauk'i ko yar dafadukar taliyace... yabita da kallo bawai jikin na ta yake k'arema kallo ba,a ah tunanin irin ramar datayi kawai yakeyi,kuma acewarta wai ba kome?
Yatashi yabita"ni fa bazanci wata taliya da daddaren nan ba gaskiya.To me zaka ci? Yakar6i albasar da take 6arewa ya mayar ma'ajiyarta"dafamin shayi kawai.Tayamutsa fuska "shayi dai shayi dai?Taturo baki gaba"nima gaskiya baza ka sha wani bak'in ruwa da daddaren nan ba,kai baka gajiya da shayi kamar wani d'an Niger?Yayi yar dariya"bari sujiki ba ruwa na,ke dan baki san sirrin da yake cikin wannan shayin nasu bane da neman shi zaki dingayi ruwa a jallo.
Takyalkyale da dariya"ALLAH yasauwake in nemi shayin da ba madara.Hum yarinya baki san amfanin wad'annan ganyayyakin bane. Takalleshi"toh meye amfanin su?Yagirgiza kai"zan fad'a miki amma ba yanzu ba.Sai yaushe?Sai lokacin dana koya miki sha,idan nafad'a miki amfanin nasu zaki yadda dani d'ari bisa d'ari dan kinji a jikinki,amma yanzu idan nafad'a miki,ba lallai ne kiyadda ba"gani ya kori ji.Tashagwa6e ni dai tunda baza kaci taliya ba to kaima baka shan shayin sai dai muje kaci donut da yoghort.Yarik'o hannunta"na yadda muje.
Dasafe tafito tsab cikin shigar kamala da mutunta kai"Tazauna a hannun kujerar da yake"Yaya D'ansarai taso ka kaini na kusa makara.Batare daya d'ago yakalle taba yanuna mata abinci"zauna ki karya kafin in gama abinda nake yi asibiti zamuje a miki General-check up. Tabishi da kallo cikin mad'aukakin mamaki"asibiti kuma? Tagirgiza kai ni dai gaskiya lafiya ta k'alau ba abinda yake damuna.Yad'ago yakalleta a gajerce yacigaba da danna na'ura me k'wak'walwa"kizauna kici abinci nace ko?
Ni fa banajin yunwa kuma ai...sai yad'aga mata hannu ya isa.Duk sukayi shiru nawucewar wasu dak'ik'u,tasake kallanshi"Yaya D'ansarai zan makara fa.Yayi kamar baiji abinda take fad'a ba.Haushi yakamata tamik'e tsaye"ni na tafi.Nan ma shiru yayi.Tajuya tayi tafiyarta tana surutai"da baka sa min rai ba da tuntuni banyi tafiya taba?Dama ai na saba tafiya ni kad'ai, ALLAH yasauwak'e maka wannan halin.
Da yamma tadawo daga makaranta a gajiye,ba abinda take buk'atar yi sai bacci danko jiya ba wani baccin kirki tayi ba Julaibib ya hanata sakattt...Tana shawo kwanar gidan su tahango wata mota me d'aukar hankali fara karrr...sai d'aukar idanu takeyi a cikin hasken rana,wata kyakkyawar macece me garin jiki wankan tarwad'a tabud'e motar tafito tanama Sudaida sallama. Sudaida ta amsa sannan suka gaisa a takaice... tacigaba da tafiyarta,matar tace"Dan ALLAH jimana "tajuyo tad'an kalleta sai ta matsa kusa da ita,matar tagyara farin medicated glass d'in data rufe idanun ta. Takalleta sama da k'asa wani murmushi yasu6uce mata,tanunata da yatsa "Sudaida ko?Sudaida tad'ago suka kalli juna,sai ta gyad'a kai kawai dan bata san a ina matar tasanta har tasan sunan taba.
Toh kiyi hak'uri na tsayar dake ba tare da kin san koni wacece ba,ina fata mijinki D'ansarai yafad'a miki zuwa na?Tak'ara kallan matar"wallahi ba k'arya hutu ya gama ratsata,ido ba muduba amma ai yasan kima,kayan jikinta na alfarma,a inda Sudaida taji dama-dama wai kibiya a cikin idanu shine shigar sanin darajar kai tayi harda hijab d'inta tsawonshi yawuce gwiwa da kad'an,tarasa amsar da zata bata tunda Julaibib bai mata maganar wata za tazoba gaskiya,sai tayi murmushi tana gyad'a kai"sannu da zuwa,toh bismillah "suka jera suna tafiya har tabud'e D'akin-shak'awa tanuna mata wajen zama taje takawo mata abin motsa baki suka sake gaisawa sannan tamik'e"bari a mishi magana.
Suka kalli juna yana mata wannan rikitaccen kallan nashi da bata so dan haushi yake bata,yafito daga wanka yana shafa mai.Yaya Julaibib wani irin mutum ne me tsatstsauran ra'ayi da baza ka ta6a gane inda yadosa kai tsaye ba a wasu lokutan."kayi bak'uwa. Fuskarshi ba walwala "wacece ita da baki san sunan taba? Tajuya"oho nima a ina nasan ta,kafito ka ganta mana ganin idanun ka.Sai da yagama shiryawa sannan yafito, yana ganinta yasaki fuskar shi yana mata barka da zuwa, yazauna suna gaisawa da tambayar me jiki."jiki Alhamdulillahi.Ni da Baban Humaima ne yana mota. Yafita yashigo dashi..
"Doctor Garga Ibrahim Manogi "babban likitane da ake ji dashi a Teaching Hospital na Zaria,k'wararre ne akan abinda yashafi k'wak'walwa(Neurology) likitan da akace sune ma idan sunje Shika lokacin da Bilkisu tayi hatsari, shine yake auren kanwar Innar Bilkisu.
Sudaida takawo musu abinci.Doctor Manogi yanaci yad'ago yana kallansu"gaskiyar magana abincin nan yayi d'an karen d'and'anon daya burgeni,kai Ustazu haka yake kiran Julaibib dole za kayi tumbi kwanan nan,yakalli Sudaida"kin gane ko idan ya6ata miki rai karki hana shi kome da yake so sai wannan Palatable girkin na ki tunda shi baya san cin abincin waje kinga ai kin horashi duk da ya iya dafawa amma dai kafin yadafa ai ya d'and'ana ko?Sukayi dariya.Doctor Manogi haka ALLAH yayi shi da sauk'in hali da raha sai yanayin shi yamata shige dana Yaya Aminu.Yakalli matar shi"Bongel Ustazu da matar shi basu burge kiba?Tayi murmushi"sun burgeni musamman ita, kaga bata sanni ba amma har tabarni nashigo mata gida duk da taji na ambaci sunan mijin ta,ka san wasu matan da kishin rashin hankali. Yad'an harareta"toh waya fad'a miki bata kishin shi? Kawai ta hak'urane dan ta san itace kad'ai a zuciyar shi, kin san jiya muna tare dashi bayan sallar magriba sai kawai yace min wai gida za shi,nayi-nayi dashi yabari yau mu bugo sammako amma yanok'e"wai ai yau d'in da sassafe zai dawo,amma kinga d'an rainin hankali gashi nan a zaune har bayan la'asar.Julaibib yasa hannu yana shafa kwantaccen bak'in gashin kanshi yana murmushi.
Bongel tad'an kalli Julaibib"ina son ganin Adnan Ibrahim Me-Lambu inji abinda yahana shi dawowa makaranta yayi B.ed d'in shi. Ai Adnan ya san dad'in kud'i ya zama d'an kasuwa kwanaki na mishi magana yace wai shi bazai iyaba wanda yayi abaya ALLAH amfana.Tace kash...na mishi sha'awar karatun saboda yaron yanada k'ok'ari yana d'aya daga cikin d'alibaina yan gaban goshi. Da muna magana ta waya daga baya na daina samun shi. Eh wayar tashice tafad'i yanzu wani sabon layine dashi.Ai ko zaka bani zamu muyi magana...
Sai yanzu Sudaida ta fahimci wacece ita.Bongel Lecturer ce,yaren turanci (English) take koyarwa a FCE Zaria,lokacin da Adnan yake karatu tasha jin sunan Malama Bongel a bakinshi da irin kirkinta,da taimakonta ga d'alibai,bata san d'alibai wad'anda basu da himma,tafi matsa ma irinsu da yawan tambayoyi dan zaburar dasu, masu san karatun suna zage dantse ko dan kar susha kunya a gaban d'umbun jama'a yan uwanshi d'alibai,yan abi yarima asha kid'a,yan kyalekyale suna adawa da irin halaiyarta musamman na zuwa musu aji a bazata ta na musu jarabawar gwaji,irin su Adnan a lokacin sune yan gaba gaba,baya yadda yarasa laccanta sai da dalili me k'arfi.Malama Bongel ALLAH yabata k'warewa da juriyar koyarwa,ga kuma ilmin tsurar shi Ubangiji me kyauta da k'ari ya ba ta,babban kuma abinda yak'ara mata farin jini shine bata kada d'alibai a jarabawarta (carry over)
Sunyi sabo da Adnan,saboda wani ciwo da yayi taje gaishe shi anan take tambayar shi d'an wani gari ne?Yafad'a mata Zonkwa,tayi murmushi kace kai d'an gidane,shikenan dazarar anyi hutu zata ba shi sak'o yakaima Innar Bilkisu a garin Matsirga,kanwartace uwa d'aya uba d'aya.A wasu lokutan ma takan ai ko shi takanas da kud'in mota yakai mata sak'o yakoma Zari'a a ranar. Malama Bongel tana da sauk'in kai,ba ta d'agawa da ilmin da take dashi,sai dai tana fama da ciwon idanu,tasha wahala dan akwai lokacin data ajiye aikin koyarwa saboda kome sai da lafiya akeyi, cutar glaucoma tayi mugun kamata,sai da suka tashi tsaye sannan tasamu lafiya,suka kuma ba ta medicated glass da take amfani dashi.
Sudaida tasake kallanta cikin zancen zuci"kowani d'an Adam tara yake bai cika goma ba,kowa da irin tashi matsalar.Wato wannan zuwan kuma Innarsu Bilkisu ce ba ta da lafiya kenan,dan dasafe taji Julaibib yana tambayar mai jiki tawaya lokacin datake shiryawa,sai dai bata tambayeshi waye ba lafiya ba,shima bai fad'a mata ba,dan idan bai ga damaba ko ta tambaye shi,shiru zai mata kamar baiji ba.
Shi kuma Julaibib sun had'u da Doctor Manogi ne a wani taran MSSN da akayi a jahar Taraba,sun fito sallah dan Julaibib shi yamusu limanci,suna yar hira yake tambayar shi shi d'an wani gari ne?Yafad'a mishi Zonkwa amma a Zari'a yake zama a halin yanzu dan shi d'alibine a jami'ar Ahmadu Bello.Doctor Manogi yanuna shi da yatsa"kar dai kai ne D'ansarai sarauyin wata Bilkisu data rasu?Yajijjiga kai"eh ni ne.Yace ALLAHU-AKBAR yamishi ta'aziyya sannan shima yamishi bayanin ko shi waye...daga nan hira ta 6alle har suka dawo Zari'a suka cigaba da mutunci da zumunci.
Bayan sallar Isha'i tana zaune tana nazarin littafan data barbaza akan daddumar datayi sallah, hankalinta yayi nisa akan karatun kamar a sama taji an maida k'ofar D'akin-shak'atawa an rufe,ba tare dataji motsin shigowa ba,tamik'e dasauri kamar za ta hantsila littafin hannunta yafad'i k'asa,tarintse idanun ta tana Istirja'i zuciyarta tana bugawa da k'arfi saboda tsoro, d'akin yayi tsit ba motsin kome sai karar agogon bango tik tik tik...Tasake kasa kunne,nan ma shiru bataji kome ba,sai tabud'e idanun ta wato kawai tsorata tayi?Takad'a kai"wallahi mutum rahama ne,yanzu ma dan dare yayi ne amma da gidan Inna za ta tafi,ALLAH yakaimu gobe na daina kwana ni kad'ai.Caraf idanun su yahad'u,yana tsaye nad'e da hannayenshi a k'irji, kafad'ar shi tadama rataye da jakar matafiya ruwan toka,yayi sharrr...dashi cikin farin yadi da farar hula zita.Tanunashi da yatsa"Yaya D'ansarai kaine da gaske ko kuma gizo ne?Yak'arasa kujera yazauna "matsoraciya kawai,to da gaske ni d'inne.
Tasauke numfashi"wai ALLAH to sannu da zuwa,sai kuma tad'an turo baki gaba"amma gaskiya ka tsora tani,kuma d'azu munyi waya amma baka fad'amin yau zaka dawo ba?Nasamu sarari ne shi yasa nace yau kome dare sai nazo na ga Zaujatiii...Takawo mishi ruwa da lemu,yad'auki ruwan yanasha yana mata kallan nazari ta dad'a ramewa.Ya ajiye kofin yarik'ota"Zaujatiii...me yake damun kine? Tad'ago kai takalleshi kamar bata ji ba"na'am me kace?Sai kuma tagirgiza kai"ni ba abinda yake damuna,tamik'e barin maka abinci me sauk'i ko yar dafadukar taliyace... yabita da kallo bawai jikin na ta yake k'arema kallo ba,a ah tunanin irin ramar datayi kawai yakeyi,kuma acewarta wai ba kome?
Yatashi yabita"ni fa bazanci wata taliya da daddaren nan ba gaskiya.To me zaka ci? Yakar6i albasar da take 6arewa ya mayar ma'ajiyarta"dafamin shayi kawai.Tayamutsa fuska "shayi dai shayi dai?Taturo baki gaba"nima gaskiya baza ka sha wani bak'in ruwa da daddaren nan ba,kai baka gajiya da shayi kamar wani d'an Niger?Yayi yar dariya"bari sujiki ba ruwa na,ke dan baki san sirrin da yake cikin wannan shayin nasu bane da neman shi zaki dingayi ruwa a jallo.
Takyalkyale da dariya"ALLAH yasauwake in nemi shayin da ba madara.Hum yarinya baki san amfanin wad'annan ganyayyakin bane. Takalleshi"toh meye amfanin su?Yagirgiza kai"zan fad'a miki amma ba yanzu ba.Sai yaushe?Sai lokacin dana koya miki sha,idan nafad'a miki amfanin nasu zaki yadda dani d'ari bisa d'ari dan kinji a jikinki,amma yanzu idan nafad'a miki,ba lallai ne kiyadda ba"gani ya kori ji.Tashagwa6e ni dai tunda baza kaci taliya ba to kaima baka shan shayin sai dai muje kaci donut da yoghort.Yarik'o hannunta"na yadda muje.
Dasafe tafito tsab cikin shigar kamala da mutunta kai"Tazauna a hannun kujerar da yake"Yaya D'ansarai taso ka kaini na kusa makara.Batare daya d'ago yakalle taba yanuna mata abinci"zauna ki karya kafin in gama abinda nake yi asibiti zamuje a miki General-check up. Tabishi da kallo cikin mad'aukakin mamaki"asibiti kuma? Tagirgiza kai ni dai gaskiya lafiya ta k'alau ba abinda yake damuna.Yad'ago yakalleta a gajerce yacigaba da danna na'ura me k'wak'walwa"kizauna kici abinci nace ko?
Ni fa banajin yunwa kuma ai...sai yad'aga mata hannu ya isa.Duk sukayi shiru nawucewar wasu dak'ik'u,tasake kallanshi"Yaya D'ansarai zan makara fa.Yayi kamar baiji abinda take fad'a ba.Haushi yakamata tamik'e tsaye"ni na tafi.Nan ma shiru yayi.Tajuya tayi tafiyarta tana surutai"da baka sa min rai ba da tuntuni banyi tafiya taba?Dama ai na saba tafiya ni kad'ai, ALLAH yasauwak'e maka wannan halin.
Da yamma tadawo daga makaranta a gajiye,ba abinda take buk'atar yi sai bacci danko jiya ba wani baccin kirki tayi ba Julaibib ya hanata sakattt...Tana shawo kwanar gidan su tahango wata mota me d'aukar hankali fara karrr...sai d'aukar idanu takeyi a cikin hasken rana,wata kyakkyawar macece me garin jiki wankan tarwad'a tabud'e motar tafito tanama Sudaida sallama. Sudaida ta amsa sannan suka gaisa a takaice... tacigaba da tafiyarta,matar tace"Dan ALLAH jimana "tajuyo tad'an kalleta sai ta matsa kusa da ita,matar tagyara farin medicated glass d'in data rufe idanun ta. Takalleta sama da k'asa wani murmushi yasu6uce mata,tanunata da yatsa "Sudaida ko?Sudaida tad'ago suka kalli juna,sai ta gyad'a kai kawai dan bata san a ina matar tasanta har tasan sunan taba.
Toh kiyi hak'uri na tsayar dake ba tare da kin san koni wacece ba,ina fata mijinki D'ansarai yafad'a miki zuwa na?Tak'ara kallan matar"wallahi ba k'arya hutu ya gama ratsata,ido ba muduba amma ai yasan kima,kayan jikinta na alfarma,a inda Sudaida taji dama-dama wai kibiya a cikin idanu shine shigar sanin darajar kai tayi harda hijab d'inta tsawonshi yawuce gwiwa da kad'an,tarasa amsar da zata bata tunda Julaibib bai mata maganar wata za tazoba gaskiya,sai tayi murmushi tana gyad'a kai"sannu da zuwa,toh bismillah "suka jera suna tafiya har tabud'e D'akin-shak'awa tanuna mata wajen zama taje takawo mata abin motsa baki suka sake gaisawa sannan tamik'e"bari a mishi magana.
Suka kalli juna yana mata wannan rikitaccen kallan nashi da bata so dan haushi yake bata,yafito daga wanka yana shafa mai.Yaya Julaibib wani irin mutum ne me tsatstsauran ra'ayi da baza ka ta6a gane inda yadosa kai tsaye ba a wasu lokutan."kayi bak'uwa. Fuskarshi ba walwala "wacece ita da baki san sunan taba? Tajuya"oho nima a ina nasan ta,kafito ka ganta mana ganin idanun ka.Sai da yagama shiryawa sannan yafito, yana ganinta yasaki fuskar shi yana mata barka da zuwa, yazauna suna gaisawa da tambayar me jiki."jiki Alhamdulillahi.Ni da Baban Humaima ne yana mota. Yafita yashigo dashi..
"Doctor Garga Ibrahim Manogi "babban likitane da ake ji dashi a Teaching Hospital na Zaria,k'wararre ne akan abinda yashafi k'wak'walwa(Neurology) likitan da akace sune ma idan sunje Shika lokacin da Bilkisu tayi hatsari, shine yake auren kanwar Innar Bilkisu.
Sudaida takawo musu abinci.Doctor Manogi yanaci yad'ago yana kallansu"gaskiyar magana abincin nan yayi d'an karen d'and'anon daya burgeni,kai Ustazu haka yake kiran Julaibib dole za kayi tumbi kwanan nan,yakalli Sudaida"kin gane ko idan ya6ata miki rai karki hana shi kome da yake so sai wannan Palatable girkin na ki tunda shi baya san cin abincin waje kinga ai kin horashi duk da ya iya dafawa amma dai kafin yadafa ai ya d'and'ana ko?Sukayi dariya.Doctor Manogi haka ALLAH yayi shi da sauk'in hali da raha sai yanayin shi yamata shige dana Yaya Aminu.Yakalli matar shi"Bongel Ustazu da matar shi basu burge kiba?Tayi murmushi"sun burgeni musamman ita, kaga bata sanni ba amma har tabarni nashigo mata gida duk da taji na ambaci sunan mijin ta,ka san wasu matan da kishin rashin hankali. Yad'an harareta"toh waya fad'a miki bata kishin shi? Kawai ta hak'urane dan ta san itace kad'ai a zuciyar shi, kin san jiya muna tare dashi bayan sallar magriba sai kawai yace min wai gida za shi,nayi-nayi dashi yabari yau mu bugo sammako amma yanok'e"wai ai yau d'in da sassafe zai dawo,amma kinga d'an rainin hankali gashi nan a zaune har bayan la'asar.Julaibib yasa hannu yana shafa kwantaccen bak'in gashin kanshi yana murmushi.
Bongel tad'an kalli Julaibib"ina son ganin Adnan Ibrahim Me-Lambu inji abinda yahana shi dawowa makaranta yayi B.ed d'in shi. Ai Adnan ya san dad'in kud'i ya zama d'an kasuwa kwanaki na mishi magana yace wai shi bazai iyaba wanda yayi abaya ALLAH amfana.Tace kash...na mishi sha'awar karatun saboda yaron yanada k'ok'ari yana d'aya daga cikin d'alibaina yan gaban goshi. Da muna magana ta waya daga baya na daina samun shi. Eh wayar tashice tafad'i yanzu wani sabon layine dashi.Ai ko zaka bani zamu muyi magana...
Sai yanzu Sudaida ta fahimci wacece ita.Bongel Lecturer ce,yaren turanci (English) take koyarwa a FCE Zaria,lokacin da Adnan yake karatu tasha jin sunan Malama Bongel a bakinshi da irin kirkinta,da taimakonta ga d'alibai,bata san d'alibai wad'anda basu da himma,tafi matsa ma irinsu da yawan tambayoyi dan zaburar dasu, masu san karatun suna zage dantse ko dan kar susha kunya a gaban d'umbun jama'a yan uwanshi d'alibai,yan abi yarima asha kid'a,yan kyalekyale suna adawa da irin halaiyarta musamman na zuwa musu aji a bazata ta na musu jarabawar gwaji,irin su Adnan a lokacin sune yan gaba gaba,baya yadda yarasa laccanta sai da dalili me k'arfi.Malama Bongel ALLAH yabata k'warewa da juriyar koyarwa,ga kuma ilmin tsurar shi Ubangiji me kyauta da k'ari ya ba ta,babban kuma abinda yak'ara mata farin jini shine bata kada d'alibai a jarabawarta (carry over)
Sunyi sabo da Adnan,saboda wani ciwo da yayi taje gaishe shi anan take tambayar shi d'an wani gari ne?Yafad'a mata Zonkwa,tayi murmushi kace kai d'an gidane,shikenan dazarar anyi hutu zata ba shi sak'o yakaima Innar Bilkisu a garin Matsirga,kanwartace uwa d'aya uba d'aya.A wasu lokutan ma takan ai ko shi takanas da kud'in mota yakai mata sak'o yakoma Zari'a a ranar. Malama Bongel tana da sauk'in kai,ba ta d'agawa da ilmin da take dashi,sai dai tana fama da ciwon idanu,tasha wahala dan akwai lokacin data ajiye aikin koyarwa saboda kome sai da lafiya akeyi, cutar glaucoma tayi mugun kamata,sai da suka tashi tsaye sannan tasamu lafiya,suka kuma ba ta medicated glass da take amfani dashi.
Sudaida tasake kallanta cikin zancen zuci"kowani d'an Adam tara yake bai cika goma ba,kowa da irin tashi matsalar.Wato wannan zuwan kuma Innarsu Bilkisu ce ba ta da lafiya kenan,dan dasafe taji Julaibib yana tambayar mai jiki tawaya lokacin datake shiryawa,sai dai bata tambayeshi waye ba lafiya ba,shima bai fad'a mata ba,dan idan bai ga damaba ko ta tambaye shi,shiru zai mata kamar baiji ba.
Shi kuma Julaibib sun had'u da Doctor Manogi ne a wani taran MSSN da akayi a jahar Taraba,sun fito sallah dan Julaibib shi yamusu limanci,suna yar hira yake tambayar shi shi d'an wani gari ne?Yafad'a mishi Zonkwa amma a Zari'a yake zama a halin yanzu dan shi d'alibine a jami'ar Ahmadu Bello.Doctor Manogi yanuna shi da yatsa"kar dai kai ne D'ansarai sarauyin wata Bilkisu data rasu?Yajijjiga kai"eh ni ne.Yace ALLAHU-AKBAR yamishi ta'aziyya sannan shima yamishi bayanin ko shi waye...daga nan hira ta 6alle har suka dawo Zari'a suka cigaba da mutunci da zumunci.