Sashe 53
Gwajin Dafi Complete Hausa Novel · about 8 min read
Facebook:سودة ا.باب
Facebook:Bilkisu Ibrahim Bilkisu Ibrahim
Email:[email protected]
23 Jumaada Thani 1441
17 February 2020
We Ibrahim's Daughters👇
Asdilat KD...2geda with Ra'ibs.
DANGIN NONO WRITERS ASSOCIATION
{Da Inganci Mukayi Fintinkau}
Bismillahi wabihi nasta'in
...GWAJI DAFI💔
Almost true story
Daga alk'alamin🖊
Ya'yan Ibrahim
Saudat A.Baba ( Aadilat KD)
Da
Bara'atu Ibrahim (Ra'ibs)
Shafi na ashirin da d'aya.
Dasafe yayi wanka yana sanye da yadi ruwan madara mara nauyi,yayi lamooo a cikin kujera.Tashigo da sallama tabi kayan abincin da kallo yana nan yadda ta ajiye"Yaya Julaibib har yanzu baka karya ba? Yagyara zama"na d'an sha kunun gyad'an, ina jin bakina ba d'and'ano ne.Tad'ago tana mishi kallan tuhuma bayan ta bud'e kofin"na ce bakaji sauk'iba ka ce ba haka ba,yanzu wannan kunnun an sha shi kenan?Kur6a d'aya kayi ko? Yad'anyi murmushi"afwan Zaujatiii...zan sha anjima.A hankali yamik'e"barin je gidan Inna ko za kimin rakiya?Uh uh adawo lafiya.ALLAH yasa.Ta amsa da amin tabi bayanshi da kallo wata irin k'auna da tausayin shi suka tsirga ilahirin gangar jiki da zuciyarta,bata ta6a ganinshi a irin wannan yanayin na daren jiya ba.Tasauke gwauran numfashi"Ubangiji yasa kaffarace Yaya D'ansarai nah... Takoma D'akin-girki tak'arasa ayyukanta sannan taje tayi wanka ta shirya cikin shigar mutunci da sanin kimar kai kamar ko yaushe tatafi makaranta.
Bayan sallar Isha'i yashigo yana kallanta, itama ta idar da sallah tana azkar,tagama ta mishi sannu da zuwa zata cire hijab yarik'o ta"bar hijab d'in ki muje kimin rakiya gidan Hajiya d'azu ban samu na shiga ba, muna ta hidimar jama'a a shago.Tad'an turo baki gaba"a hakan da ba ka da lafiya me makon kadawo gida kayi kwanciyar ka,kaima kahuta ma ranka?Ai naji sauk'i. Tazuba mishi idanu nawasu yan dak'ik'u sannan tace"tun safe har zuwa yanzu me kaci?Na sha shayi a gidan Inna. Tad'an harareshi"shayi dai shayi dai ai sai kaje kayi ta sha, toh yanzu ga abincin dare na jiranka muje kaci sai mutafi gidan Hajiyan.Yagirgiza kai"bari mu dawo sai in ci yanzu banajin yunwa.
Hajiya tana shan dabgen bindin sa suka shigo da sallama.Sudaida tasa hannu wai wai wai gaskiya matar nan kina sha'aninki wallahi,tagalla mata harara"kema wa yahanaki na ki sha'anin? Sakarya kanki kawai kika sani,toh maza d'auki faranti ki zubama mijin naki mana.Yad'aga hannu"a ah barshi kawai Sudaida bazan iya ciba.Suka zuba mishi idanu"har yanzu jikin ne Julaibibi? Hajiya ta tambaye shi.A ah naji sauk'i Alhamdulillahi.
Ganin ya sake anata hira yasa suka saki ransu.Hajiya ta ajiye tsinken data gama sakacen naman daya mak'ale mata a hak'ori"to ko wannan zirga-zirga da kukeyi ai dole yakarar daku daga kai har matar taka,duk da yanzu na ga tafara sabawa, tana maida jikinta a hankali.Yad'anyi murmushi yana kallan Sudaida"ai Insha-ALLAH zirga-zirgan zai ragu dan an d'aukeni koyarwa a Gidan-Waya, farkon wata me kamawa zan fara zuwa.Hajiya tafad'ad'a murmushinta zuwa dariya"kai Masha-ALLAH...Wow Congratulations.
Suka kyalkyale da dariya"Hajjaju makkatan ashe dai baki manta karatun ba?Inji Sudaida.Tamata dakuwa"ungo nan,mu turancin muma gangariya turawa yan misionaries su suka koya mana baki da baki.Toh Hajiya kingama aji bakwai d'in danaji ance anayi a zamanin da amma bakiyi aikin gwamnati ba?Oh oh k'arya ciwo aji hud'u nayi Baba ALLAH yajik'anshi da rahama yamin aure.Sudaida takalleta cikin natsuwa"toh kema nan kunyi soyayya ke da mijin naki?Hajiya tafara tafa hannaye cikin salati da sallallami.
Sudaida tad'an yamutsa fuska "daga tambaya sai ki fara salati.Hajiya tajawo carbi zata shaud'a mata tamik'e dasauri tafita da kwanan da tagama cin dabgen tawanko hannunta sannan tadawo tana kallan Julaibib daya tsaida gwiwoyinshi yasa duka hannayen shi ya rungumesu,tazauna kusa dashi tad'an marairaice" Yaya D'ansarai anya kaji dad'in zaman nan?Yakalleta me kika gani?Kamar kana jin sanyi...Tabbasss sanyin ne yafara ratsashi amma bai nuna ba,sai yamik'ar da k'afafun na shi yasa hannu yana shafa kwantaccen bakin gashin kanshi "ba kome fa.Tagyad'a kai.Hajiya kuma tagalla mata harara "to iyayin yace me?Julaibib yakalli Hajiya "Sudaida fa amaryace kin kuma san amarya bata laifi,idan kina matsa mata to abu me sauk'i ne tayi yajin zuwa gidan nan.
Takad'a kai tana yar dariya ALLAH sarki wacece amaryar? A in da ba amarya dai a kira ta da hakan,to dan ta daina zuwa gidan nan sai me? Sudaida takalle shi"lallai naji da kunnene dan haka Yaya Julaibib tashi mu kama gabanmu wannan farin watan sai yamana illah gwamma dake Hajiya auren ki da gata.Hajiya tagyad'a kai"ba shakka ai wuyanki ya isa yanka.Suka mata sallama tarako su har zaure "ALLAH yamuku albarka nagode,nagode Ubangiji yabamu alheri, yatashe mu lafiya.Amin Hajiya.
Suka jera suna tafiyarsu a hankali suna hira har suka zo gida.Takawo mishi abinci yabud'e yana gani tuwon alkama miyar ku6ewa d'anya,yad'an kalleta a marairaice"Zaujatiii...dare yayi fa...itama ta kalleshi"uhun me yafaru?Yamayar da murfin miyar ya rufe"bai kamata in ci abinci me nauyi da yawa ba tunda kwanciya zan yi.Tayi shiru kamar bataji abinda yafad'a ba.Zaujatiii...ba ki jine?Na ji...amma da kasan baza kaci ba tun farko ai da mun tafima da almajirai suma suci da d'uminshi,takalleshi cikin kulawa"toh yanzu me za kaci?Yasake wani marairaicewa yanata kallanta yak'i magana,ta kyalkyale da dariya dan abin dariya yabata"Yaya D'ansarai wai meye haka kake ta wani kallo na kamar wata bak'uwarka? Me za kacine?Za ki bani abinda nake so?Tana yar dariya tagayd'a kai"ALLAH zan ba ka.To ni dai shayi zaki had'a min kuma dan ALLAH kar kimin mugunta kisa min siga,dan haka take mishi wani lokacin idan ba taso yasha shayin shi kuma ya nace sai yasha.
Angama autan Inna"ke zo nan dawa kikeyi ne? Tashige D'akin-girki da wanda ya tsargu nake yi.Taje tahad'o kofi biyu tamik'a mishi d'aya ta rik'e d'aya yabita da kallan k'arin bayani,tagyad'a kai "tayaka shan abinda kake so zanyi ko ban kyauta bane?Yayi murmushi"kin kyauta mana,tad'ibo donut tabashi amma baici ba haka yasha na shi,itace dai taci guda d'aya suka gama takai kayan D'akin-girki sukaje suka wanke baki sannan sukayi shirin bacci.
Cikin sulusin daren yaketa juyi dan ya kasa bacci,yatashi yazauna,yakoma yakwanta yayi hakan kusan sau biyar,har bacci yafara d'aukeshi yasake tashi zaune yakama kanshi da duka tafukan hannayenshi abin ba sauk'i wai ciwon arna,wani zazzafan zazza6i yarufeshi sai kuma sanyi yafara ratsashi"Sudaida...a hankali yafara kiranta ita kuma baccinta yayi nisa,yakai hannu yana d'an bubbuga k'afarta Sudaida...kamar a mafarki taji kiran tayi juyi sai tasake jin kiran tabud'e idanun ta taganshi jingine da gadon yana cigaba da kiranta,dasauri tamik'e zaune kamar zata hantsila zuciyarta na bugawa da k'arfin gaske tayi Istirja'i"Yaya Julaibib wai meke faruwane?
Wani irin ciwone haka sai cikin dare? Yadamke hannunta gangam Sudaida sanyi nake ji rufeni.Tagyad'a kai" tabbasss garin akwai sanyi ga sanyin farin wata daya haske doron duniya kaafatan, dole mara lafiya yaji sanyi,to amma jikinshi yayi mugun zafi kuma yana jin sanyi to bai kamata kuma a rufe shi da abu me nauyi ba dan ba a so zafin yakoma jikinshi.Yana karkarwa yace"Sudaida rufeni sanyi nake ji,dakyar yayi furucin,tamik'e ta d'auko zanin a tamfa ta rufeshi. Yagirgiza kai"ban daina jin sanyin ba d'auko bargon mana,ta lalla6ashi yakwanta"yanzu zan d'auko kaji?Tarik'o hannunshi"kayi hak'uri Yaya D'ansarai tajik'a k'aramin tawul a ruwa tana fara goge mishi jiki yarik'e tawul d'in tamauuu"kyaleni bana so,kwanta kiyi baccin ki.Takwanta tanata kallanshi har wani baccin wahala yad'aukeshi dan daga ganin yanayin fitar numfashin ka san baya jin dad'i.
Yashigo da sallama yazauna a kujera yana kallanta har ta idar da sallar,ta sunkuyo tana mishi sannu da jiki tana ta6a jikinshi har yanzu da zafi, a ranta tana yaba k'ok'arinshi dakyar yayi alwala saboda ciwon kan bai sake shiba,amma a haka yagangand'a yatafi masallaci dan samun jam'in sallar asubahi"ALLAH gari na dad'a wayewa asibiti zamu tafi,ni ciwo cikin dare tsoro yake bani.Yayi yar dariya"tsoro kikeji kar in mace miki? Sudaida ai ko da rana idan lokaci yayi tafiya zan yi. Tamishi wani kallo dayaji tasirin shi har a zuciya"ni bana san irin wannnan kalaman fa gaskiya,cuta ai ba mutuwa bace, wata kilama ni zan rigaka macewa,ba dai wanda yasan gawar fari"ALLAH dai yasa mucika da kyau da imani.Amin Zaujatiii...yazame yakwanta yanata kallanta tana shige da ficenta har wani bacci yasake awon gaba dashi.
Sai da tagama shiryawa sannan ta tasheshi yaje yayi wanka su tafi asibiti.Yamaida kanshi saman kujera yana kallanta cikin shigar doguwar rigar atamfa da dogon hijab me hannu"ba makaranta za ki tafi bane?Can ne amma sai mun gama da asibiti zan wuce.Yamik'a hannu yakar6i jakarta yasa mata kud'i a ciki yamik'a mata,tasa hannu biyu takar6a tana godiya "ALLAH yak'aro bud'i Yaya Julaibib.Yayi murmushi kawai sannan yamik'e muje in taka miki.Takalleshi kayi wanka dai mutafi ko? A ah naji sauk'i fa ni anjima kad'an ma Kafanchan zan tafi.Takalleshi wani iri kamar za tayi magana sai kuma tayi shiru.
Yau da wuri tadawo sai kawai tawuce gidan Inna suka sha hirar su Inna tamusu faten tsaki sai bayan la'asar tamata sallama takoma gida,tana ganin kiran Julaibib tad'aga a kame sallama kawai tamishi tayi shiru"Zautajiii...kin dawo daga makaranta ko kina can in biya in d'auko ki.A takaice ta amsa"nadawo.Lafiya kuwa?Tasake amsawa da"Uh batare data bud'e baki ba.Baki da lafiya ne najiki wata iri"k'alau nake.Yasauke numfashi"toh shikenan ganinan zuwa.Ta amsa da uhun.
Taje tayi wanka tana zaune a gaban madubi tana kwalliya ya shigo da sallama ta amsa sallamar tare da mishi sannu da zuwa tacigaba da abinda takeyi bata wani damu da ganin shiba,yanad'e hannayen shi a k'irji yana k'are mata kallo,yau ta mishi kyau fiye da kullum,yak'arasa wajen ta da karsashi "Zaujatiii...kinyi kyau fa.Ganin ya d'okantu da ita yasa tad'an tsuke baki kamar me shirin yin fito,kamar bataji abinda yafad'a ba tacigaba da shafama la66anta jambaki ruwan hoda.
Sai yad'ora mata ledar raken a jikinta"ga mutumin ki.Tad'anyi tsaki. Yabita da kallon nazari"tun a waya nakiji wata iri yanzu kuma tsakin me kikeyi Sudaida?ALLAH dai yasa banine na 6ata miki rai ba.Tad'an harareshi tana k'unk'uni.Ke karki sani a uku fa kin san ina k'aunarki.Ganin ta mik'e zata bar d'akin yasa yarik'ota da sauri sannan yakalleta cikin natsuwa"fad'a min laifina zan baki hak'uri,durk'usama wada ba gajiyawa bane.
Facebook:Bilkisu Ibrahim Bilkisu Ibrahim
Email:[email protected]
23 Jumaada Thani 1441
17 February 2020
We Ibrahim's Daughters👇
Asdilat KD...2geda with Ra'ibs.
DANGIN NONO WRITERS ASSOCIATION
{Da Inganci Mukayi Fintinkau}
Bismillahi wabihi nasta'in
...GWAJI DAFI💔
Almost true story
Daga alk'alamin🖊
Ya'yan Ibrahim
Saudat A.Baba ( Aadilat KD)
Da
Bara'atu Ibrahim (Ra'ibs)
Shafi na ashirin da d'aya.
Dasafe yayi wanka yana sanye da yadi ruwan madara mara nauyi,yayi lamooo a cikin kujera.Tashigo da sallama tabi kayan abincin da kallo yana nan yadda ta ajiye"Yaya Julaibib har yanzu baka karya ba? Yagyara zama"na d'an sha kunun gyad'an, ina jin bakina ba d'and'ano ne.Tad'ago tana mishi kallan tuhuma bayan ta bud'e kofin"na ce bakaji sauk'iba ka ce ba haka ba,yanzu wannan kunnun an sha shi kenan?Kur6a d'aya kayi ko? Yad'anyi murmushi"afwan Zaujatiii...zan sha anjima.A hankali yamik'e"barin je gidan Inna ko za kimin rakiya?Uh uh adawo lafiya.ALLAH yasa.Ta amsa da amin tabi bayanshi da kallo wata irin k'auna da tausayin shi suka tsirga ilahirin gangar jiki da zuciyarta,bata ta6a ganinshi a irin wannan yanayin na daren jiya ba.Tasauke gwauran numfashi"Ubangiji yasa kaffarace Yaya D'ansarai nah... Takoma D'akin-girki tak'arasa ayyukanta sannan taje tayi wanka ta shirya cikin shigar mutunci da sanin kimar kai kamar ko yaushe tatafi makaranta.
Bayan sallar Isha'i yashigo yana kallanta, itama ta idar da sallah tana azkar,tagama ta mishi sannu da zuwa zata cire hijab yarik'o ta"bar hijab d'in ki muje kimin rakiya gidan Hajiya d'azu ban samu na shiga ba, muna ta hidimar jama'a a shago.Tad'an turo baki gaba"a hakan da ba ka da lafiya me makon kadawo gida kayi kwanciyar ka,kaima kahuta ma ranka?Ai naji sauk'i. Tazuba mishi idanu nawasu yan dak'ik'u sannan tace"tun safe har zuwa yanzu me kaci?Na sha shayi a gidan Inna. Tad'an harareshi"shayi dai shayi dai ai sai kaje kayi ta sha, toh yanzu ga abincin dare na jiranka muje kaci sai mutafi gidan Hajiyan.Yagirgiza kai"bari mu dawo sai in ci yanzu banajin yunwa.
Hajiya tana shan dabgen bindin sa suka shigo da sallama.Sudaida tasa hannu wai wai wai gaskiya matar nan kina sha'aninki wallahi,tagalla mata harara"kema wa yahanaki na ki sha'anin? Sakarya kanki kawai kika sani,toh maza d'auki faranti ki zubama mijin naki mana.Yad'aga hannu"a ah barshi kawai Sudaida bazan iya ciba.Suka zuba mishi idanu"har yanzu jikin ne Julaibibi? Hajiya ta tambaye shi.A ah naji sauk'i Alhamdulillahi.
Ganin ya sake anata hira yasa suka saki ransu.Hajiya ta ajiye tsinken data gama sakacen naman daya mak'ale mata a hak'ori"to ko wannan zirga-zirga da kukeyi ai dole yakarar daku daga kai har matar taka,duk da yanzu na ga tafara sabawa, tana maida jikinta a hankali.Yad'anyi murmushi yana kallan Sudaida"ai Insha-ALLAH zirga-zirgan zai ragu dan an d'aukeni koyarwa a Gidan-Waya, farkon wata me kamawa zan fara zuwa.Hajiya tafad'ad'a murmushinta zuwa dariya"kai Masha-ALLAH...Wow Congratulations.
Suka kyalkyale da dariya"Hajjaju makkatan ashe dai baki manta karatun ba?Inji Sudaida.Tamata dakuwa"ungo nan,mu turancin muma gangariya turawa yan misionaries su suka koya mana baki da baki.Toh Hajiya kingama aji bakwai d'in danaji ance anayi a zamanin da amma bakiyi aikin gwamnati ba?Oh oh k'arya ciwo aji hud'u nayi Baba ALLAH yajik'anshi da rahama yamin aure.Sudaida takalleta cikin natsuwa"toh kema nan kunyi soyayya ke da mijin naki?Hajiya tafara tafa hannaye cikin salati da sallallami.
Sudaida tad'an yamutsa fuska "daga tambaya sai ki fara salati.Hajiya tajawo carbi zata shaud'a mata tamik'e dasauri tafita da kwanan da tagama cin dabgen tawanko hannunta sannan tadawo tana kallan Julaibib daya tsaida gwiwoyinshi yasa duka hannayen shi ya rungumesu,tazauna kusa dashi tad'an marairaice" Yaya D'ansarai anya kaji dad'in zaman nan?Yakalleta me kika gani?Kamar kana jin sanyi...Tabbasss sanyin ne yafara ratsashi amma bai nuna ba,sai yamik'ar da k'afafun na shi yasa hannu yana shafa kwantaccen bakin gashin kanshi "ba kome fa.Tagyad'a kai.Hajiya kuma tagalla mata harara "to iyayin yace me?Julaibib yakalli Hajiya "Sudaida fa amaryace kin kuma san amarya bata laifi,idan kina matsa mata to abu me sauk'i ne tayi yajin zuwa gidan nan.
Takad'a kai tana yar dariya ALLAH sarki wacece amaryar? A in da ba amarya dai a kira ta da hakan,to dan ta daina zuwa gidan nan sai me? Sudaida takalle shi"lallai naji da kunnene dan haka Yaya Julaibib tashi mu kama gabanmu wannan farin watan sai yamana illah gwamma dake Hajiya auren ki da gata.Hajiya tagyad'a kai"ba shakka ai wuyanki ya isa yanka.Suka mata sallama tarako su har zaure "ALLAH yamuku albarka nagode,nagode Ubangiji yabamu alheri, yatashe mu lafiya.Amin Hajiya.
Suka jera suna tafiyarsu a hankali suna hira har suka zo gida.Takawo mishi abinci yabud'e yana gani tuwon alkama miyar ku6ewa d'anya,yad'an kalleta a marairaice"Zaujatiii...dare yayi fa...itama ta kalleshi"uhun me yafaru?Yamayar da murfin miyar ya rufe"bai kamata in ci abinci me nauyi da yawa ba tunda kwanciya zan yi.Tayi shiru kamar bataji abinda yafad'a ba.Zaujatiii...ba ki jine?Na ji...amma da kasan baza kaci ba tun farko ai da mun tafima da almajirai suma suci da d'uminshi,takalleshi cikin kulawa"toh yanzu me za kaci?Yasake wani marairaicewa yanata kallanta yak'i magana,ta kyalkyale da dariya dan abin dariya yabata"Yaya D'ansarai wai meye haka kake ta wani kallo na kamar wata bak'uwarka? Me za kacine?Za ki bani abinda nake so?Tana yar dariya tagayd'a kai"ALLAH zan ba ka.To ni dai shayi zaki had'a min kuma dan ALLAH kar kimin mugunta kisa min siga,dan haka take mishi wani lokacin idan ba taso yasha shayin shi kuma ya nace sai yasha.
Angama autan Inna"ke zo nan dawa kikeyi ne? Tashige D'akin-girki da wanda ya tsargu nake yi.Taje tahad'o kofi biyu tamik'a mishi d'aya ta rik'e d'aya yabita da kallan k'arin bayani,tagyad'a kai "tayaka shan abinda kake so zanyi ko ban kyauta bane?Yayi murmushi"kin kyauta mana,tad'ibo donut tabashi amma baici ba haka yasha na shi,itace dai taci guda d'aya suka gama takai kayan D'akin-girki sukaje suka wanke baki sannan sukayi shirin bacci.
Cikin sulusin daren yaketa juyi dan ya kasa bacci,yatashi yazauna,yakoma yakwanta yayi hakan kusan sau biyar,har bacci yafara d'aukeshi yasake tashi zaune yakama kanshi da duka tafukan hannayenshi abin ba sauk'i wai ciwon arna,wani zazzafan zazza6i yarufeshi sai kuma sanyi yafara ratsashi"Sudaida...a hankali yafara kiranta ita kuma baccinta yayi nisa,yakai hannu yana d'an bubbuga k'afarta Sudaida...kamar a mafarki taji kiran tayi juyi sai tasake jin kiran tabud'e idanun ta taganshi jingine da gadon yana cigaba da kiranta,dasauri tamik'e zaune kamar zata hantsila zuciyarta na bugawa da k'arfin gaske tayi Istirja'i"Yaya Julaibib wai meke faruwane?
Wani irin ciwone haka sai cikin dare? Yadamke hannunta gangam Sudaida sanyi nake ji rufeni.Tagyad'a kai" tabbasss garin akwai sanyi ga sanyin farin wata daya haske doron duniya kaafatan, dole mara lafiya yaji sanyi,to amma jikinshi yayi mugun zafi kuma yana jin sanyi to bai kamata kuma a rufe shi da abu me nauyi ba dan ba a so zafin yakoma jikinshi.Yana karkarwa yace"Sudaida rufeni sanyi nake ji,dakyar yayi furucin,tamik'e ta d'auko zanin a tamfa ta rufeshi. Yagirgiza kai"ban daina jin sanyin ba d'auko bargon mana,ta lalla6ashi yakwanta"yanzu zan d'auko kaji?Tarik'o hannunshi"kayi hak'uri Yaya D'ansarai tajik'a k'aramin tawul a ruwa tana fara goge mishi jiki yarik'e tawul d'in tamauuu"kyaleni bana so,kwanta kiyi baccin ki.Takwanta tanata kallanshi har wani baccin wahala yad'aukeshi dan daga ganin yanayin fitar numfashin ka san baya jin dad'i.
Yashigo da sallama yazauna a kujera yana kallanta har ta idar da sallar,ta sunkuyo tana mishi sannu da jiki tana ta6a jikinshi har yanzu da zafi, a ranta tana yaba k'ok'arinshi dakyar yayi alwala saboda ciwon kan bai sake shiba,amma a haka yagangand'a yatafi masallaci dan samun jam'in sallar asubahi"ALLAH gari na dad'a wayewa asibiti zamu tafi,ni ciwo cikin dare tsoro yake bani.Yayi yar dariya"tsoro kikeji kar in mace miki? Sudaida ai ko da rana idan lokaci yayi tafiya zan yi. Tamishi wani kallo dayaji tasirin shi har a zuciya"ni bana san irin wannnan kalaman fa gaskiya,cuta ai ba mutuwa bace, wata kilama ni zan rigaka macewa,ba dai wanda yasan gawar fari"ALLAH dai yasa mucika da kyau da imani.Amin Zaujatiii...yazame yakwanta yanata kallanta tana shige da ficenta har wani bacci yasake awon gaba dashi.
Sai da tagama shiryawa sannan ta tasheshi yaje yayi wanka su tafi asibiti.Yamaida kanshi saman kujera yana kallanta cikin shigar doguwar rigar atamfa da dogon hijab me hannu"ba makaranta za ki tafi bane?Can ne amma sai mun gama da asibiti zan wuce.Yamik'a hannu yakar6i jakarta yasa mata kud'i a ciki yamik'a mata,tasa hannu biyu takar6a tana godiya "ALLAH yak'aro bud'i Yaya Julaibib.Yayi murmushi kawai sannan yamik'e muje in taka miki.Takalleshi kayi wanka dai mutafi ko? A ah naji sauk'i fa ni anjima kad'an ma Kafanchan zan tafi.Takalleshi wani iri kamar za tayi magana sai kuma tayi shiru.
Yau da wuri tadawo sai kawai tawuce gidan Inna suka sha hirar su Inna tamusu faten tsaki sai bayan la'asar tamata sallama takoma gida,tana ganin kiran Julaibib tad'aga a kame sallama kawai tamishi tayi shiru"Zautajiii...kin dawo daga makaranta ko kina can in biya in d'auko ki.A takaice ta amsa"nadawo.Lafiya kuwa?Tasake amsawa da"Uh batare data bud'e baki ba.Baki da lafiya ne najiki wata iri"k'alau nake.Yasauke numfashi"toh shikenan ganinan zuwa.Ta amsa da uhun.
Taje tayi wanka tana zaune a gaban madubi tana kwalliya ya shigo da sallama ta amsa sallamar tare da mishi sannu da zuwa tacigaba da abinda takeyi bata wani damu da ganin shiba,yanad'e hannayen shi a k'irji yana k'are mata kallo,yau ta mishi kyau fiye da kullum,yak'arasa wajen ta da karsashi "Zaujatiii...kinyi kyau fa.Ganin ya d'okantu da ita yasa tad'an tsuke baki kamar me shirin yin fito,kamar bataji abinda yafad'a ba tacigaba da shafama la66anta jambaki ruwan hoda.
Sai yad'ora mata ledar raken a jikinta"ga mutumin ki.Tad'anyi tsaki. Yabita da kallon nazari"tun a waya nakiji wata iri yanzu kuma tsakin me kikeyi Sudaida?ALLAH dai yasa banine na 6ata miki rai ba.Tad'an harareshi tana k'unk'uni.Ke karki sani a uku fa kin san ina k'aunarki.Ganin ta mik'e zata bar d'akin yasa yarik'ota da sauri sannan yakalleta cikin natsuwa"fad'a min laifina zan baki hak'uri,durk'usama wada ba gajiyawa bane.