Sashe 18
Gwajin Dafi Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tamik'ama babban katin hannunta, yad'an kalleta da mamaki bayan ya duba katin, sanin Alhaji Hafiz da yayi mutumin kirki me rik'o da addini,dan babban d'an Alhaji Hafiz abokin Kawun sune, to ita kuma wannnan me zak'o-zak'on faratan rumfar shaid'an fa?Kuma ko mayafi babu haka take tafiya kamar wata namiji,a gidan Alhaji Hafiz ma basa mu'amala da kome sai hijab,to kuma meye darin gamanka da ita? Tamabayarka tayi idan ka sani fad'a mata,idan baka sani ba fad'a mata.Zuciyarshi tafad'a mishi haka.sai yagyad'a kai.
Yamik'a mata katin,gidan wanda nasani nake kuma kyautata zatan shine to kinga wancan titin yanuna mata titin da d'an yatsan shi tagyad'a kai tana kallan titin, to kimik'e shi,kwana tafarko zaki shiga,gida na hudu nan ne gidan ai zama kigani idan kika duba katin. Tahad'a tafukan hannayanta"nagode.A ah ba kome yarik'o hannun k'aninshi suka tafi.
Tacigaba da tafiya har tazo gidan me k'atuwar k'ofa ruwan zinare,tayi tsai...na wucewar wasu dak'ik'u,ta kai hannu zata fara rank'washin k'ofar kenan sai gata a bud'e wata farar mota kirar marsandi tana fitowa, yabita da kallo ta cikin madubi,itama shi take kallo, yashiga tunanin a ina yasan wannnan fuskar ne? "Mahaifiyarshi"abinda yafad'omishi kenan daya ga manyan idanunta masu maik'o da yanayin k'irar jikinta,sai yayi ribas tabbas wannan yar'shice,yar d'an uwanshi Kantiok ga kamanni nan,yafito daga motar suna kallan juna,itama tagyad'a kai cikin gamsuwa tabbas wannan dan uwan Baban tane sai dai shi bak'i ne,Babanta kuma fari,yana sanye da dogayan fararan kaya,bak'ar hular dara akanshi da bak'in takalmi,yanata k'amshin turare me sanyin dad'i wajan shak'a.
Tayi yar dariyar murna"Uncle.Yayi murmushi"na'am.Rahab ce ko Kasham ko Judith? Uncle Kasham ce.Masha-ALLAH sannu da zuwa, yakulle motar yazare makullin"to bismillah yanuna mata hanya mushiga ciki,yakar6i trolley d'in har suka shiga wani babban D'akin-shak'atawa me cike da ni'ima,wani sassanyar iska da k'amshin turaran d'aki ya mamaye ko'ina,kome agyara tsab a muhallinshi,tazauna a kujera tare da lumshe idanun ta tana zuk'e k'amshin tana zancen zuci "Lallai Uncle yana jin dad'in shi,tasauke numfashi sannan ta bud'e idanunta, suka kalli juna sai ta d'anji kunya ta kauda kanta gefe.
Yayi murmushi kinsha hanya ai na san kin gaji,yad'auko abinci da ruwa da lemun kwali na biyar a raye (five alive) yamik'a mata kofi,tazuba ruwa tafara sha sannan taci abincin ya kuma mata dad'i taci to k'oshi dan bata wani tsaya bak'unta ba,kad'an tasha lemun ta godema Jesus Christ,Yesu almasihu me ce to.
Saida da tagama suka fara hirar yaushe gamo?Shi dama bai san taba dan tun kafin a haife ta rabonshi da kauyansu Madauci.Ikon ALLAH banyi zaton wani a cikin ku zai zo inda nake ba,wai Kantiok ne da kanshi yafad'a miki inda nake?Tagirgiza kai"a ah ba shi bane,ni nayi ta bincike har naga complementary card d'inka, ni ba ma wanda yasan wajan ka na zo dan na fad'a ma Mama wajan k'awata Tina za ni.
Yayi yar dariya"Dinatu kenan,wato me hali baya fasa halinshi,amma ba abinda yafaru ko?Eh Uncle ba abinda yafaru kowa lafiya.suka cigaba da hirar yan uwa ya tambayeta wannan,ya tambayeta wancan, wata amsar ta bashi dariya, wata kuma tabashi tausayi, wata tambayar kuma tace bata gane ko suwa yake nufi ba,dan tun kan a haife ta fa,har suka gangaro kan yan uwanta.
Alhamdu Ya'yanshi nawa yanzu? Tad'an ta6e baki ita kanta tana dad'ewa bata ganshi ba"ai duk cikinsu Bitrus ne kawai yayi auran majami'a,amma Alhamdu ai gaba d'aya ya koma D one(D'orawa one)yana tsiran naman kare,baka ga yadda ya lalace ba saboda shaye-shayen miyagun k'wayoyi,amma watannin baya budurwar shi ta haihu ta kawo mana yarinyar data haifa mun gani.Yakad'a kai cikin damuwa,wannan irin rayuwa dame tayi kama?
Yakalleta ke kuma na ki Y'ayan guda nawane?Bazaice kaso nawa bisa d'ari ba dan ba shi da k'ididdiga amma dai ya san samun cikakkun 'yan mata(Virgin)a cikinsu,ba masu yawa bane saboda wata irin rayuwar san zuciya,taci barkatai da suka za6a suke yinta cikin kwanciyar hankali.Tagirgiza kai"Uncle ban ta6a haihuwa ba,kuma duk abinda muka yi da Baranzan"I repent"Ya yadda da ita,yajijjiga kai"toh ya karatu kin gama secondary ko anan zaki k'arasa?Ta ajiye kofin lemun a saman tebur sannan ta bud'e jakar hannunta taciro wani babban envelop ruwan k'asa ta mik'a mishi.
Yad'ago cikin mamaki da murmushin jin dad'in ganin sakamokon jarabawar ta na College of Education.Kinyi k'ok'ari kuma na yadda lallai baki tsaya shashanci ba"wai rok'o a gidan bebe"suka cigaba da tattauna al'amura mabambanta har Kasham tafad'a mishi gaba d'aya abinda yakawota.
Yakalleta lallai kin yadda za ki musulunta Kasham?"Eh Uncle na yadda zan musulunta.Yagyad'a kai"To ki sani musulunci yana da sharud'd'a guda biyar duk wanda kika ganshi a cikin musulunci to tabbaci hak'ik'a sai da ya yadda da wad'annan sharud'd'an, Sharad'in farko kuma mafi girma a cikin su shine kalmar shahada.
Shaidawa babu abin bautawa da gaskiya, bisa cancanta sai ALLAH,kuma Annabi Muhammad bawan shine kuma manzan shine.
Ma'anar kalmar {لاإله} tana kore duk wani abin bauta ne koma bayan ALLAH{إلاالله}wannan kuma tana tabbatar da bauta ne ga ALLAH shi kad'ai ba tare da abokin tarayya ba.
Sharud'd'an kalmar shahada kuma sune:
1.Ilimi wanda yake kawar da jahilci.
2.Yak'ini wanda yake kawar da kokwanto.
3.Ikhlasi wanda yake kawar da shirka.
4.Gaskiya wacce take kawar da k'arya.
5.Soyayya wacce take kawar da k'iyayya.
6.Janyuwa wajan yin aiki wacce ke kawar da k'in yin aiki.
7.Yadda wacce ke kawar da juyarwa.
8.Kafircewa da kin yadda da duk wani abin bauta koma bayan ALLAH.
Tare da sanin cikakken bayani danga ne da"Shahdatu anna Muhammadan rasulullah.
Ma'anar kuwa:Gasgata Manzon ALLAH a duk abinda yaba da labari,da yin biyayya ga abinda yayi umarni dashi,da nisantar abin da yaja kunne ko yayi hani dashi,da kuma bautawa ALLAH dai-dai da koyarwarshi.
Bayan wannan sai sauran sharud'd'an musulunci sune Sallah,Azumin watan Ramadan, Zakka ga wanda yake da dukiyar data kai nisabin yin Zakkar,Aikin Hajji ga wanda yasamu iko. Kingane ko?Naga ne Uncle, kuma na yadda da duk abinda kafad'a to yanzun nan za ki kar6i musulunci.
Ashhadu anla'ila ha'illallahu wahdahu laashari kalah...Wa ashhadu anna muhammadan abduhu wara suluhu.Yana fad'a tana fad'a har suka zo k'arshe. Yayi murmushi Alhamdulillahi yanzu kin zama musulma, ALLAH yamiki albarka. Acikin sunayan musulunci da kike ji wanne kike so a dinga kiranki dashi?Tad'anyi jimmm...na wucewar wasu dak'ik'u sannan tace"Uncle Sumayya nake so...Yayi murmushi ALLAHU-AKBAR kin za6i suna me daraja a tarihin addinin musulunci,Sumayya mace ta farko data kar6i addinin musulunci.
Tunda kin zama musulma to akwai wankan shiga musulunci dan haka nake so ki natsu kiga yadda zan kwatanta miki.Yadinga mata bayani dalla-dalla sannan yace ta mishi bayanin yagani inda tayi kuskure ya gyara mata.
"Dafarko tsarki zan fara sau uku,sai in wanke hannayena zuwa mad'aurin agogo sau uku,kurkure baki,shak'a ruwa a hanci da fyacewa sau uku,wanke fuska daga matsirar gashin kai zuwa k'arshen ha6a,daga gefen kunnan dama zuwa gefen kunnan hagu sau uku,wanke hannun dama zuwa gwiwar hannu sai uku,wanke hannun hagu zuwa gwiwar hannu sau uku,shafan kai daga matsirar gashin kai zuwa keya,a kuma dawo dashi da duka tafukan hannaye sau d'aya, sai shafan kunnuwa ciki da waje sau d'aya,wanke k'afar dama saman k'afa da tafin k'afar ko ina ya jike da ruwa zuwa k'wauri ko idan sawu sai an tabbatar ta wanku,ta hagu ma haka za a mata, wannan itace cikakkiyar alwala.
Sannan sai in zuba ruwa a kaina da duka tafukan hannayena in cuccud'a in tabbatar gashin kaina ya jik'e da ruwa,zanyi hakan har sau uku,sai in wanke barin jikina na dama har zuwa tafin k'afar dama,sai in wanke 6arin hagu har zuwa tafin k'afa,sai ingame jikina da ruwan in tabbatar ko ina ya jik'e da ruwa,lungu da sak'on jikina.
Idan kuma na so bayan nayi tsarki sai kawai ingame jikina tun daga kai har zuwa tafin k'afafuna da ruwa in cuccud'a ko ina nanma wanka yayi.Tad'an kalleshi amma Uncle wannan wanka zaifi dad'i a shower(shaya)ko?Yayi murmushi wannan sharhin kine amma ko ba shaya mutum idan yaso zaiyi abinshi.Kin burgeni yadda kika kowa kome dalla-dalla kamar yadda na fad'a miki,da alama zaki fahimci kome a d'an k'ank'anin lokaci.
Wannan wankan shi za kiyi duk lokacin da jinin al'adarki tad'auke,shi za kiyi idan janaba tasa meki, shi za kiyi idan jinin biki yadauke,bambancin dake tsakaninsu kawai wajan niyya ne.
Cikin d'an shakku takalleshi "to Uncle kana ganin Julaibib zai aure ni?Sumayya sanin gaibu sai ALLAH, tunda yafad'a miki ko zakiyi sallah shifa bazai iya auran kiba,amma babban abinda za ki fara yanzu shine addu'a"Allah ai maji rok'on bawane,ba kuma abinda ya gagara a wajan ubangiji".
Yanzu kinga za kiyi wankan tsarki amma dole fa sai kin cire wannan faratan roban(nail fixes)dan a addinin musulunci sa shi haramun ne,tad'auki abin yanke farce tafara k'ok'arin ciresu,data gama yakaita wani d'aki, kishiga kiyi wanka,d'akin yar uwan kice,kome yana zaune a muhallinshi Dammm...Zuciyar ta tabuga saboda irin wannan k'amshin a d'akinsu Julaibib ta ta6a jinshi wallahi ranar data mamayeshi tashiga.Ta tsuke baki kamar zata rufeshi tana zuk'e sassanyar k'amshin tabaki ta hanci tare da lumshe idanunta,tana wata kissima a zuci,wani murmushi ya su6uce mata wucewar dak'ik'u masu yawa, tasauke gwauran numfashi sannan tarage kayan jikinta tashiga wanka.
Yakoma D'akin-shakatawa yazauna, tunanin ya cika k'wak'walwarshi har baiji fitowar taba.Uncle na gama tafad'a lokacin da take k'ok'arin zama,ya kalli agogon dake d:aure a hannunshi lokacin sallar la'asar ya gabato.Yamik'e "zani masallaci,daga nan zan wuce in d'auko mutan gidan,ko kin jini shiru karki damu dan wata kila zamu had'u da cunkuson abubuwan hawa.Ta amsa da"to Uncle a dawo lafiya.Tad'auki wani littafi data gani a saman kujera"Islamic Perspectives On Reproduction, Health ChildBirth Spacing In Nigeria.Tafara karantawa.
Miqdad ne yafara dawowa a sanda rana ta tafi za ta fad'i magriba na shirin kunno kai,ya san ba kowa a gidan shi yasama yatafi da mukulli amma yana ta6a kofar yajita a bud'e,yasa kai cikin murmushi tare da sallama bak'uwar fuskar yagani a kwance tana karanta littafin da ya ajiye a saman kujera jiya da daddare, tamik'e zaune daga kwanciyar da tayi,tajuya inda taji sallamar Dammmm...Zuciyarshi ta buga da suka had'a idanu,Hafsa yake gani a fuskar ta,hatta manyan idanunta masu maik'o irin na Hafsa ne.
Tad'anyi murmushi"Sannu da zuwa. Yagyad'a kai"yauwa.Tanuna mishi kujera"kazauna mana, mutan gidan ba sa nann ne Uncle ya tafi d'auko su.Yasake kallanta jin tace Uncle wannan yar uwarsu ce ta Zonkwa yayi yar dariya sannnan ya zauna"kema sannunki da zuwa,daga Madauci ko?Tagyad'a kai.
Yamik'a mata katin,gidan wanda nasani nake kuma kyautata zatan shine to kinga wancan titin yanuna mata titin da d'an yatsan shi tagyad'a kai tana kallan titin, to kimik'e shi,kwana tafarko zaki shiga,gida na hudu nan ne gidan ai zama kigani idan kika duba katin. Tahad'a tafukan hannayanta"nagode.A ah ba kome yarik'o hannun k'aninshi suka tafi.
Tacigaba da tafiya har tazo gidan me k'atuwar k'ofa ruwan zinare,tayi tsai...na wucewar wasu dak'ik'u,ta kai hannu zata fara rank'washin k'ofar kenan sai gata a bud'e wata farar mota kirar marsandi tana fitowa, yabita da kallo ta cikin madubi,itama shi take kallo, yashiga tunanin a ina yasan wannnan fuskar ne? "Mahaifiyarshi"abinda yafad'omishi kenan daya ga manyan idanunta masu maik'o da yanayin k'irar jikinta,sai yayi ribas tabbas wannan yar'shice,yar d'an uwanshi Kantiok ga kamanni nan,yafito daga motar suna kallan juna,itama tagyad'a kai cikin gamsuwa tabbas wannan dan uwan Baban tane sai dai shi bak'i ne,Babanta kuma fari,yana sanye da dogayan fararan kaya,bak'ar hular dara akanshi da bak'in takalmi,yanata k'amshin turare me sanyin dad'i wajan shak'a.
Tayi yar dariyar murna"Uncle.Yayi murmushi"na'am.Rahab ce ko Kasham ko Judith? Uncle Kasham ce.Masha-ALLAH sannu da zuwa, yakulle motar yazare makullin"to bismillah yanuna mata hanya mushiga ciki,yakar6i trolley d'in har suka shiga wani babban D'akin-shak'atawa me cike da ni'ima,wani sassanyar iska da k'amshin turaran d'aki ya mamaye ko'ina,kome agyara tsab a muhallinshi,tazauna a kujera tare da lumshe idanun ta tana zuk'e k'amshin tana zancen zuci "Lallai Uncle yana jin dad'in shi,tasauke numfashi sannan ta bud'e idanunta, suka kalli juna sai ta d'anji kunya ta kauda kanta gefe.
Yayi murmushi kinsha hanya ai na san kin gaji,yad'auko abinci da ruwa da lemun kwali na biyar a raye (five alive) yamik'a mata kofi,tazuba ruwa tafara sha sannan taci abincin ya kuma mata dad'i taci to k'oshi dan bata wani tsaya bak'unta ba,kad'an tasha lemun ta godema Jesus Christ,Yesu almasihu me ce to.
Saida da tagama suka fara hirar yaushe gamo?Shi dama bai san taba dan tun kafin a haife ta rabonshi da kauyansu Madauci.Ikon ALLAH banyi zaton wani a cikin ku zai zo inda nake ba,wai Kantiok ne da kanshi yafad'a miki inda nake?Tagirgiza kai"a ah ba shi bane,ni nayi ta bincike har naga complementary card d'inka, ni ba ma wanda yasan wajan ka na zo dan na fad'a ma Mama wajan k'awata Tina za ni.
Yayi yar dariya"Dinatu kenan,wato me hali baya fasa halinshi,amma ba abinda yafaru ko?Eh Uncle ba abinda yafaru kowa lafiya.suka cigaba da hirar yan uwa ya tambayeta wannan,ya tambayeta wancan, wata amsar ta bashi dariya, wata kuma tabashi tausayi, wata tambayar kuma tace bata gane ko suwa yake nufi ba,dan tun kan a haife ta fa,har suka gangaro kan yan uwanta.
Alhamdu Ya'yanshi nawa yanzu? Tad'an ta6e baki ita kanta tana dad'ewa bata ganshi ba"ai duk cikinsu Bitrus ne kawai yayi auran majami'a,amma Alhamdu ai gaba d'aya ya koma D one(D'orawa one)yana tsiran naman kare,baka ga yadda ya lalace ba saboda shaye-shayen miyagun k'wayoyi,amma watannin baya budurwar shi ta haihu ta kawo mana yarinyar data haifa mun gani.Yakad'a kai cikin damuwa,wannan irin rayuwa dame tayi kama?
Yakalleta ke kuma na ki Y'ayan guda nawane?Bazaice kaso nawa bisa d'ari ba dan ba shi da k'ididdiga amma dai ya san samun cikakkun 'yan mata(Virgin)a cikinsu,ba masu yawa bane saboda wata irin rayuwar san zuciya,taci barkatai da suka za6a suke yinta cikin kwanciyar hankali.Tagirgiza kai"Uncle ban ta6a haihuwa ba,kuma duk abinda muka yi da Baranzan"I repent"Ya yadda da ita,yajijjiga kai"toh ya karatu kin gama secondary ko anan zaki k'arasa?Ta ajiye kofin lemun a saman tebur sannan ta bud'e jakar hannunta taciro wani babban envelop ruwan k'asa ta mik'a mishi.
Yad'ago cikin mamaki da murmushin jin dad'in ganin sakamokon jarabawar ta na College of Education.Kinyi k'ok'ari kuma na yadda lallai baki tsaya shashanci ba"wai rok'o a gidan bebe"suka cigaba da tattauna al'amura mabambanta har Kasham tafad'a mishi gaba d'aya abinda yakawota.
Yakalleta lallai kin yadda za ki musulunta Kasham?"Eh Uncle na yadda zan musulunta.Yagyad'a kai"To ki sani musulunci yana da sharud'd'a guda biyar duk wanda kika ganshi a cikin musulunci to tabbaci hak'ik'a sai da ya yadda da wad'annan sharud'd'an, Sharad'in farko kuma mafi girma a cikin su shine kalmar shahada.
Shaidawa babu abin bautawa da gaskiya, bisa cancanta sai ALLAH,kuma Annabi Muhammad bawan shine kuma manzan shine.
Ma'anar kalmar {لاإله} tana kore duk wani abin bauta ne koma bayan ALLAH{إلاالله}wannan kuma tana tabbatar da bauta ne ga ALLAH shi kad'ai ba tare da abokin tarayya ba.
Sharud'd'an kalmar shahada kuma sune:
1.Ilimi wanda yake kawar da jahilci.
2.Yak'ini wanda yake kawar da kokwanto.
3.Ikhlasi wanda yake kawar da shirka.
4.Gaskiya wacce take kawar da k'arya.
5.Soyayya wacce take kawar da k'iyayya.
6.Janyuwa wajan yin aiki wacce ke kawar da k'in yin aiki.
7.Yadda wacce ke kawar da juyarwa.
8.Kafircewa da kin yadda da duk wani abin bauta koma bayan ALLAH.
Tare da sanin cikakken bayani danga ne da"Shahdatu anna Muhammadan rasulullah.
Ma'anar kuwa:Gasgata Manzon ALLAH a duk abinda yaba da labari,da yin biyayya ga abinda yayi umarni dashi,da nisantar abin da yaja kunne ko yayi hani dashi,da kuma bautawa ALLAH dai-dai da koyarwarshi.
Bayan wannan sai sauran sharud'd'an musulunci sune Sallah,Azumin watan Ramadan, Zakka ga wanda yake da dukiyar data kai nisabin yin Zakkar,Aikin Hajji ga wanda yasamu iko. Kingane ko?Naga ne Uncle, kuma na yadda da duk abinda kafad'a to yanzun nan za ki kar6i musulunci.
Ashhadu anla'ila ha'illallahu wahdahu laashari kalah...Wa ashhadu anna muhammadan abduhu wara suluhu.Yana fad'a tana fad'a har suka zo k'arshe. Yayi murmushi Alhamdulillahi yanzu kin zama musulma, ALLAH yamiki albarka. Acikin sunayan musulunci da kike ji wanne kike so a dinga kiranki dashi?Tad'anyi jimmm...na wucewar wasu dak'ik'u sannan tace"Uncle Sumayya nake so...Yayi murmushi ALLAHU-AKBAR kin za6i suna me daraja a tarihin addinin musulunci,Sumayya mace ta farko data kar6i addinin musulunci.
Tunda kin zama musulma to akwai wankan shiga musulunci dan haka nake so ki natsu kiga yadda zan kwatanta miki.Yadinga mata bayani dalla-dalla sannan yace ta mishi bayanin yagani inda tayi kuskure ya gyara mata.
"Dafarko tsarki zan fara sau uku,sai in wanke hannayena zuwa mad'aurin agogo sau uku,kurkure baki,shak'a ruwa a hanci da fyacewa sau uku,wanke fuska daga matsirar gashin kai zuwa k'arshen ha6a,daga gefen kunnan dama zuwa gefen kunnan hagu sau uku,wanke hannun dama zuwa gwiwar hannu sai uku,wanke hannun hagu zuwa gwiwar hannu sau uku,shafan kai daga matsirar gashin kai zuwa keya,a kuma dawo dashi da duka tafukan hannaye sau d'aya, sai shafan kunnuwa ciki da waje sau d'aya,wanke k'afar dama saman k'afa da tafin k'afar ko ina ya jike da ruwa zuwa k'wauri ko idan sawu sai an tabbatar ta wanku,ta hagu ma haka za a mata, wannan itace cikakkiyar alwala.
Sannan sai in zuba ruwa a kaina da duka tafukan hannayena in cuccud'a in tabbatar gashin kaina ya jik'e da ruwa,zanyi hakan har sau uku,sai in wanke barin jikina na dama har zuwa tafin k'afar dama,sai in wanke 6arin hagu har zuwa tafin k'afa,sai ingame jikina da ruwan in tabbatar ko ina ya jik'e da ruwa,lungu da sak'on jikina.
Idan kuma na so bayan nayi tsarki sai kawai ingame jikina tun daga kai har zuwa tafin k'afafuna da ruwa in cuccud'a ko ina nanma wanka yayi.Tad'an kalleshi amma Uncle wannan wanka zaifi dad'i a shower(shaya)ko?Yayi murmushi wannan sharhin kine amma ko ba shaya mutum idan yaso zaiyi abinshi.Kin burgeni yadda kika kowa kome dalla-dalla kamar yadda na fad'a miki,da alama zaki fahimci kome a d'an k'ank'anin lokaci.
Wannan wankan shi za kiyi duk lokacin da jinin al'adarki tad'auke,shi za kiyi idan janaba tasa meki, shi za kiyi idan jinin biki yadauke,bambancin dake tsakaninsu kawai wajan niyya ne.
Cikin d'an shakku takalleshi "to Uncle kana ganin Julaibib zai aure ni?Sumayya sanin gaibu sai ALLAH, tunda yafad'a miki ko zakiyi sallah shifa bazai iya auran kiba,amma babban abinda za ki fara yanzu shine addu'a"Allah ai maji rok'on bawane,ba kuma abinda ya gagara a wajan ubangiji".
Yanzu kinga za kiyi wankan tsarki amma dole fa sai kin cire wannan faratan roban(nail fixes)dan a addinin musulunci sa shi haramun ne,tad'auki abin yanke farce tafara k'ok'arin ciresu,data gama yakaita wani d'aki, kishiga kiyi wanka,d'akin yar uwan kice,kome yana zaune a muhallinshi Dammm...Zuciyar ta tabuga saboda irin wannan k'amshin a d'akinsu Julaibib ta ta6a jinshi wallahi ranar data mamayeshi tashiga.Ta tsuke baki kamar zata rufeshi tana zuk'e sassanyar k'amshin tabaki ta hanci tare da lumshe idanunta,tana wata kissima a zuci,wani murmushi ya su6uce mata wucewar dak'ik'u masu yawa, tasauke gwauran numfashi sannan tarage kayan jikinta tashiga wanka.
Yakoma D'akin-shakatawa yazauna, tunanin ya cika k'wak'walwarshi har baiji fitowar taba.Uncle na gama tafad'a lokacin da take k'ok'arin zama,ya kalli agogon dake d:aure a hannunshi lokacin sallar la'asar ya gabato.Yamik'e "zani masallaci,daga nan zan wuce in d'auko mutan gidan,ko kin jini shiru karki damu dan wata kila zamu had'u da cunkuson abubuwan hawa.Ta amsa da"to Uncle a dawo lafiya.Tad'auki wani littafi data gani a saman kujera"Islamic Perspectives On Reproduction, Health ChildBirth Spacing In Nigeria.Tafara karantawa.
Miqdad ne yafara dawowa a sanda rana ta tafi za ta fad'i magriba na shirin kunno kai,ya san ba kowa a gidan shi yasama yatafi da mukulli amma yana ta6a kofar yajita a bud'e,yasa kai cikin murmushi tare da sallama bak'uwar fuskar yagani a kwance tana karanta littafin da ya ajiye a saman kujera jiya da daddare, tamik'e zaune daga kwanciyar da tayi,tajuya inda taji sallamar Dammmm...Zuciyarshi ta buga da suka had'a idanu,Hafsa yake gani a fuskar ta,hatta manyan idanunta masu maik'o irin na Hafsa ne.
Tad'anyi murmushi"Sannu da zuwa. Yagyad'a kai"yauwa.Tanuna mishi kujera"kazauna mana, mutan gidan ba sa nann ne Uncle ya tafi d'auko su.Yasake kallanta jin tace Uncle wannan yar uwarsu ce ta Zonkwa yayi yar dariya sannnan ya zauna"kema sannunki da zuwa,daga Madauci ko?Tagyad'a kai.