Sashe 37
Gwajin Dafi Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tana d'ago kai,caraf idanun su yahad'u, wani sanyi dad'i taji a ilahirin gangar jiki da sararin zuciyar ta. Alk'asim yak'araso wajan "gaskiya yan matan nan kun had'u,zai mik'a ma Sudaida rufaffen envelop A'isha takai hannu za ta kar6e,yajanye hannunshi da sauri"a ah ya haka? Tagyad'a kai"eh haka nake nufi,kai kaga hakan zata sa6u bindiga acikin ruwa? Wasa tare ci bamban?Khausar tace ko muma abamu ko itama tarasa. Yayi yar dariya "mata problem kunga fa ba wani abu bane a ciki,rubutune kawai akayi da biro bulu.Eh koma dai menene to abamu na mu. Nasmat ta katseshi"to wai ma yahaka?Ana zatan wuta a mak'era sai ga ta kuma a masak'a?Wallahi wanda nayi hasashen zai bata kyautar kaasatan bai yiba sai kai?Yamaida envelop d'in aljihu "shikenan karku samu damuwa za kuji a salansa, Sudaida sun hana in baki hannu da hannu zan aiko miki dashi gida,yajuya yayi tafiyarshi bai saurari hayagagar da suke mishi ba.Suka jera suna tafiya zuwa gidan Hajiya"Aisha tace wai me yahana Sinan zuwa wajan saukar mu,naga har Hashim daba d'an gari ba ya zo?Tawatsa hannu"nima ban sani ba amma ina ga kamar ba k'alau ba.
Dayammacin ranar sai ga shi da kaya nik'i-nik'i lemukan gwangawani dana kwali, yana zaune a dakalin k'ofar gidan tafito cikin fushi Sagir na biye da ita da kayan,takar6a ta ajiye mishi "Sinan ba wad'annan nafi buk'ata ba,zuwanka wajan ya fi duk abinda za ka bani. Tajuya...Yasha gabanta da sauri yahad'a tafukan hannayen shi da sigar rarrashi"Sarauniyar Sinan kiyi hak'uri "Tagirgiza kai"ban hak'ura ba sai ka fad'a min abinda yahana ka zuwa.Yad'anyi jimmm... na wucewar wasu dak'ik'u"za ki yadda dani?Tayi shiru sai yacigaba"to ni dai na san na miki laifin da ban ta6a miki irin shi ba,Sudaida baccine yayi awan gaba dani,to ya zanyi?To wayar ka amfanin me takeyi na kira ka sau shurin masak'i baka d'aga ba,sai kace me baccin mutuwa? Yakad'a kai cikin damuwa"lallai na cancanci abani horo,itama fa wayar a yanayin shiru nasa ta,kiyi hak'uri Sudaida "ALLAH yana san masu hak'uri,masu had'iye fushi, suna da dama su rama abinda aka musu amma sai suke hak'ura su yafe,su maida kome ba kome ba saboda ganin girman ALLAH...yacika da dad'ad'an kalamai har sai da yashawo kanta. ALLAH da gaske ke nake so Sudaida alk'awari ba karyawa ni da ke sai mun zama abin kwatance mutu ka raba takalmin kaza. Da haka yaba Sagir kayan yamayar dasu cikin gida..
Kwana biyu da fara azumin watan ramadan yashirya shi da Musaddiq sai Matsirga. Inna tana zaune a d'aki taga ana shigo da kayayyaki tasa hijab tafito tsakar gida tana tambayarsu daga ina wad'annnan kayan? Sai ga Bello yashigo da murnar shi yana fad'a mata su Yaya Julaibib ne.Jikinta yayi sanyi tabi kayayyakin da kallo cikin zancen zuci"wato k'auna ta gaskiya tana d'orewa koda ba wanda ake k'aunar a doron duniya. Bello yarik'o hannunta "Inna na shigo dasu. Tayi murmushi"lale maraba,sannunku da zuwa bismillah tajuya zuwa cikin d'aki suka bita,cikin girmamawa suka gaisheta"Iyayan na ku k'alau ko? A lafiya k'alau Inna suna gaishe ku.To madalla ALLAH yamuku albarka,ku bakwa gajiya da hadima?Musaddiq yace"haba Inna ai bakome... yiwa kaine.To Ubangiji yasa ka muku da mafificin sakamakon shi;ALLAH yasa hakan amizaninku na kyawawan aiyuka. Amin,amin Inna.
Inna su Malam basa nan ne?Eh d'azu shi da Maude suka tafi Zango wajan k'annin mahaifanshi,Tukur kuma jiya yakoma makaranta. Suka d'an ta6a hira sannan suka mata sallama taciko musu jarkoki da kindirmo da manshanu, Bello yasa kuka shi dole sai sun tafi dashi Inna tayi-tayi ya zauna amma ya kafe ya nata ihu shi dai zai bi su,duk yamak'alk'ale Julaibib ya 6ata mishi farar shaddar da yasa da majina da ruwan hawaye,yarik'o hannun shi.
Inna bari muje waje muyi magana tabisu da kallo,a mota suka dinga rarrashin shi "kaga idan muka tafi dakai Malam bai sani ba idan ya dawo zaima Inna fad'a muma zai mana fad'a, yamak'ale kafad'a"uh uh ai idan tace kaine bazai yi fad'an ba,kuma kana da waya kafad'a mishi na san zai yadda,ni dai kawai ALLAH mutafi"to naji na kuma maka alk'awari idan aka samu hutu Insha-ALLAH zan zo in tafi dakai Zonkwa.Yad'ibo dabinon ajwa da yawa a aljihunshi idan ka yadda sai in bar maka wannan dabinon,yakalleshi sannan yakalli dabinon" to duka zaka barmin?Yayi murmushi"eh mana sa hannunka ka kwashe ma, yana ta d'auka da d'ai-d'ai da d'ai-d'ai yana sawa a aljihunshi har ya kwashe duka sannan yayi dariya aina kwashe, to sai ka zo d'in barinje in nuna ma Inna,yauwa Bello mutumin kirki barin rakaka,har ciki ya kaishi ya kuma fad'a mata yadda sukayi tayi murmushi kawai sannan suka sake yin sallama sunama juna asha ruwa lafiya.
Rana ta tafi zata fad'i magriba na shirin kunno kai,an kusa shan ruwa takashe rediyon da take sauraran tafsirin Alqur'ani me girma a gidan rediyon jahar Kaduna(FRCN)farin gida kafin Sardauna.Tayi doguwar hamma tasa tafin hannun dama tarufe bakin ta, tana Isti'aza yau ba laifi tana jin azumin nan ajika dan ma yau Khausar ce da aiki da wallahi bata san yadda za tayi ba kanta har barazanar ciwo yake yi,daga can D'akin-girki tajiyo kiran Umma tamik'e da sauri tafita.
Umma gani.Umma tamata wani kallo "ba tun d'azu nace ki d'auki dabgen Hajiya ki kai mata ba?Baki ji bane ko zuwan ne baza kiyi ba? Tad'an sosa kai Umma fa boss ce,bata d'aukar raini ko na sisin kwabo"Yi hak'uri Umma barin d'auko hijab,tasa hijab ta d'auki kwanan samiran sannan tad'an kalketa cikin shakka"Umma dan ALLAH daga nan zan biya gidan Inna.Tayi shiru kamar bata jiba sai da tagama zuba wani dabgen a wani samiran ta rufe sannan takalleta"adawo lafiya suma ki tafi musu da wannan.Wani murmushi yasu6uce mata dan ba k'aramin aikin Umma bane tahana"nagode Umma tarik'o hannun Hanifa'yar Musaddiq ta fari suka tafi.
Tana shiga sai ga Nasmat itama takawo ma Inna hadaddan kunun aya kafin a kira sallar magriba sunyi alwala,ana kiran sallah sukaci dabino da lemun 6awo da ruwa me rangwamen sanyi sannan suka tada kabbarar sallah.
Julaibib da Baba suka shigo da sallama sukama juna barka da shan ruwa sannan ya ajiye ledan hannunshi a gaban Inna.Nasmat tajawo ledan gabanta tafara shan abarban da yake ciki da kankana yankakku tana fadin"kyan rawa da makar6i.Sudaida ma tasa hannu ta d'auki kankana tana cema Hanifa sa hannu ki d'auka...Baba yayi murmushi ganin irin kallan da yake musu,yayi k'wafa yajuya zuwa d'akin shi Inna tana mishi dariya itama.Sudaida ta ka sa cigaba da sha, ranta ba dad'i har yanzu bai dawo yadda tasan shiba, ba wani kyan gani da yayi,yabar k'asumba ba wani gyara,kana mishi magana zai bika da wannan rikitaccen kallan,ya ya6a maka bak'ar maganar da ko barinje (mahauci) iya karta kenan.
A sanda hantsi yadubi ludayi na safiyar laraba yana nazarin wani littafin tafsirin Alqur'ani me girma Hajiya tashigo da sallama,yamik'e da sauri yataro ta"maraba da zuwa Hajiyar mu,ta ture shi"kai tafi can matsa kabani waje,ta zauna a kujera tana murza k'afafunta,ya d'auko man zafi zai shafa mata tajanye k'afafunta da sauri"bana so.Yayi murmushi"haba Hajjaju makkatu wal madinatu gwiwata a k'asa,kaina bisa wuyana.Oho ashe kaima ka san kayi laifi,saboda ALLAH Julaibibi tunda kazo garin nan sau d'aya rakkin rak kazo gidana,ba fad'a to me yakawo wannan gabar? Kiyi hak'uri Hajiya bana jin dad'i ne.Tajijjiga kai tana mishi kallan nazari"kai Julaibibi tunanin Bilkisun ce yake susuta ka haka?Yagirgiza kai "haba dai Hajiya ba wannan bane.
Yamik'e da sauri ya d'auko madara da maltina da kofi.Hajiya tabishi da kallo cikin mad'aukakin mamaki"ciwon har yakai ba ka iya yin azumi ne Julaibibi?Yadafe kai "Innalillahi.Ina yi, wai dama ke zan kawo ma na man tane.Tamik'e wa?Ni kaga tafiya ta.Yarufo gidan"barin taka miki suna tafiya suna hira"anjima da daddare zan zo miki hira sai ki tanadar min garwashi zan zo da d'anyan masara in gasa mana"To ALLAH ya kaimu har gidan Kawun shi yakaita.
A D'akin-shak'atawa Sudaida ce kawai tana kwance a doguwar kujera tana waya,tamik'e zaune saboda shigowar su,kusan dak'ik'u goma sannan tagama wayar,tad'ago tana kallan Julaibib bayan ta d'ora ha6arta a kafad'ar Hajiya"Hajiyarmu you're welcome.Kin san abinda bature me jan kunne yake nufi da haka?Tajijjaga kai"tun kafin in haifi uban ki ya haifeki kuwa.Tad'an turo baki, Julaibib yayi murmushi yana shafa k'wantaccen bak'in gashin kanshi"Yo kya 6ata fuska ba tambaya kikayi nabaki amsa ba?
Mu turancin mu ma gangariya masu abu da abun su kura da kallabin kitse, turanwan ne fa suka koya mana baki da baki,To me yasa bakya yi?Tad'an kalleta kaji wata magana to yaran turanci yarena ne?Ni yarene hausa idan takama ayi turan cin inayi mana"do you get me? Sudaida takyalkyale da dariya saboda yadda Hajiya tayi furucin tagyad'a kai"yes grandam.Su Mama suka shigo suna gaishe da surukar ta su cikin girma da mutuntawa.
Da daddare yana gidan Hajiya suna hirarsu takalleshi"tunda katafi Azare kayi zaman ka shiru ba amo ba labari ko wata bafulatanarce takuma rik'e mana kai?Ya jujjjuya masarar sannan yad'ago yakalleta"ko d'aya Hajiya.To in dai haka ne ya kamata ka nemi wata,ga yan mata nan burjik a cikin dangi sai ka za6a ka darje,kana gani ganin idanun ka Musaddiq Ya'yan shi biyu ga cikin na uku nan.Cikin wasa yace"Hajiya banga wacce nake so ba ko za ki tayani nema?Tagyada kai"anyi an gama maye ya auri makauniya.Bai wani dad'e ba yamata sai da safe, saboda akwai tashi cikin dare domin yin munajaati ga ALLAH buwayi gagara koyo ga kuma tashi yin sahur.
K'arfe-k'arfene sai dai a cikin k'arafan akwai zinare da azurfa.
Idan baka san gari ba...saurari daka.
Abdullahi Lawal Abdullahi (D'ansarai)
Saudat Ibrahim Yahya (Takwara ta)
Mungode da tunatarwan ku bisa wani kuskure da mukayi a shafi na goma sha biyar..
Falmata Maiduguri mungode da kulawa.
28 Jumaada Awwal 1441
23 January 2020
We Ibrahim's Daughters 👇
Asdilat KD...2geda with Ra'ibs.
DANGIN NONO WRITERS ASAOCIATION
{Da Inganci Mukayi Fintinkau}
Bismillahi wabihi nasta'in
...GWAJIN DAFI💔
Almost true story
Daga alk'alamin🖊
Ya'yan Ibrahim
Saudat A.Baba (Asdilat KD)
Da
Bara'atu Ibrahim (Ra'iba)
Shafi nagoma sha bakwai.
Dayammacin ranar sai ga shi da kaya nik'i-nik'i lemukan gwangawani dana kwali, yana zaune a dakalin k'ofar gidan tafito cikin fushi Sagir na biye da ita da kayan,takar6a ta ajiye mishi "Sinan ba wad'annan nafi buk'ata ba,zuwanka wajan ya fi duk abinda za ka bani. Tajuya...Yasha gabanta da sauri yahad'a tafukan hannayen shi da sigar rarrashi"Sarauniyar Sinan kiyi hak'uri "Tagirgiza kai"ban hak'ura ba sai ka fad'a min abinda yahana ka zuwa.Yad'anyi jimmm... na wucewar wasu dak'ik'u"za ki yadda dani?Tayi shiru sai yacigaba"to ni dai na san na miki laifin da ban ta6a miki irin shi ba,Sudaida baccine yayi awan gaba dani,to ya zanyi?To wayar ka amfanin me takeyi na kira ka sau shurin masak'i baka d'aga ba,sai kace me baccin mutuwa? Yakad'a kai cikin damuwa"lallai na cancanci abani horo,itama fa wayar a yanayin shiru nasa ta,kiyi hak'uri Sudaida "ALLAH yana san masu hak'uri,masu had'iye fushi, suna da dama su rama abinda aka musu amma sai suke hak'ura su yafe,su maida kome ba kome ba saboda ganin girman ALLAH...yacika da dad'ad'an kalamai har sai da yashawo kanta. ALLAH da gaske ke nake so Sudaida alk'awari ba karyawa ni da ke sai mun zama abin kwatance mutu ka raba takalmin kaza. Da haka yaba Sagir kayan yamayar dasu cikin gida..
Kwana biyu da fara azumin watan ramadan yashirya shi da Musaddiq sai Matsirga. Inna tana zaune a d'aki taga ana shigo da kayayyaki tasa hijab tafito tsakar gida tana tambayarsu daga ina wad'annnan kayan? Sai ga Bello yashigo da murnar shi yana fad'a mata su Yaya Julaibib ne.Jikinta yayi sanyi tabi kayayyakin da kallo cikin zancen zuci"wato k'auna ta gaskiya tana d'orewa koda ba wanda ake k'aunar a doron duniya. Bello yarik'o hannunta "Inna na shigo dasu. Tayi murmushi"lale maraba,sannunku da zuwa bismillah tajuya zuwa cikin d'aki suka bita,cikin girmamawa suka gaisheta"Iyayan na ku k'alau ko? A lafiya k'alau Inna suna gaishe ku.To madalla ALLAH yamuku albarka,ku bakwa gajiya da hadima?Musaddiq yace"haba Inna ai bakome... yiwa kaine.To Ubangiji yasa ka muku da mafificin sakamakon shi;ALLAH yasa hakan amizaninku na kyawawan aiyuka. Amin,amin Inna.
Inna su Malam basa nan ne?Eh d'azu shi da Maude suka tafi Zango wajan k'annin mahaifanshi,Tukur kuma jiya yakoma makaranta. Suka d'an ta6a hira sannan suka mata sallama taciko musu jarkoki da kindirmo da manshanu, Bello yasa kuka shi dole sai sun tafi dashi Inna tayi-tayi ya zauna amma ya kafe ya nata ihu shi dai zai bi su,duk yamak'alk'ale Julaibib ya 6ata mishi farar shaddar da yasa da majina da ruwan hawaye,yarik'o hannun shi.
Inna bari muje waje muyi magana tabisu da kallo,a mota suka dinga rarrashin shi "kaga idan muka tafi dakai Malam bai sani ba idan ya dawo zaima Inna fad'a muma zai mana fad'a, yamak'ale kafad'a"uh uh ai idan tace kaine bazai yi fad'an ba,kuma kana da waya kafad'a mishi na san zai yadda,ni dai kawai ALLAH mutafi"to naji na kuma maka alk'awari idan aka samu hutu Insha-ALLAH zan zo in tafi dakai Zonkwa.Yad'ibo dabinon ajwa da yawa a aljihunshi idan ka yadda sai in bar maka wannan dabinon,yakalleshi sannan yakalli dabinon" to duka zaka barmin?Yayi murmushi"eh mana sa hannunka ka kwashe ma, yana ta d'auka da d'ai-d'ai da d'ai-d'ai yana sawa a aljihunshi har ya kwashe duka sannan yayi dariya aina kwashe, to sai ka zo d'in barinje in nuna ma Inna,yauwa Bello mutumin kirki barin rakaka,har ciki ya kaishi ya kuma fad'a mata yadda sukayi tayi murmushi kawai sannan suka sake yin sallama sunama juna asha ruwa lafiya.
Rana ta tafi zata fad'i magriba na shirin kunno kai,an kusa shan ruwa takashe rediyon da take sauraran tafsirin Alqur'ani me girma a gidan rediyon jahar Kaduna(FRCN)farin gida kafin Sardauna.Tayi doguwar hamma tasa tafin hannun dama tarufe bakin ta, tana Isti'aza yau ba laifi tana jin azumin nan ajika dan ma yau Khausar ce da aiki da wallahi bata san yadda za tayi ba kanta har barazanar ciwo yake yi,daga can D'akin-girki tajiyo kiran Umma tamik'e da sauri tafita.
Umma gani.Umma tamata wani kallo "ba tun d'azu nace ki d'auki dabgen Hajiya ki kai mata ba?Baki ji bane ko zuwan ne baza kiyi ba? Tad'an sosa kai Umma fa boss ce,bata d'aukar raini ko na sisin kwabo"Yi hak'uri Umma barin d'auko hijab,tasa hijab ta d'auki kwanan samiran sannan tad'an kalketa cikin shakka"Umma dan ALLAH daga nan zan biya gidan Inna.Tayi shiru kamar bata jiba sai da tagama zuba wani dabgen a wani samiran ta rufe sannan takalleta"adawo lafiya suma ki tafi musu da wannan.Wani murmushi yasu6uce mata dan ba k'aramin aikin Umma bane tahana"nagode Umma tarik'o hannun Hanifa'yar Musaddiq ta fari suka tafi.
Tana shiga sai ga Nasmat itama takawo ma Inna hadaddan kunun aya kafin a kira sallar magriba sunyi alwala,ana kiran sallah sukaci dabino da lemun 6awo da ruwa me rangwamen sanyi sannan suka tada kabbarar sallah.
Julaibib da Baba suka shigo da sallama sukama juna barka da shan ruwa sannan ya ajiye ledan hannunshi a gaban Inna.Nasmat tajawo ledan gabanta tafara shan abarban da yake ciki da kankana yankakku tana fadin"kyan rawa da makar6i.Sudaida ma tasa hannu ta d'auki kankana tana cema Hanifa sa hannu ki d'auka...Baba yayi murmushi ganin irin kallan da yake musu,yayi k'wafa yajuya zuwa d'akin shi Inna tana mishi dariya itama.Sudaida ta ka sa cigaba da sha, ranta ba dad'i har yanzu bai dawo yadda tasan shiba, ba wani kyan gani da yayi,yabar k'asumba ba wani gyara,kana mishi magana zai bika da wannan rikitaccen kallan,ya ya6a maka bak'ar maganar da ko barinje (mahauci) iya karta kenan.
A sanda hantsi yadubi ludayi na safiyar laraba yana nazarin wani littafin tafsirin Alqur'ani me girma Hajiya tashigo da sallama,yamik'e da sauri yataro ta"maraba da zuwa Hajiyar mu,ta ture shi"kai tafi can matsa kabani waje,ta zauna a kujera tana murza k'afafunta,ya d'auko man zafi zai shafa mata tajanye k'afafunta da sauri"bana so.Yayi murmushi"haba Hajjaju makkatu wal madinatu gwiwata a k'asa,kaina bisa wuyana.Oho ashe kaima ka san kayi laifi,saboda ALLAH Julaibibi tunda kazo garin nan sau d'aya rakkin rak kazo gidana,ba fad'a to me yakawo wannan gabar? Kiyi hak'uri Hajiya bana jin dad'i ne.Tajijjiga kai tana mishi kallan nazari"kai Julaibibi tunanin Bilkisun ce yake susuta ka haka?Yagirgiza kai "haba dai Hajiya ba wannan bane.
Yamik'e da sauri ya d'auko madara da maltina da kofi.Hajiya tabishi da kallo cikin mad'aukakin mamaki"ciwon har yakai ba ka iya yin azumi ne Julaibibi?Yadafe kai "Innalillahi.Ina yi, wai dama ke zan kawo ma na man tane.Tamik'e wa?Ni kaga tafiya ta.Yarufo gidan"barin taka miki suna tafiya suna hira"anjima da daddare zan zo miki hira sai ki tanadar min garwashi zan zo da d'anyan masara in gasa mana"To ALLAH ya kaimu har gidan Kawun shi yakaita.
A D'akin-shak'atawa Sudaida ce kawai tana kwance a doguwar kujera tana waya,tamik'e zaune saboda shigowar su,kusan dak'ik'u goma sannan tagama wayar,tad'ago tana kallan Julaibib bayan ta d'ora ha6arta a kafad'ar Hajiya"Hajiyarmu you're welcome.Kin san abinda bature me jan kunne yake nufi da haka?Tajijjaga kai"tun kafin in haifi uban ki ya haifeki kuwa.Tad'an turo baki, Julaibib yayi murmushi yana shafa k'wantaccen bak'in gashin kanshi"Yo kya 6ata fuska ba tambaya kikayi nabaki amsa ba?
Mu turancin mu ma gangariya masu abu da abun su kura da kallabin kitse, turanwan ne fa suka koya mana baki da baki,To me yasa bakya yi?Tad'an kalleta kaji wata magana to yaran turanci yarena ne?Ni yarene hausa idan takama ayi turan cin inayi mana"do you get me? Sudaida takyalkyale da dariya saboda yadda Hajiya tayi furucin tagyad'a kai"yes grandam.Su Mama suka shigo suna gaishe da surukar ta su cikin girma da mutuntawa.
Da daddare yana gidan Hajiya suna hirarsu takalleshi"tunda katafi Azare kayi zaman ka shiru ba amo ba labari ko wata bafulatanarce takuma rik'e mana kai?Ya jujjjuya masarar sannan yad'ago yakalleta"ko d'aya Hajiya.To in dai haka ne ya kamata ka nemi wata,ga yan mata nan burjik a cikin dangi sai ka za6a ka darje,kana gani ganin idanun ka Musaddiq Ya'yan shi biyu ga cikin na uku nan.Cikin wasa yace"Hajiya banga wacce nake so ba ko za ki tayani nema?Tagyada kai"anyi an gama maye ya auri makauniya.Bai wani dad'e ba yamata sai da safe, saboda akwai tashi cikin dare domin yin munajaati ga ALLAH buwayi gagara koyo ga kuma tashi yin sahur.
K'arfe-k'arfene sai dai a cikin k'arafan akwai zinare da azurfa.
Idan baka san gari ba...saurari daka.
Abdullahi Lawal Abdullahi (D'ansarai)
Saudat Ibrahim Yahya (Takwara ta)
Mungode da tunatarwan ku bisa wani kuskure da mukayi a shafi na goma sha biyar..
Falmata Maiduguri mungode da kulawa.
28 Jumaada Awwal 1441
23 January 2020
We Ibrahim's Daughters 👇
Asdilat KD...2geda with Ra'ibs.
DANGIN NONO WRITERS ASAOCIATION
{Da Inganci Mukayi Fintinkau}
Bismillahi wabihi nasta'in
...GWAJIN DAFI💔
Almost true story
Daga alk'alamin🖊
Ya'yan Ibrahim
Saudat A.Baba (Asdilat KD)
Da
Bara'atu Ibrahim (Ra'iba)
Shafi nagoma sha bakwai.