Sashe 54
Gwajin Dafi Complete Hausa Novel · about 8 min read
Haushin shi yakamata"na rantse maka da girman ALLAH idan bakazo munje asibiti ba to ko ciwon ka yatashi cikin dare ni karka tasheni ina tsaka dajin dad'in bacci na eheee,yasan za a rina...wannan fushin,haba-haba dai ke kuwa ya zaki fad'i haka? Yanzu lalurata ba taki bace?Takwace hannayenta tana turo baki gaba"eh batawa bace,ta kace kai kad'ai dan haka kaje kaji da ita kai kad'ai tunda na baka shawara baka jiba...Yayi yar dariya"kinga to kisha kuruminki Sudaidan D'ansarai yajata suka zauna a kujera sannan yaciro ledar magani da d'an k'aramin katin shi na ganin likita"duba kigani"daga asibiti nake abinda yasa ban dawo da wuri ba kenan,likita yamin test,wai typhoid ke damuna ga magungunan daya bani da allurai"anjima bayan sallar Isha'i za ki rakani allurar,kin san bana son allura idan nak'i tsayawa sai ki d'an bud'e idanun ki nan da nan sai kiga na tsaya amin ba tare da ankai ruwa ranaba ko kuwa?Tayi dariya"lallai kuwa wannan shine ta6ara megida da kukan yunwa.
Tad'auki rakenta tafara sha da bismillah"da fa yau har yajin shan raken nan zanyi da bakaje asibitin ba.Ke d'in kuwa?Ke mayyar rake ce kuma ban ta6a k'in siyo miki ba,amma ni idan nace ki had'a min shayi sai kawai ki kama fushi wai bazan sha bak'in ruwa ba to haka a ke rayuwa?Kowa ba da abinda yafi so ai ko kuwa? Tajijjiga kai"ka fini gaskiya, toh kayi hak'uri na dai fushi da shan bak'in ruwa... tawani shagwa6e"nima ai gashinan a hankali na fara koyan sha,shekaran jiya ba tare muka shaba? Yagyad'a kai"Yau me kike dafa mana be?Tad'an kalleshi"ni fa da bazanyi wani girki ba,idan zamuje allura muje gidan Inna kaci tuwo ni zan sha Yoghort dan bana jin yunwa.Yamik'e"to shikenan,yatafi d'auro alwala dan anfara kiraye-kirayen sallar magriba daga mabambantan masallatan unguwa.
A hankali cigaban rayuwa take zuwa daki-daki har zuwa sanda bawa zai had'u da aljalinshi,alokacin numfashi da duk wani abinda ALLAH yarubuta zai samu ko zaiyi a doron duniya ya gamayin shi.Julaibib Abdullahi D'ansarai a yanzu yasake samun cigaba daga matakin lecturer zuwa senior lecturer.
Yana zaune a D'akin-shak'atawa yana yan rubuce-rubucen shi a na'ura me kwakwalwa,yayi k'iba yak'ara kyau da wayewa,bak'ar fatarshi tanata shek'i dan ta jik'e da hutu da kwanciyar hankali,shigarshi kamar kullum ta fararen kaya,hularshi dara daratsin fari da ruwan k'asa, agefe kuma Ya'yanshine Ya'yan abokinshi amininshi,kuma d'an'uwan shi Musaddiq suna zaune tankwashe da k'afafunsu cikin ladabi suna cin abincin rana. Asma'u tayi sallama tashigo. Julaibib yad'ago yana amsa sallamar yana mata sannu da zuwa,tazauna suka gaisa sannan tabi d'akin da kallo"ina madugar baza ta fito mu gaisa bane? Yagirgiza kai"Sudaida baza tak'i fitowa ku gaisa ba matuk'ar tana cikin gidan nan ko da kuwa bata jin dad'ine.Tata6e baki"haka fa, toh madallah.
Suka cigaba da hirarsu ta zumunci,a hankali har tasako mishi zancen k'arin aure"Lillahi warasulihi ka dinga zama kenan da mace juya? D'ansarai ai kowa yana son ganin d'a na kanshi. Yad'anyi murmushi"haihuwa ai d'an lokacine Yaya Asma'u.Tawatsa hannu" kai tafi can,tunda an maida kai hannun zani dole za ka fad'i haka mana,ka barta tana ta karatu to yaushe kuwa zata yadda da haihuwa, haihuwa yaja mata koma baya a wajen karatunta,na sha fad'a maka yarinyar nan tsarin Iyali takeyi,idan ba haka ba me zaisa har yanzu bata haihuba? Su sauran da akayi bikinsu rana d'aya ba ga shinan daga me haihuwa biyu sai me uku ba?
Jiya kuma nake jin wani k'arin abin haushin,abin duka ba sanda wai Gidan-Waya sun fara degree program dan haka ka barta tacigaba,haba dan ALLAH D'ansarai ina hankalinka da tunaninka suke ne?Ganin yayi shiru yasa tacigaba da zugashi da k'ara tabbatar mishi lallai tabbasss Sudaida ita take hana kwanshi zuwa duniya.
Zuciyarshi tafara mishi tubka da warwara game da kalaman Asma'u.Tasake kallanshi "D'ansarai wai kai har yanzu baka ga biri yaso yayi kama da mutum bane?Yazuba mata idanu yana zancen zuci"anya Sudaida za ta mishi haka?Yana lura da ita,ita kanta fa tana san Ya'ya dan duk lokacin da za suje siyayya a kasuwa taga unisex riga indai ya mata kyau to sai ta siya,ran nan yashiga d'akin baccin su yatarar da ita tana jera kayan a babban a kwati trolley;yazauna yana kallanta
"Zaujatiii...wai wa kike sai ma wad'annan kayan ne?Tad'anyi murmushi idanun ta sun ciko da kwallah alamar zuciyarta tayi rauni "takauda kai sha'awa suke bani Yaya D'ansarai musamman wad'annan biri da wandon(over roll) duk lokacin da ALLAH ya bamu d'a toh na shine ko na tane...kawai sai ta fashe da kuka"d'azu A'isha takirani wai ta kuma haihuwa d'a na uku kenan ta haifa... Maryam ta kusa haihuwan na ukun...kowacce tana da Ya'ya mu kad'ai ne bamu dasu...yafara rarrashi"kiyi hak'uri Zaujatiii... ALLAH yana sane damu bai manta damu ba,kome d'an lokaci ne,wata rana sai labari yayi ta rarrashinta har yasamu tayi shiru sannan yakalleta cikin natsuwa "Zaujatiii... ki daina wahalar da kanki a kan tara kayan yara na sha'awa duk wannan me sauk'i ne in dai ALLAH ya azurtamu da samun d'an, dan kyale-kyalen kullum sabunta su akeyi"budurwar bana tafi ta bara...
Bayan haka kuma kullum gidan nasu cike yake da Ya'yan yan'uwa in dai tana gida,kai ko bata gidan in dai shi yana nan kuma ba makaranta za suje ba toh zama sukeyi su jirata,saboda san su da takeyi da kuma irin garar da take had'a musu,duk abinda yaro yake so in dai tana dashi to anyi angama maye ya auri makauniya"in dai abin ta6akalashe ne. Toh Lillahi warasulihi me irin wannan halin ce,za a ce baza ta bar nata Ya'yan suzo duniya ba saboda karatu?Anya kuwa?Yariga yasan Yaya Asma'u kowa ma za ta iya kushewa tazaga in dai taku batazo d'aya ba.Yakad'a kai cikin sauke numfashi"ALLAH yakyauta. Tabishi da kallan mamaki"ALLAH yakyauta fa kace? Eh Yaya Asma'u to me zance daya wuce haka?
Tadad'a gyara zama"kai ko kake da abin cewa,cene da ita aure za kayi...kayi auren ka amarya tazo taita haifa maka Ya'ya,toh idan taga Ya'yan kake so taga amaryar taka tafara cika maka gidan da sanyin idanu to ai zata daina abinda takeyi na tsarin iyali ko kuwa?Toh zanyi tunani.Tamik'e"ya dai kamata,ni me zan samune a gidan? Tana fad'in haka ta nufi d'akin da suke ajiye kayayyaki tagama dube-dubenta tafito"kome ma ya k'are.Yauwa gwamma da kika gani ganin idanunki,dana fad'a miki ba kome ba yadda za kiyiba,kin san ni d'an albashine ga shi kuma wata yakai tsakiya,abubuwan sai dai godiyar Ubangijinmu a kowani hali da yanayi.
Taja dogon tsaki tana mishi kallon uku ahu"amma a hakan kake k'ok'arin biya mata wasu mak'udan kud'ad'e dan tacigaba da karatu, tamik'a mishi hannu"ni bani abinda kayi niyyar bani kawai in tafi.Zan ai ko miki dashi har gida,Yaya Asma'u kidinga tausaya min mana.Tanunashi da yatsa"kai d'in?Na rantse da girman ALLAH ba ka da matausaya.Yakalleta da mad'aukakin mamaki yana nuna kanshi"ni d'in ne bani da matausaya Yaya Asma'u?Ko shakka babu dan ni banga matausayan ba,ba d'a ba jika to ko hidimar me kakeyi da har za a tausaya maka saboda yawan buk'atu?Daga kai sai matarka kuke cin karanku ba babbaka,takalleshi"za ka bani ne ko sai madugar ta dawo in zo in kar6a? Baice kome ba yasa hannu a aljihun gabar rigarshi yaciro kud'ad'en ciki yana nuna mata"kingani yan canjine wallahi bani da kud'i.Tasa hannu takar6a"eh kawo da hanau gwamma mannau ni na wuce.Yabita da kallo har tafita a D'akin-shak'atawar, yagirgiza kai "Yaya Asma'u matsala,ALLAH yashirye ta da masu hali irin na ta.
Sun dawo sallar la'asar da yammacin,shi da Musaddiq suka tsaya a k'ofar gidan suna tattauna al'amuran daya shafi kasuwancinsu ta dawo daga makaranta,ta tsaya suka gaisa da Musaddiq sannan tawuce ciki da mamakin kallan k'urillan da Julaibib yake binta dashi wanda ba halinshi bane yawan kallan da har sai kaga munin mutum.Tana kwance a tsakar d'akin yashigo,tamik'e zaune suna kallan-kallo na wucewar wasu dak'ik'u "Yaya D'ansarai lafiya kuwa? Me yafaru ne? Yasunkwui da kai,sai gwiwoyinta suka sage dan ta san wannan halin na shi tuntuni in dai yasunkwui da kai to bazaiyi magana ba ko da menene,tajingina bayanta da kujera tare da lumshe idanun ta,tunani barkatai ya cika k'wak'walwarta"ita dai tasan lafiyar ALLAH suka rabu har tana tsokanarshi
"Zaujiii...kafin in dawo kamana faten tsaki mana.Yagalla mata harara"na rantse da ALLAH tun kafin wankin bargo yakaiki ga dare ki tsaya kiyi abinki, danni ba bawa bane.Takyalkyle da dariya wato ya rama abinda ta ta6a fad'a mishi shekarun baya,farkon auren su kenan.Tawani marairaice"haba mijin Sudaida tamu dakai fa ba ta 6aci,kar fa faten tsaki yasa a ganmu a rana,tarik'o hannayenshi"dan darajar k'auna da soyayyata da take dank'are anan tad'an daki k'irjinshi dai-dai saitin da zuciya take, kamana faten tsaki,sukayi dariya,yagyad'a kai"eh zanyi amma ba fate ba tunda nima a wancan lokacin ba a hanani ba sai dai an jamin zarene.
Yamik'e,tabishi da kallo"Yaya D'ansarai... takira sunanshi.Yakalleta kawai"dan ALLAH kayi hak'uri idan na maka wani abu ne.Yayi kamar baiji abinda tafad'a ba,zuwa can kuma yasake kallanta sai yad'anyi murmushi yad'auki mukullin mota a saman tebur yafita.Ta lumshe idanun ta tanata ayyane-ayyabe a zuci.
A sanda hantsi yadubi ludayi rana ta haske ko'ina na safiyar talata,tana zaune a in da ta idar da sallar walha Hauwa'u tashigo tana fad'in"ina wannnan mijin naki me bak'in idanu da ba ya san zuwa gaisheni? Abokan wasa suke da Julaibib Ya'ya maza amma tasu da Sudaida ta zo d'aya,suna mutunta juna.Sudaida takama ha6a"yanzu mijin nawane me bak'in idanu Hauwa'u? Tajijjiga kai 'tabbasss,to ni duk zuri'ar D'ansarai da wanda yafishi bak'i ne?Sudaida tad'an harareta"lallai daga yau na san in da zan ajiyeki tunda kike cima rabin raina fuska a gaban idanuna,to amma kuma kyau tsagwaron shi da wanda yakama k'afar Yaya D'ansarai nahhh a duk zuri'ar Doctor Julaibb D'ansarai? Bata bata masa ba taje tad'auko lemun peach.
Sudaida tawatsa hannaye"ahab ni dama na san irin abin nan ne na na makaho da yace ido da wari.Hauwa'u tayi murmushi"mu ai gaba d'aya a zuri'ar Doctor Julaibib Abdullahi D'ansarai kyawawane.Sudaida tagyad'a kai"muma ai hakan take a zuri'ar Ibrahim Me-Lambu.Sukayi dariya sannan suka gaisa suna hirarsu ta yaushe gamo dan sun d'an kwana biyu basu ga juna ba saboda yanayin karatun Sudaida da baya barinta zama a gida musamma tada fara karatun degree.
Tad'auki rakenta tafara sha da bismillah"da fa yau har yajin shan raken nan zanyi da bakaje asibitin ba.Ke d'in kuwa?Ke mayyar rake ce kuma ban ta6a k'in siyo miki ba,amma ni idan nace ki had'a min shayi sai kawai ki kama fushi wai bazan sha bak'in ruwa ba to haka a ke rayuwa?Kowa ba da abinda yafi so ai ko kuwa? Tajijjiga kai"ka fini gaskiya, toh kayi hak'uri na dai fushi da shan bak'in ruwa... tawani shagwa6e"nima ai gashinan a hankali na fara koyan sha,shekaran jiya ba tare muka shaba? Yagyad'a kai"Yau me kike dafa mana be?Tad'an kalleshi"ni fa da bazanyi wani girki ba,idan zamuje allura muje gidan Inna kaci tuwo ni zan sha Yoghort dan bana jin yunwa.Yamik'e"to shikenan,yatafi d'auro alwala dan anfara kiraye-kirayen sallar magriba daga mabambantan masallatan unguwa.
A hankali cigaban rayuwa take zuwa daki-daki har zuwa sanda bawa zai had'u da aljalinshi,alokacin numfashi da duk wani abinda ALLAH yarubuta zai samu ko zaiyi a doron duniya ya gamayin shi.Julaibib Abdullahi D'ansarai a yanzu yasake samun cigaba daga matakin lecturer zuwa senior lecturer.
Yana zaune a D'akin-shak'atawa yana yan rubuce-rubucen shi a na'ura me kwakwalwa,yayi k'iba yak'ara kyau da wayewa,bak'ar fatarshi tanata shek'i dan ta jik'e da hutu da kwanciyar hankali,shigarshi kamar kullum ta fararen kaya,hularshi dara daratsin fari da ruwan k'asa, agefe kuma Ya'yanshine Ya'yan abokinshi amininshi,kuma d'an'uwan shi Musaddiq suna zaune tankwashe da k'afafunsu cikin ladabi suna cin abincin rana. Asma'u tayi sallama tashigo. Julaibib yad'ago yana amsa sallamar yana mata sannu da zuwa,tazauna suka gaisa sannan tabi d'akin da kallo"ina madugar baza ta fito mu gaisa bane? Yagirgiza kai"Sudaida baza tak'i fitowa ku gaisa ba matuk'ar tana cikin gidan nan ko da kuwa bata jin dad'ine.Tata6e baki"haka fa, toh madallah.
Suka cigaba da hirarsu ta zumunci,a hankali har tasako mishi zancen k'arin aure"Lillahi warasulihi ka dinga zama kenan da mace juya? D'ansarai ai kowa yana son ganin d'a na kanshi. Yad'anyi murmushi"haihuwa ai d'an lokacine Yaya Asma'u.Tawatsa hannu" kai tafi can,tunda an maida kai hannun zani dole za ka fad'i haka mana,ka barta tana ta karatu to yaushe kuwa zata yadda da haihuwa, haihuwa yaja mata koma baya a wajen karatunta,na sha fad'a maka yarinyar nan tsarin Iyali takeyi,idan ba haka ba me zaisa har yanzu bata haihuba? Su sauran da akayi bikinsu rana d'aya ba ga shinan daga me haihuwa biyu sai me uku ba?
Jiya kuma nake jin wani k'arin abin haushin,abin duka ba sanda wai Gidan-Waya sun fara degree program dan haka ka barta tacigaba,haba dan ALLAH D'ansarai ina hankalinka da tunaninka suke ne?Ganin yayi shiru yasa tacigaba da zugashi da k'ara tabbatar mishi lallai tabbasss Sudaida ita take hana kwanshi zuwa duniya.
Zuciyarshi tafara mishi tubka da warwara game da kalaman Asma'u.Tasake kallanshi "D'ansarai wai kai har yanzu baka ga biri yaso yayi kama da mutum bane?Yazuba mata idanu yana zancen zuci"anya Sudaida za ta mishi haka?Yana lura da ita,ita kanta fa tana san Ya'ya dan duk lokacin da za suje siyayya a kasuwa taga unisex riga indai ya mata kyau to sai ta siya,ran nan yashiga d'akin baccin su yatarar da ita tana jera kayan a babban a kwati trolley;yazauna yana kallanta
"Zaujatiii...wai wa kike sai ma wad'annan kayan ne?Tad'anyi murmushi idanun ta sun ciko da kwallah alamar zuciyarta tayi rauni "takauda kai sha'awa suke bani Yaya D'ansarai musamman wad'annan biri da wandon(over roll) duk lokacin da ALLAH ya bamu d'a toh na shine ko na tane...kawai sai ta fashe da kuka"d'azu A'isha takirani wai ta kuma haihuwa d'a na uku kenan ta haifa... Maryam ta kusa haihuwan na ukun...kowacce tana da Ya'ya mu kad'ai ne bamu dasu...yafara rarrashi"kiyi hak'uri Zaujatiii... ALLAH yana sane damu bai manta damu ba,kome d'an lokaci ne,wata rana sai labari yayi ta rarrashinta har yasamu tayi shiru sannan yakalleta cikin natsuwa "Zaujatiii... ki daina wahalar da kanki a kan tara kayan yara na sha'awa duk wannan me sauk'i ne in dai ALLAH ya azurtamu da samun d'an, dan kyale-kyalen kullum sabunta su akeyi"budurwar bana tafi ta bara...
Bayan haka kuma kullum gidan nasu cike yake da Ya'yan yan'uwa in dai tana gida,kai ko bata gidan in dai shi yana nan kuma ba makaranta za suje ba toh zama sukeyi su jirata,saboda san su da takeyi da kuma irin garar da take had'a musu,duk abinda yaro yake so in dai tana dashi to anyi angama maye ya auri makauniya"in dai abin ta6akalashe ne. Toh Lillahi warasulihi me irin wannan halin ce,za a ce baza ta bar nata Ya'yan suzo duniya ba saboda karatu?Anya kuwa?Yariga yasan Yaya Asma'u kowa ma za ta iya kushewa tazaga in dai taku batazo d'aya ba.Yakad'a kai cikin sauke numfashi"ALLAH yakyauta. Tabishi da kallan mamaki"ALLAH yakyauta fa kace? Eh Yaya Asma'u to me zance daya wuce haka?
Tadad'a gyara zama"kai ko kake da abin cewa,cene da ita aure za kayi...kayi auren ka amarya tazo taita haifa maka Ya'ya,toh idan taga Ya'yan kake so taga amaryar taka tafara cika maka gidan da sanyin idanu to ai zata daina abinda takeyi na tsarin iyali ko kuwa?Toh zanyi tunani.Tamik'e"ya dai kamata,ni me zan samune a gidan? Tana fad'in haka ta nufi d'akin da suke ajiye kayayyaki tagama dube-dubenta tafito"kome ma ya k'are.Yauwa gwamma da kika gani ganin idanunki,dana fad'a miki ba kome ba yadda za kiyiba,kin san ni d'an albashine ga shi kuma wata yakai tsakiya,abubuwan sai dai godiyar Ubangijinmu a kowani hali da yanayi.
Taja dogon tsaki tana mishi kallon uku ahu"amma a hakan kake k'ok'arin biya mata wasu mak'udan kud'ad'e dan tacigaba da karatu, tamik'a mishi hannu"ni bani abinda kayi niyyar bani kawai in tafi.Zan ai ko miki dashi har gida,Yaya Asma'u kidinga tausaya min mana.Tanunashi da yatsa"kai d'in?Na rantse da girman ALLAH ba ka da matausaya.Yakalleta da mad'aukakin mamaki yana nuna kanshi"ni d'in ne bani da matausaya Yaya Asma'u?Ko shakka babu dan ni banga matausayan ba,ba d'a ba jika to ko hidimar me kakeyi da har za a tausaya maka saboda yawan buk'atu?Daga kai sai matarka kuke cin karanku ba babbaka,takalleshi"za ka bani ne ko sai madugar ta dawo in zo in kar6a? Baice kome ba yasa hannu a aljihun gabar rigarshi yaciro kud'ad'en ciki yana nuna mata"kingani yan canjine wallahi bani da kud'i.Tasa hannu takar6a"eh kawo da hanau gwamma mannau ni na wuce.Yabita da kallo har tafita a D'akin-shak'atawar, yagirgiza kai "Yaya Asma'u matsala,ALLAH yashirye ta da masu hali irin na ta.
Sun dawo sallar la'asar da yammacin,shi da Musaddiq suka tsaya a k'ofar gidan suna tattauna al'amuran daya shafi kasuwancinsu ta dawo daga makaranta,ta tsaya suka gaisa da Musaddiq sannan tawuce ciki da mamakin kallan k'urillan da Julaibib yake binta dashi wanda ba halinshi bane yawan kallan da har sai kaga munin mutum.Tana kwance a tsakar d'akin yashigo,tamik'e zaune suna kallan-kallo na wucewar wasu dak'ik'u "Yaya D'ansarai lafiya kuwa? Me yafaru ne? Yasunkwui da kai,sai gwiwoyinta suka sage dan ta san wannan halin na shi tuntuni in dai yasunkwui da kai to bazaiyi magana ba ko da menene,tajingina bayanta da kujera tare da lumshe idanun ta,tunani barkatai ya cika k'wak'walwarta"ita dai tasan lafiyar ALLAH suka rabu har tana tsokanarshi
"Zaujiii...kafin in dawo kamana faten tsaki mana.Yagalla mata harara"na rantse da ALLAH tun kafin wankin bargo yakaiki ga dare ki tsaya kiyi abinki, danni ba bawa bane.Takyalkyle da dariya wato ya rama abinda ta ta6a fad'a mishi shekarun baya,farkon auren su kenan.Tawani marairaice"haba mijin Sudaida tamu dakai fa ba ta 6aci,kar fa faten tsaki yasa a ganmu a rana,tarik'o hannayenshi"dan darajar k'auna da soyayyata da take dank'are anan tad'an daki k'irjinshi dai-dai saitin da zuciya take, kamana faten tsaki,sukayi dariya,yagyad'a kai"eh zanyi amma ba fate ba tunda nima a wancan lokacin ba a hanani ba sai dai an jamin zarene.
Yamik'e,tabishi da kallo"Yaya D'ansarai... takira sunanshi.Yakalleta kawai"dan ALLAH kayi hak'uri idan na maka wani abu ne.Yayi kamar baiji abinda tafad'a ba,zuwa can kuma yasake kallanta sai yad'anyi murmushi yad'auki mukullin mota a saman tebur yafita.Ta lumshe idanun ta tanata ayyane-ayyabe a zuci.
A sanda hantsi yadubi ludayi rana ta haske ko'ina na safiyar talata,tana zaune a in da ta idar da sallar walha Hauwa'u tashigo tana fad'in"ina wannnan mijin naki me bak'in idanu da ba ya san zuwa gaisheni? Abokan wasa suke da Julaibib Ya'ya maza amma tasu da Sudaida ta zo d'aya,suna mutunta juna.Sudaida takama ha6a"yanzu mijin nawane me bak'in idanu Hauwa'u? Tajijjiga kai 'tabbasss,to ni duk zuri'ar D'ansarai da wanda yafishi bak'i ne?Sudaida tad'an harareta"lallai daga yau na san in da zan ajiyeki tunda kike cima rabin raina fuska a gaban idanuna,to amma kuma kyau tsagwaron shi da wanda yakama k'afar Yaya D'ansarai nahhh a duk zuri'ar Doctor Julaibb D'ansarai? Bata bata masa ba taje tad'auko lemun peach.
Sudaida tawatsa hannaye"ahab ni dama na san irin abin nan ne na na makaho da yace ido da wari.Hauwa'u tayi murmushi"mu ai gaba d'aya a zuri'ar Doctor Julaibib Abdullahi D'ansarai kyawawane.Sudaida tagyad'a kai"muma ai hakan take a zuri'ar Ibrahim Me-Lambu.Sukayi dariya sannan suka gaisa suna hirarsu ta yaushe gamo dan sun d'an kwana biyu basu ga juna ba saboda yanayin karatun Sudaida da baya barinta zama a gida musamma tada fara karatun degree.