Sashe 34
Gwajin Dafi Complete Hausa Novel · about 8 min read
Yafito daga mota yana kallan ta, tana sanye da shadda me maik'o ruwan makuba tayi kyau sosai a cikin yammacin"Bilkisu Megadon zinare...zinariya kike kinfi azurfa,na rasa yadda zanyi in fasalta miki irin kyan da kike k'arayi amaryar D'ansarai.Tasunkwui da kai ganin wani irin kallo dayake mata,abinda yake so tattausan jajayan labbanta kamar ta turasu da jan jambaki "wai yau saura kwana nawa yarage muzama abu d'aya?Tagirgiza kai"nima ban sani ba,dan bana lissafi.Sai yakama kai"Innalillahi Megado bakya lissafi?Lallai baki damu dani kamar yadda nadamu dake ba.Tayi murmushi me sauti, kumatunta suka lotsa"ai ba anan take ba Julaibib, abari agani mana an ba bature 'yar bak'ar fata. Yagyad'a kai"kema kince wani abu,ALLAH yabamu rai da lafiya yanuna mana lokacin.
Sudaida takalleshi"Sinan jiya inata d'aga maka hannu.Fargaba taka ma shi, da d'an rawar murya yace"jiya da yaushe?Tayi shiru cikin nazarin shi kamar ya shiga rud'u"jiya da yamma, lafiya kuwa?Yasa hannu yashare zufan daya tsatstsafo mishi a goshi"jiya ya yi kato6ara amma da rana abin yafaru.Yad'anyi murmushi"a ah ba kome, kiyi hak'uri ban ganki bane. Nima ai na san da ka ganni baza ka shareni ba.
Tibishi aka sauke akan mashin yak'araso wajan cikin tam6ele da sambatun da kamru uwar laifi take haifarwa,yamik'ama Sinan hannu"sai ka bani kud'in da zan sallami me mashin ko?Dasauri yaciro yabashi; yajuya cikin irin tafiyar bugaggun mashaya"ka rufa ma kanka asiri da wallahi yau allura sai ta tono garma,banza kawai,wawa.Suka bishi da kallo Sudaida toshe da hanci saboda wari da hamamin daya cika wajan,ta tsirtar da miyau"kai ALLAH ya sauwak'e...ya amsa da amin.Ya bud'e baki zai mata magana sai ga Tibishi yasake dunfaro su"kai d'an iska kura da fatar akuya.Sinan yamik'e da sauri"Sudaida shiga gida kawai anjima zan dawo,tajuya da sauri dan cikinta ya fara hautsinewa saboda warin Tibishi. Yaja shi suka bar k'ofar gidan.
Danbarwa sosai sukayi da Tibishi bayan mayen uwar laifin ta sakeshi"Yahankad'e shi yafad'i tabaya,Sinan yafara nuna shi da yatsa"kar ka sake biyoni wajan Sudaida.Yamishi wani kallo"ALLAH ko?Na Sudaida ba da kanka asare idan kaje gida kace ya fad'i,haka kirarin na ku na hausawa yake ko?Eh hakane saura na Katafawa,yayi dariyar tura haushi"ai sama-sama kake jin yaran Kataf dan haka kona maka ba zaka fahimta ba,yamik'e yana kakka6e bayan wandan shi"ajuri zuwa rafi...wannan ma karin maganar ku ta hausawa ce ko?Sinan yakai mishi naushi cikin tafasar zuciya,shima da zafin nama yakauce yana fad'in"yau dai baka san gani na,to gwamma cikin girma da arziki in san inda dare yamin,yad'aga hannu yana mishi adabo sai mun had'u a D'One.
Aminu yana aikin sticker na wani biki da aka bashi kwangila,Sudaida tashiga da sallama, yace yauwa dama ina neman d'an tayan aiki na leka d'akin ku banga kowa ba,tazauna tana tayashi suna hira har suka gama,sannan ta tambaye shi abinda take so ta tambayar shi "Yaya Aminu Sinan baya shaye-shaye kuwa? Yamata kallan nazari"me yasa kikayi wannan tambayar Sudaida?Saboda duk abokan dayake mu'amala dasu yan maro ne (wiwi)Tibishi kuma bayan maro har uwar laifi yana korawa,idan hali bai zo d'aya ba anya za'ayi abota?Ni kwanaki ya min bayani amma danayi d'an nazari sai nake ganin kamar akwai lauje cikin nad'i.
Gaskiya a iya sani na dashi baya shan kome,to amma kinzo da magana abar dubawa,kibar kome a hannuna,zan bincika koma menene zamu gano Insha-ALLAH,yad'an d'age mata gira"kinga ne ko?Tayi yar dariya na gane, ALLAH yabarka da Siddika.Tazama sarauniyar Aminu kamar yadda kika zama sarauniyar Sinan ko?Sukayi dariya.Tana jin k'aunar Aminu fiye da duk sauran Yayyin su saboda sauk'in kan shi,yana jan su ajiki kamar ba babba ba,wasu lukutan har wajan budurwar shi Siddika tana raka shi hira,ko kuma yaba ta abu takai mata,shi Yaya Adnan shine me irin halin Umma baya san raini ko kad'an,da shine babban gidan nan ai da sun gama kad'ewa har ganyan su dan har yafi Yaya Musaddiq za fi.
'Yan lek'en asiri yasa amma basu gano mishi kome game da abotar Tibishi da Sinan ba.Yakalleta da kulawa,sun dai tabbar suna tare kuma sauran suna shaye-shayensu amma ko karan taba su dai da idanun su basu ga Sinan dashi ba,dan haka shawarar da zan ba ki tunda kin yadda dashi a matsayin mijin da za ki aura to karki tsananta binciken shi, babu wanda za'a tsananta ma bincike face sai an kama shi da laifi,su Baba sun amince dashi,kuma basuyi hakan ba sai da sukayi bincike,na kuma tabbatar da yana da babbar illar da zata shafi zaman takewar auran ku to baza su yadda dashi amatsayin surikiba,kiyita addu'a kina kuma nusarshe shi illar zama da irin wad'annan mutanan.To Yaya Aminu nagode. ALLAH yaba ka Siddika.Yayi murmushi.
Tana gidan Hajiya taji sallamar Julaibib.Yanad'e hannayen shi ak'irji yana kallan ta"kina kwance anan gashi can anata karatu a makaranta.Tad'an harare shi"uh na gajine yau da gobe ai sai ALLAH,dan dai rana d'aya mutum ya huta sai afara binshi da k'orafi? Yatsuguna yana duba wasu tsofaffin littafai adirowan Hajiya"hutun jaki da kaya aka ba.Tad'auki man zafi asaman kujerar"kai baka san k'afafuna ciwo suke yiba "me zai hana su ciwo tunda jiya kinsha rawar samba" daga baya suka jiyo muryar shi, Musaddiq ne.
Yagalla mata harara,sai ta sunkwui da kai"tashi ki wuce makaranta, tamarairaice"dan ALLAH Yaya Musaddiq...yatari numfashin ta shhh...yad'ora yatsan shi abaki,in dai ba so kike yi ki kwashi kashin ki a hannu ba to tashi kawai "tafara matso kwalla aranta tana addu'ar ALLAH yakawo Hajiya ita kad'aice zata ta ka mishi burki,itama d'in idan ta ga dama.Julaibib yasa musu baki"amata hak'uri mana tunda tana da lalura"wa zan ma hak'urin?Wannan yarinyar? Yanuna ta da yatsa"ai da lalurar arzikice da har pain-relief zan k'arama ta dashi,ai ka san jiya anyi Inter-School a Saint-Francis College to nan suka tafi tun safe har biyar da rabi ba makarantar da suka je ta allo data Islamiyya,ashe yauma basuje ba da safe suka kwanta bacci wai sun gaji,to d'azu ina gidan Umma takorasu kasan sun maida Mama kamar sa'ar wasan su koda tayi magana basu jiba,to su sauran sunji maganar Umma sun tafi ta yamma sai ita shafaffiya da mai tazo nan tayi kwanciyarta?Tafara kuka"ni dai ALLAH yanaji yana kuma gani banyi rawar samba ba.Yakalleta cikin fushi" karya zan miki ko?Me zai za k'afufunki suyi ciwo bayan wasan discuss kike yi indai ba rawan kika yiba?
Hajiya tashigo"yayane Sudaida kike kuka kuma?Musaddiq yayi kwafa"kyale ni da ita kawai Hajiya samun waje ne kuturu da gad'a a rama.Julaibib yadafa kafad'arshi"ka kyaleta mana wata kila bayan ciwon k'afafun akwai hujjar datasa tak'i zuwa,ka san hali da dabi'ar mata Iyayanmu, yan'uwanmu,k'anninmu sai hak'uri, sai ana kawar dakai awasu lokutan idan ba haka ba,sai su maida kai wani iri,yazame hannun Julaibib daga kafad'ar shi, yajuya yayi tafiyar shi;tasauke numfashi sai a lokacin tashak'i iskar yanci"kai Yaya Musaadiq barkono ne,yanzu haka yakema Safiyya wannan halin?Hajiya tace"barin kira miki shi yaba ki amsa dan wak'a abakin me ita ta fi dad'i.Takama ha6a"wuuu...Tabbb Hajiya rufa min asiri kar k'ilu taja bauuu...
Ya tashi sahur azumin nafila na ranar alhamis yana juya zuman dayasa a shayin na'a na'a da 'ya'yan algarib yayi tsai...cikin tunano mafarkin dayayi da daddare...
"Kasham yake gani da kayan fulani tayi kyau k'irar kalangunta ya fito rad'am,amma idan tayi magana muryar Sudaida yake ji.
Shekarun baya yayi wannan mafarkin to yanzu ma mafarkin ya dawo shi ya rasa gane kan wannan mafarkin.Yayi bismillah yafara kur6a amma ko kwata bai sha ba kome ya gundire shi,shayin yamishi wani irin d'and'ano mara dad'i,ya ajiye kofin a saman tebur.Yad'auki farar hular zita yasa yad'auki Alqur'ani me girma yana karantawa har aka kira assalatu daga mabambantan masallatai na unguwar,yayi raka'atal fajri sannan yafito suka tafi masallaci shi da Baba.
Tana fitowa daga asibiti motar shi tana tsayawa,yabita da kallo tayi kyau a cikin fararan kayan riga da wando da d'an madaidaicin farin hijab,suka kalli juna sai yamik'a mata hannu ta san me yake so dan haka tamik'a mishi ragowan Schweppes d'in da yake hannun ta"ya ajiye a mota dashi zan yi bud'a baki "Megado kinga kyan da kike k'arawa kuwa tun bamu fara cin Shahrul-Asal (Honey Moon) ba?Ya d'aga kai sama alamar tunani"Bilkisu k'wak'walwata 6angaren nazari da tunani ta gaza gano yadda zan fasalta irin kyan da kike tayi,wai meye sirrin ne?Yazubama tattausan jajayan la66anta idanu;tayi dariyar da tun had'uwar su bata ta6a irinta agabanshi ba, kumatunta suka lotsa ciki sosai yar siririyar wushiryar ta,ta dad'a k'awata fuskar ta,Ya ilahi... shi da kanshi ya kauda kai yana jin wani irin yanayi a ilahirin gangar jiki da sararin zuciyar shi game da ita.
Wai kai kwana biyun nan me yake damun kane sai kadinga wasu maganganu kamar lokacin kafara gani na?Yamata wani kallo"yunwar so ke damun zuciya ta. Matsirga zan tafi,takawar da wannan maganar.Yakalleta cikin makaki"wani irin Matsirga kuma da safen nan?Haba kibari kid'an samu bacci koda awa uku ne,kinga aikin dare kika yi na san baki yi bacci ba,idan kika d'an huta bayan azahar ba sai ki tafi ba?"ni dai dan ALLAH yanzu nake san tafiya kar inyi hutun jaki da kaya aka,agida sai in huta gaba d'aya.A ah Megado ban yadda ba,ba ranar lahadi da yamma kika dawo daga Matsirgan ba?Tagyad'a kai"Inna nake san gani, tayi yar dariya"wallahi gobe da safe zan dawo Insha-ALLAH.Ba ga waya ba kikara ta mana.Tad'an marairaice"ni dai nafi so inganta ganin idanu na.Yad'an harareta"shikenan tunda kin na ce sai kin tafi to muje in kaiki,idan muka kwana sai mubugo sammako da sassafe dan nima Zari'a zani a goben.
Tad'an bud'e idanu dan mamaki"ka kwana a ina?Bai bata amsa ba yashiga mota yazauna sannan yakalle ta"shigo mutafi mun... kiran wayar Baba takatse shi yad'aga da sallama "kazo yanzu na yi baki suna jiran ka a shago.Ya amsa cikin ladabi"to Baba gani nan zuwa.Yad'anyi jimmm...D'ansarai lafiya kuwa?Kiyi hak'uri Megado na so kwarai mutafi tare to sai dai hak'ata bata tadda ruwa ba,akwai bak'in da suke jirana a shago.A ah ba kome" tashiga ta zauna yaja motar.
Sudaida takalleshi"Sinan jiya inata d'aga maka hannu.Fargaba taka ma shi, da d'an rawar murya yace"jiya da yaushe?Tayi shiru cikin nazarin shi kamar ya shiga rud'u"jiya da yamma, lafiya kuwa?Yasa hannu yashare zufan daya tsatstsafo mishi a goshi"jiya ya yi kato6ara amma da rana abin yafaru.Yad'anyi murmushi"a ah ba kome, kiyi hak'uri ban ganki bane. Nima ai na san da ka ganni baza ka shareni ba.
Tibishi aka sauke akan mashin yak'araso wajan cikin tam6ele da sambatun da kamru uwar laifi take haifarwa,yamik'ama Sinan hannu"sai ka bani kud'in da zan sallami me mashin ko?Dasauri yaciro yabashi; yajuya cikin irin tafiyar bugaggun mashaya"ka rufa ma kanka asiri da wallahi yau allura sai ta tono garma,banza kawai,wawa.Suka bishi da kallo Sudaida toshe da hanci saboda wari da hamamin daya cika wajan,ta tsirtar da miyau"kai ALLAH ya sauwak'e...ya amsa da amin.Ya bud'e baki zai mata magana sai ga Tibishi yasake dunfaro su"kai d'an iska kura da fatar akuya.Sinan yamik'e da sauri"Sudaida shiga gida kawai anjima zan dawo,tajuya da sauri dan cikinta ya fara hautsinewa saboda warin Tibishi. Yaja shi suka bar k'ofar gidan.
Danbarwa sosai sukayi da Tibishi bayan mayen uwar laifin ta sakeshi"Yahankad'e shi yafad'i tabaya,Sinan yafara nuna shi da yatsa"kar ka sake biyoni wajan Sudaida.Yamishi wani kallo"ALLAH ko?Na Sudaida ba da kanka asare idan kaje gida kace ya fad'i,haka kirarin na ku na hausawa yake ko?Eh hakane saura na Katafawa,yayi dariyar tura haushi"ai sama-sama kake jin yaran Kataf dan haka kona maka ba zaka fahimta ba,yamik'e yana kakka6e bayan wandan shi"ajuri zuwa rafi...wannan ma karin maganar ku ta hausawa ce ko?Sinan yakai mishi naushi cikin tafasar zuciya,shima da zafin nama yakauce yana fad'in"yau dai baka san gani na,to gwamma cikin girma da arziki in san inda dare yamin,yad'aga hannu yana mishi adabo sai mun had'u a D'One.
Aminu yana aikin sticker na wani biki da aka bashi kwangila,Sudaida tashiga da sallama, yace yauwa dama ina neman d'an tayan aiki na leka d'akin ku banga kowa ba,tazauna tana tayashi suna hira har suka gama,sannan ta tambaye shi abinda take so ta tambayar shi "Yaya Aminu Sinan baya shaye-shaye kuwa? Yamata kallan nazari"me yasa kikayi wannan tambayar Sudaida?Saboda duk abokan dayake mu'amala dasu yan maro ne (wiwi)Tibishi kuma bayan maro har uwar laifi yana korawa,idan hali bai zo d'aya ba anya za'ayi abota?Ni kwanaki ya min bayani amma danayi d'an nazari sai nake ganin kamar akwai lauje cikin nad'i.
Gaskiya a iya sani na dashi baya shan kome,to amma kinzo da magana abar dubawa,kibar kome a hannuna,zan bincika koma menene zamu gano Insha-ALLAH,yad'an d'age mata gira"kinga ne ko?Tayi yar dariya na gane, ALLAH yabarka da Siddika.Tazama sarauniyar Aminu kamar yadda kika zama sarauniyar Sinan ko?Sukayi dariya.Tana jin k'aunar Aminu fiye da duk sauran Yayyin su saboda sauk'in kan shi,yana jan su ajiki kamar ba babba ba,wasu lukutan har wajan budurwar shi Siddika tana raka shi hira,ko kuma yaba ta abu takai mata,shi Yaya Adnan shine me irin halin Umma baya san raini ko kad'an,da shine babban gidan nan ai da sun gama kad'ewa har ganyan su dan har yafi Yaya Musaddiq za fi.
'Yan lek'en asiri yasa amma basu gano mishi kome game da abotar Tibishi da Sinan ba.Yakalleta da kulawa,sun dai tabbar suna tare kuma sauran suna shaye-shayensu amma ko karan taba su dai da idanun su basu ga Sinan dashi ba,dan haka shawarar da zan ba ki tunda kin yadda dashi a matsayin mijin da za ki aura to karki tsananta binciken shi, babu wanda za'a tsananta ma bincike face sai an kama shi da laifi,su Baba sun amince dashi,kuma basuyi hakan ba sai da sukayi bincike,na kuma tabbatar da yana da babbar illar da zata shafi zaman takewar auran ku to baza su yadda dashi amatsayin surikiba,kiyita addu'a kina kuma nusarshe shi illar zama da irin wad'annan mutanan.To Yaya Aminu nagode. ALLAH yaba ka Siddika.Yayi murmushi.
Tana gidan Hajiya taji sallamar Julaibib.Yanad'e hannayen shi ak'irji yana kallan ta"kina kwance anan gashi can anata karatu a makaranta.Tad'an harare shi"uh na gajine yau da gobe ai sai ALLAH,dan dai rana d'aya mutum ya huta sai afara binshi da k'orafi? Yatsuguna yana duba wasu tsofaffin littafai adirowan Hajiya"hutun jaki da kaya aka ba.Tad'auki man zafi asaman kujerar"kai baka san k'afafuna ciwo suke yiba "me zai hana su ciwo tunda jiya kinsha rawar samba" daga baya suka jiyo muryar shi, Musaddiq ne.
Yagalla mata harara,sai ta sunkwui da kai"tashi ki wuce makaranta, tamarairaice"dan ALLAH Yaya Musaddiq...yatari numfashin ta shhh...yad'ora yatsan shi abaki,in dai ba so kike yi ki kwashi kashin ki a hannu ba to tashi kawai "tafara matso kwalla aranta tana addu'ar ALLAH yakawo Hajiya ita kad'aice zata ta ka mishi burki,itama d'in idan ta ga dama.Julaibib yasa musu baki"amata hak'uri mana tunda tana da lalura"wa zan ma hak'urin?Wannan yarinyar? Yanuna ta da yatsa"ai da lalurar arzikice da har pain-relief zan k'arama ta dashi,ai ka san jiya anyi Inter-School a Saint-Francis College to nan suka tafi tun safe har biyar da rabi ba makarantar da suka je ta allo data Islamiyya,ashe yauma basuje ba da safe suka kwanta bacci wai sun gaji,to d'azu ina gidan Umma takorasu kasan sun maida Mama kamar sa'ar wasan su koda tayi magana basu jiba,to su sauran sunji maganar Umma sun tafi ta yamma sai ita shafaffiya da mai tazo nan tayi kwanciyarta?Tafara kuka"ni dai ALLAH yanaji yana kuma gani banyi rawar samba ba.Yakalleta cikin fushi" karya zan miki ko?Me zai za k'afufunki suyi ciwo bayan wasan discuss kike yi indai ba rawan kika yiba?
Hajiya tashigo"yayane Sudaida kike kuka kuma?Musaddiq yayi kwafa"kyale ni da ita kawai Hajiya samun waje ne kuturu da gad'a a rama.Julaibib yadafa kafad'arshi"ka kyaleta mana wata kila bayan ciwon k'afafun akwai hujjar datasa tak'i zuwa,ka san hali da dabi'ar mata Iyayanmu, yan'uwanmu,k'anninmu sai hak'uri, sai ana kawar dakai awasu lokutan idan ba haka ba,sai su maida kai wani iri,yazame hannun Julaibib daga kafad'ar shi, yajuya yayi tafiyar shi;tasauke numfashi sai a lokacin tashak'i iskar yanci"kai Yaya Musaadiq barkono ne,yanzu haka yakema Safiyya wannan halin?Hajiya tace"barin kira miki shi yaba ki amsa dan wak'a abakin me ita ta fi dad'i.Takama ha6a"wuuu...Tabbb Hajiya rufa min asiri kar k'ilu taja bauuu...
Ya tashi sahur azumin nafila na ranar alhamis yana juya zuman dayasa a shayin na'a na'a da 'ya'yan algarib yayi tsai...cikin tunano mafarkin dayayi da daddare...
"Kasham yake gani da kayan fulani tayi kyau k'irar kalangunta ya fito rad'am,amma idan tayi magana muryar Sudaida yake ji.
Shekarun baya yayi wannan mafarkin to yanzu ma mafarkin ya dawo shi ya rasa gane kan wannan mafarkin.Yayi bismillah yafara kur6a amma ko kwata bai sha ba kome ya gundire shi,shayin yamishi wani irin d'and'ano mara dad'i,ya ajiye kofin a saman tebur.Yad'auki farar hular zita yasa yad'auki Alqur'ani me girma yana karantawa har aka kira assalatu daga mabambantan masallatai na unguwar,yayi raka'atal fajri sannan yafito suka tafi masallaci shi da Baba.
Tana fitowa daga asibiti motar shi tana tsayawa,yabita da kallo tayi kyau a cikin fararan kayan riga da wando da d'an madaidaicin farin hijab,suka kalli juna sai yamik'a mata hannu ta san me yake so dan haka tamik'a mishi ragowan Schweppes d'in da yake hannun ta"ya ajiye a mota dashi zan yi bud'a baki "Megado kinga kyan da kike k'arawa kuwa tun bamu fara cin Shahrul-Asal (Honey Moon) ba?Ya d'aga kai sama alamar tunani"Bilkisu k'wak'walwata 6angaren nazari da tunani ta gaza gano yadda zan fasalta irin kyan da kike tayi,wai meye sirrin ne?Yazubama tattausan jajayan la66anta idanu;tayi dariyar da tun had'uwar su bata ta6a irinta agabanshi ba, kumatunta suka lotsa ciki sosai yar siririyar wushiryar ta,ta dad'a k'awata fuskar ta,Ya ilahi... shi da kanshi ya kauda kai yana jin wani irin yanayi a ilahirin gangar jiki da sararin zuciyar shi game da ita.
Wai kai kwana biyun nan me yake damun kane sai kadinga wasu maganganu kamar lokacin kafara gani na?Yamata wani kallo"yunwar so ke damun zuciya ta. Matsirga zan tafi,takawar da wannan maganar.Yakalleta cikin makaki"wani irin Matsirga kuma da safen nan?Haba kibari kid'an samu bacci koda awa uku ne,kinga aikin dare kika yi na san baki yi bacci ba,idan kika d'an huta bayan azahar ba sai ki tafi ba?"ni dai dan ALLAH yanzu nake san tafiya kar inyi hutun jaki da kaya aka,agida sai in huta gaba d'aya.A ah Megado ban yadda ba,ba ranar lahadi da yamma kika dawo daga Matsirgan ba?Tagyad'a kai"Inna nake san gani, tayi yar dariya"wallahi gobe da safe zan dawo Insha-ALLAH.Ba ga waya ba kikara ta mana.Tad'an marairaice"ni dai nafi so inganta ganin idanu na.Yad'an harareta"shikenan tunda kin na ce sai kin tafi to muje in kaiki,idan muka kwana sai mubugo sammako da sassafe dan nima Zari'a zani a goben.
Tad'an bud'e idanu dan mamaki"ka kwana a ina?Bai bata amsa ba yashiga mota yazauna sannan yakalle ta"shigo mutafi mun... kiran wayar Baba takatse shi yad'aga da sallama "kazo yanzu na yi baki suna jiran ka a shago.Ya amsa cikin ladabi"to Baba gani nan zuwa.Yad'anyi jimmm...D'ansarai lafiya kuwa?Kiyi hak'uri Megado na so kwarai mutafi tare to sai dai hak'ata bata tadda ruwa ba,akwai bak'in da suke jirana a shago.A ah ba kome" tashiga ta zauna yaja motar.