Sashe 31
Gwajin Dafi Complete Hausa Novel · about 8 min read
Iska me k'arfi tafara ta sowa garin yahad'e yayi bak'i sai cida akeyi ba k'ak'k'autawa, abubuwan hawa suka dinga k'ara guda dan tsira daga dukan ruwan watan bakwai,tak'ara sauri akwai gidan yar ajinsu Zamburan agaba sai ta samu tafake,amma ina hak'anta bata tadda ruwa ba,kad'an-kad'an yayyafi yafara sauka tanad'e hannayanta a cikin hijab,sanyi yafara ratsata tarintse idanu"wayyo ALLAH na! Shikenan sabuwar mura zata dawo!
Dagudu motar tazo tawuce ta,wacce yahango tacikin madubi yasa yayi ribas har yak'araso inda take,Caraf idanun su yahad'u yana bud'e motar,wani sanyin dad'i ya mamayeta. Yabud'e mata"to shigo mutafi mana kina ganin ruwan yana k'aruwa...tad'an harareshi sannan tashiga kamar wacce zata zauna a garwashin wuta.
Yaja motar"me kika zauna yi a makaranta? Kamar ba da ita yake magana b.Ba tambayar nake yi ba? Dak'yar kamar me ciwon baki dan haushin shi takeji tace"baccine yad'aukeni a dormitry"bai sake magana ba yacigaba da tuk'inshi cikin natsuwa,sai dai ruwan daya cigaba da zuba kamar da bak'in k'warya yasa shi gangarawa gefen titi yatsaya har sai yad'an tsagaita.
Yaya D'ansarai...
Yad'an kalleta"na'am.Taturo baki gaba"nifa gaskiya in dai ba so kakeyi in k'arasa mutuwa ba to kashe wannan mukayyib d'in(Air Condition) ...kafin tagama rufe baki tafara atishawa,sai da tayi biyar ajere"Yar hamukallah "yace mata bayan ta godema ALLAH."Yahdi kumullahu wayuslih baalakum"tasa hannu tana jan hancin ta daya fara toshewa,k'wallah yacika idanun ta dan wallahi sanyi takeji bana wasa ba gashi kayan jikinta ajik'e suke.Sai da yamaida ita heater sannan tafara dawowa hayyacinta motar ta d'auki d'umi,ruwan yad'an tsaigaita motocin dasuka tsaya kowa yaja yacigaba da tafiya.
Suna shiga gida Mama tace"Masha-ALLAH dama yanzu nake dad'a yima Adnan magana yad'auki mashin yabita makaranta yad'aukota"Yayi d'an murmushi"a hanya muka had'u dawowa ta daga Kaduna kenan.Adnan yafito daga d'akinshi yana mita"Mama banda kece da kanki kin cika min idanu kin shak'emin wuya da wallahi ba inda zani ruwa bai gama d'aukewa ba. Tagyad'a kai"to kayi zaman ka mana.Yak'arasa kulle k'ofar tashi"a haba dai Mama ai wata fuskar tafi gaban mari har abadan duniya.Yana shiga D'akin-shak'atawar yagansu...yauwa yayi yar dariya"kai madallah da autan Inna.Yamik'a mishi hannu sukayi musafaha,yajefama Sudaida mukullin"kai min d'aki".
Khausar tashigo da lemu ta'ajiye agaban shi bismillah fa.Yagirgiza kai"bazan shaba,kirasa abinda za ki kawomin sai lemu me sanyi bayan yanzu aka gama tsuuga ruwan sama har da k'ank'ara?Yamik'e dai-dai da shigowar Mama."Mama na wuce.A ah ka tsaya yanzu nasa Sudaida takawo maka kayan bud'a baki.Yad'an shafa kai"Nagode Mama amma kiyi hak'uri sauri nake yi dan gidan Hajiya zani kafin in wuce gida" To ai ba kome musha ruwa lafiya.Amin Mama.
Hey autan Inna...
Zai shiga mota yaji kiranta yajuya yana kallanta ta canja kayan jikinta da riga da wando kirar Pakistan ruwan k'asa da yarfin k'anana filawoyi ruwan hoda me haske,tad'ora farar rigar sanyi tasak'a da farar hula me harafin M.Gashi inji Mama.Bai kar6i ledar ba yace me wannan harafin M d'in yake nufi?Takai hannu tashafa harafin"Masoyi na Sinan ko da wani masoyi ne bayan shi?Yamata wannan rikitaccen kallan nashi takauda kai "gashi ni sauri nake yi. Yashige mota ya zauna"ki kaimin gida yayi tafiyar shi.Tabi danjojin motar da kallo har ta 6ace ma ganin ta.Takalli ledar taja dogon tsaki"kawai dan kabani wahala,shi dai wannan halin na shi ALLAH yasauwak'e mishi...tashige gida tana k'unk'uni.
A safiyar asabar suna hirarsu da Inna yana shan shayin na'a-na'a da ya'yan algarib tashigo da sallama, tagaishe da Inna sannan tazauna a kusa da ita tana fad'a mata sak'on Hajiya.
Yamaida hankalin shi ga sauraran wak'ar wani balarabe yana wake Habibti d'in shi da irin soyayyar daya ke mata wai"ya kamu da yunwar son ta,kuma ita kad'ai take da irin nau'in abincin da za ta bashi idan yaci sai yadawo hayyacin shi,dan yanzu shi ya zama kamar gawane da rai"yad'auki remote yad'an rage k'ara yana cigaba da sauraran tsadaddun kalmomin da yaketa bayyana irin k'aunar shi gareta me sanya zuciya bugawa a cikin shauk'in so,har baitin k'arshe sannan ya canja tasha.
Kiran daya shigo wayar shi yasa yamik'e yafita,Sudaida tabishi da kallo sai kuma tamik'e itama dan makarantar allo za ta wuce.
Yana tsaye a k'ofar gida yana wayar cikin sakin fuska,yayi k'asa da murya yana gyad'a kai"na sani Megado amma na manta ne,ALLAH yamiki albarka da wannan tunatarwan.Yayi jimmm...yana sauraro"to shikenan karki damu kinji ko?...yauwa to nagode sai na shigo.
Tawuce kamar bata ganshi ba.
"Am Sudaida...
Takalleshi fuska a had'e.Yayi yar dariyar data bata mamaki dan ba kasafai yake hakan ba.Yauma kin shigo gidan nan kin kuma ganni ganin idanun ki amma baki gaisheni ba,wai in tambayeki mana? Kallanshi tayi batace kome ba "Sudaida... wannan cin mad'acin da kike min bana jin dad'in shi kona miki wani laifi ne?Tad'an turo baki gaba sannan ta kauda kai"ni ba kome.Anya zan yadda dake kuwa?Takalli siririn agogon dake d'aure a hannunta sai kawai tajuya "gwamma da kai auran ka da gata kar inje insha dukan makara.Ki tsaya muyi sallama dan baza ki dawo makaranta ki same niba.Jikinta yayi sanyi amma bata tsaya ba tacigaba da tafiya"To ALLAH yakiyaye hanya ai zamuyi waya.Ki tsaya ki kar6i"tasa gudu nifa bana so.Yabita da kallo yana wata kissima a zuci.
Jikokin Hajiya sun cika mata gida sunata sha'anin gabansu.Sudaida takallesu"kun san ALLAH cikin makaranta zan koma(hostel)na gaji da trekking sai randa aka ga dama za a zo a d'aukemu.Nasmat takama ha6a"to makarantar allon kiyi yaya da ita? Idan an ba da hutu na dawo gida sai in d'ora daga in da natsaya.Hajiya tasa musu baki"yanzu ke saboda makarantar boko za ki bar makarantar Mahammadiyya? Bayan shine a hakku akanki?Taturo baki"ai ba cewa nayi na daina ba,kuma ai nafad'a ma Baba ya kuma amince.Hajiya tamata dakuwa"to ni ban amince ba zai kuma zo yasameni bokon banza bokon wofi, bokoko a wuta. Nasmat ta kyalkyake da dariya"Ke Hajiya bokon kike ma wannan zagin kamar bakiyi ba?eh na zaga,dan kayi karatun boko indai ba karatun Muhammadiyy ai shirme kayi...ko ba ga sunan ba marasa addinin k'wararrune a fagage mabambanta na cigaban rayuwa amma sai kika mutum wai yasa abinda zai bautama sai saniya ko rana ko kwad'o...wannan ba 6atan basira bace da rashin sanin tauhidi?Ai ba abinda zai baku rayuwa me inganci sama da Alqur'ani da hadisan Manzon ALLAH dan ya tattara kome shak'undum kenan.
Washe gari kuwa data je gaishe da Baba yake fad'a mata komawarta cikin makaranta an soke shi, Hajiya tazo da magana abar dubawa,yamik'a mata babban envelop foam ne guda biyar a ciki,ki kaima Nasmat na ta gida ko wacce tacike ranar Juma'a zaku fara zuwa makaranta,tasa hannu biyu takar6a"to Baba ta tashi tafita.
"HAYATUDDEEN ISLAMIYYA SAMARUN-KATAF"
yanzu har Samaru zamu dinga zuwa?Wallahi duk Hajiya ce da wannan aikin saboda kawai nace zan koma cikin makaranta shine har ranakun k'arshen makon ma bazata barmu mud'an sarara ba?Taja tsaki tana k'unk'uni,tad'auki biro tana ciccike inda ake so aciken.
Maganar Julaibib da Bilkisu ta kan-kama sun kai kome da a ke kaiwa an kuma tsayar da lokacin biki watanni uku masu zuwa dai-dai da gama karatun ta. Julaibib ya tafi bautar k'asa,jahar Bauchi aka turashi angama basu horan sati biyu a sansaninsu(camp)yakoma inda zaiyi service d'inshi a k'aramar hukumar Azare.
Sai da yayi wata d'aya sannan ya dira a Zonkwa dawani yammacin laraba rana ta tafi zata fad'i magriba na shirin kunno kai,yatsaya yayi sallar magriba sannan yatafi gida.Inna tayi murnar ganinshi dan bazata ya mata bai fad'a mata ko awaya ba.Baije ko ina ba sunata hirarasu ta yaushe gamo yana cin abinci ita kuma tanata kalan hotunan dasuka d'auka lokacin da a ke basu horo(training)tad'aga wani hoto tana murmushi ashe kunsha wahala?Yagyada kai"Eh Inna akwai wahala dan sojojine suka bamu horon cikin dare zasu kafa su tsare kowa sai yafito su fara bamu horo tayi yar dariya"lallai kun zama k'ananan sojoji.Amma ni ban wani sha wahala ba. Tagyada kai"ai baza kashaba tunda ka saba motsa jiki da manyan k'arafa yanzu har mata sai sunyi wannan?Eh har su sai sunyi masu tsohon ciki ne kawai naga an d'aga musu k'afa.Taja tsaki wannan tsarinne kawai bai min ba.Yad'anyi murmushi"To ya zamuyi Inna tsarin ne yazo da haka amma Insha-ALLAH bama cire rai da wata rana za a samu manya a harkar masu addini da zasu zamantar da abin dai-dai da shari'ar musulunci a raba mata musulmai da irin wannan shigar a bainan-nasi.Inna tad'aga hannu "Allahumma amin Julaibib.
K'arfe shida na safiya sukayi kaci6is akwanar gidansu,dawowar shi kenan daga masallaci sallar asubahi,k'afafunta sanye cikin takalmi sneaker fari igiyoyin d'aurewa ruwan bula,wando ruwan bulu,farar riga sai hijab iya gwiwa ruwan bula sun sha guga tana goye da bakar jaka da Maths-set a hannunta.Tad'an bud'e idanu cikin mamakin ganin shi"Kai Yaya D'ansarai saukar yaushe? Yabita da kallo duk da garin bai gama wayewa ko ina yayi haske ba amma dai tayi kyau"Jiya gab da magriba.Excursion za kuje? Tasake kallan farin agogon dake d'aure a hannunta na dama"ba wani excursion Mr Goje malamin turanci(English)ne yabamu jinga (Assignment) kuma to be submitted before seven O'clock"to shine kike wannan saurin kamar za ki tashi sama?Tagyad'a kai"eh mana wallahi ji nake kamar inyi tsuntsuwa,wai dan ma ba acikin makaranta muke ba shine yad'aga mana k'afa,su yan cikin hostel ai k'arfe shida yabasu,duk wacce tawuce shida koda da dak'ik'a d'aya ne bazai k'ar6a ba,shikenan kuma fa a matsayn C.A test d'in mune,kuma nayita rok'on Yaya Adnan yakaini yace ba abinda zai fitar dashi awannan sanyin,ai dai ALLAH yajik'an Yaya Aminu ba dan yamutu ba dayana gida na san zai kai ni.Tayi gaba da sauri.
A bayan ta taji horn yabud'e mata kofa"ke Sudaida zo ki shiga mutafi.Yad'an kalleta bayan sun hau titi"lallai baku raina Mr Goje ba.Yaya Julaibib wargi waje yake samu,shi wannnan Malamin mugune na gasken-gaske gashi kuma yanzu shine Labour Master,ya yanka ma mutum k'atan fili iya ganinka yace sai ka nome shi wallahi k'aramin abu ne a wajan shi.
Dagudu motar tazo tawuce ta,wacce yahango tacikin madubi yasa yayi ribas har yak'araso inda take,Caraf idanun su yahad'u yana bud'e motar,wani sanyin dad'i ya mamayeta. Yabud'e mata"to shigo mutafi mana kina ganin ruwan yana k'aruwa...tad'an harareshi sannan tashiga kamar wacce zata zauna a garwashin wuta.
Yaja motar"me kika zauna yi a makaranta? Kamar ba da ita yake magana b.Ba tambayar nake yi ba? Dak'yar kamar me ciwon baki dan haushin shi takeji tace"baccine yad'aukeni a dormitry"bai sake magana ba yacigaba da tuk'inshi cikin natsuwa,sai dai ruwan daya cigaba da zuba kamar da bak'in k'warya yasa shi gangarawa gefen titi yatsaya har sai yad'an tsagaita.
Yaya D'ansarai...
Yad'an kalleta"na'am.Taturo baki gaba"nifa gaskiya in dai ba so kakeyi in k'arasa mutuwa ba to kashe wannan mukayyib d'in(Air Condition) ...kafin tagama rufe baki tafara atishawa,sai da tayi biyar ajere"Yar hamukallah "yace mata bayan ta godema ALLAH."Yahdi kumullahu wayuslih baalakum"tasa hannu tana jan hancin ta daya fara toshewa,k'wallah yacika idanun ta dan wallahi sanyi takeji bana wasa ba gashi kayan jikinta ajik'e suke.Sai da yamaida ita heater sannan tafara dawowa hayyacinta motar ta d'auki d'umi,ruwan yad'an tsaigaita motocin dasuka tsaya kowa yaja yacigaba da tafiya.
Suna shiga gida Mama tace"Masha-ALLAH dama yanzu nake dad'a yima Adnan magana yad'auki mashin yabita makaranta yad'aukota"Yayi d'an murmushi"a hanya muka had'u dawowa ta daga Kaduna kenan.Adnan yafito daga d'akinshi yana mita"Mama banda kece da kanki kin cika min idanu kin shak'emin wuya da wallahi ba inda zani ruwa bai gama d'aukewa ba. Tagyad'a kai"to kayi zaman ka mana.Yak'arasa kulle k'ofar tashi"a haba dai Mama ai wata fuskar tafi gaban mari har abadan duniya.Yana shiga D'akin-shak'atawar yagansu...yauwa yayi yar dariya"kai madallah da autan Inna.Yamik'a mishi hannu sukayi musafaha,yajefama Sudaida mukullin"kai min d'aki".
Khausar tashigo da lemu ta'ajiye agaban shi bismillah fa.Yagirgiza kai"bazan shaba,kirasa abinda za ki kawomin sai lemu me sanyi bayan yanzu aka gama tsuuga ruwan sama har da k'ank'ara?Yamik'e dai-dai da shigowar Mama."Mama na wuce.A ah ka tsaya yanzu nasa Sudaida takawo maka kayan bud'a baki.Yad'an shafa kai"Nagode Mama amma kiyi hak'uri sauri nake yi dan gidan Hajiya zani kafin in wuce gida" To ai ba kome musha ruwa lafiya.Amin Mama.
Hey autan Inna...
Zai shiga mota yaji kiranta yajuya yana kallanta ta canja kayan jikinta da riga da wando kirar Pakistan ruwan k'asa da yarfin k'anana filawoyi ruwan hoda me haske,tad'ora farar rigar sanyi tasak'a da farar hula me harafin M.Gashi inji Mama.Bai kar6i ledar ba yace me wannan harafin M d'in yake nufi?Takai hannu tashafa harafin"Masoyi na Sinan ko da wani masoyi ne bayan shi?Yamata wannan rikitaccen kallan nashi takauda kai "gashi ni sauri nake yi. Yashige mota ya zauna"ki kaimin gida yayi tafiyar shi.Tabi danjojin motar da kallo har ta 6ace ma ganin ta.Takalli ledar taja dogon tsaki"kawai dan kabani wahala,shi dai wannan halin na shi ALLAH yasauwak'e mishi...tashige gida tana k'unk'uni.
A safiyar asabar suna hirarsu da Inna yana shan shayin na'a-na'a da ya'yan algarib tashigo da sallama, tagaishe da Inna sannan tazauna a kusa da ita tana fad'a mata sak'on Hajiya.
Yamaida hankalin shi ga sauraran wak'ar wani balarabe yana wake Habibti d'in shi da irin soyayyar daya ke mata wai"ya kamu da yunwar son ta,kuma ita kad'ai take da irin nau'in abincin da za ta bashi idan yaci sai yadawo hayyacin shi,dan yanzu shi ya zama kamar gawane da rai"yad'auki remote yad'an rage k'ara yana cigaba da sauraran tsadaddun kalmomin da yaketa bayyana irin k'aunar shi gareta me sanya zuciya bugawa a cikin shauk'in so,har baitin k'arshe sannan ya canja tasha.
Kiran daya shigo wayar shi yasa yamik'e yafita,Sudaida tabishi da kallo sai kuma tamik'e itama dan makarantar allo za ta wuce.
Yana tsaye a k'ofar gida yana wayar cikin sakin fuska,yayi k'asa da murya yana gyad'a kai"na sani Megado amma na manta ne,ALLAH yamiki albarka da wannan tunatarwan.Yayi jimmm...yana sauraro"to shikenan karki damu kinji ko?...yauwa to nagode sai na shigo.
Tawuce kamar bata ganshi ba.
"Am Sudaida...
Takalleshi fuska a had'e.Yayi yar dariyar data bata mamaki dan ba kasafai yake hakan ba.Yauma kin shigo gidan nan kin kuma ganni ganin idanun ki amma baki gaisheni ba,wai in tambayeki mana? Kallanshi tayi batace kome ba "Sudaida... wannan cin mad'acin da kike min bana jin dad'in shi kona miki wani laifi ne?Tad'an turo baki gaba sannan ta kauda kai"ni ba kome.Anya zan yadda dake kuwa?Takalli siririn agogon dake d'aure a hannunta sai kawai tajuya "gwamma da kai auran ka da gata kar inje insha dukan makara.Ki tsaya muyi sallama dan baza ki dawo makaranta ki same niba.Jikinta yayi sanyi amma bata tsaya ba tacigaba da tafiya"To ALLAH yakiyaye hanya ai zamuyi waya.Ki tsaya ki kar6i"tasa gudu nifa bana so.Yabita da kallo yana wata kissima a zuci.
Jikokin Hajiya sun cika mata gida sunata sha'anin gabansu.Sudaida takallesu"kun san ALLAH cikin makaranta zan koma(hostel)na gaji da trekking sai randa aka ga dama za a zo a d'aukemu.Nasmat takama ha6a"to makarantar allon kiyi yaya da ita? Idan an ba da hutu na dawo gida sai in d'ora daga in da natsaya.Hajiya tasa musu baki"yanzu ke saboda makarantar boko za ki bar makarantar Mahammadiyya? Bayan shine a hakku akanki?Taturo baki"ai ba cewa nayi na daina ba,kuma ai nafad'a ma Baba ya kuma amince.Hajiya tamata dakuwa"to ni ban amince ba zai kuma zo yasameni bokon banza bokon wofi, bokoko a wuta. Nasmat ta kyalkyake da dariya"Ke Hajiya bokon kike ma wannan zagin kamar bakiyi ba?eh na zaga,dan kayi karatun boko indai ba karatun Muhammadiyy ai shirme kayi...ko ba ga sunan ba marasa addinin k'wararrune a fagage mabambanta na cigaban rayuwa amma sai kika mutum wai yasa abinda zai bautama sai saniya ko rana ko kwad'o...wannan ba 6atan basira bace da rashin sanin tauhidi?Ai ba abinda zai baku rayuwa me inganci sama da Alqur'ani da hadisan Manzon ALLAH dan ya tattara kome shak'undum kenan.
Washe gari kuwa data je gaishe da Baba yake fad'a mata komawarta cikin makaranta an soke shi, Hajiya tazo da magana abar dubawa,yamik'a mata babban envelop foam ne guda biyar a ciki,ki kaima Nasmat na ta gida ko wacce tacike ranar Juma'a zaku fara zuwa makaranta,tasa hannu biyu takar6a"to Baba ta tashi tafita.
"HAYATUDDEEN ISLAMIYYA SAMARUN-KATAF"
yanzu har Samaru zamu dinga zuwa?Wallahi duk Hajiya ce da wannan aikin saboda kawai nace zan koma cikin makaranta shine har ranakun k'arshen makon ma bazata barmu mud'an sarara ba?Taja tsaki tana k'unk'uni,tad'auki biro tana ciccike inda ake so aciken.
Maganar Julaibib da Bilkisu ta kan-kama sun kai kome da a ke kaiwa an kuma tsayar da lokacin biki watanni uku masu zuwa dai-dai da gama karatun ta. Julaibib ya tafi bautar k'asa,jahar Bauchi aka turashi angama basu horan sati biyu a sansaninsu(camp)yakoma inda zaiyi service d'inshi a k'aramar hukumar Azare.
Sai da yayi wata d'aya sannan ya dira a Zonkwa dawani yammacin laraba rana ta tafi zata fad'i magriba na shirin kunno kai,yatsaya yayi sallar magriba sannan yatafi gida.Inna tayi murnar ganinshi dan bazata ya mata bai fad'a mata ko awaya ba.Baije ko ina ba sunata hirarasu ta yaushe gamo yana cin abinci ita kuma tanata kalan hotunan dasuka d'auka lokacin da a ke basu horo(training)tad'aga wani hoto tana murmushi ashe kunsha wahala?Yagyada kai"Eh Inna akwai wahala dan sojojine suka bamu horon cikin dare zasu kafa su tsare kowa sai yafito su fara bamu horo tayi yar dariya"lallai kun zama k'ananan sojoji.Amma ni ban wani sha wahala ba. Tagyada kai"ai baza kashaba tunda ka saba motsa jiki da manyan k'arafa yanzu har mata sai sunyi wannan?Eh har su sai sunyi masu tsohon ciki ne kawai naga an d'aga musu k'afa.Taja tsaki wannan tsarinne kawai bai min ba.Yad'anyi murmushi"To ya zamuyi Inna tsarin ne yazo da haka amma Insha-ALLAH bama cire rai da wata rana za a samu manya a harkar masu addini da zasu zamantar da abin dai-dai da shari'ar musulunci a raba mata musulmai da irin wannan shigar a bainan-nasi.Inna tad'aga hannu "Allahumma amin Julaibib.
K'arfe shida na safiya sukayi kaci6is akwanar gidansu,dawowar shi kenan daga masallaci sallar asubahi,k'afafunta sanye cikin takalmi sneaker fari igiyoyin d'aurewa ruwan bula,wando ruwan bulu,farar riga sai hijab iya gwiwa ruwan bula sun sha guga tana goye da bakar jaka da Maths-set a hannunta.Tad'an bud'e idanu cikin mamakin ganin shi"Kai Yaya D'ansarai saukar yaushe? Yabita da kallo duk da garin bai gama wayewa ko ina yayi haske ba amma dai tayi kyau"Jiya gab da magriba.Excursion za kuje? Tasake kallan farin agogon dake d'aure a hannunta na dama"ba wani excursion Mr Goje malamin turanci(English)ne yabamu jinga (Assignment) kuma to be submitted before seven O'clock"to shine kike wannan saurin kamar za ki tashi sama?Tagyad'a kai"eh mana wallahi ji nake kamar inyi tsuntsuwa,wai dan ma ba acikin makaranta muke ba shine yad'aga mana k'afa,su yan cikin hostel ai k'arfe shida yabasu,duk wacce tawuce shida koda da dak'ik'a d'aya ne bazai k'ar6a ba,shikenan kuma fa a matsayn C.A test d'in mune,kuma nayita rok'on Yaya Adnan yakaini yace ba abinda zai fitar dashi awannan sanyin,ai dai ALLAH yajik'an Yaya Aminu ba dan yamutu ba dayana gida na san zai kai ni.Tayi gaba da sauri.
A bayan ta taji horn yabud'e mata kofa"ke Sudaida zo ki shiga mutafi.Yad'an kalleta bayan sun hau titi"lallai baku raina Mr Goje ba.Yaya Julaibib wargi waje yake samu,shi wannnan Malamin mugune na gasken-gaske gashi kuma yanzu shine Labour Master,ya yanka ma mutum k'atan fili iya ganinka yace sai ka nome shi wallahi k'aramin abu ne a wajan shi.