Sashe 45
Gwajin Dafi Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sinan sai da yayi bacin awanni biyu sannan suka tasheshi,har lokacin bai gama dawowa dai-dai ba,sai suka dura mishi giya nan fa yadad'a rikicewa.Wani abokin Tibishi yakalli Sinan"wannan ba yau za a d'aura mishi aure ba amma yazo nan yashare waje ko auran dole za a mishi? Dammm...zuciyar shi tabuga duk da yana cikin maye.Yata shi yana tangad'i da tam6ele yashiga mota.Yana tafe jama'a na kaucewa da ababan hawansu, yana kuma shan zagi da tsinuwa daga bakin wasu,saboda k'iris yarage yahad'a hatsari mummuna,a haka har ya isa masallacin juma'a wajan d'aurin auren...wasu zafafan hawaye suka zubo mishi"Zigwai tasa ya zubar da mutuncin shi dana gidan su abainan-nasi, kalaman Sudaida suka dawo mishi duk da k'anka'ntar shekarun ta amma tayi hagen nesan da san zuciya yahana shi hangowa...
Zama da madaukin kanwa...wai kai ba ka da wajan zamane sai acikin yan maro(wiwi)?...yatuno da maganar mahaifin shi na wancan makon"Sinan ba girma aganka kana mu'amala da wad'annan k'adangarun barikin... mun baka tarbiya gwargwadon iyawarmu... tunatarwa ce kawai...Yamik'e cikin tafasar zuciya "lallai yau za ayi ta tak'are me raba shi da Tibishi da Zigwai sai ALLAH Hamidan yakalle shi ganin yana bud'e kofa"Ina za ka a wannan daren Yaya? Ko kallan shi baiyiba yasa kai yafita.
Tana kwance hankali kwance iskar fanka tana kad'ata.Yadamk'o gashin dokin daya cika kanta tozon rak'umi guda.Zafi yaratsa ta tabud'e idanu cikin gigita,suka kalli juna,sai ta dad'a rikicewa.Yanemi abun duka bai samu ba dan haka yad'auki belt d'in daya gani a gefen gadon, yafara dukan ta ba ji ba gani sai da belt d'in yatsitstsinke amma duk da haka bai hak'ura ba,yafara tattaka sai da yaga ta daina motsi sannan yatsallaketa cikin jini yafita, amma har lokacin bai huce abinda suka mishi ba,wasu jijiyoyi sun fito a gefen kanshi kamar shatin bulala,ran maza ya 6aci iya 6aci.
Adaren yakoma neman Tibishi sai dai duk inda yasan zai ganshi yaje amma cikin rashin sa a bai ganshiba...tabbasss da aun had'u sai wani ya rasa ranshi ko kuma suyi mutuwar kasko.Yakama hanyar gida zuciyar shi a cunkushe, kaci6is sukayi da mahaifin shi da Hamidan za su tafi masallaci sallar asubahi. Sinan yasunkwui da kai ya ga 6acin ran da bai ta6a gani a fuskar mahaifin na suba"yanzu duk abin kunyar dakayi jiya hakan baisa ka kwana a gidaba? Yanuna shi dayatsa" anya Sinan,anya rayuwar gaba za tayi kyauvda albarka idan ba a tsaya an inganta rayuwar da ake ciki a yanzu ba? Anya Sinan kana tuna tsohon banza daga yaron banza yafara? Sinan yayi shiru a ranshi yana nadamar sanin Tibishi da Zigwai a rayuwarshi..Alhaji Kamal yakad'a kai"shikenan sai kaje ka shirya kafito masallaci, yakalleshi "kama rama sallolin jiya daka kwanta wannan baccin asaran?Tsoro yakama shi" shi Sinan yashiga ukun shi wallahi sai yanzu yatuna.Asanyaye yagirgiza kai"yanzu zan rama. Yakalli Hamidan"kaji,Ubangiji yashirye shi. Hamidan ya amsa da sauri amin Baba. Suka tafi masallaci kowanne ranshi ba dad'i.
Yana durk'ushe agaban mahaifiyar shi yana bata hak'urin abinda yafaru amma fau-fau tak'i sauraran shi, tanuna mishi k'ofa"ta shi kabani waje ganin ka yana k'ona min rai,Sinan ka bani kunya...tirrr da wannan halin na ka, albasa batayi halin ruwa ba wallahi. Yayi k'asa da murya "Mama bana shan giya,makirci kawai a ka kulla min...ta tare shi a zafafe" kai karka maidani sakarya,wa zai kulla maka makirci?Makirci da munafurci har yawuce wanda kadad'e kana aikatawa,ko kawai dan dubunka ta cika? Alhaji Kamal yashigo"haba Mamansu idan rai ya 6aci to bai kamata hankali yagusheba,d'an yau ne ka haifeshi baka haifi halin shiba.Takalleshi a rikice "yanzu kana goyon bayan shine,har kana ba shi lasisi?Tad'ora hannayenta aka"oh ni yar mutum biyu" na rantse da ALLAH Alhaji idan yaron nan bai tashi yafitaba to zan d'aga mishi nono...Tabud'e baki da niyar sake magana sai kalaman suka mak'ale saboda 6acin rai.Tasa hannu tashare hawayen daya zubo mata.
Sinan yasake shiga wani tashin hankalin gobarar gemu fiye dana d'azu"lallai ka shiga uku, rayuwarka tana cikin garari tunda har za kasa mahaifiyar ka zubar hawaye saboda mummunan laifin ka. Yanzu wa zai yadda dashi akan baya shan giya? Abu d'aya yasan yana sha a 6oye shine taba sigari,itama ba koda yaushe ba,wazai yadda dashi?Yadafa goshi"ko Alqur'ani d'ungurungum zai had'iye bashi da mafita. Nadama,haushi da bak'in ciki suka baibayeshi, kome yaji yafice mishi a rai.
Alhaji Kamal yadafa shi"tashi katafi d'akin ka.Gwiwa a sage yamik'e.Alhaji Kamal yakalli matar shi "abinda Sinan yayi tabbasss bai kyauta ba,kuma bana goyon bayan shi,to amma wani hanzari ba gudu ba, idan fa yatuba bai kuma aikata hakan ba har abadan duniya,to ALLAH me gafara ne,zai kar6i tuban shi ya yafe mishi tunda bamu yama laifi ba face mahaliccinmu gaba d'aya, dan haka karki tsananta,ke uwa ce addu'arki har kullum ita ake buk'ata, kullum addu'armu da fatanmu ace Ya'yanmu sunyi zarra fiye da duk wasu Ya'ya wajan natsuwa,sanin ya kamata, mutunci da tsantseni,to inga yanzu kin mishi baki? Bazai amfani kan shiba,bazai amfane muba,bazai amfanar da sauran al'umar manzon ALLAH ba,kin 6ata goma biyar bata samuba,baya ba zani kenan...
Yana rik'e da marik'in k'ofar d'akin shi kafin yamurd'a tabud'e jiri yayi awon gaba gaba dashi yifff...yasha k'asa.K:arar fad'uwar tashi megadi yaji.Yayi cikin gidan da sauri yana kiran Alhaji da Hamidan,sun yayyafa mishi ruwa amma shiru kamar an shuka dusa,dan haka suka wuce dashi asibiti.
Tsakanin d'a da uwa sai ALLAH, hankalin mahaifiyar tashi a tashe,takira Hamidan tana tambaya"ya jikin na shi?Yakalli roban k'arin ruwan da aka sa mishi a hankali yake d'iga a cikin siririyar robar yana shiga jijiyarshi zuwa cikin jikinshi"Mama ya samu bacci saboda allurar baccin da aka mishi,likita yace jininshi yayi mugun hawa.To Alhaji fa?Tasake tambayar shi cikin damuwa. Sun fita shi da likita.To Ubangiji yasa kaffarace nima anjima zan shigo. Yagyad'a kai"To Mama sai kin shigo a iso lafiya.Yauwa Hamidan ALLAH yamaka albarka.Amin Mama.
Tibishi yad'ora hannayen shi aka yana zare idanu"Holy ghost fire!...Inzayadami?(Me yafaru)Tafashe da kuka tana kad'a kai"ina katafi kabarni acikin wannan mawuyacin halin? Na neme ka a waya banji kaba.Yakoma yazauna"sha kuruminki Zigwai wayata nasiyar nayi kud'in mota zuwa Kafanchan kasuwar aladu, na kuma je da k'afar dama and'aukeni lodi mutanan k'asar China sunzo siya, lodin tirela hud'u mukayi,ba k'aramin kud'i nasamu ba,dan haka murabu da Sinan dan naga hak'armu baza ta tadda ruwaba.Me kake nufi? Yazuba mata idanu jikinta duk a farfashe yake"gaskiyar magana tunda Sinan yamiki irin wannan dukan kawo wuk'an to babu wata rana dazaki kuma mishi koda kun rage daga ke sai shi a doron duniya bazai kuma sauraran kiba.Tunda na samu abin yi kishare shi kawai,d'an iska yadaije amma ai munci gari,nima kwana biyu zan kiyayi zuwa cikin gari da duk inda nasan zai ganni,dan na san zai nemeni ruwa a jallo.
Takalleshi amma tunda bai auri Sudaida ba na san zai koma ruwa tsundum. Yamata wani kallon sauna"ke Sinan fa ba sin ki yakw yiba shishshigi da nacinki yasa kika samu kanshi,kuma koda kika samu kan shi ai ba wani d'ad'ashi da k'asa kikayiba,ak'arshe ma bazuwa yayi yaba ki hak'uri akan kuyi hannun rigaba? Yamik'e"nidai buri na ya cika,dama yarinyar ce bana so ta aure shi saboda girman kanta,kin san sannu wannan ta fatar baki bata ta6a cemin ba,duk da tasan nid'in abokin saurayin tane aibtasha ganin mu atare,idan nabari ya aureta to za ta rabamu tunda na san zaiji maganar ta dan yana son ta.
Zigwai takwanta"ai dai munyi biyu babu. Tibishi yakalle ta kisa ranki a inuwa,barinje kasuwa in miki siyayya,yana fita ta kyalkyale da dariya"haba Tibishi ai linzami ya fi k'arfin bakin kaza,kai ka had'ani da Sinan dan yazama saniyar tatsarmu,to mun tatseshi yadda yakamata, yanzu idanu na a bud'e suke ina ganin kowa garauuu ba ka da kud'in dazan aure ka,bari dai mucinye wanda kasamo,za ka nemeni ko sama ko k'asa karasa,garin zan bari dan yamin zafi saboda rashin Sinan, zan tafi wata jahar in bud'e sabuwar rayuwa da sababbin alhazan birni masu aljihu da kud'i ba irin kaba tsami ragowar burkutu giyar k'ok'o da hayakin maro da taba dayaci yacinye ka,sai na sai gida da mota,sannnan zan yi aure...toh maji magani an binne tsohuwa da ranta...
Haka ya yi an sai da gonar rago an sai mishi fura.
Farar dabara shiga rijiya da fura.
10 Jumaada Thani 1441
4 February 2020
We Ibrahim's Daughters👇
Asdilat KD...2geda with Ra'ibs.
DANGIN NONO WRITERS ASSOCIATION
{Da Inganci Mukayi Fintinkau}
Bismillahi wabihi nasta'in
...GWAJIN DAFI💔
Almost true story
Daga alk'alamin🖊
Ya'yan Ibrahim
Saudat A.Baba (Asdilat KD)
Da
Bara'atu Ibrahim (Ra'ibs)
Shafi na goma sha tara.
Kwanaki biyu Sinan yayi a gadon asibiti yasamu sauk'i sai dai likita bai sallame shiba sai zuwa gobe.Yakar6i wayar Hamidan dan ta shi ko ta fad'i ko kuma su Tibishi sun sace ta,yadaddanna lambobin ta sannan ya d'ora lambar a kira.Tad'aga da sallama,wani abu yatsirga ilahirin jikinshi,ta kuma yin sallama jin ba ayi magana ba sai ta katse.Yacire wayar a kunnenshi yana jujjuya ta,idanun shi sun kad'a jawur,tabbasss kukan zuci yakeyi.Yaya Sinan ba a d'aga bane ko matsalar na'urar sadarwa?Yajuya yakalli Hamidan d'in,sai ya gyad'a kai"zan cigaba da gwadawa wata k'ila tashiga.Sai da ya danna kira sannan yace"Hamidan dan ALLAH kaje gida Mama tadama min kunun tamba.Yamik'e yana murmushi"a lallai yau jikin Alhamdulillahi,a had'o da abinci ko?Yagyad'a kai"amma me d'an ruwa-ruwa.
Yana fita yakai wayar kunnenshi,tad'aga da sallama.Yasauke numfash sannan ya amsa sallamar,yakira sunan ta Sudaida...Zuciyoyinsu suka buga,sukayi shiru na wucewar wasu dak'ik'u.Da rawar murya take fad'in"Sinan ya jikin?Ance kana kwance a gadon asibiti,Sinan me yasa kabiye ma son zuciya bayan ka san son zuciya 6acin ta...dama da gaske kura ce lull6e dafatar akuya?Sinan kai masoyina ne, wallahi ban ji dad'in abinda yafaru ba ko kad'an...ALLAH yashirye ka dana... yatari numfashin ta"na rantse miki da girman ALLAH bana shan giya"ba ka shan giya to ya akayi kasha? Ba fa a wasan kwaikwayo kafito ba.Yakad'a kai, matsalar kenan ba wanda zai gasgata shi"Sudaida na san na rasa ki,to amma duk da haka bazan barki cikin duhu ba,ranar wanka ba a 6oye cibi... yafara ba ta labarin had'uwarsu da Zigwai wanda shi kanshi yasha mamakin sauk'in halin ta,saboda irin wulak'ancin dayake mata,amma tashanye kullum bata fushi kwantar da kai take mishi na gasken-gaske da haka har taja ra'ayin shi yafad'a tark'onta.
Zama da madaukin kanwa...wai kai ba ka da wajan zamane sai acikin yan maro(wiwi)?...yatuno da maganar mahaifin shi na wancan makon"Sinan ba girma aganka kana mu'amala da wad'annan k'adangarun barikin... mun baka tarbiya gwargwadon iyawarmu... tunatarwa ce kawai...Yamik'e cikin tafasar zuciya "lallai yau za ayi ta tak'are me raba shi da Tibishi da Zigwai sai ALLAH Hamidan yakalle shi ganin yana bud'e kofa"Ina za ka a wannan daren Yaya? Ko kallan shi baiyiba yasa kai yafita.
Tana kwance hankali kwance iskar fanka tana kad'ata.Yadamk'o gashin dokin daya cika kanta tozon rak'umi guda.Zafi yaratsa ta tabud'e idanu cikin gigita,suka kalli juna,sai ta dad'a rikicewa.Yanemi abun duka bai samu ba dan haka yad'auki belt d'in daya gani a gefen gadon, yafara dukan ta ba ji ba gani sai da belt d'in yatsitstsinke amma duk da haka bai hak'ura ba,yafara tattaka sai da yaga ta daina motsi sannan yatsallaketa cikin jini yafita, amma har lokacin bai huce abinda suka mishi ba,wasu jijiyoyi sun fito a gefen kanshi kamar shatin bulala,ran maza ya 6aci iya 6aci.
Adaren yakoma neman Tibishi sai dai duk inda yasan zai ganshi yaje amma cikin rashin sa a bai ganshiba...tabbasss da aun had'u sai wani ya rasa ranshi ko kuma suyi mutuwar kasko.Yakama hanyar gida zuciyar shi a cunkushe, kaci6is sukayi da mahaifin shi da Hamidan za su tafi masallaci sallar asubahi. Sinan yasunkwui da kai ya ga 6acin ran da bai ta6a gani a fuskar mahaifin na suba"yanzu duk abin kunyar dakayi jiya hakan baisa ka kwana a gidaba? Yanuna shi dayatsa" anya Sinan,anya rayuwar gaba za tayi kyauvda albarka idan ba a tsaya an inganta rayuwar da ake ciki a yanzu ba? Anya Sinan kana tuna tsohon banza daga yaron banza yafara? Sinan yayi shiru a ranshi yana nadamar sanin Tibishi da Zigwai a rayuwarshi..Alhaji Kamal yakad'a kai"shikenan sai kaje ka shirya kafito masallaci, yakalleshi "kama rama sallolin jiya daka kwanta wannan baccin asaran?Tsoro yakama shi" shi Sinan yashiga ukun shi wallahi sai yanzu yatuna.Asanyaye yagirgiza kai"yanzu zan rama. Yakalli Hamidan"kaji,Ubangiji yashirye shi. Hamidan ya amsa da sauri amin Baba. Suka tafi masallaci kowanne ranshi ba dad'i.
Yana durk'ushe agaban mahaifiyar shi yana bata hak'urin abinda yafaru amma fau-fau tak'i sauraran shi, tanuna mishi k'ofa"ta shi kabani waje ganin ka yana k'ona min rai,Sinan ka bani kunya...tirrr da wannan halin na ka, albasa batayi halin ruwa ba wallahi. Yayi k'asa da murya "Mama bana shan giya,makirci kawai a ka kulla min...ta tare shi a zafafe" kai karka maidani sakarya,wa zai kulla maka makirci?Makirci da munafurci har yawuce wanda kadad'e kana aikatawa,ko kawai dan dubunka ta cika? Alhaji Kamal yashigo"haba Mamansu idan rai ya 6aci to bai kamata hankali yagusheba,d'an yau ne ka haifeshi baka haifi halin shiba.Takalleshi a rikice "yanzu kana goyon bayan shine,har kana ba shi lasisi?Tad'ora hannayenta aka"oh ni yar mutum biyu" na rantse da ALLAH Alhaji idan yaron nan bai tashi yafitaba to zan d'aga mishi nono...Tabud'e baki da niyar sake magana sai kalaman suka mak'ale saboda 6acin rai.Tasa hannu tashare hawayen daya zubo mata.
Sinan yasake shiga wani tashin hankalin gobarar gemu fiye dana d'azu"lallai ka shiga uku, rayuwarka tana cikin garari tunda har za kasa mahaifiyar ka zubar hawaye saboda mummunan laifin ka. Yanzu wa zai yadda dashi akan baya shan giya? Abu d'aya yasan yana sha a 6oye shine taba sigari,itama ba koda yaushe ba,wazai yadda dashi?Yadafa goshi"ko Alqur'ani d'ungurungum zai had'iye bashi da mafita. Nadama,haushi da bak'in ciki suka baibayeshi, kome yaji yafice mishi a rai.
Alhaji Kamal yadafa shi"tashi katafi d'akin ka.Gwiwa a sage yamik'e.Alhaji Kamal yakalli matar shi "abinda Sinan yayi tabbasss bai kyauta ba,kuma bana goyon bayan shi,to amma wani hanzari ba gudu ba, idan fa yatuba bai kuma aikata hakan ba har abadan duniya,to ALLAH me gafara ne,zai kar6i tuban shi ya yafe mishi tunda bamu yama laifi ba face mahaliccinmu gaba d'aya, dan haka karki tsananta,ke uwa ce addu'arki har kullum ita ake buk'ata, kullum addu'armu da fatanmu ace Ya'yanmu sunyi zarra fiye da duk wasu Ya'ya wajan natsuwa,sanin ya kamata, mutunci da tsantseni,to inga yanzu kin mishi baki? Bazai amfani kan shiba,bazai amfane muba,bazai amfanar da sauran al'umar manzon ALLAH ba,kin 6ata goma biyar bata samuba,baya ba zani kenan...
Yana rik'e da marik'in k'ofar d'akin shi kafin yamurd'a tabud'e jiri yayi awon gaba gaba dashi yifff...yasha k'asa.K:arar fad'uwar tashi megadi yaji.Yayi cikin gidan da sauri yana kiran Alhaji da Hamidan,sun yayyafa mishi ruwa amma shiru kamar an shuka dusa,dan haka suka wuce dashi asibiti.
Tsakanin d'a da uwa sai ALLAH, hankalin mahaifiyar tashi a tashe,takira Hamidan tana tambaya"ya jikin na shi?Yakalli roban k'arin ruwan da aka sa mishi a hankali yake d'iga a cikin siririyar robar yana shiga jijiyarshi zuwa cikin jikinshi"Mama ya samu bacci saboda allurar baccin da aka mishi,likita yace jininshi yayi mugun hawa.To Alhaji fa?Tasake tambayar shi cikin damuwa. Sun fita shi da likita.To Ubangiji yasa kaffarace nima anjima zan shigo. Yagyad'a kai"To Mama sai kin shigo a iso lafiya.Yauwa Hamidan ALLAH yamaka albarka.Amin Mama.
Tibishi yad'ora hannayen shi aka yana zare idanu"Holy ghost fire!...Inzayadami?(Me yafaru)Tafashe da kuka tana kad'a kai"ina katafi kabarni acikin wannan mawuyacin halin? Na neme ka a waya banji kaba.Yakoma yazauna"sha kuruminki Zigwai wayata nasiyar nayi kud'in mota zuwa Kafanchan kasuwar aladu, na kuma je da k'afar dama and'aukeni lodi mutanan k'asar China sunzo siya, lodin tirela hud'u mukayi,ba k'aramin kud'i nasamu ba,dan haka murabu da Sinan dan naga hak'armu baza ta tadda ruwaba.Me kake nufi? Yazuba mata idanu jikinta duk a farfashe yake"gaskiyar magana tunda Sinan yamiki irin wannan dukan kawo wuk'an to babu wata rana dazaki kuma mishi koda kun rage daga ke sai shi a doron duniya bazai kuma sauraran kiba.Tunda na samu abin yi kishare shi kawai,d'an iska yadaije amma ai munci gari,nima kwana biyu zan kiyayi zuwa cikin gari da duk inda nasan zai ganni,dan na san zai nemeni ruwa a jallo.
Takalleshi amma tunda bai auri Sudaida ba na san zai koma ruwa tsundum. Yamata wani kallon sauna"ke Sinan fa ba sin ki yakw yiba shishshigi da nacinki yasa kika samu kanshi,kuma koda kika samu kan shi ai ba wani d'ad'ashi da k'asa kikayiba,ak'arshe ma bazuwa yayi yaba ki hak'uri akan kuyi hannun rigaba? Yamik'e"nidai buri na ya cika,dama yarinyar ce bana so ta aure shi saboda girman kanta,kin san sannu wannan ta fatar baki bata ta6a cemin ba,duk da tasan nid'in abokin saurayin tane aibtasha ganin mu atare,idan nabari ya aureta to za ta rabamu tunda na san zaiji maganar ta dan yana son ta.
Zigwai takwanta"ai dai munyi biyu babu. Tibishi yakalle ta kisa ranki a inuwa,barinje kasuwa in miki siyayya,yana fita ta kyalkyale da dariya"haba Tibishi ai linzami ya fi k'arfin bakin kaza,kai ka had'ani da Sinan dan yazama saniyar tatsarmu,to mun tatseshi yadda yakamata, yanzu idanu na a bud'e suke ina ganin kowa garauuu ba ka da kud'in dazan aure ka,bari dai mucinye wanda kasamo,za ka nemeni ko sama ko k'asa karasa,garin zan bari dan yamin zafi saboda rashin Sinan, zan tafi wata jahar in bud'e sabuwar rayuwa da sababbin alhazan birni masu aljihu da kud'i ba irin kaba tsami ragowar burkutu giyar k'ok'o da hayakin maro da taba dayaci yacinye ka,sai na sai gida da mota,sannnan zan yi aure...toh maji magani an binne tsohuwa da ranta...
Haka ya yi an sai da gonar rago an sai mishi fura.
Farar dabara shiga rijiya da fura.
10 Jumaada Thani 1441
4 February 2020
We Ibrahim's Daughters👇
Asdilat KD...2geda with Ra'ibs.
DANGIN NONO WRITERS ASSOCIATION
{Da Inganci Mukayi Fintinkau}
Bismillahi wabihi nasta'in
...GWAJIN DAFI💔
Almost true story
Daga alk'alamin🖊
Ya'yan Ibrahim
Saudat A.Baba (Asdilat KD)
Da
Bara'atu Ibrahim (Ra'ibs)
Shafi na goma sha tara.
Kwanaki biyu Sinan yayi a gadon asibiti yasamu sauk'i sai dai likita bai sallame shiba sai zuwa gobe.Yakar6i wayar Hamidan dan ta shi ko ta fad'i ko kuma su Tibishi sun sace ta,yadaddanna lambobin ta sannan ya d'ora lambar a kira.Tad'aga da sallama,wani abu yatsirga ilahirin jikinshi,ta kuma yin sallama jin ba ayi magana ba sai ta katse.Yacire wayar a kunnenshi yana jujjuya ta,idanun shi sun kad'a jawur,tabbasss kukan zuci yakeyi.Yaya Sinan ba a d'aga bane ko matsalar na'urar sadarwa?Yajuya yakalli Hamidan d'in,sai ya gyad'a kai"zan cigaba da gwadawa wata k'ila tashiga.Sai da ya danna kira sannan yace"Hamidan dan ALLAH kaje gida Mama tadama min kunun tamba.Yamik'e yana murmushi"a lallai yau jikin Alhamdulillahi,a had'o da abinci ko?Yagyad'a kai"amma me d'an ruwa-ruwa.
Yana fita yakai wayar kunnenshi,tad'aga da sallama.Yasauke numfash sannan ya amsa sallamar,yakira sunan ta Sudaida...Zuciyoyinsu suka buga,sukayi shiru na wucewar wasu dak'ik'u.Da rawar murya take fad'in"Sinan ya jikin?Ance kana kwance a gadon asibiti,Sinan me yasa kabiye ma son zuciya bayan ka san son zuciya 6acin ta...dama da gaske kura ce lull6e dafatar akuya?Sinan kai masoyina ne, wallahi ban ji dad'in abinda yafaru ba ko kad'an...ALLAH yashirye ka dana... yatari numfashin ta"na rantse miki da girman ALLAH bana shan giya"ba ka shan giya to ya akayi kasha? Ba fa a wasan kwaikwayo kafito ba.Yakad'a kai, matsalar kenan ba wanda zai gasgata shi"Sudaida na san na rasa ki,to amma duk da haka bazan barki cikin duhu ba,ranar wanka ba a 6oye cibi... yafara ba ta labarin had'uwarsu da Zigwai wanda shi kanshi yasha mamakin sauk'in halin ta,saboda irin wulak'ancin dayake mata,amma tashanye kullum bata fushi kwantar da kai take mishi na gasken-gaske da haka har taja ra'ayin shi yafad'a tark'onta.