← Book details Gwajin Dafi Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 43 OF 74

Sashe 43

Gwajin Dafi Complete Hausa Novel · about 8 min read

Alhaji Kamalu mutumin kirki me karamci shi yakar6ama Julaibib auran Sudaida, dubban nin jama'a sun shaida wannan aure. Hamidan yasauke numfashi,sai yanzu yashak'i iskar yanci dayaji ba dashi aka d'aura ba, yama Julaibib da Sudaida fatan alheri da sauran angwaye da amaren,yamik'e yayi tafiyar shi yana rok'ama Sinan shiriya...ALLAH kenan buwayi gagara misali,namiji baya auran macen da ba ta shiba,hakama mace bata auran mijin da bana ta ba...al'amarin aure,al'amarine daga Indallahi,shi yake had'awa sai dai wani yazama silar faruwar shi.

Baban Abdul dake gefen shi yayi murmushi"ango ka sha k'amshi,aure d'an lokaci ne,idan lokaci yayi ko ba a shirya ba haka dole za ayi...ka tuno hirar mu ta kwanaki?Wannan gaskiya ne shirye-shiryen a yi daga baya,yamik'a mishi hannu sukayi musafaha suna murmushi, wallahi shima haka yake ganin abun kamar almara,har suka fito yan'uwa da abokan arziki sun baibaye shi suna taya shi murna da fatan alheri"Dare ga mai rabo...hantsi.Sunan wani littafi na gwanarmu (Halima Abdullahi Amma)Ubangiji ya kyautata makwanci👏

D'ansarai...yaji an kira shi.Yad'ago kai bakin shi d'auke da addu'ar"Alhamdulillahil-lazi bi ni'ima tihi ta tummussalihat"jin an daki kafad'arshi.Aminu ne yazare mishi idanu"toh daga yau sai yau na zama surukin ka,dan haka ba sauran raini,idan ba haka ba in k'wace k'anwata ka gane ko?Kome girma-girma kamar tusar jaki. Julaibib yamishi wani kallo "ai aikin gama ya gama,wuk'a da nama yanzu a hannu na suke da dai kafin a d'aura ne to danaji kurarin ka,nagaba yayi gaba Alhaji...Su Musaddiq suka yi dariya.

Yara kowa yafara noman kare(gudu) dan yaje kai rahoto kuma kowa so yakeyi ace shine na farko, tun daga zaure Abdul yake k'walama Inna kira iya k'arfin shi har yashiga tsakar gidan,duk suna tsaye cirko-cirko cikin tararrabin abinda Abdul din zai shigo dashi na tashin hankali"lafiya kuwa Abdul?Sai numfarfashin gudun dayasha yake yi,yana haki da dariya yace"Inna Kawu D'ansarai aka d'aura ma aure. Asma'u dake tsaye kusa dashi batayi k'asa a gwuiwaba ta d'auke shi da wani bahagon mari,ji da ganin shi sai da ya d'auke na wucin gadi"wato wasan da takeyi da kai har yakai haka? Ka dinga mata kiran yan farauta tun daga waje duk ka tashi hankalin mu sannan kashigo mana da maganar banza"wa D'ansarai ya aura?K'anwar ubanka? Yadafe wajen dan ya maru idanun shi suka kawo ruwa,ya kasa magana sai kawai yajuya zai fita. Inna tarik'o rigar shi "Zo mana Abdul d'ina mai gida ran gida,me gida takobi...tayi furucin da sigar rarrashi,tasa hannu tashare mishi hawayen da suke zubo sharrr..."fad'amin gaskiya Abdul,me yafaru a masallaci... bata gama rufe baki ba sai ga Adnan yashigo da sallama,suka bishi da kallo, yaja kujera yazauna.Cikin jimami yafad'a musu kome. Masu murna na yi masu komawa gefe suna k'unk'uni na yi.Asma'u tajuya zata ba Abdul hak'uri taga ya fita.

Asma'u tana jin abinda Sagir ya gama fad'a takai goshinta k'asa cikin sujudush-shukuri "yanzu ne za suyi rawar gaban hantsi ita da Alk'asim,tad'auki jakar da Sudaida tace tashiga d'akin Yaya Aminu tad'auko takai mata gidan Hajiya.Tana dire jakar a k'asa tayi tsalle cikin ihun murna ta rungume Sudaida"albishirinku?Duk amaren da suka sha wanka da kwalliya suka bita da kallo.Ta lumshe idanun ta cikin jan numfashi "wai me yafi dad'ine an tambayi na d'aure? Saki...tayi lallausan murmushi sannan tabud'e idanun ta"toh an d'aure lafiya an kuma gama lafiya, sai dai an samu akasi Yaya Sudaida dai da autan Inna aka d'aura...

"Da Julaibib???

Suka had'a baki wajan tambayar ta cikin mad'aukakin mamaki.Nasmat ta san halin Asma'u ba mamaki tace da wasa take yi.A'isha ta d'aure fuska"ke Asma'u wacece sa ar wasanki a cikin mu?Tafara rantse-rantse gaskiya take fad'a...Daga tsakar gida suka fara jiyo tafa hannaye cikin sallallami.Nasmat talek'a Yaya Aminu ta hango suna masu Hajiya bayanin abinda yafara, a hankali tasaki labulan tana jijjiga kai"ga kai ga kafa ai ba tambayar me aka yanka.Maryam takada kai cikin damuwa "amma dai Sinan bai kyauta ba,ya 6ata rawar shi da tsalle.Zainab ta ta6e baki"wannan kuma ai can gasu gada kura ta ji kid'an farauta... kowacce ta tofa albarkacin bakinta.

Sheshshekan kukan Sudaida sukaji, gaba d'aya suka juya suna kallanta.Aisha tace kiyi hak'uri Sudaida ALLAH yaso ki da rahama yato na asirin shi,da an d'aura auran ne bayan kin zama matar shi fa? Ai ko za a raba auren ku a yadda yake son ki ai ba k'aramar tata6urza za ayi ba.

Takalli A'usha"wai da D'ansarai fa wannan me miskilancin tsiyan?Khausar tagalla mata harara sannan taja dogon tsaki"rainin hankalin ki yana da yawa wallahi.Su Aisha suka kyalkyale da dariya"duk miskilancin shi ai taku dashi ta zo d'aya,har hira fa kunayi.Takoma ta kwanta a ranta tana mita"maganar da sai ya ga dama yake yi.Aisha tasake kallanta"a shekarun baya dana fara k'orafi a kan halin shi kece fa me k'alubalantar kalamaina,bayani sosai kike min har nima daga baya nagane,tadafa kafad'arta haba ta D'ansarai ki daina asarar hawayen ki dan Julaibib mijin nuna ma sa a ne wallahi...tayi shiru kamar bataji me suke ta fad'a ba...tacigaba da zancen zuci"tabbass tana son Yaya Julaibib,to amma yanzu da fad'uwar tazo dai-dai da zama, kayan suka tsinke a gaban kaba sai ranta bai so ba. Tarintse idanu hawayen suka sake zubowa a kyakkyawar fuskar ta me d'auke da hasken amarci.Sinan baka kyauta ba, ka ci amanar k'auna, wato ranar da aka kira wayar shi a bai-bai yarufe ta,saboda sunan Zigwai suna sa ma maza suna sa ma mata,ashe kalaman Tibishi duk gugar zana ne,tadafe kanta daya fara barazanar ciwo,ai ko ba ta san Sinan to dad'ewar su tasa sun yi sabo na ban mamaki.

Biki sai yadad'a komawa gidan Inn,bayan sallar Isha'i kowace amarya aka sadata da d'akin miji gidan aure, aure yak'in mata inji hausawa...Su angwayan da tawagar abokan su,su suka yanke shawarar a fara raka Julaibib gidan shi.Aminu dake cikin tawagar abokai yarik'o hannun shi"dare fa na dad'a yi zo muje kama Innarmu sai da safe,dan ka san bazan lamunta kadinga share waje kana barin k'anwata a gida ba,yanuna shi da yatsa"sai fa ka kula da kyau idan ba haka ba har gidan zani in tasa k'eyarta zuwa gida.Julaibib yakai mishi naushi a kafad'a amma bai same shiba dan ya goce da sauri"kar ka 6alla min kafad'a kasa gobe in shiga uku,aikin billboards ne dani guda wajan takwas.To ni ai bata shafeni ba.Yagyad'a kai"gaskiya ne ba ka da asara ko na miyan bacci.

Inna tayi murmushin jin dad'i yau ALLAH ya nuna mata auran autan ta.Ta musu nasiha gaba d'ayan su sosai akan su zauna lafiya da matayan su.Alhaji Abdullahi shima ya d'ora"Ku kyautata musu Manzon ALLAH yace mafifici a cikin ku,mafifici a kyautatama Iyalin shi,ni na fiku kyautatama Iyalina,kuji tausayin su,kuyi hak'uri da dabi'unsu dan da k'ashin hak'ark'arin hagu aka halicce su.Yakalli Julaibib"Malam D'ansarai ai ka san ina yawan fad'a maka shi zaman aure gaba d'ayan shi hak'uri ne ko? Toh yau ka shiga daga ciki,yanzu za ka fara aiwatar da wannan nasihar a aikace,aure hak'uri ne,d'awainiyace me tarin yawa, shi yasa ake buk'atar juriya da jajircewa. Yarufe nasihar ta shi da wannan addu'ar ga wanda yayi sabon aure...

"Barakallahu lakum,wabaraka alaikum, wajama'a bayyana kuma fi khair.

Duk suka had'a baki wajan amsawa da amin,amin,amin.

Inna da Baba suka bisu da kallo bayan sunma juna sai da safe suna fita d'aya bayan d'aya daga D'akin shak'atawar,kowanne yayi sharrr... dashi cikin farar shadda.

Garin yayi tarwai da hasken farin wata, sassayar iska tana kad'awa a cikin daren,ga k'amshin furen filawar sarauniyar dare(Queen of the night) d'in k'ofar gidan yamamaye ilahirin ciki da wajen gidan. D'akin- shak'atawar a gyare yake, sai dai yau gyaran na musamman ne,k'amshin amarci ya cika ko ina.Suka zazzauna,aka d'an ta6a hira kamar yadda akan yi idan an rako ango sannan suka mik'e.Aminu yad'an daga murya "toh amarya mukwana lafiya, mun sai bakin ki akan kud'i masu tarin yawa,mun kuma damk'asu a hannun angon ki, dan haka yana shigowa mik'a hannu yaba ki yan kud'ad'enki,idan kuma kinci girma kin bar mishi to kinyi mafi kyawun karamci, duk ke d'in ce dai za ki amfana...Huzaifa yature shi"saboda ALLAH meye haka?Yad'aga mishi hannu"muje na ka gidan kaji abinda zan fad'a ma ta ka amaryar, suka fita suna mishi mita.

Julaibib yarakasu k'ofar gida yadawo bayan ya kulle ko ina.Yarike k'ugu a tsakiyar D'akin shak'atawar cikin karatun wasikar jaki na wucewar wasu dak'ik'u,yasauke numfashi sannan yasa hannu yad'auki ledar da Musaddiq yaba shi yanufi d'akin da sallama.Yashak'i wani k'amshin turarenta dana turaren d'akin,k'amshin ne me sanyin dad'i,ya lumshe idanu yana dad'a shak'ar k'amshin cikin jan numfashi...

Oh Ya Salam...dausayin ni'imahhh...

A hankali yabud'e idanun shi yana bin d'akin da kallo,kome an tsara shi,ya zauna a muhallin shi,abun ya burge,ya k'ayatar duk da anyi shi a k'urarren lokaci,yau d"in nan fa.

Shauk'in k'aunar daya mamaye ilahirin gangar jiki da sararin zuciyar shi tun bayan d'aurin auren sai yadad'a ninkuwa sau shurin masak'i,yaja stool yazauna yana k'are mata kallo tun daga k'afafunta da suka sha jan lalle da yarfin baki,har zuwa polish lace d'in data sa,zani da riga ruwan k'waiduwar kwai(beig)da mayafi ruwan kwai me shara-shara,k'ananan sabon kitson ta yar-yar-yar yadad'a fito da kyan fuskar ta,hannayen ta suma sunsha jan lalle da yarfin baki,d'an kunne, sark'a,zobe da siraran warawaranta na zinare sai d'aukar idanu sukeyi,ga kuma hasken amarci, yana kallan fuskar ta kome ya tarwatse mishi,murna ta koma ciki,saboda damuwa da tashin hankali dasu ke tattare da ita ruwan hawaye ne suka ta sinsitiri a kyakkyawar fuskar me d'auke da hasken amarci, yahad'e hannayen shi yad'ora ha6arshi akai"kar dai tsugune bata k'are ba...an sai da kare an sai biri?ALLAH dai yasa ba shi kad'ai yake kid'a da rawar shi ba!

'Sudaida..Yakira sunan ta cikin natsuwa.
Chapter 43 · 0% Book details