Sashe 48
Gwajin Dafi Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tacire wayar ta a caji tahaye gado sannan ta kunna data,sak'onni suka dinga shigowa bata ta6a wayar ba har sai da suka gama shigowa sannan ta fara duba Status d'in su Khausar,haushi yadad'a kamata,ganin kowacce tana cikin shauk'in k'auna ita da masoyin ta...A status d'in A'isha ne taga Hashim ya zage yana daka shakwara a turmi tana ce mishi baiyi laushi ba sai ya k'ara dakawa,shi kuma yana fad'in nagaji fa gaskiya..ga wanda suke cin sakwaran da miyar Ogu suna dariya.
Ga na Khausar nan ita da Huzaifa sunyi wani irin kyau na ban mamaki gaba d'ayan su sun canja,ta d'ora ha6arta a kafad'arshi suna dariya, d'ayan kuma wasu irin kalamai ne na tsananin k'auna ta rubuta shi ga hoton zuciya an gewaye ta da adon filawar Damask rose-flower.
Na maryam kuma hummm sallah ba a magana,ta yi mugun mamakin abinda ta d'ora a irin yanayin zaman da tayi da kuma kayan jikin ta,a k'asa ta rubuta"My Snuggle...I miss you deadly... tabbb...ai bata gama kallo ba tabari tana zagin ta "abinda yasa meki ALLAH yasa kar yasamu sauran dangi.Tayita kira layin ta a kashe, duk da ta san taza6i wad'anda za su ga Status d'in na tane,amma ita sai hakan bai gamshe taba gaskiya.
"Nasmat tamata magana"
Hummm...Amaryar autan Inna kuna shan sharafin ku fa..
Sudaida ta6ata fuska"a ah abinda yafi sharafi muke sha.
Nasmat takyalkyale da dariya...nima naga alama shi yasa sai jefi-jefi a ke ganin ki online...har yanzu kanwa bata kar tsamin bane k'wannafin yakwanta?
Sudaida taja dogon tsaki"ke dai kika sani da neman magana ni sai da safe...kawai ta kashe data ta kwanta;bata duba sak'o ko guda d'aya ba,tunani barkatai ya cika k'wak'walwarta "hummm yunwar ya tashi"taja dogon tsaki wallahi ai ba lallai ba tilas.
Washe gari ma da sassafe yabar gidan wai suna da taro a Zango Urban kamar tace yasiyo mata d'anbagalaje amma ta shareshi,ta d'auki wayar ta takira Yaya Aminu tana tambayar shi"kaima kana Zangon ne?Eh Sudaida.Dan ALLAH Yaya Aminu d'anbagalaje nake so amma me taushi.Kai kai kai Sudaida ai gwamma me k'arfin kinga za ki motsa muk'amuk'inki da dasashi ko kuwa? Tad'an marairaice"Yaya Aminu ni dai me taushi.To zan siyo miki Insha-ALLAH. Yauwa Yaya Aminu wallahi, shi yasa nake son ka ALLAH yabarka da Sidddiqa tazama sarauniyar ka.Amin Sudaida. Sukayi dariya.
Abubuwa suke ta maimaituwa na rashin fahimtar juna a tsakanin su,musamman Sudaida da take d'aukar fushi a abinda bai kamata ayi fushin ba,abun ya k'i ci ya k'i cinyewa kamar cin k'wan makauniya.Yauma tunda yatafi masallaci sallar asubahi bai dawo gidan ba.A hankali taji ana k'wank'wansa k'ofar gidan ta san shine, dan taji tsayuwar motar shi.Tatashi tabud'e takoma tayi kwanciyar ta.Yatsaya a tsakiyar d'akin hannayen shi nad'e a k'irji.
"Sudaida bak'in Matsirga sun zo.
Dammm...zuciyar ta tabuga da k'arfin gaske.Tafara zancen zuci"Kutumelesi wato zuwa yayi dakan shi yad'auko su?Su suna da mutunci da kima a idanun shi,ya kuma damu dasu amma ita ko oho ko?
Tajijjiga kai wani...kumallon mata yata so mata har wuya,amma ba tayi ko kawa da zuciyar ta bata amayo shiba.Tad'ago takalleshi"Oh sun zo?Tagyad'a kai"toh sannun su da zuwa. Yabita da kallan nazari ganin tana dad'a gyara kwanciya har da jan bargo ta lullu6a"ke wai menene haka?Kitashi kije ku gaisa mana. Tayamutsa fuska sannan tajuya mishi k'eya "gaskiya ni har yanzu bacci ne a cikin idanu na kum...Yatari numfashin ta "Innar su Bilkisu ce fa?
Furucin shi yamata sukar wuk'a a k'ahon zuciya wallahi ta kasa daurewa,idanun ta suka kawo ruwa"shikenan kuma dan kayi bak'i bazan yi bacci ba,bayan idanu na har wani zafi da yaji-yaji suke min saboda rashin baccin?Ni fa na rantse da girman ALLAH bazan iya wannan zaman ba,tunda baka d'auke ni wata tsiya ba,toh ba dani ba wannan takuran,ko dan kaga gidan kane? Tagalla mishi harara"an hak'ura ana shan kukar k'azama kuma dole sai tayi tsada?Wallahi sai a hak'ura tunda ba mutuwa za ayi ba ehemmm.
Suka zubama juna idanu cikin kallan-kallo nawucewar wasu dak'ik'u kowa zuciyar shi ba dad'i. Sudaida tana jiran martani ne tayi abinda idan ta tafasa za ta k'one,sai shi kuma yamata shiru,dan yadda ta6ata mishi rai idan yatsaya toh aika-aika za ayi,sai kawai yagyad'a kai"ki cigaba da abinda kike yi,amma fa kowa yaci ladan kuturu sai ya mishi aski,wanda ya girmama iyayen wani to bana kowa ya girmama ba sai na shi.Yakai hannu yak'ara mata gudun fankar "shikenan kiyi baccin ki.Yajuya yafita fuskar shi ba walwala,labarin zuciya a tambayi fuska.
Tad'aga murya"eh yanzu kuwa zanyi baccin.Sai kuma tamik'e jikin ta yayi sanyi gaskiyar magana bai kamata tayi haka ba"ai bak'on ka annabinka, wanda yadamu dakai shine zai zo inda kake to bai kamata kanuna mishi halin-ko-inkula ba"bak'in karen masoyinka ai yafi farin ragon mak'iyinka.
Yayi jimmm...nawucewar wasu dak'ik'u a bak'in k'ofa,Sudaida ta k'i fitowa ta musu sannu da zuwa to me zai fad'ama Inna?Sai yajuya zuwa D'akin-girki yad'ibo musu kofuna da lemun biyar a raye da ruwa har zuwa lokacin bai samo amsar dazai ba Inna ba,yahura iskar bakin shi"lallai Sudaida zata gane da gero ake koko yacigaba da tafiya,zai fad'a mata Sudaida bata nan.
Yamurd'a k'ofar D'akin-shak'atawar da sallama yashiga,sai dai abun mamaki Baturiya da suna manga Sudaida yagani durk'ushe a gaban Inna tana gaisheta cikin girmamawa"kun zo lafiya? Yasu Malam da sauran mutan gidan?A Alhamdulillahi lafiya lau,duk suna gaishe ki,sannu mungode.Daganin yadda Inna take amsawa itama taji dad'in shimfid'ar fuskar da Sudaida tamata wacce tafi ta tabarma.Tamik'ama Bello hannu sukayi musafaha "d'an kanina kaga dana iya yaren fulatanci toh da yau duk hirarmu da fillanci za muyi shi. Bello yad'an bud'e idanu"kai dama baki iya ba?To kisa Yaya D'ansarai ya dinga koya miki mana,kinga lokacin da Adda batayi wannan tafiya me nisan nan ba to idan yazo da fillanci suke magana suyi ta dariya,ranan nan ma yace mata wai...Kai Bello Inna ta tari numfashin shi'ba na hana ka fad'an abinda ba a tambaye kaba? Sai yayi shiru.
Da sauri Sudaida tamik'e ta kar6i kayan ta zuzzuba musu lemon a kofuna sanna tashiga D'akin-girki ta d'auko musu abincin data dafa tajuye a food-flask tana mita a ranta"kai ALLAH yasuwake da halin D'ansarai yanzu da suna da yawa dole sai tayi wani sabon girkin. Inna tasha lemon amma tak'i cin abincin.Sudaida ta karyar da kai gefen dama"haba Innarmu idan baki ciba ai baza muji dad'i ba,ni 'ya ce awajen ki,uwa kuma ai bazata k'i cin abincin 'yar taba ko da tak'oshi za tasa albarka,Inna idan bakiciba sai inga kamar da wata a k'asa a yadda muka d'aukeki ni da Yaya D'ansarai ke ba haka kika d'auke muba...suna had'a idanu tad'an harare shi sannan ta kauda kai. Inna tace"ba haka babe Sudaida, karki kuma furta irin wad'annan kalaman,ni na d'aukeku kamar Ya'yan dana haifa,ALLAH yamuku albarka,yabaku zuri'a d'ayyiba. Dole ta d'auki cokali tayi bismillah sannan tad'an ci kad'an, Bello kuma yace shi baya shi dan bayajin yunwa yanata cin meatpie da su Inibin da Julaibib ya bashi.Da za su tafi Sudaida tabata turmin atamfa,taba da Shadda yadi goma da turare wai aba Malam tana kuma gaishe shi,tak'aro ma Bello meatpie dayawa dan jiya tayi kuma ba wanda yazo gidan shiyasa bai k'areba.Yakalleta yana ta murmushi "kince za ki Matsirga?Tagyad'a kai"eh Bello zamu zo Insha-ALLAH.Yamik'a mata hannu sukayi musafaha "Adda Sudaida sai kinzo zan tatso miki madarar saniyata da Malam yabani karsana guda biyu nawa ni kad'ai ina kaisu kiwo har rafin Matsirga nake kaisu susha ruwa sai mudawo gida,sukayi dariya.Sannan ta rakasu haraban gidan suka shiga mota.Sudaida tasunkuyo tana maimata" ALLAH yatsare Innarmu,ALLAH yakaiku gida lafiya.Amin Sudaida, Inna tadinga shi mata albarka,tasa gefen hijab d'inta tana share ruwan hawaye,yau mutuwar Bilkisu ta dawo mata sabuwa.Suka d'aga hannu suna ma juna adabo.Julaibib yaja motar cikin karsashi,yana murmushi jin dad'i abinda tama Innar Bilkisu ya kankare duk wani bak'in laifi data mishi dayake jin haushi...wata irin k'auna da kewar ta suka mamaye ilahirin gangar jiki da zuciyar shi.
Yadawo yatar da jarkokin kindirmo dana manshanu da sauran tsarabar da Inna takawo a inda yatafi yabar su.Yatsaya a gabanta hannayen shi suna cikin aljihun doguwar farar rigar shi,yakalleta cikin natsuwa"Sudaida ya baki adana suba?Saboda bani da buk'atar sune. Tagama wanke-wanken da take yi tamik'e tana yarfar da ruwan hannayen ta,tawani tsuke baki kamar me shirin yin fito.Yagyad'a kai"toh bani abinci sauri nake yi zan tafi Samaru.Cikin fushi tace"na rantse da girman ALLAH tun kafin wankin hula yakaika ga dare kasan inda za kaje kaci abincin ka,danni ba baiwa bace. Yazuba mata idanu"ji wasu soki burutsu da yarinyar nan take fad'a,yakalleta cikin natsuwa"nine bawan ki kenan, tunda duk rintse zan fita in nemo in kawo miki ki ci ko? Taturo baki gaba"ko bani dolen-dole kafita ka nemo,to ni guda nawa nake cin abincin?
Kinga ba wannan ba d'auko min abinci na fad'a miki sauri nake yi"na daina girki a gidan nan, tunda ko a tsarin shari'a ai cewa akayi miji yaciyar da matar shi bawai mace tayi girki ba.Yagyad'a kai"to amma dai yin girki a wajen mace dole ne,tunda kyautatawace idan miji yafita ya nemo muku,ke kuma sai ki dafa muku, a kuma al'adar duk mutanen dana sani galibi matane suke yin girki haka aka taso anayi Iyaye da kakanni tun tale-tale.Ba sai da so da k'auna za ayi hakan ba?Tafara k'unk'uni.Shima sai yanzu ya harbo jirginta...kumallon mata ke d'awainiya da ita,to amma me san d'an tsuntsu shi yake binshi da jifa.
Yarik'o ta tana k'ok'arin fizgewa sai yamata rik'on kura ta samu nama,sai ta koma tayi lamooo "Sudaida a duniyar ALLAH me namiki da bakya so na?Yad'ago fuskar ta suka kalli juna"haba Zaujatiii...Dan girman ALLAH fad'amin abinda zan miki dan in samu k'auna da soyayyarki.. yagewaye hannayeshi a jikinta yana mata wani salo...yayi k'asa da murya yana mata wasu irin kalamai na rarrashi da bambaki me k'aryar da damuwar data mamaye sararin zuciya.
Sak'onnin na shi yana shiga ilahirin gangar jiki da zuciyarta duk da bata so hakan ba amma zuciyar ta tak'i bujirema hakan,k'aunar shi da haushin shi yamamaye ta,sai kawai ta fashe da kuka ta k'wace tashige d'akin bacci tafad'a gado takifa fuskar ta a jikin matashi tana jin wani irin abu dabata san ko menene ba.
Ga na Khausar nan ita da Huzaifa sunyi wani irin kyau na ban mamaki gaba d'ayan su sun canja,ta d'ora ha6arta a kafad'arshi suna dariya, d'ayan kuma wasu irin kalamai ne na tsananin k'auna ta rubuta shi ga hoton zuciya an gewaye ta da adon filawar Damask rose-flower.
Na maryam kuma hummm sallah ba a magana,ta yi mugun mamakin abinda ta d'ora a irin yanayin zaman da tayi da kuma kayan jikin ta,a k'asa ta rubuta"My Snuggle...I miss you deadly... tabbb...ai bata gama kallo ba tabari tana zagin ta "abinda yasa meki ALLAH yasa kar yasamu sauran dangi.Tayita kira layin ta a kashe, duk da ta san taza6i wad'anda za su ga Status d'in na tane,amma ita sai hakan bai gamshe taba gaskiya.
"Nasmat tamata magana"
Hummm...Amaryar autan Inna kuna shan sharafin ku fa..
Sudaida ta6ata fuska"a ah abinda yafi sharafi muke sha.
Nasmat takyalkyale da dariya...nima naga alama shi yasa sai jefi-jefi a ke ganin ki online...har yanzu kanwa bata kar tsamin bane k'wannafin yakwanta?
Sudaida taja dogon tsaki"ke dai kika sani da neman magana ni sai da safe...kawai ta kashe data ta kwanta;bata duba sak'o ko guda d'aya ba,tunani barkatai ya cika k'wak'walwarta "hummm yunwar ya tashi"taja dogon tsaki wallahi ai ba lallai ba tilas.
Washe gari ma da sassafe yabar gidan wai suna da taro a Zango Urban kamar tace yasiyo mata d'anbagalaje amma ta shareshi,ta d'auki wayar ta takira Yaya Aminu tana tambayar shi"kaima kana Zangon ne?Eh Sudaida.Dan ALLAH Yaya Aminu d'anbagalaje nake so amma me taushi.Kai kai kai Sudaida ai gwamma me k'arfin kinga za ki motsa muk'amuk'inki da dasashi ko kuwa? Tad'an marairaice"Yaya Aminu ni dai me taushi.To zan siyo miki Insha-ALLAH. Yauwa Yaya Aminu wallahi, shi yasa nake son ka ALLAH yabarka da Sidddiqa tazama sarauniyar ka.Amin Sudaida. Sukayi dariya.
Abubuwa suke ta maimaituwa na rashin fahimtar juna a tsakanin su,musamman Sudaida da take d'aukar fushi a abinda bai kamata ayi fushin ba,abun ya k'i ci ya k'i cinyewa kamar cin k'wan makauniya.Yauma tunda yatafi masallaci sallar asubahi bai dawo gidan ba.A hankali taji ana k'wank'wansa k'ofar gidan ta san shine, dan taji tsayuwar motar shi.Tatashi tabud'e takoma tayi kwanciyar ta.Yatsaya a tsakiyar d'akin hannayen shi nad'e a k'irji.
"Sudaida bak'in Matsirga sun zo.
Dammm...zuciyar ta tabuga da k'arfin gaske.Tafara zancen zuci"Kutumelesi wato zuwa yayi dakan shi yad'auko su?Su suna da mutunci da kima a idanun shi,ya kuma damu dasu amma ita ko oho ko?
Tajijjiga kai wani...kumallon mata yata so mata har wuya,amma ba tayi ko kawa da zuciyar ta bata amayo shiba.Tad'ago takalleshi"Oh sun zo?Tagyad'a kai"toh sannun su da zuwa. Yabita da kallan nazari ganin tana dad'a gyara kwanciya har da jan bargo ta lullu6a"ke wai menene haka?Kitashi kije ku gaisa mana. Tayamutsa fuska sannan tajuya mishi k'eya "gaskiya ni har yanzu bacci ne a cikin idanu na kum...Yatari numfashin ta "Innar su Bilkisu ce fa?
Furucin shi yamata sukar wuk'a a k'ahon zuciya wallahi ta kasa daurewa,idanun ta suka kawo ruwa"shikenan kuma dan kayi bak'i bazan yi bacci ba,bayan idanu na har wani zafi da yaji-yaji suke min saboda rashin baccin?Ni fa na rantse da girman ALLAH bazan iya wannan zaman ba,tunda baka d'auke ni wata tsiya ba,toh ba dani ba wannan takuran,ko dan kaga gidan kane? Tagalla mishi harara"an hak'ura ana shan kukar k'azama kuma dole sai tayi tsada?Wallahi sai a hak'ura tunda ba mutuwa za ayi ba ehemmm.
Suka zubama juna idanu cikin kallan-kallo nawucewar wasu dak'ik'u kowa zuciyar shi ba dad'i. Sudaida tana jiran martani ne tayi abinda idan ta tafasa za ta k'one,sai shi kuma yamata shiru,dan yadda ta6ata mishi rai idan yatsaya toh aika-aika za ayi,sai kawai yagyad'a kai"ki cigaba da abinda kike yi,amma fa kowa yaci ladan kuturu sai ya mishi aski,wanda ya girmama iyayen wani to bana kowa ya girmama ba sai na shi.Yakai hannu yak'ara mata gudun fankar "shikenan kiyi baccin ki.Yajuya yafita fuskar shi ba walwala,labarin zuciya a tambayi fuska.
Tad'aga murya"eh yanzu kuwa zanyi baccin.Sai kuma tamik'e jikin ta yayi sanyi gaskiyar magana bai kamata tayi haka ba"ai bak'on ka annabinka, wanda yadamu dakai shine zai zo inda kake to bai kamata kanuna mishi halin-ko-inkula ba"bak'in karen masoyinka ai yafi farin ragon mak'iyinka.
Yayi jimmm...nawucewar wasu dak'ik'u a bak'in k'ofa,Sudaida ta k'i fitowa ta musu sannu da zuwa to me zai fad'ama Inna?Sai yajuya zuwa D'akin-girki yad'ibo musu kofuna da lemun biyar a raye da ruwa har zuwa lokacin bai samo amsar dazai ba Inna ba,yahura iskar bakin shi"lallai Sudaida zata gane da gero ake koko yacigaba da tafiya,zai fad'a mata Sudaida bata nan.
Yamurd'a k'ofar D'akin-shak'atawar da sallama yashiga,sai dai abun mamaki Baturiya da suna manga Sudaida yagani durk'ushe a gaban Inna tana gaisheta cikin girmamawa"kun zo lafiya? Yasu Malam da sauran mutan gidan?A Alhamdulillahi lafiya lau,duk suna gaishe ki,sannu mungode.Daganin yadda Inna take amsawa itama taji dad'in shimfid'ar fuskar da Sudaida tamata wacce tafi ta tabarma.Tamik'ama Bello hannu sukayi musafaha "d'an kanina kaga dana iya yaren fulatanci toh da yau duk hirarmu da fillanci za muyi shi. Bello yad'an bud'e idanu"kai dama baki iya ba?To kisa Yaya D'ansarai ya dinga koya miki mana,kinga lokacin da Adda batayi wannan tafiya me nisan nan ba to idan yazo da fillanci suke magana suyi ta dariya,ranan nan ma yace mata wai...Kai Bello Inna ta tari numfashin shi'ba na hana ka fad'an abinda ba a tambaye kaba? Sai yayi shiru.
Da sauri Sudaida tamik'e ta kar6i kayan ta zuzzuba musu lemon a kofuna sanna tashiga D'akin-girki ta d'auko musu abincin data dafa tajuye a food-flask tana mita a ranta"kai ALLAH yasuwake da halin D'ansarai yanzu da suna da yawa dole sai tayi wani sabon girkin. Inna tasha lemon amma tak'i cin abincin.Sudaida ta karyar da kai gefen dama"haba Innarmu idan baki ciba ai baza muji dad'i ba,ni 'ya ce awajen ki,uwa kuma ai bazata k'i cin abincin 'yar taba ko da tak'oshi za tasa albarka,Inna idan bakiciba sai inga kamar da wata a k'asa a yadda muka d'aukeki ni da Yaya D'ansarai ke ba haka kika d'auke muba...suna had'a idanu tad'an harare shi sannan ta kauda kai. Inna tace"ba haka babe Sudaida, karki kuma furta irin wad'annan kalaman,ni na d'aukeku kamar Ya'yan dana haifa,ALLAH yamuku albarka,yabaku zuri'a d'ayyiba. Dole ta d'auki cokali tayi bismillah sannan tad'an ci kad'an, Bello kuma yace shi baya shi dan bayajin yunwa yanata cin meatpie da su Inibin da Julaibib ya bashi.Da za su tafi Sudaida tabata turmin atamfa,taba da Shadda yadi goma da turare wai aba Malam tana kuma gaishe shi,tak'aro ma Bello meatpie dayawa dan jiya tayi kuma ba wanda yazo gidan shiyasa bai k'areba.Yakalleta yana ta murmushi "kince za ki Matsirga?Tagyad'a kai"eh Bello zamu zo Insha-ALLAH.Yamik'a mata hannu sukayi musafaha "Adda Sudaida sai kinzo zan tatso miki madarar saniyata da Malam yabani karsana guda biyu nawa ni kad'ai ina kaisu kiwo har rafin Matsirga nake kaisu susha ruwa sai mudawo gida,sukayi dariya.Sannan ta rakasu haraban gidan suka shiga mota.Sudaida tasunkuyo tana maimata" ALLAH yatsare Innarmu,ALLAH yakaiku gida lafiya.Amin Sudaida, Inna tadinga shi mata albarka,tasa gefen hijab d'inta tana share ruwan hawaye,yau mutuwar Bilkisu ta dawo mata sabuwa.Suka d'aga hannu suna ma juna adabo.Julaibib yaja motar cikin karsashi,yana murmushi jin dad'i abinda tama Innar Bilkisu ya kankare duk wani bak'in laifi data mishi dayake jin haushi...wata irin k'auna da kewar ta suka mamaye ilahirin gangar jiki da zuciyar shi.
Yadawo yatar da jarkokin kindirmo dana manshanu da sauran tsarabar da Inna takawo a inda yatafi yabar su.Yatsaya a gabanta hannayen shi suna cikin aljihun doguwar farar rigar shi,yakalleta cikin natsuwa"Sudaida ya baki adana suba?Saboda bani da buk'atar sune. Tagama wanke-wanken da take yi tamik'e tana yarfar da ruwan hannayen ta,tawani tsuke baki kamar me shirin yin fito.Yagyad'a kai"toh bani abinci sauri nake yi zan tafi Samaru.Cikin fushi tace"na rantse da girman ALLAH tun kafin wankin hula yakaika ga dare kasan inda za kaje kaci abincin ka,danni ba baiwa bace. Yazuba mata idanu"ji wasu soki burutsu da yarinyar nan take fad'a,yakalleta cikin natsuwa"nine bawan ki kenan, tunda duk rintse zan fita in nemo in kawo miki ki ci ko? Taturo baki gaba"ko bani dolen-dole kafita ka nemo,to ni guda nawa nake cin abincin?
Kinga ba wannan ba d'auko min abinci na fad'a miki sauri nake yi"na daina girki a gidan nan, tunda ko a tsarin shari'a ai cewa akayi miji yaciyar da matar shi bawai mace tayi girki ba.Yagyad'a kai"to amma dai yin girki a wajen mace dole ne,tunda kyautatawace idan miji yafita ya nemo muku,ke kuma sai ki dafa muku, a kuma al'adar duk mutanen dana sani galibi matane suke yin girki haka aka taso anayi Iyaye da kakanni tun tale-tale.Ba sai da so da k'auna za ayi hakan ba?Tafara k'unk'uni.Shima sai yanzu ya harbo jirginta...kumallon mata ke d'awainiya da ita,to amma me san d'an tsuntsu shi yake binshi da jifa.
Yarik'o ta tana k'ok'arin fizgewa sai yamata rik'on kura ta samu nama,sai ta koma tayi lamooo "Sudaida a duniyar ALLAH me namiki da bakya so na?Yad'ago fuskar ta suka kalli juna"haba Zaujatiii...Dan girman ALLAH fad'amin abinda zan miki dan in samu k'auna da soyayyarki.. yagewaye hannayeshi a jikinta yana mata wani salo...yayi k'asa da murya yana mata wasu irin kalamai na rarrashi da bambaki me k'aryar da damuwar data mamaye sararin zuciya.
Sak'onnin na shi yana shiga ilahirin gangar jiki da zuciyarta duk da bata so hakan ba amma zuciyar ta tak'i bujirema hakan,k'aunar shi da haushin shi yamamaye ta,sai kawai ta fashe da kuka ta k'wace tashige d'akin bacci tafad'a gado takifa fuskar ta a jikin matashi tana jin wani irin abu dabata san ko menene ba.