Sashe 12
Gwajin Dafi Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bismillahi wabihi nasta'in
...GWAJIN DAFI💔
Almost true story
Daga alk'alamin🖊
Ya'yan Ibrahim
Saudat A.Baba (Asdilat KD)
Da
Bara'atu Ibrahim (Ra'ibs)
Shafi na bakwai.
Kasan mafarkin danayi daren jiya kuwa? Musaddiq yagirgiza kai.Wai Julaibib ne da Kasham suke kiwon shanu a wani k'aton fili iya ganinka me cike da koren ciyayi.Musaddiq yakyalkyale da dariya"D'ansarai fulani ka koma har matarka take taya ka kiwo saboda tsabar k'auna?Musaddiq da Maimun d'in da yayi mafarkin suka kalleshi yana zuba d'anyan na'a na'a, d'anyan citta da ya'yan algarib a ruwan shayin da yake dafa musu,zuman da suke shan shayi ya k'are,sai yazuba sikari d'an kad'an dan dukkansu basa san zak'i,yamaida murfin tukunyar yarufe,yayi kamar baiji abinda suke fad'a ba.
"Julaibib.
Maimun yakirashi.Yajuyo da saurinshi yana amsawa"na'am.Bakaji abinda nafad'a bane? Shiruma amsace.Yad'auki wasu kud'i a saman tebur yamik'a ma Musaddiq "Malam tashi ka kar6o mana biredi.
Cikin natsuwa yake tafiya dawowar shi kenan daga gidansu A'isha amma cikin rashin sa a yatarar wai sunyi tafiya,ya dai barma Nasir sallahu idan ta dawo yazo yafad'a mishi.Sudaida tana hangoshi tafara murmushi dan ta kwana biyu bata ganshiba,jiya da akace ya zo, taje ta gaisheshi bata jeba.
"Yaya D'ansarai sannu da zuwa...
Iskar data d'ibo tama bai kalla ba bare yasan ALLAH yayi ruwan tsiranta.Ita da Sinan d'in daya ke shirin yimishi sallama suka bishi da kallo har yashige cikin gidan.Sinan yakad'a kai"Julaibib sai a hankali.Suka gama hirar su sukayi sallama.
A D'akin-girki ta tarar da Mama.Mama tace yauwa d'auki abincin nan ki kaima D'ansarai.Haushinshi takeji ta turo baki gaba"Mama shi yace miki yana jin yunwa?Mama tabita da kallan mamaki,sannan tamata dak'uwa gidan ku"Sai yace yana jin yunwa za a bashi abinci a gidan nan?ke wace irin yarinyace?Jiyama danace kiji ki gaisheshi ashe ko bakije ba,saida zai tafi yake tambayar ki sai Sagir ne yace kina d'akinku kin kulle k'ofa.Sa an kine D'ansarai? Tad'auki abincin tabar Mama na mata addu'ar shiriya.Dak'yar tayi sallama dan tasan idan ma bata yiba,sai ya korata ta yishi.Ko kallanta bai yiba har ta ajiye abincin tajuya.
Umma tashigo D'akin- shak'atawar dan lokacin da yashigo tana sallar.Yagaisheta cikin girmamawa.Tayi murmushi"D'an Sarai yaro ne me hankali, yasan ya kamata sosai"Karatu ya k'are sai jiran sakamako ko?To Ubangiji yabada abinda ake nema.Yad'an shafa kwantaccen bak'in gashin kanshi."amin ya rabbi Umma". Tamik'e to bakaci abincin ba?Yakalli kwanon abincin"ai ni ban san ni takawo ma ba,dan a jiyewa tayi tafita.Kai kawai tagyad'a tafita.
Tana cin na ta abincin Umma tasa meta batace kome ba hannunta kawai ta damk'o,rik'on data matane yasa tasan cewa lallai bana wasa bane"Umma me nayi?Bakiyi kome ba ko?Sai tafara tirjewa dan wallahi idan ta yadda Umma takaita d'akinta to na jaki zata sha ba kad'an ba dan Umma ba sauk'i,shi yasama ba ta wani wasa dasu akwaita da zafi,sam ba ta d'aukar rashin kunya shi yasa kowa yake shakkarta a gidan,yana yinsu ba d'aya bane da Mama,da wasu lokutan suke maida ita kamar wata kakarsu,sai tazo ta tsawatar musu suke daina wani abun.
Umma dan girman ALLAH kiyi hak'uri na tuba nabi ALLAH na biki,kiyi ha...saukan marin yasa sauran kalaman suka mak'ale. Idanunta suka ciko da k'wallan wuya, dan marin ya ratsata yadda yakamata.Tasa ihu Mama dan girman ALLANMU zo ki ceceni,wayyo ALLAH! Ke...!Umma tace tana kallanta cikin zaro idanu "rufemin baki ke mara kunya ko?Ai ina jinku da Mama a D'akin-girki..Umma dan darajar Annabi Muhammadu kiyi hak'uri.... Mama wai kina inane?!
Mama tak'araso wajan da saurinta"a ah to me tamiki kuma?Ni tama laifi dama jira nake Musaddiq yashigo in fad'a mishi.Sudaida kuka takeyi da gaskiyar ta ita dai aba Umma hak'uri dan idan ba itace da bakin ta,tace ta hak'ura ba to lallai sai tayi dukan nan ko kuma ta had'a ka da Adnan shima kwallan shege a wajan iya ba da na jaki.Mama takan cemishi "Sarki zalimu dan dai ba ya'yanka bane,baka san zafin suba shi yasa kake musu wannan dukan na rashin tausayi.Sai yayi dariya "ai ko su d'in ne haka zan musu indai sukace baza su bi abinda zan fad'a musu ba wallahi.Dak'yar takwace Sudaida a hannun Umma.Sudaida tace" nagode"to amma Mama kibata hak'uri.Tagyad'a kai"ai zata hak'ura ne.Umma tace"na rantse da girman ALLAH zan hak'ura ne kawai idan taje takaima D'ansarai ruwan sha,tamatsa da abincin gabanshi, takuma gaisheshi tabashi hak'urin dangwarar da abincin da akace takai mishi.Idan ba haka ba tayi d'as d'as d'as da yan yatsunta ta shige d'aki.
Duk yadda taso dakewa idan zata shiga d'akin abin yaci tura.Cikin kuka tayi sallama.Yad'ago yana kallanta ta ajiye ruwan ta d'auko abincin,wani haushinshi yacika mata zuciya saboda shi aka so a bata na jaki,da Mama ba tanan a yadda ran Umma ya6aci ba k'aramar wahala zata shaba,shi ba a ganin abinda yakema mutane na halin-ko-inkula sai ita?Dak'yar tace"Ina wuni...wani sabon kuka ya kufce mata wai har hak'uri sai tabashi? Yaya...kayi hak'uri... tausayinta yaka mashi koma menene yasan Umma ce ta sata wannan ban hak'urin.Nayi hak'uri Sudaida ai dama baki min kome ba,to zuba min abincin kad'an, tadauki faranti tazuba ta mik'a mishi.Yayi bismillah yafara ci.
Kafanchan ne garin dasu A'isha suka tafi. Babban gidane a Magiya Street me sassa guda bakwai sai dai a kulle suke da kwad'o saboda mutanan ciki ma'aikatane a garuruwa mabambanta,idan ana sha'ani ko sun samu hutun aikine za kaga gidan ya cika da jama'a. Sashin Kaka dana kusa da itane kawai koda yaushe a bud'e jama'a na kai kawo.
Gidan yayi shiru saboda sauran yaran gidan sun tafi makaranta sai kukan tsuntsaye da suke ta shawaginsu."Hantsi ya dubi ludayi rana ta haska ko'ina. Hashim bacci yake so yayi amma wani nishad'd'd'an al'amari ya hanashi sak'at bare yabarshi yarintsa.
"Aishahhh...
Yafurta sunan a zuci sannan yabud'e idanunshi cikin agogon dake manne a bangon d'akin "goma da rabi na safiya.
Sai yamik'e, sashin Kaka yanufa Alhamdulillahi"yafad'a daya fara jiyo dariyar ta, hira sukeyi da Kaka.Yayi sallama sannan yad'aga labulan dak'in,caraf idanunsu yahad'u tace"Hum manya gatan wasa,akwana a hantse... Kaka ta 6alli goronta tajefa a baki sannan ta d'an harareshi"to kar dai kanka yayi girma dan tace haka. Yak'arasa shiga yazauna a d'aya kujerar suna fuskantar juna da A'isha.Shi dai A'isha tana burgeshi baya gajiya da kallanta da duk wani abu data keyi.Yamaida kallanshi ga Kaka saboda me kikace kar kaina yayi girma?Tace naga dai wannan kirarin kyawawa akema. Aisha tasa baki "yanzu Hashim yana da makusa neKaka?Aiko makaho yashafa wannan k'ayatacciyar fuskar zaice me kyauce. Yad'an motsa kafad'a"Ah to gane min hanya...wai yaushane tafiyar taki?Tawatsa hannaye"ganinan dai, amma ba wani dad'ewa zanyi ba, tare dasu Mama zamu tafi,kasan har yanzu bamuyi hutu ba, amma da zamana zanyi wallahi garin bai ishe niba.
Yagyara zama"Shikenan sai a miki babban gida kawai yadda zai dad'a burgeki,kidinga jin dad'in zama.Cikin rashin fahimta tayi yar dariya "Kaji Hashim fa babban gida sai kace wacce zata dawo da zamanta gaba d'aya? Yagyada kai"To menene A'isha dan kin dawo gaba d'aya? Ai kamar ba matsala bace garin da kike so ne,ga kuma mutanan da kike so.
Yakalli Kaka da take ta cin goronta "Ke dai kamar mayya haka kike da goro.Eh koma dai mecece ni ba daina ci zanyi ba ko kai kake siyomin?Ya yamutsa fuska"To da wacce hujjar nasara zaiyi hawan k'aho? Tamishi dak'uwa idan baka siyo ba ai ubanka zai siyo.Shi da Aisha suka d'aure fuska wai su an ta6a musu Iyaye. Hashim yace"a ah Kaka wasa kar yayi wasa a tsikari uwar miji fa.A'isha tagyad'a kai"gaskiya ne dan uba baifi uba ba "Kaka tafara tafa hannaye cikin sallallami.Sai suka kyalkyale da dariya.Ba shakka wuyanku ya isa yanka. Tad'auko carbi zata shaud'ama A'isha ALLAH yabata sa a tayi tsalle gefe"Tabbb yanzu dan ALLAH sai ki shaud'amin wannan k'irgin carbin na ki me siffar rodi?To dawo ki gani mana.Tagirgiza kai"a ah wallahi ai sai in kwanta jinya, suka gama mata shak'iyanci san ransu sannan suka fara hirar arzik'i.
Hashim yadad'a gyara zama sannan yakalli Kaka cikin natsuwa"Kaka gaskiyar magana nifa A'isha nake so ba wani 6oye-6oye dama karatune yahanani sak'at to yanzu kam sai dai godiyar Ubangiji an gama har kuma an samu abun yi basai maganar iyaliba? Kaka tad'aga hannayenta sama tanama ALLAH godiya"Ashe tuntuni dakake fad'in Aisha ce matarka na d'auka na k'uruciyane nan gaba idan aka maka zance za kayi tawaye?To masha-ALLAH,ALLAH yasanya alheri,naji dad'in wannan al'amari,dakan d'aka shik'an d'aka tankad'en bakin gado.
Hashim yayi yar dariya"Aiko dai ba wani tawaye da zanyi yakalli Aisha ta sunkwui da kai amma labarin zuciya a tambayi fuska murmushi takeyi.Kaka tamik'e zata shaud'a mata carbin"Munafuka ana zance auranta ta nemi waje ta zauna saboda rashin kunya irin na ya'yan yau.Tashige d'akin baccin Kaka da gudu dan wallahi bata manta dukan carbin Kaka ba akwai mugun zafi.
Hashim yayi murmushi Kakarmu ta kanmu ALLAH dai yabamu i taku.tsufa me amfani acikin hayyaci da tunani.To Amin Hashimu,amma ba abinda yake kawo tsufa me kyau me amfani sai aikin k'warai lokacin k'uruciya"tsohon banza daga yaran banza yafara"kurik'e karatun"Alqur'ani da sauran kyawawan dabi'u da halaye, kuyi gaskiya da adalci a kome,idan kuka d'ore a haka Insha-ALLAH babu ta6ewa a rayuwarku.
IImi shine jigon rayuwa,shine abinda yake gyara d'an Adam,yagayara tunaninshi dan haka ku kara zage dantse da kwazo wajan nemanshi,Ilmi ko wani irine to yanada amfaninshi. ALLAH yama rayuwarku albarka. Amin Kaka.
Hashim da A'sha sai rawar kai sukeyi kamar k'adangaran gobara,daga ranar yakoma cin abincin darenshi a d'akin Kaka abinda da ba yayi sai can nisan dare sannan yake tafiya na shi d'akin wani lokacinma Kaka ce take korarshi yatafi yabasu waje za su kwanta. Kafin su A'isha subar garin Kafanchan sai da aka tsaida magana tana gama makarantar secondary za ayi bikinsu ba wata matsala da aka samu kasancewar su Ya'ya mazane kuma duk Kakace ta haifi Iyayan nasu. Shi kuma nan da nan yafara aikin ginin gidanshi a Zaria Street.
Kasham tana shafa ma faratanta jan farce (nail polish)ruwan k'asa,Baranzan yashigo cikin kakin soja. Suka kalli juna na wucewar wasu dak'ik'u."Beauty ina kikaje tun d'azu nake ta jiranki?Kamar ba da ita yake magana ba,zuwan can kuma bayan ta shak'i iska ta baki ta hanci sannan tace kasuwa naje siyo wannnan tanuna mishi nail polish d'in.Yazauna"anjima zani Jos amma kwanaki uku zanyi,to na baki time kafin indawo ki shirya kayanki zamu wuce barrack.
...GWAJIN DAFI💔
Almost true story
Daga alk'alamin🖊
Ya'yan Ibrahim
Saudat A.Baba (Asdilat KD)
Da
Bara'atu Ibrahim (Ra'ibs)
Shafi na bakwai.
Kasan mafarkin danayi daren jiya kuwa? Musaddiq yagirgiza kai.Wai Julaibib ne da Kasham suke kiwon shanu a wani k'aton fili iya ganinka me cike da koren ciyayi.Musaddiq yakyalkyale da dariya"D'ansarai fulani ka koma har matarka take taya ka kiwo saboda tsabar k'auna?Musaddiq da Maimun d'in da yayi mafarkin suka kalleshi yana zuba d'anyan na'a na'a, d'anyan citta da ya'yan algarib a ruwan shayin da yake dafa musu,zuman da suke shan shayi ya k'are,sai yazuba sikari d'an kad'an dan dukkansu basa san zak'i,yamaida murfin tukunyar yarufe,yayi kamar baiji abinda suke fad'a ba.
"Julaibib.
Maimun yakirashi.Yajuyo da saurinshi yana amsawa"na'am.Bakaji abinda nafad'a bane? Shiruma amsace.Yad'auki wasu kud'i a saman tebur yamik'a ma Musaddiq "Malam tashi ka kar6o mana biredi.
Cikin natsuwa yake tafiya dawowar shi kenan daga gidansu A'isha amma cikin rashin sa a yatarar wai sunyi tafiya,ya dai barma Nasir sallahu idan ta dawo yazo yafad'a mishi.Sudaida tana hangoshi tafara murmushi dan ta kwana biyu bata ganshiba,jiya da akace ya zo, taje ta gaisheshi bata jeba.
"Yaya D'ansarai sannu da zuwa...
Iskar data d'ibo tama bai kalla ba bare yasan ALLAH yayi ruwan tsiranta.Ita da Sinan d'in daya ke shirin yimishi sallama suka bishi da kallo har yashige cikin gidan.Sinan yakad'a kai"Julaibib sai a hankali.Suka gama hirar su sukayi sallama.
A D'akin-girki ta tarar da Mama.Mama tace yauwa d'auki abincin nan ki kaima D'ansarai.Haushinshi takeji ta turo baki gaba"Mama shi yace miki yana jin yunwa?Mama tabita da kallan mamaki,sannan tamata dak'uwa gidan ku"Sai yace yana jin yunwa za a bashi abinci a gidan nan?ke wace irin yarinyace?Jiyama danace kiji ki gaisheshi ashe ko bakije ba,saida zai tafi yake tambayar ki sai Sagir ne yace kina d'akinku kin kulle k'ofa.Sa an kine D'ansarai? Tad'auki abincin tabar Mama na mata addu'ar shiriya.Dak'yar tayi sallama dan tasan idan ma bata yiba,sai ya korata ta yishi.Ko kallanta bai yiba har ta ajiye abincin tajuya.
Umma tashigo D'akin- shak'atawar dan lokacin da yashigo tana sallar.Yagaisheta cikin girmamawa.Tayi murmushi"D'an Sarai yaro ne me hankali, yasan ya kamata sosai"Karatu ya k'are sai jiran sakamako ko?To Ubangiji yabada abinda ake nema.Yad'an shafa kwantaccen bak'in gashin kanshi."amin ya rabbi Umma". Tamik'e to bakaci abincin ba?Yakalli kwanon abincin"ai ni ban san ni takawo ma ba,dan a jiyewa tayi tafita.Kai kawai tagyad'a tafita.
Tana cin na ta abincin Umma tasa meta batace kome ba hannunta kawai ta damk'o,rik'on data matane yasa tasan cewa lallai bana wasa bane"Umma me nayi?Bakiyi kome ba ko?Sai tafara tirjewa dan wallahi idan ta yadda Umma takaita d'akinta to na jaki zata sha ba kad'an ba dan Umma ba sauk'i,shi yasama ba ta wani wasa dasu akwaita da zafi,sam ba ta d'aukar rashin kunya shi yasa kowa yake shakkarta a gidan,yana yinsu ba d'aya bane da Mama,da wasu lokutan suke maida ita kamar wata kakarsu,sai tazo ta tsawatar musu suke daina wani abun.
Umma dan girman ALLAH kiyi hak'uri na tuba nabi ALLAH na biki,kiyi ha...saukan marin yasa sauran kalaman suka mak'ale. Idanunta suka ciko da k'wallan wuya, dan marin ya ratsata yadda yakamata.Tasa ihu Mama dan girman ALLANMU zo ki ceceni,wayyo ALLAH! Ke...!Umma tace tana kallanta cikin zaro idanu "rufemin baki ke mara kunya ko?Ai ina jinku da Mama a D'akin-girki..Umma dan darajar Annabi Muhammadu kiyi hak'uri.... Mama wai kina inane?!
Mama tak'araso wajan da saurinta"a ah to me tamiki kuma?Ni tama laifi dama jira nake Musaddiq yashigo in fad'a mishi.Sudaida kuka takeyi da gaskiyar ta ita dai aba Umma hak'uri dan idan ba itace da bakin ta,tace ta hak'ura ba to lallai sai tayi dukan nan ko kuma ta had'a ka da Adnan shima kwallan shege a wajan iya ba da na jaki.Mama takan cemishi "Sarki zalimu dan dai ba ya'yanka bane,baka san zafin suba shi yasa kake musu wannan dukan na rashin tausayi.Sai yayi dariya "ai ko su d'in ne haka zan musu indai sukace baza su bi abinda zan fad'a musu ba wallahi.Dak'yar takwace Sudaida a hannun Umma.Sudaida tace" nagode"to amma Mama kibata hak'uri.Tagyad'a kai"ai zata hak'ura ne.Umma tace"na rantse da girman ALLAH zan hak'ura ne kawai idan taje takaima D'ansarai ruwan sha,tamatsa da abincin gabanshi, takuma gaisheshi tabashi hak'urin dangwarar da abincin da akace takai mishi.Idan ba haka ba tayi d'as d'as d'as da yan yatsunta ta shige d'aki.
Duk yadda taso dakewa idan zata shiga d'akin abin yaci tura.Cikin kuka tayi sallama.Yad'ago yana kallanta ta ajiye ruwan ta d'auko abincin,wani haushinshi yacika mata zuciya saboda shi aka so a bata na jaki,da Mama ba tanan a yadda ran Umma ya6aci ba k'aramar wahala zata shaba,shi ba a ganin abinda yakema mutane na halin-ko-inkula sai ita?Dak'yar tace"Ina wuni...wani sabon kuka ya kufce mata wai har hak'uri sai tabashi? Yaya...kayi hak'uri... tausayinta yaka mashi koma menene yasan Umma ce ta sata wannan ban hak'urin.Nayi hak'uri Sudaida ai dama baki min kome ba,to zuba min abincin kad'an, tadauki faranti tazuba ta mik'a mishi.Yayi bismillah yafara ci.
Kafanchan ne garin dasu A'isha suka tafi. Babban gidane a Magiya Street me sassa guda bakwai sai dai a kulle suke da kwad'o saboda mutanan ciki ma'aikatane a garuruwa mabambanta,idan ana sha'ani ko sun samu hutun aikine za kaga gidan ya cika da jama'a. Sashin Kaka dana kusa da itane kawai koda yaushe a bud'e jama'a na kai kawo.
Gidan yayi shiru saboda sauran yaran gidan sun tafi makaranta sai kukan tsuntsaye da suke ta shawaginsu."Hantsi ya dubi ludayi rana ta haska ko'ina. Hashim bacci yake so yayi amma wani nishad'd'd'an al'amari ya hanashi sak'at bare yabarshi yarintsa.
"Aishahhh...
Yafurta sunan a zuci sannan yabud'e idanunshi cikin agogon dake manne a bangon d'akin "goma da rabi na safiya.
Sai yamik'e, sashin Kaka yanufa Alhamdulillahi"yafad'a daya fara jiyo dariyar ta, hira sukeyi da Kaka.Yayi sallama sannan yad'aga labulan dak'in,caraf idanunsu yahad'u tace"Hum manya gatan wasa,akwana a hantse... Kaka ta 6alli goronta tajefa a baki sannan ta d'an harareshi"to kar dai kanka yayi girma dan tace haka. Yak'arasa shiga yazauna a d'aya kujerar suna fuskantar juna da A'isha.Shi dai A'isha tana burgeshi baya gajiya da kallanta da duk wani abu data keyi.Yamaida kallanshi ga Kaka saboda me kikace kar kaina yayi girma?Tace naga dai wannan kirarin kyawawa akema. Aisha tasa baki "yanzu Hashim yana da makusa neKaka?Aiko makaho yashafa wannan k'ayatacciyar fuskar zaice me kyauce. Yad'an motsa kafad'a"Ah to gane min hanya...wai yaushane tafiyar taki?Tawatsa hannaye"ganinan dai, amma ba wani dad'ewa zanyi ba, tare dasu Mama zamu tafi,kasan har yanzu bamuyi hutu ba, amma da zamana zanyi wallahi garin bai ishe niba.
Yagyara zama"Shikenan sai a miki babban gida kawai yadda zai dad'a burgeki,kidinga jin dad'in zama.Cikin rashin fahimta tayi yar dariya "Kaji Hashim fa babban gida sai kace wacce zata dawo da zamanta gaba d'aya? Yagyada kai"To menene A'isha dan kin dawo gaba d'aya? Ai kamar ba matsala bace garin da kike so ne,ga kuma mutanan da kike so.
Yakalli Kaka da take ta cin goronta "Ke dai kamar mayya haka kike da goro.Eh koma dai mecece ni ba daina ci zanyi ba ko kai kake siyomin?Ya yamutsa fuska"To da wacce hujjar nasara zaiyi hawan k'aho? Tamishi dak'uwa idan baka siyo ba ai ubanka zai siyo.Shi da Aisha suka d'aure fuska wai su an ta6a musu Iyaye. Hashim yace"a ah Kaka wasa kar yayi wasa a tsikari uwar miji fa.A'isha tagyad'a kai"gaskiya ne dan uba baifi uba ba "Kaka tafara tafa hannaye cikin sallallami.Sai suka kyalkyale da dariya.Ba shakka wuyanku ya isa yanka. Tad'auko carbi zata shaud'ama A'isha ALLAH yabata sa a tayi tsalle gefe"Tabbb yanzu dan ALLAH sai ki shaud'amin wannan k'irgin carbin na ki me siffar rodi?To dawo ki gani mana.Tagirgiza kai"a ah wallahi ai sai in kwanta jinya, suka gama mata shak'iyanci san ransu sannan suka fara hirar arzik'i.
Hashim yadad'a gyara zama sannan yakalli Kaka cikin natsuwa"Kaka gaskiyar magana nifa A'isha nake so ba wani 6oye-6oye dama karatune yahanani sak'at to yanzu kam sai dai godiyar Ubangiji an gama har kuma an samu abun yi basai maganar iyaliba? Kaka tad'aga hannayenta sama tanama ALLAH godiya"Ashe tuntuni dakake fad'in Aisha ce matarka na d'auka na k'uruciyane nan gaba idan aka maka zance za kayi tawaye?To masha-ALLAH,ALLAH yasanya alheri,naji dad'in wannan al'amari,dakan d'aka shik'an d'aka tankad'en bakin gado.
Hashim yayi yar dariya"Aiko dai ba wani tawaye da zanyi yakalli Aisha ta sunkwui da kai amma labarin zuciya a tambayi fuska murmushi takeyi.Kaka tamik'e zata shaud'a mata carbin"Munafuka ana zance auranta ta nemi waje ta zauna saboda rashin kunya irin na ya'yan yau.Tashige d'akin baccin Kaka da gudu dan wallahi bata manta dukan carbin Kaka ba akwai mugun zafi.
Hashim yayi murmushi Kakarmu ta kanmu ALLAH dai yabamu i taku.tsufa me amfani acikin hayyaci da tunani.To Amin Hashimu,amma ba abinda yake kawo tsufa me kyau me amfani sai aikin k'warai lokacin k'uruciya"tsohon banza daga yaran banza yafara"kurik'e karatun"Alqur'ani da sauran kyawawan dabi'u da halaye, kuyi gaskiya da adalci a kome,idan kuka d'ore a haka Insha-ALLAH babu ta6ewa a rayuwarku.
IImi shine jigon rayuwa,shine abinda yake gyara d'an Adam,yagayara tunaninshi dan haka ku kara zage dantse da kwazo wajan nemanshi,Ilmi ko wani irine to yanada amfaninshi. ALLAH yama rayuwarku albarka. Amin Kaka.
Hashim da A'sha sai rawar kai sukeyi kamar k'adangaran gobara,daga ranar yakoma cin abincin darenshi a d'akin Kaka abinda da ba yayi sai can nisan dare sannan yake tafiya na shi d'akin wani lokacinma Kaka ce take korarshi yatafi yabasu waje za su kwanta. Kafin su A'isha subar garin Kafanchan sai da aka tsaida magana tana gama makarantar secondary za ayi bikinsu ba wata matsala da aka samu kasancewar su Ya'ya mazane kuma duk Kakace ta haifi Iyayan nasu. Shi kuma nan da nan yafara aikin ginin gidanshi a Zaria Street.
Kasham tana shafa ma faratanta jan farce (nail polish)ruwan k'asa,Baranzan yashigo cikin kakin soja. Suka kalli juna na wucewar wasu dak'ik'u."Beauty ina kikaje tun d'azu nake ta jiranki?Kamar ba da ita yake magana ba,zuwan can kuma bayan ta shak'i iska ta baki ta hanci sannan tace kasuwa naje siyo wannnan tanuna mishi nail polish d'in.Yazauna"anjima zani Jos amma kwanaki uku zanyi,to na baki time kafin indawo ki shirya kayanki zamu wuce barrack.