Sashe 28
Gwajin Dafi Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tad'an 6ata fuska ni dai gaskiya... Yatari numfashin ta"haba Sumayya ta tawa ni kad'ai yad'an d'age gira"bazan iya hakurin jure rashin ki bane,magana awaya kad'ai ni dai bata gamshe ni ba shi yasama kika ganni ganin idanunki yamata wani kallo"mhm me kika ce ne?
Tasunkwui da kai"haba Sumayya yi magana mana,Salim mijiki ke kad'ai ne fa.Tad'an harareshi bayan kace ba alk'awari kad'auka ba,dan dai dole sai ka k'ara auren nan.Yagyad'a kai"gaskiya banyi wannan alk'awarin ba,kar baki yaci idanu su zo suna jin kunya.Tace"Uhhh madallah to yanzu kake so mutafi?A ah ai yamma ta yi kuma kinga Mama bata dawo daga kasuwa ba dole ai sai mun mata sallama, gobe da sassafe sai muwuce.
Sumayya takoma makaranta dan hutun da aka basu ya k'are,karatu sosai sukeyi ba kama hannun yaro saboda wannan shekarar za su gama.Sumayya ba ta da wata gagarumar matsala a bangaran karatu duk abinda bata gane ba, to tana dawowa gida Salim zai warware mata shi,bata ta6a sanin me tarin ilmi bane sai bayan auransu data shiga wani d'an d'aki dayake yin nazari da bincike wallahi tasha mamakin irin tarin littafan addinin data gani.bai ta6a nuna mata ya san wani abu ba sai da zama yahad'asu. Salim jarumine me damuwa da damuwar iyalinshi.
Suna hirarsu a D'akin-shak'atawa cikin nishad'i yajuyo kukan Ummi daga d'akin baccinsu ta tashi daga bacci kenan, yaje yad'auko ta,yabata ruwan zamzam d'in da suke bata tasha ya mik'a mata ita" ga ta ki bata abincin ta yunwa take ji.Tamarairaice Sumayya a wajan shayarwa ba ta da jarumta"kai ma ka san daga ta shinta a bacci baza tasha ba.Yagalla mata harara"ba yunwa take ji ba amma take ta k'ok'arin kai hannuna bakinta? Kar6eta mana.Tamika hannu ta kar6eta Tad'an 6ata fuska"ai ban san kana harara ba sai na ga idanun a k'asa.Yayi yar dariya"Hunn Sumayya ta ke dai bata abincin ta kawai ba na san neman magana.
Sun gama karatu lafiya kuma sakomako yayi kyau Malam Muhammad Aminu shi yasamo mata gurbin karatu a Jami'ar Madina dan babban d'anshi a can yake da zama shi da iyalinshi Salim shi yanemi wannan alfarmar kuma aka mishi amma ba da san zuciya ba, a ah adadin makin da suke nema to na Sumayya ya kai...anata mata shirin tafiya inda zataje ta yi Masters a kan dai Islamic Studies.Kamar wasa tafara rashin lafiya yau ciwo gobe sauk'i,suka tafi asibiti aka mata gwaje-gwaje har aka gano abinda yake damunta ciwon siga(diabetes) amma sun d'ora ta akan magani da wasu sharud'd'ai da dole sai ta kiyayesu in dai tana san zaman lafiya,kuma sun bata kwanakin da zata sake komawa asibiti dan su tabbatar magungunan suna aikin da ake so ? Idan basa yi sai a canja wasu.
Abokan karatunta kullum suna tafe, basa gajiya da zuwa gaisheta saboda halinta na karamci "masoya da mak'iya ba a guzurin su duk inda kaje halin ka zai ba kasu"abun hannu ta bai ta6a rufe mata idanu ba.Ranan Salim yakalleta "yaushe na baki kud'in da har za kice sun k'are Sumayya?Tad'an marairaice"Baban Ummi ni dai dan ALLAH kataimake ni kawai,akwai wacce mukama alk'awarin ba ta tallafi a k'ungiyarmu ni wallahi na manta,anjima za tazo k'ar6a ai da bazan kashe wadan can ba aciki zan bata" haba nijina duk abinda kaba wani shine na ka,wanda kaci kashi yake zama,wanda kake ajiyewa ba lallai kai d'in ne za kayi amfani dashi ba, wata kila sai dai magada su gada.Alheri dank'one da baya fad'uwa k'asa banza.
Yak'irgo adadin data fad'a yabata"ina sanki Sumayya ta tawa ni kad'ai"Tasa hannu biyu takar6a nima haka mungode madallah Ubangiji yak'aro bud'i. Yad'an d'age gira yana mata wani kallo. Tagyad'a kai"Eh mana you're a good samaritan"Yad'an bata marin soyayya suka kyalkyale da dariya.
Abu kamar wasa k'aramar magana ta zama babba,ciwo ya tasa Sumayya a gaba, kullum magani akeyi ciwo yana dad'a k'aruwa, watan ta d'aya cur tana kwance a gadan asibiti sannan tad'an dawo hayyacin ta,ita tamatsa aka sallame ta tare da k'arin wasu sharud'd'ai da zata kuma kiyayewa dan ta zauna lafiya.
Yazuba mata idanu bacci take yi, tayi bak'i ta fita hayyacin ta,shima wallahi jinshi yake kamar mara lafiya.Yadad'a rungume Ummi da take bacci bayan ta gama rigimar a bata abincin ta kuma an yaye ta,ya had'a mata shayi amma tak'i sha,dak'yar dai ya rarrashe ta takoma bacci sai ajiyar zuciya take yi.Ya sauke gwauran numfashi "ALLAH yabaki lafiya Sumayya,ALLAH yasa kaffara ce".
A hankali tabud'e idanun ta takai hannu tana d'an shafa kan Ummi sannan ta kalleshi "sannu Baban Ummi wai har yanzu baka fita ba?Yakad'a kai"Kayyah... Sumayya duk inda naje tunanin halin da na barki bazai barni inyi wani sukuni ba. Amma ai yau naga jikin na ki da sauk'i ko?To me za ta ce? Ita kad'ai tasan azabar ciwon da take ji,ba tasan yawan k'orafi tunda yana matuk'ar k'ok'ari da jikinshi,aljihunshi,kalamanshi da kuma lokacin shi, duk tsadar magana bai ta6a nuna gazawarshi wajan siyo mata shi ba, haka irin kalar abincin da akace shi zata dinga ci dayawa yasiyo mata ya ajiye. Tad'an yi yak'e dayafi kuka ciwo"Alhamdulillahi ala kulli halin".
Ummi tasa hannu a baki tana tsotsa cikin dabara yazare hannu sannan ya kwantar da ita yana tambayar Sumayya abinda za taci da rana duk da a yanzu cin abincin na ta,ba wani na azo a gani bane,wasu lokutan ma sai yanuna 6acin rai sannan take d'an tsakura.
Salim...tabishi da kallo yazauna a gefen gadan yana kallanta shima ya d'anji mamakin kiran sunan shi da tayi yanzu kai tsaye.Yarik'o hannayan ta yana kallan yadda tafin ciki ya d'ashe kamar mara jini amma ko d'azu da safe Doctor Zainab ta tabbatar mishi tana da jini dai-dai yadda ake so baiyi kad'an ba"Uhun me kike so kifad'a min ne?Sharrr...sharrr...wasu hawaye masu d'umi suke zubo mata"muryar ta tafara rawa"ni dai nagode ma Ubangijin mu daya min gata da samun ka a matsayin miji. Ina san ka Baban Ummi...tamishi wani irin kallo da yasa zuciyar shi bugawa da k'arfin gaske.Yakauda kai "Sumayya me za kici?Yasake tambayar ta.Kar ka damu zan sha shayi.Yasa hannu yana share mata hawayen"ki daina kuka ALLAH zai ba ki lafiya mukoma cin had'ad'd'an abincin ki me rai da motsi.Tabishi da kallo cikin kissima wani irin yanayi a zuciyarta.Hawayen suka sake zubo mata sharrr...idan tafad'a mishi yadda take ji a cikin jikinta tayar me da hankali za tayi zai rasa sukuni dan haka taja bakinta tayi shiru.
Ranar da taje gidan Alhaji Hafiz suka wuni suna hira sai bayan isha'i yazo ya d'auke su.Sun kwanta lafiya lau cikin farin ciki sun dad'e suna hirar su kafin bacci yayi awan gaba dasu, amma cikin dare nishinta metsananin k'arfine yafarkar dashi daga bacci, yakunna wutar d'akin tana kwance cikin mawuyacin hali. Sumayya...!ko kallanshi ba tayiba, dan ba ta cikin hayyacin ta ne, idanunta sai rufewa da bud'ewa suke yi kamar wacce tasha kayan maye ta bugu sosai,bakin ta a bud'e ya bushe k'amas,ta rasa inda za ta tsoma ranta taji dad'i sai tafara wata irin shak'uwa,a gigice ya d'auko ruwa yana bata amma bata iya had'iya ba haka yake biyo gefen bakinta yana zubewa tana wata irin jijjiga... Sumayya...! Yafara girgiza ta Sumayya kalleni...!Ina hankalin ta baya jikinta tana gargara..."Laahaula wala quuwata illa billah "kome na ta ya saki a hankali tafara jan numfashi me tsawo sai ta sauke shi a hankali,sai takuma janshi sai yayi kamar ya tafi bazai dawo ba zuwa can sai ta sauke shi a hankali, haka tadingayi,yakwantar da ita yafara neman makullin motarshi amma tsabar rud'ewa wallahi sai yarasa a inda ya ajiyeshi,a fizge tafara kalmar shahada abinda yadad'a gigitashi kenan...zuwa can kuma kamar anyi ruwa an d'auke sai yaji d'ifff...
Sumayya...!yakira sunanta da k'arfi yata6a kirjinta difff...Numfashi baya shiga da fita...Sumayya! Yad'aga hannun ta na dama yarafff...yafad'i a kan katifa.Abubuwa da yawa suka yamutsa k'wak'walwar shi bangaran tunani sai yaji ruguzowar wani abu a k'ahon zuciyar shi da k'arfin gaske Dammm...!!!
Ta mutu...!Sumayya ta mutu...?!!!
Sai yafara k'arya ta zuciyar shi dan idanun sun fara mishi gizo sun nuna mishi ga tanan tana numfashin ta"Sumayya au dama baki mutu ba? Yasake kallanta idanun ta a k'ak'k'afe ruwan ciki yak'ame k'amas suna kallan sama tayi tsawo da wani irin kyau na ban mamaki shi bai ta6a ganin wannan kyan ba ko lokacin da take ganiyar lafiyar ta take kwalliya da gayu...bai san awani yanayi yake ba har sai da aka kirashi a waya.
Miqdad ne yake tambayar shi lafiya kuwa ban ganka a masallaci sallar asubahi ba,ko jikin Sumayyan ne?Asanyaye yace"Sumayya ta mutu.Cikin k'araji Miqdad ya sake tambayar shi"ta mutu? Yaushe?Wasu irin hawaye masu d'umi suka zubo mishi sharrr...sai kawai ya katse wayar yakifa kanshi a kusa da fuskar ta, ya rasa abinda yake mishi dad'i sai yafara Istirja'i...Miqdad shi yaje gida yad'auko su Alhaji Hafiz suka d'unguma gaba d'ayansu zuwa gidan hankali a tashe.Amma Salim yayi dauriya dan shi yamata wanka yashirya ta tsab aka mata sallah aka d'auketa a makara sai makwancinta na gaskiya kabari d'aki a cikin kasa"Uh uhun duniya rumfar kara...Wata rana zai fad'i.ALLAH yajikanki Sumayya yasa k'arshen wahalar kenan!
Lokaci d'aya Salim yayi wata rin rama kamar wanda ya shekara yana jinya.A ranar Iyayanta suka zo.Maman tana kuka ta rungume Ummi tana sambatu "Holy Jesus why? Why? Me yasa Kasham za ta mutu yanzu? Me yasa za ka bari a kashe min yarinya...To wallahi bazan ta6a yafewa ba...me Kasham ta tare muku ne?
Alhaji Hafiz ya k'araso wajan da sauri "haba Dinatu ya kike irin wannna kalaman ne? Mutane fa za suyi zatan kasheta akayi.To dama ba kasheta akayi ba? Kaima ai ka sani ko har ka manta tunda ba 'yar ka bace? Yakad'a kai cikin damuwa"ko na sani a yanzu dai na manta,mudai a addininmu na musulunci duk wanda yamutu to tabbaci hak'ik'a kwananshine kawai yak'are, amma ba mayune suka kashe shiba "ai sara da sassak'a basa hana gamji toho...a ah Shedrak wallahi Kasham dai kashe min ita akayi, ba ta zo sun ganta cikin rufin asiri ba?Takuma yin kururuwa cikin tafasar zuciya"Wai...Wayyoh...ALLAH!!! Kasham ta mutu...Judith ta mutu...oh Jesus Christ of Nazareth!
Shedrak!
Tasunkwui da kai"haba Sumayya yi magana mana,Salim mijiki ke kad'ai ne fa.Tad'an harareshi bayan kace ba alk'awari kad'auka ba,dan dai dole sai ka k'ara auren nan.Yagyad'a kai"gaskiya banyi wannan alk'awarin ba,kar baki yaci idanu su zo suna jin kunya.Tace"Uhhh madallah to yanzu kake so mutafi?A ah ai yamma ta yi kuma kinga Mama bata dawo daga kasuwa ba dole ai sai mun mata sallama, gobe da sassafe sai muwuce.
Sumayya takoma makaranta dan hutun da aka basu ya k'are,karatu sosai sukeyi ba kama hannun yaro saboda wannan shekarar za su gama.Sumayya ba ta da wata gagarumar matsala a bangaran karatu duk abinda bata gane ba, to tana dawowa gida Salim zai warware mata shi,bata ta6a sanin me tarin ilmi bane sai bayan auransu data shiga wani d'an d'aki dayake yin nazari da bincike wallahi tasha mamakin irin tarin littafan addinin data gani.bai ta6a nuna mata ya san wani abu ba sai da zama yahad'asu. Salim jarumine me damuwa da damuwar iyalinshi.
Suna hirarsu a D'akin-shak'atawa cikin nishad'i yajuyo kukan Ummi daga d'akin baccinsu ta tashi daga bacci kenan, yaje yad'auko ta,yabata ruwan zamzam d'in da suke bata tasha ya mik'a mata ita" ga ta ki bata abincin ta yunwa take ji.Tamarairaice Sumayya a wajan shayarwa ba ta da jarumta"kai ma ka san daga ta shinta a bacci baza tasha ba.Yagalla mata harara"ba yunwa take ji ba amma take ta k'ok'arin kai hannuna bakinta? Kar6eta mana.Tamika hannu ta kar6eta Tad'an 6ata fuska"ai ban san kana harara ba sai na ga idanun a k'asa.Yayi yar dariya"Hunn Sumayya ta ke dai bata abincin ta kawai ba na san neman magana.
Sun gama karatu lafiya kuma sakomako yayi kyau Malam Muhammad Aminu shi yasamo mata gurbin karatu a Jami'ar Madina dan babban d'anshi a can yake da zama shi da iyalinshi Salim shi yanemi wannan alfarmar kuma aka mishi amma ba da san zuciya ba, a ah adadin makin da suke nema to na Sumayya ya kai...anata mata shirin tafiya inda zataje ta yi Masters a kan dai Islamic Studies.Kamar wasa tafara rashin lafiya yau ciwo gobe sauk'i,suka tafi asibiti aka mata gwaje-gwaje har aka gano abinda yake damunta ciwon siga(diabetes) amma sun d'ora ta akan magani da wasu sharud'd'ai da dole sai ta kiyayesu in dai tana san zaman lafiya,kuma sun bata kwanakin da zata sake komawa asibiti dan su tabbatar magungunan suna aikin da ake so ? Idan basa yi sai a canja wasu.
Abokan karatunta kullum suna tafe, basa gajiya da zuwa gaisheta saboda halinta na karamci "masoya da mak'iya ba a guzurin su duk inda kaje halin ka zai ba kasu"abun hannu ta bai ta6a rufe mata idanu ba.Ranan Salim yakalleta "yaushe na baki kud'in da har za kice sun k'are Sumayya?Tad'an marairaice"Baban Ummi ni dai dan ALLAH kataimake ni kawai,akwai wacce mukama alk'awarin ba ta tallafi a k'ungiyarmu ni wallahi na manta,anjima za tazo k'ar6a ai da bazan kashe wadan can ba aciki zan bata" haba nijina duk abinda kaba wani shine na ka,wanda kaci kashi yake zama,wanda kake ajiyewa ba lallai kai d'in ne za kayi amfani dashi ba, wata kila sai dai magada su gada.Alheri dank'one da baya fad'uwa k'asa banza.
Yak'irgo adadin data fad'a yabata"ina sanki Sumayya ta tawa ni kad'ai"Tasa hannu biyu takar6a nima haka mungode madallah Ubangiji yak'aro bud'i. Yad'an d'age gira yana mata wani kallo. Tagyad'a kai"Eh mana you're a good samaritan"Yad'an bata marin soyayya suka kyalkyale da dariya.
Abu kamar wasa k'aramar magana ta zama babba,ciwo ya tasa Sumayya a gaba, kullum magani akeyi ciwo yana dad'a k'aruwa, watan ta d'aya cur tana kwance a gadan asibiti sannan tad'an dawo hayyacin ta,ita tamatsa aka sallame ta tare da k'arin wasu sharud'd'ai da zata kuma kiyayewa dan ta zauna lafiya.
Yazuba mata idanu bacci take yi, tayi bak'i ta fita hayyacin ta,shima wallahi jinshi yake kamar mara lafiya.Yadad'a rungume Ummi da take bacci bayan ta gama rigimar a bata abincin ta kuma an yaye ta,ya had'a mata shayi amma tak'i sha,dak'yar dai ya rarrashe ta takoma bacci sai ajiyar zuciya take yi.Ya sauke gwauran numfashi "ALLAH yabaki lafiya Sumayya,ALLAH yasa kaffara ce".
A hankali tabud'e idanun ta takai hannu tana d'an shafa kan Ummi sannan ta kalleshi "sannu Baban Ummi wai har yanzu baka fita ba?Yakad'a kai"Kayyah... Sumayya duk inda naje tunanin halin da na barki bazai barni inyi wani sukuni ba. Amma ai yau naga jikin na ki da sauk'i ko?To me za ta ce? Ita kad'ai tasan azabar ciwon da take ji,ba tasan yawan k'orafi tunda yana matuk'ar k'ok'ari da jikinshi,aljihunshi,kalamanshi da kuma lokacin shi, duk tsadar magana bai ta6a nuna gazawarshi wajan siyo mata shi ba, haka irin kalar abincin da akace shi zata dinga ci dayawa yasiyo mata ya ajiye. Tad'an yi yak'e dayafi kuka ciwo"Alhamdulillahi ala kulli halin".
Ummi tasa hannu a baki tana tsotsa cikin dabara yazare hannu sannan ya kwantar da ita yana tambayar Sumayya abinda za taci da rana duk da a yanzu cin abincin na ta,ba wani na azo a gani bane,wasu lokutan ma sai yanuna 6acin rai sannan take d'an tsakura.
Salim...tabishi da kallo yazauna a gefen gadan yana kallanta shima ya d'anji mamakin kiran sunan shi da tayi yanzu kai tsaye.Yarik'o hannayan ta yana kallan yadda tafin ciki ya d'ashe kamar mara jini amma ko d'azu da safe Doctor Zainab ta tabbatar mishi tana da jini dai-dai yadda ake so baiyi kad'an ba"Uhun me kike so kifad'a min ne?Sharrr...sharrr...wasu hawaye masu d'umi suke zubo mata"muryar ta tafara rawa"ni dai nagode ma Ubangijin mu daya min gata da samun ka a matsayin miji. Ina san ka Baban Ummi...tamishi wani irin kallo da yasa zuciyar shi bugawa da k'arfin gaske.Yakauda kai "Sumayya me za kici?Yasake tambayar ta.Kar ka damu zan sha shayi.Yasa hannu yana share mata hawayen"ki daina kuka ALLAH zai ba ki lafiya mukoma cin had'ad'd'an abincin ki me rai da motsi.Tabishi da kallo cikin kissima wani irin yanayi a zuciyarta.Hawayen suka sake zubo mata sharrr...idan tafad'a mishi yadda take ji a cikin jikinta tayar me da hankali za tayi zai rasa sukuni dan haka taja bakinta tayi shiru.
Ranar da taje gidan Alhaji Hafiz suka wuni suna hira sai bayan isha'i yazo ya d'auke su.Sun kwanta lafiya lau cikin farin ciki sun dad'e suna hirar su kafin bacci yayi awan gaba dasu, amma cikin dare nishinta metsananin k'arfine yafarkar dashi daga bacci, yakunna wutar d'akin tana kwance cikin mawuyacin hali. Sumayya...!ko kallanshi ba tayiba, dan ba ta cikin hayyacin ta ne, idanunta sai rufewa da bud'ewa suke yi kamar wacce tasha kayan maye ta bugu sosai,bakin ta a bud'e ya bushe k'amas,ta rasa inda za ta tsoma ranta taji dad'i sai tafara wata irin shak'uwa,a gigice ya d'auko ruwa yana bata amma bata iya had'iya ba haka yake biyo gefen bakinta yana zubewa tana wata irin jijjiga... Sumayya...! Yafara girgiza ta Sumayya kalleni...!Ina hankalin ta baya jikinta tana gargara..."Laahaula wala quuwata illa billah "kome na ta ya saki a hankali tafara jan numfashi me tsawo sai ta sauke shi a hankali,sai takuma janshi sai yayi kamar ya tafi bazai dawo ba zuwa can sai ta sauke shi a hankali, haka tadingayi,yakwantar da ita yafara neman makullin motarshi amma tsabar rud'ewa wallahi sai yarasa a inda ya ajiyeshi,a fizge tafara kalmar shahada abinda yadad'a gigitashi kenan...zuwa can kuma kamar anyi ruwa an d'auke sai yaji d'ifff...
Sumayya...!yakira sunanta da k'arfi yata6a kirjinta difff...Numfashi baya shiga da fita...Sumayya! Yad'aga hannun ta na dama yarafff...yafad'i a kan katifa.Abubuwa da yawa suka yamutsa k'wak'walwar shi bangaran tunani sai yaji ruguzowar wani abu a k'ahon zuciyar shi da k'arfin gaske Dammm...!!!
Ta mutu...!Sumayya ta mutu...?!!!
Sai yafara k'arya ta zuciyar shi dan idanun sun fara mishi gizo sun nuna mishi ga tanan tana numfashin ta"Sumayya au dama baki mutu ba? Yasake kallanta idanun ta a k'ak'k'afe ruwan ciki yak'ame k'amas suna kallan sama tayi tsawo da wani irin kyau na ban mamaki shi bai ta6a ganin wannan kyan ba ko lokacin da take ganiyar lafiyar ta take kwalliya da gayu...bai san awani yanayi yake ba har sai da aka kirashi a waya.
Miqdad ne yake tambayar shi lafiya kuwa ban ganka a masallaci sallar asubahi ba,ko jikin Sumayyan ne?Asanyaye yace"Sumayya ta mutu.Cikin k'araji Miqdad ya sake tambayar shi"ta mutu? Yaushe?Wasu irin hawaye masu d'umi suka zubo mishi sharrr...sai kawai ya katse wayar yakifa kanshi a kusa da fuskar ta, ya rasa abinda yake mishi dad'i sai yafara Istirja'i...Miqdad shi yaje gida yad'auko su Alhaji Hafiz suka d'unguma gaba d'ayansu zuwa gidan hankali a tashe.Amma Salim yayi dauriya dan shi yamata wanka yashirya ta tsab aka mata sallah aka d'auketa a makara sai makwancinta na gaskiya kabari d'aki a cikin kasa"Uh uhun duniya rumfar kara...Wata rana zai fad'i.ALLAH yajikanki Sumayya yasa k'arshen wahalar kenan!
Lokaci d'aya Salim yayi wata rin rama kamar wanda ya shekara yana jinya.A ranar Iyayanta suka zo.Maman tana kuka ta rungume Ummi tana sambatu "Holy Jesus why? Why? Me yasa Kasham za ta mutu yanzu? Me yasa za ka bari a kashe min yarinya...To wallahi bazan ta6a yafewa ba...me Kasham ta tare muku ne?
Alhaji Hafiz ya k'araso wajan da sauri "haba Dinatu ya kike irin wannna kalaman ne? Mutane fa za suyi zatan kasheta akayi.To dama ba kasheta akayi ba? Kaima ai ka sani ko har ka manta tunda ba 'yar ka bace? Yakad'a kai cikin damuwa"ko na sani a yanzu dai na manta,mudai a addininmu na musulunci duk wanda yamutu to tabbaci hak'ik'a kwananshine kawai yak'are, amma ba mayune suka kashe shiba "ai sara da sassak'a basa hana gamji toho...a ah Shedrak wallahi Kasham dai kashe min ita akayi, ba ta zo sun ganta cikin rufin asiri ba?Takuma yin kururuwa cikin tafasar zuciya"Wai...Wayyoh...ALLAH!!! Kasham ta mutu...Judith ta mutu...oh Jesus Christ of Nazareth!
Shedrak!