Sashe 20
Gwajin Dafi Complete Hausa Novel · about 8 min read
Rannan dai Miqdad ya galla mata harara"Ke malama kar ki damume da maganar wani D'ansarai mutumin da ko hoton shi baki dashi.Wani lallausan murmushi yasu6uce mata"na rantse maka da ALLAH inada hotunanshi,ni ban san yadda akayi da nazo nan ban gansuba ina tunanin Lidiya ce ta bincike min jaka ta kwashe su amma da hannuna na sakasu.Bros karka damu duk ranar danaje Zonkwa bazan dawoba sai da hotunan shi"za kaga kyakkyawan bak'in mutumi na,me tsabta,ma'abocin sa fararan kaya.
Sumayya...a d'an firgice tad'ago sannan ta amsa"Na'am.Lafiya kika zabga wannan tagumin?Takad'a kai kwallah sun cika idanunta tamaida kanta jikin kujeran dan ba ta so su zubo "Maman Hasan Julaibib ne na kasa yin yak'i da zuciyata wajan cireshi a cikinta, kullum sai na yi mafarkin shi sai dai ban kwanta bacci ba me yasa?Saboda abinda kika sa a zuciyarki kenan tunanin shi,duk abinda ka kwallafa rai da shi to a mafi yawan lokaci sai kayi mafarkin shi"sa rai a ci shi ke kawo jin yunwa"
Takamo hannayenta,Sumayya ki fahimci wani abu"D'an Adam da kike ganinshi to shi yake saima kanshi mutunci da daraja,shi zai kame kanshi sannan mutane su d'aukeshi da mutunci su girmama shi"Haja ita takema kanta kud'i.kin damu dashi da yawa,sannan abin takaicin bai san kina yi ba harara a duhu..kilama ya manta ya ta6a ganinki,shi yana can hankalin shi a kwance yana gudanar da al'amuran rayuwar shi,ke kina nan kin takure kanki cikin tunanin shi"wannan fa kamar aikin banza ne sammakon gaida mak'iyi.
...Julaibib yana da matar aure makaranta ake jira tagama musha biki,kuma k'anwata ce...kalaman matar Musaddiq kenan ranar dataje musu murnar aure...
Tasauke numfashi"to amma ai banyi laifi ba ko a addinance.Maman Hasan tajijjiga kai"kwarai kuwa bakiyi laifi ba,hakan ya halatta sai dai a yadda muka saba a al'adance namijine yake furta hakan ga 'ya mace,saboda kawaici irin na Hausa-Fulani,sai dai ban san sauran al'ummatai ba,ba kasafai matan suke yin haka ba.Kiyita addu'a ALLAH alhakimune ba yadda ba ya shirya al'amura. Jikinta yayi sanyi ba wata gaskiya bayan wannan"a hankali tayi furucin nagode Maman Hasan da wannan tunatarwa.
Miqdad yafito daga d'akinshi yana karya hula.Sumayya tabishi da kallo yanayi da d'abi'unshi suna mata shige dana D'ansarai shima ma'abocin sa fararan kayane.Yayi murmushi ganin kallan da take mishi"Sumayya ya akayi ne? Tayi yar dariya"wallahi Bros kayi kyau ba k'arya wannan shigar sunnan ta k'ayar dani fa. To nagode,yau ba Islamiyya ne?Akwai sai zuwa anjima.
Hafsa tafito daga D'akin-girki tana kallanshi "Yaya Miqdad baza ka tsaya kaci abincin bane?Yad'an sosa kunne"fita zanyi.Tad'an marairaice"ALLAH sarki Yaya Miqdad inata sauri ne fa,wallahi na kusa gamawa. Yakalli agogon dake d'aure a hannun shi na dama"Ina bazan tsaya ci ba gaskiya.Ta turo baki gaba gaskiya ni dai banji dad'iba.Sai kawai tajuya tana k'unk'uni. Yarik'o hannunta"baba tawaje nah,kiyi hak'uri kiran gaggawa aka min a wajan aiki,yadafa kafad'arta yad'an d'age gira cikin murmushi"Yaya Miqdad ne fa?Tad'an harareshi tana dad'a turo baki ni dai...yatari numfashin ta"kinga kwantar da hankalin ki"bayan sallar azahar zan aiko a kar6a sai inci acan shikenan ko?Tad'anyi tsallan murna"yauwa Yayanmu to adawo lafiya"tabashi hannu sukayi musafaha suna dariya.ALLAH yasa tawaje nah...suka d'aga hannu suna ma juna adabo.
Julaibib tunda yatafi sau d'aya yazo sai yanzu da suka samu hutun Semester, haka yadinga zaga gidajan yan'uwa yana gaishesu.Suna zaune shi da Musaddiq suna tattauna al'amuran daya shafesu Safiyya tayi sallama tashigo D'akin-shak'atawar sanye da dogon hijab suka gaisa cikin mutunta juna ta tashi tafita,bata sake shigowaba sai da tagama abincin rana tahad'a duk ahinda za su buk'ata a babban tire takai musu.Musaddiq yakar6eta da saurin shi"yauwa Safiyya,ALLAH dai yak'ara miki albarka da lafiya.Shida ita suka kalli juna suna murmushi,ta tsuguna da niyyar zuba musu yace"a ah wallahi amaryata ai kinyi me wuyar jeki kawai tuzuru zaiyi kome.
Julaibib yayi kamar bai gane shagu6en ba,yad'auki kofi yazuba lemun kashu da abarba,yayi hismillah yafara kur6a.Musaddiq yace kai ni bangane bane anyi yamma da kare ni baza ka zuba min bane?Ya ajiye kofin yana nuna kanshi da yatsa"ni kace zanyi kome ko tuzuru? Ni sunana Julaibib ban san wani tuzuru kake nufi ba, ka san dama ni ban saba da sai anyi service d'ina ba, yazuba abincin a faranti yafara ci.Musaddiq yagalla mishi harara"wa za ka raina ma hankali? malam kayi aure kaji dad'in rayuwar ka,dawani tuzuru ne bayan kai?Yayi kamar ba dashi yake magana ba.Musaddiq yad'auki cokali to ajiye abincin muci mana. Yajanye farantin da sauri"a ah yau bazan ci abinci dakai ba,tashi katafi wajan matarka taba ka abincin abaki ma wannan ba damuwata bace.Au haka za kace?Yad'an d'age gira yana mishi wannan rikitaccen kallan nashi"Eh haka nace da magana ne?A ah ba ni da tacewa...wai ankama 6arawo da kayan sa ta.
A sanda hantsi ya dubi ludayi na safiyar alhamis Sudaida da d'an d'okinta na san ganinshi ta tafi gidan Inna,amma irin amsa gaisuwar daya mata yasa jikinta yayi sanyi"wai an jefi kaza da gishiri,baiko d'ago kai ya kalleta daga tarin littafan daya barbaza a saman tebur ba,a dak'ile yake amsa gaisuwar da take mishi da lafiya...Tazuba mishi idanu na wucewar wasu dak'ik'u sannan ta d'ora envelop d'in hannunta a saman tebur d'in gabanshi.Yakalli envelop d'in a gajarce yacigaba da rubutun shi ba tare kuma daya d'ago kanshi ba yake tambayar ta"na meye? Haushinshi yakamata,ta galla mishi harara tajuya"nima ban sani ba.garammm tabugo k'ofar da k'arfi.Sai lokacin yad'ago yakalli k'ofar,yad'an motsa kafad'a yacigaba da abinda yakeyi har aka fara kiraye-kirayen sallar azahar bai gama ba, turesu kawai yayi gefe yayi alwala yatafi masallaci.
Bai samu damar bud'e envelop d'in ba sai daya zo kwanciyar bacci"D'an k'aramin frame ne me hoton ayatul Qursiyu,a kasanshi wani tsibiri ne me ban sha'awa ruwa yana gudu...sai d'an takadda anyi rubutu sad'ara hud'u.
...Julaibib...na san kome zan ba ka a banza zaga ganshi,amma wannan na tabbatar ma kaina koda ba ka so na,na san za ka alkinta shi ko???
I dore you my Enigma...
Kasham Kantiok Donatus.
Yakaranta yasake karantawa,yakai hancinshi yana shinshina frame d'in daya ke k'amshin irin turaran ta.Yayi lallausan murmushi dan yaji dad'i har ranshi yajijjiga kai"Tabbas kin bani abinda zan alkin ta Kasham...na kuma gode. Sai ya d'orashi agefen gado yakwanta yana azkar d'in bacci, yanata kallan frame d'in yana tuna had'uwarsu da Kasham tun ranar farko da kallan farko da sukama juna a haka har bacci yayi awan gaba dashi.
Azaure sukayi kaci6is taja baya da sauri jakar hannunta ta su6uce zata fad'i a k'asa,cikin zafi nama yacafe,yamik'a mata, takar6a tana gaishe shi. Idanunshi akanta"wa yabaki envelop d'in nan?Tamishi wani irin kallo fuska a d'an yamutse"Malama Kasham.Tun yaushe?Baku dad'e da tafiya Zaria ba.Yad'anyi murmushi cikin gyad'a kai"To nagode,Kawu yana ciki?Eh yana ciki.Yajuya zuwa cikin gidan tabishi da kallan mamaki D'ansarai kamar kuli-kuli yake da ba a gane gabanshi wallahi,Jiya fa shine yamata halin-ko-inkula amma yanzu har da wani murmushi taja dogon tsaki "Kai ALLAH yasauwake maka.
Sumayya ta zage dantse tana kwankwad'ar madarar ilimi,gaba d'aya ta canja ta zama wata ta musamman"Unique charisma"fatar jikinta ma ta canja saboda canjin cima,a gidan Alhaji Hafiz za a ci abincin safe me kyau me gina jiki,da ranama haka a mafi yawan lokuta ba sa kasafai suke yin girki da daddare ba,sai dai asha su gwanda,Inibi,tuffa,dabino a kora da madara idan kuma abincin za ayi to mara nauyi za a dafa.
Tana zaune a D'akin-shakatawa sanye cikin bak'ar doguwar riga kirar Saudiya,tayi rolling da mayafin tana nazarin"Dealing with Depression Islamically na Dr.Bilal Philips.Ta gaji lik'is a gangar jiki,amma zuciyar ta, tana k'ara k'arfafarta tad'aure ta k'arasa.Karo na uku kenan tana kallan d'an siririn bak'in agogon dake d'aure a hannunta ta k'osalokacin dawowar Hafsa yayi daga makaranta ta tambayeta wani abu.Tatsiyaya ruwa a k'aramin kofi daga babban tambulan takai bakinta da bismillah kad'an kad'an take kur6a tana jujjuya kofin kamar tana nazarin ruwan har ta shanye,ta ajiye kofin tana fad'in Alhamdulillah...
Ahankali ta d'ora kanta ajikin kujerar tare da lumshe idanunta tana addu'a "Yahaiyu Yaqaiyumu birahmatika astagis,aslihli fi sha'ani kulluh,wala takilni ila nafsika d'arfata ainin" wato "Ya Rayayye dauwamamme,da rahamarka nake niman taimako ka gyara min al'amurana gaba d'aya,ALLAH karka barni da kaina koda da k'iftawar idanu ne".
Miqdad daya shigo yatarar tana wannan addu'ar ya amsa da amin Sumayya. Tabud'e manyan idanunta masu maik'o da suka d'an canja kala saboda baccin da yake shirin kamasu.
Abrugo? (Ka dawo)
Yagyad'a kai dan shima yanajin yaran,Alhaji Hafiz ya koya musu kuma duk sun iya ko Maman Hasan tanaji.
Umburak (Na dawo)
Wannan addu'ar muhimmiyace daya kamata ace kowani musulmi yana yinta kullum ta ALLAH.Yad'auki littafi d'aya daga cikin tarin littafan data barbaza a saman tebur yana dubawa, yaciro biron daya soke a aljihun gaban rigarshi yana gyara mata wata kalma data rubuta ba dai-dai ba,yanuna mata kinga yadda ake rubutata, wancan wata ma'ana ta daban tabayar ba wacce aka tambaya ba.Tagyad'a kai "na gane,nagode Babban Yaya.
Yamik'e zai shige d'akinshi, danshi ba ma'abocin zaman D'akin-shak'atawar bane. Tad'an kalleshi"afwan Yaya Miqdad ga wata tambaya,yakoma yazauna"Uhun ina jinki"Tace yau Malam nasiha yamana da muke rik'e sunanil rawatib kar muyi sakaci dasu,to ni kuma gaskiya ban san meye su d'in ba,to kuma dana tambaye shi shima bai fad'a min wai ya bani jinga (Assignment)in tambayo gobe yana jiran amsa. Yayi murmushi gaskiya Sumayya kina burgeni nan gaba da alama babbar malama za ki zama. Tajijjiga kai"Insha-ALLAH nima sai na ba al'umar manzon ALLAH gudummawa daga d'an abinda Ubangijinmu yanufeni da sani na ilimi,ka san fatana Yaya Miqdad?Yagirgiza kai.Fatana ALLAH yabani miji me ilimi wanda zai dad'a d'orani akan tafarkin dai-dai, wanda zai sa in zama productive akaran kaina,how I wish Julaibib ya aure ni...
Yanunata da yatsa"ke dai da Julaibib d'in nan?Enigma man ko?Tayi yar dariya ai kuwa, yana da wuyar fahimta sai dai ni na fahimce shi, baya so adame shi,baya san hayaniya,baya shiga abinda ba da shi akeyi ba,amma ni har yanzu ina san shi"so gamon jini"yakad'a kai"ga shi kuma so ba samu ba,sai dai fatanmu har kullum ALLAH yaji6anci al'amuran mu.Amin big Bros.Sukayi murmushi.
Mukoma kan tambayarki abinda ake nufi da sunanil rawatib sune sallolin da akeyi na nafila kafin sallar farilla ko bayan sallar farilla kamar :-
Sallah raka'a hudu kafin sallar azahar da kuma rak'a biyu bayanta.
Sallah raka'a biyu bayan la'asar.
Sallah raka'a biyu bayan magriba.
Sallah raka'a biyu kafin sallar asubahi.
Sumayya...a d'an firgice tad'ago sannan ta amsa"Na'am.Lafiya kika zabga wannan tagumin?Takad'a kai kwallah sun cika idanunta tamaida kanta jikin kujeran dan ba ta so su zubo "Maman Hasan Julaibib ne na kasa yin yak'i da zuciyata wajan cireshi a cikinta, kullum sai na yi mafarkin shi sai dai ban kwanta bacci ba me yasa?Saboda abinda kika sa a zuciyarki kenan tunanin shi,duk abinda ka kwallafa rai da shi to a mafi yawan lokaci sai kayi mafarkin shi"sa rai a ci shi ke kawo jin yunwa"
Takamo hannayenta,Sumayya ki fahimci wani abu"D'an Adam da kike ganinshi to shi yake saima kanshi mutunci da daraja,shi zai kame kanshi sannan mutane su d'aukeshi da mutunci su girmama shi"Haja ita takema kanta kud'i.kin damu dashi da yawa,sannan abin takaicin bai san kina yi ba harara a duhu..kilama ya manta ya ta6a ganinki,shi yana can hankalin shi a kwance yana gudanar da al'amuran rayuwar shi,ke kina nan kin takure kanki cikin tunanin shi"wannan fa kamar aikin banza ne sammakon gaida mak'iyi.
...Julaibib yana da matar aure makaranta ake jira tagama musha biki,kuma k'anwata ce...kalaman matar Musaddiq kenan ranar dataje musu murnar aure...
Tasauke numfashi"to amma ai banyi laifi ba ko a addinance.Maman Hasan tajijjiga kai"kwarai kuwa bakiyi laifi ba,hakan ya halatta sai dai a yadda muka saba a al'adance namijine yake furta hakan ga 'ya mace,saboda kawaici irin na Hausa-Fulani,sai dai ban san sauran al'ummatai ba,ba kasafai matan suke yin haka ba.Kiyita addu'a ALLAH alhakimune ba yadda ba ya shirya al'amura. Jikinta yayi sanyi ba wata gaskiya bayan wannan"a hankali tayi furucin nagode Maman Hasan da wannan tunatarwa.
Miqdad yafito daga d'akinshi yana karya hula.Sumayya tabishi da kallo yanayi da d'abi'unshi suna mata shige dana D'ansarai shima ma'abocin sa fararan kayane.Yayi murmushi ganin kallan da take mishi"Sumayya ya akayi ne? Tayi yar dariya"wallahi Bros kayi kyau ba k'arya wannan shigar sunnan ta k'ayar dani fa. To nagode,yau ba Islamiyya ne?Akwai sai zuwa anjima.
Hafsa tafito daga D'akin-girki tana kallanshi "Yaya Miqdad baza ka tsaya kaci abincin bane?Yad'an sosa kunne"fita zanyi.Tad'an marairaice"ALLAH sarki Yaya Miqdad inata sauri ne fa,wallahi na kusa gamawa. Yakalli agogon dake d'aure a hannun shi na dama"Ina bazan tsaya ci ba gaskiya.Ta turo baki gaba gaskiya ni dai banji dad'iba.Sai kawai tajuya tana k'unk'uni. Yarik'o hannunta"baba tawaje nah,kiyi hak'uri kiran gaggawa aka min a wajan aiki,yadafa kafad'arta yad'an d'age gira cikin murmushi"Yaya Miqdad ne fa?Tad'an harareshi tana dad'a turo baki ni dai...yatari numfashin ta"kinga kwantar da hankalin ki"bayan sallar azahar zan aiko a kar6a sai inci acan shikenan ko?Tad'anyi tsallan murna"yauwa Yayanmu to adawo lafiya"tabashi hannu sukayi musafaha suna dariya.ALLAH yasa tawaje nah...suka d'aga hannu suna ma juna adabo.
Julaibib tunda yatafi sau d'aya yazo sai yanzu da suka samu hutun Semester, haka yadinga zaga gidajan yan'uwa yana gaishesu.Suna zaune shi da Musaddiq suna tattauna al'amuran daya shafesu Safiyya tayi sallama tashigo D'akin-shak'atawar sanye da dogon hijab suka gaisa cikin mutunta juna ta tashi tafita,bata sake shigowaba sai da tagama abincin rana tahad'a duk ahinda za su buk'ata a babban tire takai musu.Musaddiq yakar6eta da saurin shi"yauwa Safiyya,ALLAH dai yak'ara miki albarka da lafiya.Shida ita suka kalli juna suna murmushi,ta tsuguna da niyyar zuba musu yace"a ah wallahi amaryata ai kinyi me wuyar jeki kawai tuzuru zaiyi kome.
Julaibib yayi kamar bai gane shagu6en ba,yad'auki kofi yazuba lemun kashu da abarba,yayi hismillah yafara kur6a.Musaddiq yace kai ni bangane bane anyi yamma da kare ni baza ka zuba min bane?Ya ajiye kofin yana nuna kanshi da yatsa"ni kace zanyi kome ko tuzuru? Ni sunana Julaibib ban san wani tuzuru kake nufi ba, ka san dama ni ban saba da sai anyi service d'ina ba, yazuba abincin a faranti yafara ci.Musaddiq yagalla mishi harara"wa za ka raina ma hankali? malam kayi aure kaji dad'in rayuwar ka,dawani tuzuru ne bayan kai?Yayi kamar ba dashi yake magana ba.Musaddiq yad'auki cokali to ajiye abincin muci mana. Yajanye farantin da sauri"a ah yau bazan ci abinci dakai ba,tashi katafi wajan matarka taba ka abincin abaki ma wannan ba damuwata bace.Au haka za kace?Yad'an d'age gira yana mishi wannan rikitaccen kallan nashi"Eh haka nace da magana ne?A ah ba ni da tacewa...wai ankama 6arawo da kayan sa ta.
A sanda hantsi ya dubi ludayi na safiyar alhamis Sudaida da d'an d'okinta na san ganinshi ta tafi gidan Inna,amma irin amsa gaisuwar daya mata yasa jikinta yayi sanyi"wai an jefi kaza da gishiri,baiko d'ago kai ya kalleta daga tarin littafan daya barbaza a saman tebur ba,a dak'ile yake amsa gaisuwar da take mishi da lafiya...Tazuba mishi idanu na wucewar wasu dak'ik'u sannan ta d'ora envelop d'in hannunta a saman tebur d'in gabanshi.Yakalli envelop d'in a gajarce yacigaba da rubutun shi ba tare kuma daya d'ago kanshi ba yake tambayar ta"na meye? Haushinshi yakamata,ta galla mishi harara tajuya"nima ban sani ba.garammm tabugo k'ofar da k'arfi.Sai lokacin yad'ago yakalli k'ofar,yad'an motsa kafad'a yacigaba da abinda yakeyi har aka fara kiraye-kirayen sallar azahar bai gama ba, turesu kawai yayi gefe yayi alwala yatafi masallaci.
Bai samu damar bud'e envelop d'in ba sai daya zo kwanciyar bacci"D'an k'aramin frame ne me hoton ayatul Qursiyu,a kasanshi wani tsibiri ne me ban sha'awa ruwa yana gudu...sai d'an takadda anyi rubutu sad'ara hud'u.
...Julaibib...na san kome zan ba ka a banza zaga ganshi,amma wannan na tabbatar ma kaina koda ba ka so na,na san za ka alkinta shi ko???
I dore you my Enigma...
Kasham Kantiok Donatus.
Yakaranta yasake karantawa,yakai hancinshi yana shinshina frame d'in daya ke k'amshin irin turaran ta.Yayi lallausan murmushi dan yaji dad'i har ranshi yajijjiga kai"Tabbas kin bani abinda zan alkin ta Kasham...na kuma gode. Sai ya d'orashi agefen gado yakwanta yana azkar d'in bacci, yanata kallan frame d'in yana tuna had'uwarsu da Kasham tun ranar farko da kallan farko da sukama juna a haka har bacci yayi awan gaba dashi.
Azaure sukayi kaci6is taja baya da sauri jakar hannunta ta su6uce zata fad'i a k'asa,cikin zafi nama yacafe,yamik'a mata, takar6a tana gaishe shi. Idanunshi akanta"wa yabaki envelop d'in nan?Tamishi wani irin kallo fuska a d'an yamutse"Malama Kasham.Tun yaushe?Baku dad'e da tafiya Zaria ba.Yad'anyi murmushi cikin gyad'a kai"To nagode,Kawu yana ciki?Eh yana ciki.Yajuya zuwa cikin gidan tabishi da kallan mamaki D'ansarai kamar kuli-kuli yake da ba a gane gabanshi wallahi,Jiya fa shine yamata halin-ko-inkula amma yanzu har da wani murmushi taja dogon tsaki "Kai ALLAH yasauwake maka.
Sumayya ta zage dantse tana kwankwad'ar madarar ilimi,gaba d'aya ta canja ta zama wata ta musamman"Unique charisma"fatar jikinta ma ta canja saboda canjin cima,a gidan Alhaji Hafiz za a ci abincin safe me kyau me gina jiki,da ranama haka a mafi yawan lokuta ba sa kasafai suke yin girki da daddare ba,sai dai asha su gwanda,Inibi,tuffa,dabino a kora da madara idan kuma abincin za ayi to mara nauyi za a dafa.
Tana zaune a D'akin-shakatawa sanye cikin bak'ar doguwar riga kirar Saudiya,tayi rolling da mayafin tana nazarin"Dealing with Depression Islamically na Dr.Bilal Philips.Ta gaji lik'is a gangar jiki,amma zuciyar ta, tana k'ara k'arfafarta tad'aure ta k'arasa.Karo na uku kenan tana kallan d'an siririn bak'in agogon dake d'aure a hannunta ta k'osalokacin dawowar Hafsa yayi daga makaranta ta tambayeta wani abu.Tatsiyaya ruwa a k'aramin kofi daga babban tambulan takai bakinta da bismillah kad'an kad'an take kur6a tana jujjuya kofin kamar tana nazarin ruwan har ta shanye,ta ajiye kofin tana fad'in Alhamdulillah...
Ahankali ta d'ora kanta ajikin kujerar tare da lumshe idanunta tana addu'a "Yahaiyu Yaqaiyumu birahmatika astagis,aslihli fi sha'ani kulluh,wala takilni ila nafsika d'arfata ainin" wato "Ya Rayayye dauwamamme,da rahamarka nake niman taimako ka gyara min al'amurana gaba d'aya,ALLAH karka barni da kaina koda da k'iftawar idanu ne".
Miqdad daya shigo yatarar tana wannan addu'ar ya amsa da amin Sumayya. Tabud'e manyan idanunta masu maik'o da suka d'an canja kala saboda baccin da yake shirin kamasu.
Abrugo? (Ka dawo)
Yagyad'a kai dan shima yanajin yaran,Alhaji Hafiz ya koya musu kuma duk sun iya ko Maman Hasan tanaji.
Umburak (Na dawo)
Wannan addu'ar muhimmiyace daya kamata ace kowani musulmi yana yinta kullum ta ALLAH.Yad'auki littafi d'aya daga cikin tarin littafan data barbaza a saman tebur yana dubawa, yaciro biron daya soke a aljihun gaban rigarshi yana gyara mata wata kalma data rubuta ba dai-dai ba,yanuna mata kinga yadda ake rubutata, wancan wata ma'ana ta daban tabayar ba wacce aka tambaya ba.Tagyad'a kai "na gane,nagode Babban Yaya.
Yamik'e zai shige d'akinshi, danshi ba ma'abocin zaman D'akin-shak'atawar bane. Tad'an kalleshi"afwan Yaya Miqdad ga wata tambaya,yakoma yazauna"Uhun ina jinki"Tace yau Malam nasiha yamana da muke rik'e sunanil rawatib kar muyi sakaci dasu,to ni kuma gaskiya ban san meye su d'in ba,to kuma dana tambaye shi shima bai fad'a min wai ya bani jinga (Assignment)in tambayo gobe yana jiran amsa. Yayi murmushi gaskiya Sumayya kina burgeni nan gaba da alama babbar malama za ki zama. Tajijjiga kai"Insha-ALLAH nima sai na ba al'umar manzon ALLAH gudummawa daga d'an abinda Ubangijinmu yanufeni da sani na ilimi,ka san fatana Yaya Miqdad?Yagirgiza kai.Fatana ALLAH yabani miji me ilimi wanda zai dad'a d'orani akan tafarkin dai-dai, wanda zai sa in zama productive akaran kaina,how I wish Julaibib ya aure ni...
Yanunata da yatsa"ke dai da Julaibib d'in nan?Enigma man ko?Tayi yar dariya ai kuwa, yana da wuyar fahimta sai dai ni na fahimce shi, baya so adame shi,baya san hayaniya,baya shiga abinda ba da shi akeyi ba,amma ni har yanzu ina san shi"so gamon jini"yakad'a kai"ga shi kuma so ba samu ba,sai dai fatanmu har kullum ALLAH yaji6anci al'amuran mu.Amin big Bros.Sukayi murmushi.
Mukoma kan tambayarki abinda ake nufi da sunanil rawatib sune sallolin da akeyi na nafila kafin sallar farilla ko bayan sallar farilla kamar :-
Sallah raka'a hudu kafin sallar azahar da kuma rak'a biyu bayanta.
Sallah raka'a biyu bayan la'asar.
Sallah raka'a biyu bayan magriba.
Sallah raka'a biyu kafin sallar asubahi.