Sashe 65
Gwajin Dafi Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sai dai cikin baccin na shi yayi mafarkin daya dinga na shud'ad'd'en shekaru"Kasham dai yau ma yasake gani cikin shigar Fulani kirar kalangunta ya fito rad'am kamar dai wancan lokacin amma idan tayi magana sai yaji muryar Sudaida...ya farka yanata nazarin wannan mafarki"toh me yak'un sane?...baccin da bai kuma komawa ba kenan har aka fara kiraye-kirayen sallar asubahin farko...
Hausa/Fulani Community Development Association(HAFCODA)Taza6i manya daga cikin su, suka tafi fadar sarkin Bajju,ya kuma kar6esu cikin mutuntawa, sun gabatar da abinda yakawo su,nasan zaman lafiya,da hak'uri da juna,shima Agwam Bajju a zahirance dai ya nuna 6acin ranshi"dan sanin asirin ciki sai hanji,ya kuma tabbatar musu su kwantar da hankalinsu lallai zai tsawatar musu ta hanyar yin gargad'i a dukkan majami'u(churches)ga wad'annan samari yan zauna gari banza masu son tada hargitsi,idan kuma basuji ba to lallai zai buga musu sandar shi(a al'adarsu idan har agwam Bajju yace zai buga sandarshi to duk abinda mutum zaiyi to ba zaiyi nasara ba)
Wad'anda ba son zaman lafiyar suke yiba suka had'a taron su.Shugaban nasu yabisu da kallo d'aya bayan d'aya"kunji abinda yake faruwa, dama hausawa masu san zaman lafiya ne tunda duk abinda muke musu basu ta6a mai da martani ba...toh ni dai kawai bana son ganinsu a garin mune,kome sune suke dashi sama damu sannan hakan bai wadatar dasu ba kullum aure mana Ya'ya suke k'arayi,wani abin takaicin ko da wasa baza kaga wata yarsu kace kana sonta zaka aureta ta yadda da kaiba,sai tace bata yadda ba tunda baka yadda da addinin taba,kunaji suna fad'a kakar za6e me zuwa zasu za6i mutum biyu daga cikinsu su tsaya takarar Chairman to kuna gani za su yadda su sake dangalama wani na mu k'uri'arsune?Yaja dogon tsaki"infact I'm sick and tired of seeing all those masu sallah bounch of idiot,we've to do something,something seriously againts them.
Wani daga cikinsu me rangwamen kafircin yace"da munyi hak'uri kawai ai mun riga mun zama d'aya,ga Ya'yanmu a cikinsu idan munyi yak'i mun kashe mazaje to yaya zamuyi da tarin mata da Ya'yansu?Nifa Ya'yana guda uku ne masu sallah.Cikin fushi shugaban nasu ya daka mishi tsawa"enough of this stupidity,so bloody what da Ya'yanka uku ne a cikinsu? Ko akwai 'yata a cikinsu na rantse muku zan iya kasheta, ba sune shegu masu kwad'ayin abin hannun hausawa ba? To da irin suma zan fara kisa,so dubu nawa suna wulak'antasu? Yanuna mishi k'ofa yana mazurai"now get out! Kai baka cikinmu.
Yasake bin sauran da kallo,suma shi suke kallo suna jijjiga kai alamar gamsuwa da matakin daya d'auka,fuskokin nan babu rahama da tausayi kona sisin kwabo,idanuwa jawur saboda shan burkutu da hayakin maro."nayi dai-dai?Suka had'a baki wajen amsawa"kayi dai-dai.Yakyalkyale da wata irin gur6atacciyar dariya da bata da dadin ji saboda giya da hayaki sun gama lalata hunhunshi"that's very good of you... Suka rufe k'ofa suna cigaba da k'usk'us d'insu na yadda zasu canja salon takunsu akan hausawa, d'akin ya kaure da dariyarsu dan sun gamsu d'ari bisa d'ari da matakin da suka d'auka...
Hankulan jama'a ya kwanta an cigaba da harkoki kamar yadda aka saba,sai dai kuma watanni kad'an a hankali abubuwa suka fara rinca6ewa za a koma yar gidan jiya,aka sake komawa cikin zaman d'ar-d'ar,basu da wani kwanciyar hankali, harbin bindigogi daga daji haka yake shigowa cikin gari ba dare ba rana alamar suna koyan harbi amma abun duka ba sanda da yake kuma dama bahaushen me ban haushinne na tanko me kan bashi,hakan bai d'ad'asu da k'asa ba,su dai neman halalinsu kawai. Mtswww ALLAH yakyauta.
Gidan shiru saboda yaran yanzu a gidan Inna suke kwana a duk ranakun k'arshen mako,Julaibib ya d'auko musu abinci,tamik'e zaune dakyar suka faraci da bismillah yana kuma mata bayanin aikin kafa ma'adanar littafai(bookshelves)da aka fara a d'akin nazari da bincike na makarantar (library)Tayi lallausan murmushi"Ubangiji yacigaba da rufa mana asiri duniya da lahira,gaskiya naji dad'i wallahi.Amin Zaujatiii...
Cikin firgici ta farka daga bacci a sulusin daren,wasu irin munanan mafarkai takeyi duk dare,har fargaba duk lokacin da rana tatafi zata fad'i magriba ta kunno kai,saboda da zarar ta kwanta baccin dare zata fara wannan mafarkan masu tashin hankali da sanya damuwa a zuciya.Julaibib yana zaune yana cike wasu bayanai a na'ura me kwakwalwa yaji motsinta,yajuya yana kallanta,tana zaune a tsakiyar gadon ta kama kanta da duka hannayenta cikin maimaita Istirja'i,rigar shimin dake jikinta ta jik'e sharkaf da zufa"Sudaida lafiya?Zafi kikeji haka?
Yamik'e barin kunna miki mukayyib. Takalleshi a rikice"Yaya D'ansarai ba zafi nake jiba,jikinta yakama rawa"kasan abinda nake gani kuwa?Wai...yatari numfashinta ta hanyar sa tafin hannun damarshi ya rufe mata baki sannan yakalleta cikin kulawa"ba wai bana so inji abinda zaki fad'a bane a ah ina miki kwad'ayin samun lada saboda bin umarnin Manzon ALLAH dan yayi hani da bayyana mummunan mafarki,duk abinda kike gani to ki nemi tsarin ALLAH akan abinda kike ganin,kiyi tofi a gefen hagunki sau uku"A'uzu billahi minashshaid'anir rajim "sai ki juya daga gefen da kika kwanta zuwa d'aya gefen.Wannan shine abinda yadace.Ta rungumeshi tana sauke numfashi"nagode da wannan tunatarwan.
Ranar wata Litini aka bud'e makarantar Julaibib a zangon karatu na farko me suna...
"Alfurqan Science Academy.
Musulman Zonkwa sunyi murna da farin ciki da samuwar wannan makaranta,Ya'ya dayawa an ciresu daga wasu makarantu an dawo dasu nan.Julaibib ya so kwarai ya zauna da Iyalinshi dan bata jin dad'i,sai dai hakanshi bata tadda ruwa ba dan da yammacin ranar ya mata sallama yakama hanyar Gidan-Waya washe gari da sassafe zasu tafi Jos asibitin k'ashi na Bima abokin karatunsune yayi hatsari a hanyar shi takomawa garin na su na Jos yakakkarye.
Sai k'arshen mako yazo,gidan Hajiya yafara zuwa kamar yadda yasaba,su Hajiya an dad'a tsufa sai dai Alhamdulillah tsufa me amfani tayi dan bata rikice ba,tana gane kome da kowa,sun dad'e suna hairarsu kamar yadda suka saba.Bilkisu kuma tagaji da jiranshi kamar yadda Sudaida tace mata ta zauna ta jirashi ba sai ta bishi ba ai zo.Tanata k'unk'uni tana turo baki gaba,Sudaida tana shiga D'akin-girki Bilkisu tasa dogon hijab d'inta har yana jan k'asa,wai haka sabuwar malamarsu ta Alfurqan take sawa,shine tace lallai itama haka zata dinga sawa Julaibib kuwa yad'inka musu ita da Walida kala-kala,tayi sand'a tafice da sauri.
Hajiya tana ganinta tace kai wannan yarinya da gaggawa kike hannun hagu a romo"sarauniya me D'ansarai ai ban ce zan rik'e miki uba ba.Julaibib yayi yar dariya ya tuno da Sudaida itace me fad'a mata haka musamman idan tana jin haushin su.Bata kula Hajiya ba tarungumeshi tawani shagwa6e"Baba tun d'azu kazo kayi zamanka anan.Yashafa kanta "Esbeeer Megadona yanzu zamu tafi.
Takalleshi cikin farin ciki"Baba yau Mama ta barni ni na had'a maka lemun karas,kashu da citta"kaji d'and'anon kuwa?Yagirgiza kai.Wallahi sooo luciousss...yadda tayi furucin yabasu dariya. Shima yace"thank you sooo very much my dear Bilkisu. Yarik'o hannunta suka mik'e"Hajiya barinje in sha lemun nan tunda sanyin shi. Bilkisu tad'an zaro idanu tana kallan Hajiya"ALLAH na mantane amma yanzu zan kawo miki naki dama Mama bata san nafito ba.Hajiya tace"tafi can sai yanzu kika tuna dani to bana sha.Tabi Julaibib da sauri da yasa takalmanshi yafara tafiya"ALLAH kuwan sai kin sha idan ba haka ba nima bazan kuma shan dabgenkiba.
Da daddare Julaibib yatafi kai Bilkisu da Walida hutun k'arshen mako gidan Inna,Sudaida tana shan rake taji tauuu...tauuu...tauuu...!k'arar harbin bindiga har tana hango kyallinshi ta tagar da take bud'e,raken hannunta ya su6uce, tarintse idanunta cikin matsanancin tsoro duk da abin ya zame musu jiki to amma na yanzu ya firgitata wallahi, tana Istirja'i yashigo da sallama yazauna yana kallanta"lafiya kuwa?Tad'ago tana kallan shi cikin mad'aukakin mamaki"kai bakaji harbin bindigar da akayi yanzu a jere har sau uku ba?
Yaya D'ansarai anya garin nan za a samu kwanciyar hankali a cikin shi? Yamaida kai da bayanshi jikin kujerar yana murmushi"matsoraciya kawai...Ta tsare shi da idanu. Yad'an kalleta" ke ba kome fa na...Ta girgiza kai"ba kome fa kace?Haka shekaran jiya danaje gida muna magana da Baba shima yace wai ba kome,to ni abinda bangane ba,a ba kome d'in me yakawo wannan harbe-harben ba dare ba rana?Anya ba koyan harbin suke yi ba? Baza kusa yan lek'en asiri su binciko muku me ake ciki ba Yaya Julaibib? Yaciro wata takadda daga aljihun gaban rigarshi da biro yafara lissafe-lissafenshi a ciki"to me kika ga anyi?Koma me sukeyi bata shafe muba...tayi shiru tana kallan shi aranta tanata maimaita Kalmar"kome sukeyi bata shafe muba... Yagama ya bud'e Laptop d'inshi yayi yan rubuce-rubuce a ciki ya rufe sannan ya kalleta"gobe Insha-ALLAH zani Kaduna mun tura kud'in kayayyaki amma har yanzu shiru tun wancan makon muke waya da manager na wajen amma sai wani hanya-hanya yake mana toh zani inga koma meye ganin idanuna.
Takalleshi wani iri ranta ba dad'i"nifa tafiye-tafiyen nan naka ya fara shigar min hanci da k'udundune wallahi,yana hanani rawar gaban hantsi, jiya fa yakamata kazo garin nan baka zo ba,na kauda kai banyi magana ba,yau kazo sai kuma gobe kace Kaduna za ka tafi washe gari da sassafe ka koma Gidan-Waya?A k'arshen makon ma baka hutaba?Ni gaskiya ban yadda ba shi Yaya Musaddiq d'in yatafi mana.Yayi yar dariya"Zaujatiii...uwar gidata anan duniya har a aljannah;ai ko Musaddiq yaci ya huta ko da yaushe shi yake tafiya,rabona da inje Kaduna saro kaya na kusa shekara fa,ko wannan karon bashi yace inje ba nine naga dacewar hakan shima yad'an huta...Kyan rawa da makar6i,amma kisha kurumunki Sudaidan D'ansarai ai na kusa ajiye koyarwar da nakeyi in dawo kan wannan makarantar gaba d'aya, kinga tafi-tafiye ya k'are sai mu manne kamar k'arfe da mayen k'arfe kullum muna tare mutu ka raba takalmin kaza ko?Yad'age gira yana mata wani kallon k'auna.Tayi shiru ta kyaleshi,dan wannan tafiyar da zaiyi ta 6ata mata rai sosai wallahi.
Shi kuma yacigaba da maganar shi duk da bata kulashiba,ai ya san tanaji tunda ba kurma bace,ranar litini d'inma bazan bar garin nan ba har sai munje an sake miki scanning ni wannan girman cikin yana bani mamaki a watanni biyar kacal.Hummm kawai tace tazame ta takwanta dakyar.
Hausa/Fulani Community Development Association(HAFCODA)Taza6i manya daga cikin su, suka tafi fadar sarkin Bajju,ya kuma kar6esu cikin mutuntawa, sun gabatar da abinda yakawo su,nasan zaman lafiya,da hak'uri da juna,shima Agwam Bajju a zahirance dai ya nuna 6acin ranshi"dan sanin asirin ciki sai hanji,ya kuma tabbatar musu su kwantar da hankalinsu lallai zai tsawatar musu ta hanyar yin gargad'i a dukkan majami'u(churches)ga wad'annan samari yan zauna gari banza masu son tada hargitsi,idan kuma basuji ba to lallai zai buga musu sandar shi(a al'adarsu idan har agwam Bajju yace zai buga sandarshi to duk abinda mutum zaiyi to ba zaiyi nasara ba)
Wad'anda ba son zaman lafiyar suke yiba suka had'a taron su.Shugaban nasu yabisu da kallo d'aya bayan d'aya"kunji abinda yake faruwa, dama hausawa masu san zaman lafiya ne tunda duk abinda muke musu basu ta6a mai da martani ba...toh ni dai kawai bana son ganinsu a garin mune,kome sune suke dashi sama damu sannan hakan bai wadatar dasu ba kullum aure mana Ya'ya suke k'arayi,wani abin takaicin ko da wasa baza kaga wata yarsu kace kana sonta zaka aureta ta yadda da kaiba,sai tace bata yadda ba tunda baka yadda da addinin taba,kunaji suna fad'a kakar za6e me zuwa zasu za6i mutum biyu daga cikinsu su tsaya takarar Chairman to kuna gani za su yadda su sake dangalama wani na mu k'uri'arsune?Yaja dogon tsaki"infact I'm sick and tired of seeing all those masu sallah bounch of idiot,we've to do something,something seriously againts them.
Wani daga cikinsu me rangwamen kafircin yace"da munyi hak'uri kawai ai mun riga mun zama d'aya,ga Ya'yanmu a cikinsu idan munyi yak'i mun kashe mazaje to yaya zamuyi da tarin mata da Ya'yansu?Nifa Ya'yana guda uku ne masu sallah.Cikin fushi shugaban nasu ya daka mishi tsawa"enough of this stupidity,so bloody what da Ya'yanka uku ne a cikinsu? Ko akwai 'yata a cikinsu na rantse muku zan iya kasheta, ba sune shegu masu kwad'ayin abin hannun hausawa ba? To da irin suma zan fara kisa,so dubu nawa suna wulak'antasu? Yanuna mishi k'ofa yana mazurai"now get out! Kai baka cikinmu.
Yasake bin sauran da kallo,suma shi suke kallo suna jijjiga kai alamar gamsuwa da matakin daya d'auka,fuskokin nan babu rahama da tausayi kona sisin kwabo,idanuwa jawur saboda shan burkutu da hayakin maro."nayi dai-dai?Suka had'a baki wajen amsawa"kayi dai-dai.Yakyalkyale da wata irin gur6atacciyar dariya da bata da dadin ji saboda giya da hayaki sun gama lalata hunhunshi"that's very good of you... Suka rufe k'ofa suna cigaba da k'usk'us d'insu na yadda zasu canja salon takunsu akan hausawa, d'akin ya kaure da dariyarsu dan sun gamsu d'ari bisa d'ari da matakin da suka d'auka...
Hankulan jama'a ya kwanta an cigaba da harkoki kamar yadda aka saba,sai dai kuma watanni kad'an a hankali abubuwa suka fara rinca6ewa za a koma yar gidan jiya,aka sake komawa cikin zaman d'ar-d'ar,basu da wani kwanciyar hankali, harbin bindigogi daga daji haka yake shigowa cikin gari ba dare ba rana alamar suna koyan harbi amma abun duka ba sanda da yake kuma dama bahaushen me ban haushinne na tanko me kan bashi,hakan bai d'ad'asu da k'asa ba,su dai neman halalinsu kawai. Mtswww ALLAH yakyauta.
Gidan shiru saboda yaran yanzu a gidan Inna suke kwana a duk ranakun k'arshen mako,Julaibib ya d'auko musu abinci,tamik'e zaune dakyar suka faraci da bismillah yana kuma mata bayanin aikin kafa ma'adanar littafai(bookshelves)da aka fara a d'akin nazari da bincike na makarantar (library)Tayi lallausan murmushi"Ubangiji yacigaba da rufa mana asiri duniya da lahira,gaskiya naji dad'i wallahi.Amin Zaujatiii...
Cikin firgici ta farka daga bacci a sulusin daren,wasu irin munanan mafarkai takeyi duk dare,har fargaba duk lokacin da rana tatafi zata fad'i magriba ta kunno kai,saboda da zarar ta kwanta baccin dare zata fara wannan mafarkan masu tashin hankali da sanya damuwa a zuciya.Julaibib yana zaune yana cike wasu bayanai a na'ura me kwakwalwa yaji motsinta,yajuya yana kallanta,tana zaune a tsakiyar gadon ta kama kanta da duka hannayenta cikin maimaita Istirja'i,rigar shimin dake jikinta ta jik'e sharkaf da zufa"Sudaida lafiya?Zafi kikeji haka?
Yamik'e barin kunna miki mukayyib. Takalleshi a rikice"Yaya D'ansarai ba zafi nake jiba,jikinta yakama rawa"kasan abinda nake gani kuwa?Wai...yatari numfashinta ta hanyar sa tafin hannun damarshi ya rufe mata baki sannan yakalleta cikin kulawa"ba wai bana so inji abinda zaki fad'a bane a ah ina miki kwad'ayin samun lada saboda bin umarnin Manzon ALLAH dan yayi hani da bayyana mummunan mafarki,duk abinda kike gani to ki nemi tsarin ALLAH akan abinda kike ganin,kiyi tofi a gefen hagunki sau uku"A'uzu billahi minashshaid'anir rajim "sai ki juya daga gefen da kika kwanta zuwa d'aya gefen.Wannan shine abinda yadace.Ta rungumeshi tana sauke numfashi"nagode da wannan tunatarwan.
Ranar wata Litini aka bud'e makarantar Julaibib a zangon karatu na farko me suna...
"Alfurqan Science Academy.
Musulman Zonkwa sunyi murna da farin ciki da samuwar wannan makaranta,Ya'ya dayawa an ciresu daga wasu makarantu an dawo dasu nan.Julaibib ya so kwarai ya zauna da Iyalinshi dan bata jin dad'i,sai dai hakanshi bata tadda ruwa ba dan da yammacin ranar ya mata sallama yakama hanyar Gidan-Waya washe gari da sassafe zasu tafi Jos asibitin k'ashi na Bima abokin karatunsune yayi hatsari a hanyar shi takomawa garin na su na Jos yakakkarye.
Sai k'arshen mako yazo,gidan Hajiya yafara zuwa kamar yadda yasaba,su Hajiya an dad'a tsufa sai dai Alhamdulillah tsufa me amfani tayi dan bata rikice ba,tana gane kome da kowa,sun dad'e suna hairarsu kamar yadda suka saba.Bilkisu kuma tagaji da jiranshi kamar yadda Sudaida tace mata ta zauna ta jirashi ba sai ta bishi ba ai zo.Tanata k'unk'uni tana turo baki gaba,Sudaida tana shiga D'akin-girki Bilkisu tasa dogon hijab d'inta har yana jan k'asa,wai haka sabuwar malamarsu ta Alfurqan take sawa,shine tace lallai itama haka zata dinga sawa Julaibib kuwa yad'inka musu ita da Walida kala-kala,tayi sand'a tafice da sauri.
Hajiya tana ganinta tace kai wannan yarinya da gaggawa kike hannun hagu a romo"sarauniya me D'ansarai ai ban ce zan rik'e miki uba ba.Julaibib yayi yar dariya ya tuno da Sudaida itace me fad'a mata haka musamman idan tana jin haushin su.Bata kula Hajiya ba tarungumeshi tawani shagwa6e"Baba tun d'azu kazo kayi zamanka anan.Yashafa kanta "Esbeeer Megadona yanzu zamu tafi.
Takalleshi cikin farin ciki"Baba yau Mama ta barni ni na had'a maka lemun karas,kashu da citta"kaji d'and'anon kuwa?Yagirgiza kai.Wallahi sooo luciousss...yadda tayi furucin yabasu dariya. Shima yace"thank you sooo very much my dear Bilkisu. Yarik'o hannunta suka mik'e"Hajiya barinje in sha lemun nan tunda sanyin shi. Bilkisu tad'an zaro idanu tana kallan Hajiya"ALLAH na mantane amma yanzu zan kawo miki naki dama Mama bata san nafito ba.Hajiya tace"tafi can sai yanzu kika tuna dani to bana sha.Tabi Julaibib da sauri da yasa takalmanshi yafara tafiya"ALLAH kuwan sai kin sha idan ba haka ba nima bazan kuma shan dabgenkiba.
Da daddare Julaibib yatafi kai Bilkisu da Walida hutun k'arshen mako gidan Inna,Sudaida tana shan rake taji tauuu...tauuu...tauuu...!k'arar harbin bindiga har tana hango kyallinshi ta tagar da take bud'e,raken hannunta ya su6uce, tarintse idanunta cikin matsanancin tsoro duk da abin ya zame musu jiki to amma na yanzu ya firgitata wallahi, tana Istirja'i yashigo da sallama yazauna yana kallanta"lafiya kuwa?Tad'ago tana kallan shi cikin mad'aukakin mamaki"kai bakaji harbin bindigar da akayi yanzu a jere har sau uku ba?
Yaya D'ansarai anya garin nan za a samu kwanciyar hankali a cikin shi? Yamaida kai da bayanshi jikin kujerar yana murmushi"matsoraciya kawai...Ta tsare shi da idanu. Yad'an kalleta" ke ba kome fa na...Ta girgiza kai"ba kome fa kace?Haka shekaran jiya danaje gida muna magana da Baba shima yace wai ba kome,to ni abinda bangane ba,a ba kome d'in me yakawo wannan harbe-harben ba dare ba rana?Anya ba koyan harbin suke yi ba? Baza kusa yan lek'en asiri su binciko muku me ake ciki ba Yaya Julaibib? Yaciro wata takadda daga aljihun gaban rigarshi da biro yafara lissafe-lissafenshi a ciki"to me kika ga anyi?Koma me sukeyi bata shafe muba...tayi shiru tana kallan shi aranta tanata maimaita Kalmar"kome sukeyi bata shafe muba... Yagama ya bud'e Laptop d'inshi yayi yan rubuce-rubuce a ciki ya rufe sannan ya kalleta"gobe Insha-ALLAH zani Kaduna mun tura kud'in kayayyaki amma har yanzu shiru tun wancan makon muke waya da manager na wajen amma sai wani hanya-hanya yake mana toh zani inga koma meye ganin idanuna.
Takalleshi wani iri ranta ba dad'i"nifa tafiye-tafiyen nan naka ya fara shigar min hanci da k'udundune wallahi,yana hanani rawar gaban hantsi, jiya fa yakamata kazo garin nan baka zo ba,na kauda kai banyi magana ba,yau kazo sai kuma gobe kace Kaduna za ka tafi washe gari da sassafe ka koma Gidan-Waya?A k'arshen makon ma baka hutaba?Ni gaskiya ban yadda ba shi Yaya Musaddiq d'in yatafi mana.Yayi yar dariya"Zaujatiii...uwar gidata anan duniya har a aljannah;ai ko Musaddiq yaci ya huta ko da yaushe shi yake tafiya,rabona da inje Kaduna saro kaya na kusa shekara fa,ko wannan karon bashi yace inje ba nine naga dacewar hakan shima yad'an huta...Kyan rawa da makar6i,amma kisha kurumunki Sudaidan D'ansarai ai na kusa ajiye koyarwar da nakeyi in dawo kan wannan makarantar gaba d'aya, kinga tafi-tafiye ya k'are sai mu manne kamar k'arfe da mayen k'arfe kullum muna tare mutu ka raba takalmin kaza ko?Yad'age gira yana mata wani kallon k'auna.Tayi shiru ta kyaleshi,dan wannan tafiyar da zaiyi ta 6ata mata rai sosai wallahi.
Shi kuma yacigaba da maganar shi duk da bata kulashiba,ai ya san tanaji tunda ba kurma bace,ranar litini d'inma bazan bar garin nan ba har sai munje an sake miki scanning ni wannan girman cikin yana bani mamaki a watanni biyar kacal.Hummm kawai tace tazame ta takwanta dakyar.