Sashe 9
Damuwata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
K'aunata da Mamana na daban ne wanda zance banga wata d'iya da Mahaifiyarta ke jiyo DAMUWATA ko farin cikinta ba kamar yarda Mamana ke jiyo nawa. Lokuta da dama na kan zauna ina nazarin faruwar hakan amma a k'arshe sai na d'inauce na rasa gano dalilin. Hak'ik'a nima ina son Mamana domin ita ta koyar dani k'aunarta tun bansan kaina ba tamkar yarda ta zamo ita ce malamata na farko a fannin ilimin addini."
"Masha Allah da samun managarciyar uwa kamar Mama."
Beebah ta ambata cikin murmushi.
"Godiya nake sister."
"Mention not dear cigaba ina saurarenki."
Gyaran murya nayi na d'ora "K'awancenmu da Fanta hak'ik'a ina alfahari da shi domin a lokacin na gano samun abokin hira sa'anka na sanya natsuwa sama da komi.
A haka na cigaba da rayuwa cikin godiyan Allah domin a yanzu bana tare da Damuwar rashin abokin tattauna lamurana tunda na samu Fanta dik da ba komi na ke iya sanar da ita ba makar yarda bana iya sanar da Mamana dik kan DAMUWATA har kwanar gobe lamarin da ta ke kan yimin fad'a da in daina domin bai da kyau sam.
A yanzu haka na kammala Jami'a inda na samu Degree d'ina akan harshen turanci haka na yi bautar k'asa na kammala cikin nasara sannan na yi saukan Al'qur,ani mai girma tare da haddarsa da kuma wasu littafai na addini wanda Mamana ta jagoranci karantar da ni tun ina k'arama daga bisani na k'ara gogewa a gaban malamai. Mamana nada ilimin addini sosai da na boko daidai misali, shi yasa muke rayuwa cike da wayewa. Baba kuwa na addini gareshi domin shi malamin zaure ne wanda bai barin d'iyoyinsa yin karatun boko mai zurfi dan Mata daga Primary suke tsayawa Maza kuwa daga secondary domin suna kallamawa suke kama sa'anar hannu dan ba wanda yanemi gadar Baba a fannin malumta sai babban yayanmu Auwalu. Ni ce kad'ai na samu yin karatun Boko mai zurfi har zuwa matakin Jami'a, wanda bansan dalilin faruwar hakan akaina ba sai dai wani lokacin ina danganta rashin jituwana da Babana na da nasaba da zurfin karatuna tunda kaf d'iyoyinsa ba mai ilimina maza da matan, ba alfahari ba har zuwa na addini ba wanda ya kaini domin ni ce kad'ai na haddace Al'qur,ani cikinsu amma Mazan unyi sauka a gabansa Matan kam ko saukan basa samun damar yi ya keyi musu aure.
"Ikon Allah amma kin more kam Allah yayiwa iliminki albarka."
"Amin tare da naki."
Na amsawa Beebha cikin murmushi.
"Amma sai dai ban gane Rashin jituwar dake tsakaninki da Mahaifinki ba?"
Shiru na yi ina lalibo amsan da zan bata domin ciki ba anyisa dan cin abinci bane kad'ai har da ma'adanar ajiye sirruka.
"Ok just ignore it."
Na yi Beebah ta ambata a hankali.
Ajiyar zuciya na sauke cikin jan hamdala a ruhina dan ko Fanta da ta ke ganin komi a idanun ta ban tab'a yin maganar da ita ba haka itama bata tab'a tambayar dalilin faruwan hakan ba.
"Uhm Nana Khadijatu fad'in Uncle Muhseen."
Na kuma tsinakayar muryanta daf da kunnina murmusawa na yi tare da cigaba da cewa "Na yi training a catering school inda na samu kwarewa a fannin girkin zamani da had'a snacks dan na gargajiya wannan Mamana itace malamata tun inayi bai nuna har na zamo gwana."
"Masha Allah, a fannin aiki fa?"
"Nasoma karantarwa a wani Privet Shool amma yanzu na bari, sakamakon 'yar tsaman da mukeyi da yaron mai makarantar yasa na ajiye masu aikinsu. Haka nan mutumin ya d'uaki karan tsana ya d'oramin domin ko magana bai had'amu amma a kullum zak'ulo laifina ya keyi yana tozartani a bainar jama'a, gani da saurin kuka, da girmana na yi ta zubda hawaye d'alibai nayimin dariya akan haka Mama ta maramin baya na bar musu aikinsu. Kuma tunda na bar makarantar ba wanda ya waiwayeni da ban hak'uri akan haka naji banson sake yin wani aiki ko wani iri ne duk da ina da takardu masu kyau, idan nace zan nema bazan rasa ba.
Yanzu dai ina koyar da karatun Hadda a makarantar Tahfiz da na yi bisa tursa-sawan Mama wai wannan ta addini ne zan sami lada tunda Malaman suka biyoni gida to in je. Ba dan nasoba na soma zuwa, shi bana fuskanta matsala illa ta kallon nan da maza keyimin tamkar mai d'auke da lalura sannan muna hira da malamai jefi jefi, abu d'aya ke damuna a makarantar yawan hayaniyar yara domin abinda na tsana na farko kenan hayaniya dan na sakamin ciwon kai mai zafi, haka zalika kallon banza da mata keyimin duk in na shiga taro ko had'uwa da su a wani sabgar bai sanja ba, ako da yaushe DAMUWATA shi ne sanin dalilin faruwan lamuran biyu da suka kewayeni wato kallon da Maza keyimin na k'urulla da kallon da Mata keyimin na wulak'anta, shi yasa sadda ku ka shigo gidanmu na hango kulawanku gareni nashiga nishad'i ainun sannan gashi yanzu kin kuma tabbatarmin da hakan ta hanyar nunan k'auna tamkar yarda Fanta ta nunamin a baya."
"Ikon Allah hak'ik'a rayuwarki Deejah da a baben mamaki cikinsa sannan ina hasko lauje cikin nad'i amma ko meye shi ina rok'on Allah yasa khairan ne domin ba kyau danganta lamari da wani abu daban wanda ba khairan ba ne sabida wani abin daga Allah ne."
"Ina godiya da addu'a tare da nasiha akan yarda da k'addara mai kyau ko kishiyarta."
"Bakomi sister, Allah ya shige mana gaba."
"Amin."
Munyi shiru na wasu mintoci sannan Beebah ta kuma cewa "Deejah kin gama bani labarinki a tak'aice amma har kika kammala banji kin ambaci Saurayinki ba."
Idanu waje nake kallonta ta kyalkyale da dariya na yi hanzarin kulle mata baki ina kallon agogo cikin cewa "Sister dare fa ya yi."
Motsa kai ta yi cikin murmusawa ta ce "Ina saurarenki."
"Wai Beebah ke yar jarida ce ko marubuciya?"
"Babu ko d'aya."
"To in haka ne dan Allah ki rabu dani da wannan tanbayoyin naki, kuma wannan uban surutun da kika sakani na yi shi ne kike kira da tak'aitaccen tarihi."
"Eh mana domi in nasoma baki nawa sai mun kwana munyini ban gama ba."
Sa ke ware idanu na yi ta kawo yatsarta kamar zata sakamin a cikin ido na kulle da sauri, mukasaki murmushi a tare.
"To bani naki ina saurarenki."
"Wasa na keyi miki ni bani da labarin komi sabida komi na ke muradi na sameshi abokai maza da mata, 'yan uwa na gari tare da iyaye masu k'aunar farin cikinmu. A ittifak'i Aunty Nafisa ce kawai ta fita zakka a zuri'armu dan ita ta taso da fad'a tare da kyashi, hakan nan ita mai...
D'aga mata hannu na yi da sauri ta dakata tana kallona, juya kai gefe na yi "Dan girman Allah kada ki sake yimin maganar Aunty Nafisa saboda a duniya itace ta biyu da naji banson ko jin muryanta balle sunarta."
"Waye na farkon?"
"Sirri na ne dear Beebah."
Na ambata cikin dafa kafad'arta.
"Ok nadaina sonji kuwa."
"Godiya na ke da hakan."
"Uhm da wayau dai kin kori zancen Saurayinki ko Deejah?"
"Bani da shi kuma ban tab'a yinsa ba."
"Ban yarda ba kawai kina b'oyemin ne domin Fanta ta sanarmin bakya da sabo haka kina da zurfin ciki wanda har Mama kina yiwa."
"Eh na amince duk abin da kika ambata halina ne amma ki sani ke banyi miki ko d'aya ba, in baki yarda ba gobe ki tambayi Fanta idan na tab'a sanar da ita wad'an nan labaran duk dad'ewarmu da ita."
"No basai na tambayeta ba, na yarda kin bani matsayi na daban a rayuwarki kamar yarda nima na baki dan hak'ik'a ina k'aunarki Deejah k'auna irin ta tsakani da Allah."
Rungumeta na yi da sauri ina jan siririyar dariya, itama dariyar ta keyi.
Mun raba dare da Beebah muna shan hira, barcin dake damuna tuni ya tafi kam dole.
Bayan ta idar da Sallar subahi domin ni ina fashin sallah, na dubeta cikin hasken da baiwadaci d'akin ba na ce "Sister sanar dani abinda kika hasko jiya wanda ya saka Aunty Nafisa ta k'onani."
Tasowa tayi daga saman sallayar ta dawo kan katifa ta rik'o hannuna ta ce "Na hasko Uncle Muhseen na sonki shi ne dali...
"So! Kuma? Wacce irin so?"
Na katseta da sauri idanu waje.
"It's may be na au...
"Dan girman Allah Beebah mubar maganar, rik'e abinda kika hasko a ranki na fasa jinsa."
Ina ambatar haka na zame na kwanta tare da juya mata baya, k'irjina kuwa sai harbawa ya keyi.
"Tabd'i jan kishi da Aunty Nafisa, ai abinda ma ba zai yiwu ba ne, ya Allah ka tsareni ji da ganinsa."
"Ba amin ba."
Jin maganar Beebah yasa na gano zancen da na keyi a zucci ya fito fili kenan. Shiru na yi tamkar mai barci alhalin idanuna biyu. Saukan hannun Beebah a bayana yasa na sauke numfashi ta rik'e arm d'ina ta soma magana cike da natsuwa yarda ko banso dole su shiga kunnuwana.
"Khadija wallahi Allah na hango k'aunarki a idanun Uncle Muhseen, kuma na yi murna sosai domin na sha jin Momy na addu'a akan Allah ya shirya mata Nafisa tare da bawa mijinta mafita akan bak'in cikin da yake kwasa akanta, nima danaji haka sai na soma tayata addu'a saboda na tsani mugun hakinta na rashin jituwa da dangin mijinta. Wannan dalilin ya sanya tun jiya dana hango kin fito daga motarsa tare da yarda fuskan Aunty Nafisa ya koma na amincewa ruhina kece mafitarsa kuma addu'ar mu ta karb'u."
Na juyo zanyi magana ta d'agamin hannu tare da cigaba da cewa "Ina mai baki shawara da ki amince da zarar ya ambata miki asirin ruhinsa, sannan idan har Allah ya nufa kika zamo matarsa wallahi kinyi miji na kere sa'a son dukkan d'iya mace ta sameshi a matsayin bokin rayuwar duniya har da lahira saboda yarin nagartansa a fili suke, na tabbata kema kin sansu."
Lumshe ido na yi ina jin tsigan jikina na tashi, abin mamaki sai naji tamkar in bud'e ido na yi arba da Uncle a zaune gabana kamar yarda Beebah ta ke yanzu.
"Masha Allah da samun managarciyar uwa kamar Mama."
Beebah ta ambata cikin murmushi.
"Godiya nake sister."
"Mention not dear cigaba ina saurarenki."
Gyaran murya nayi na d'ora "K'awancenmu da Fanta hak'ik'a ina alfahari da shi domin a lokacin na gano samun abokin hira sa'anka na sanya natsuwa sama da komi.
A haka na cigaba da rayuwa cikin godiyan Allah domin a yanzu bana tare da Damuwar rashin abokin tattauna lamurana tunda na samu Fanta dik da ba komi na ke iya sanar da ita ba makar yarda bana iya sanar da Mamana dik kan DAMUWATA har kwanar gobe lamarin da ta ke kan yimin fad'a da in daina domin bai da kyau sam.
A yanzu haka na kammala Jami'a inda na samu Degree d'ina akan harshen turanci haka na yi bautar k'asa na kammala cikin nasara sannan na yi saukan Al'qur,ani mai girma tare da haddarsa da kuma wasu littafai na addini wanda Mamana ta jagoranci karantar da ni tun ina k'arama daga bisani na k'ara gogewa a gaban malamai. Mamana nada ilimin addini sosai da na boko daidai misali, shi yasa muke rayuwa cike da wayewa. Baba kuwa na addini gareshi domin shi malamin zaure ne wanda bai barin d'iyoyinsa yin karatun boko mai zurfi dan Mata daga Primary suke tsayawa Maza kuwa daga secondary domin suna kallamawa suke kama sa'anar hannu dan ba wanda yanemi gadar Baba a fannin malumta sai babban yayanmu Auwalu. Ni ce kad'ai na samu yin karatun Boko mai zurfi har zuwa matakin Jami'a, wanda bansan dalilin faruwar hakan akaina ba sai dai wani lokacin ina danganta rashin jituwana da Babana na da nasaba da zurfin karatuna tunda kaf d'iyoyinsa ba mai ilimina maza da matan, ba alfahari ba har zuwa na addini ba wanda ya kaini domin ni ce kad'ai na haddace Al'qur,ani cikinsu amma Mazan unyi sauka a gabansa Matan kam ko saukan basa samun damar yi ya keyi musu aure.
"Ikon Allah amma kin more kam Allah yayiwa iliminki albarka."
"Amin tare da naki."
Na amsawa Beebha cikin murmushi.
"Amma sai dai ban gane Rashin jituwar dake tsakaninki da Mahaifinki ba?"
Shiru na yi ina lalibo amsan da zan bata domin ciki ba anyisa dan cin abinci bane kad'ai har da ma'adanar ajiye sirruka.
"Ok just ignore it."
Na yi Beebah ta ambata a hankali.
Ajiyar zuciya na sauke cikin jan hamdala a ruhina dan ko Fanta da ta ke ganin komi a idanun ta ban tab'a yin maganar da ita ba haka itama bata tab'a tambayar dalilin faruwan hakan ba.
"Uhm Nana Khadijatu fad'in Uncle Muhseen."
Na kuma tsinakayar muryanta daf da kunnina murmusawa na yi tare da cigaba da cewa "Na yi training a catering school inda na samu kwarewa a fannin girkin zamani da had'a snacks dan na gargajiya wannan Mamana itace malamata tun inayi bai nuna har na zamo gwana."
"Masha Allah, a fannin aiki fa?"
"Nasoma karantarwa a wani Privet Shool amma yanzu na bari, sakamakon 'yar tsaman da mukeyi da yaron mai makarantar yasa na ajiye masu aikinsu. Haka nan mutumin ya d'uaki karan tsana ya d'oramin domin ko magana bai had'amu amma a kullum zak'ulo laifina ya keyi yana tozartani a bainar jama'a, gani da saurin kuka, da girmana na yi ta zubda hawaye d'alibai nayimin dariya akan haka Mama ta maramin baya na bar musu aikinsu. Kuma tunda na bar makarantar ba wanda ya waiwayeni da ban hak'uri akan haka naji banson sake yin wani aiki ko wani iri ne duk da ina da takardu masu kyau, idan nace zan nema bazan rasa ba.
Yanzu dai ina koyar da karatun Hadda a makarantar Tahfiz da na yi bisa tursa-sawan Mama wai wannan ta addini ne zan sami lada tunda Malaman suka biyoni gida to in je. Ba dan nasoba na soma zuwa, shi bana fuskanta matsala illa ta kallon nan da maza keyimin tamkar mai d'auke da lalura sannan muna hira da malamai jefi jefi, abu d'aya ke damuna a makarantar yawan hayaniyar yara domin abinda na tsana na farko kenan hayaniya dan na sakamin ciwon kai mai zafi, haka zalika kallon banza da mata keyimin duk in na shiga taro ko had'uwa da su a wani sabgar bai sanja ba, ako da yaushe DAMUWATA shi ne sanin dalilin faruwan lamuran biyu da suka kewayeni wato kallon da Maza keyimin na k'urulla da kallon da Mata keyimin na wulak'anta, shi yasa sadda ku ka shigo gidanmu na hango kulawanku gareni nashiga nishad'i ainun sannan gashi yanzu kin kuma tabbatarmin da hakan ta hanyar nunan k'auna tamkar yarda Fanta ta nunamin a baya."
"Ikon Allah hak'ik'a rayuwarki Deejah da a baben mamaki cikinsa sannan ina hasko lauje cikin nad'i amma ko meye shi ina rok'on Allah yasa khairan ne domin ba kyau danganta lamari da wani abu daban wanda ba khairan ba ne sabida wani abin daga Allah ne."
"Ina godiya da addu'a tare da nasiha akan yarda da k'addara mai kyau ko kishiyarta."
"Bakomi sister, Allah ya shige mana gaba."
"Amin."
Munyi shiru na wasu mintoci sannan Beebah ta kuma cewa "Deejah kin gama bani labarinki a tak'aice amma har kika kammala banji kin ambaci Saurayinki ba."
Idanu waje nake kallonta ta kyalkyale da dariya na yi hanzarin kulle mata baki ina kallon agogo cikin cewa "Sister dare fa ya yi."
Motsa kai ta yi cikin murmusawa ta ce "Ina saurarenki."
"Wai Beebah ke yar jarida ce ko marubuciya?"
"Babu ko d'aya."
"To in haka ne dan Allah ki rabu dani da wannan tanbayoyin naki, kuma wannan uban surutun da kika sakani na yi shi ne kike kira da tak'aitaccen tarihi."
"Eh mana domi in nasoma baki nawa sai mun kwana munyini ban gama ba."
Sa ke ware idanu na yi ta kawo yatsarta kamar zata sakamin a cikin ido na kulle da sauri, mukasaki murmushi a tare.
"To bani naki ina saurarenki."
"Wasa na keyi miki ni bani da labarin komi sabida komi na ke muradi na sameshi abokai maza da mata, 'yan uwa na gari tare da iyaye masu k'aunar farin cikinmu. A ittifak'i Aunty Nafisa ce kawai ta fita zakka a zuri'armu dan ita ta taso da fad'a tare da kyashi, hakan nan ita mai...
D'aga mata hannu na yi da sauri ta dakata tana kallona, juya kai gefe na yi "Dan girman Allah kada ki sake yimin maganar Aunty Nafisa saboda a duniya itace ta biyu da naji banson ko jin muryanta balle sunarta."
"Waye na farkon?"
"Sirri na ne dear Beebah."
Na ambata cikin dafa kafad'arta.
"Ok nadaina sonji kuwa."
"Godiya na ke da hakan."
"Uhm da wayau dai kin kori zancen Saurayinki ko Deejah?"
"Bani da shi kuma ban tab'a yinsa ba."
"Ban yarda ba kawai kina b'oyemin ne domin Fanta ta sanarmin bakya da sabo haka kina da zurfin ciki wanda har Mama kina yiwa."
"Eh na amince duk abin da kika ambata halina ne amma ki sani ke banyi miki ko d'aya ba, in baki yarda ba gobe ki tambayi Fanta idan na tab'a sanar da ita wad'an nan labaran duk dad'ewarmu da ita."
"No basai na tambayeta ba, na yarda kin bani matsayi na daban a rayuwarki kamar yarda nima na baki dan hak'ik'a ina k'aunarki Deejah k'auna irin ta tsakani da Allah."
Rungumeta na yi da sauri ina jan siririyar dariya, itama dariyar ta keyi.
Mun raba dare da Beebah muna shan hira, barcin dake damuna tuni ya tafi kam dole.
Bayan ta idar da Sallar subahi domin ni ina fashin sallah, na dubeta cikin hasken da baiwadaci d'akin ba na ce "Sister sanar dani abinda kika hasko jiya wanda ya saka Aunty Nafisa ta k'onani."
Tasowa tayi daga saman sallayar ta dawo kan katifa ta rik'o hannuna ta ce "Na hasko Uncle Muhseen na sonki shi ne dali...
"So! Kuma? Wacce irin so?"
Na katseta da sauri idanu waje.
"It's may be na au...
"Dan girman Allah Beebah mubar maganar, rik'e abinda kika hasko a ranki na fasa jinsa."
Ina ambatar haka na zame na kwanta tare da juya mata baya, k'irjina kuwa sai harbawa ya keyi.
"Tabd'i jan kishi da Aunty Nafisa, ai abinda ma ba zai yiwu ba ne, ya Allah ka tsareni ji da ganinsa."
"Ba amin ba."
Jin maganar Beebah yasa na gano zancen da na keyi a zucci ya fito fili kenan. Shiru na yi tamkar mai barci alhalin idanuna biyu. Saukan hannun Beebah a bayana yasa na sauke numfashi ta rik'e arm d'ina ta soma magana cike da natsuwa yarda ko banso dole su shiga kunnuwana.
"Khadija wallahi Allah na hango k'aunarki a idanun Uncle Muhseen, kuma na yi murna sosai domin na sha jin Momy na addu'a akan Allah ya shirya mata Nafisa tare da bawa mijinta mafita akan bak'in cikin da yake kwasa akanta, nima danaji haka sai na soma tayata addu'a saboda na tsani mugun hakinta na rashin jituwa da dangin mijinta. Wannan dalilin ya sanya tun jiya dana hango kin fito daga motarsa tare da yarda fuskan Aunty Nafisa ya koma na amincewa ruhina kece mafitarsa kuma addu'ar mu ta karb'u."
Na juyo zanyi magana ta d'agamin hannu tare da cigaba da cewa "Ina mai baki shawara da ki amince da zarar ya ambata miki asirin ruhinsa, sannan idan har Allah ya nufa kika zamo matarsa wallahi kinyi miji na kere sa'a son dukkan d'iya mace ta sameshi a matsayin bokin rayuwar duniya har da lahira saboda yarin nagartansa a fili suke, na tabbata kema kin sansu."
Lumshe ido na yi ina jin tsigan jikina na tashi, abin mamaki sai naji tamkar in bud'e ido na yi arba da Uncle a zaune gabana kamar yarda Beebah ta ke yanzu.