Sashe 14
Damuwata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bayan mun sallaci isha'i muka fito baranda muka zauna, abinci Mama ta umurta da mu soma ci bayan mun gama sai muyi zancen. Kamar ko da yaushe ban wani ci abin kirki ba sai kunun Aya dana cika cikina da shi. Bayan na wanke kayan da muka b'ata na dawo na zauna na tsirawa Mama ido murmushi ta sakarmin tare da tashi ta nufi zaure ba jimawa ta dawo.
"Na kulle gidan ne sabida na fahimci yanzu Malam ya koma yimana lab'e."
Kauda kai gefe na yi batare da na ce komi ba.
"Uwata kinajin haushina akan lamarinmu da Malam ko?"
"A'a Mama kawai dai raina baya son tanki in tanka da kukeyi ne akaina."
"Uwata bana iya jure ganin Malam na tab'amin ke ce."
"Shi d'in mahaifina ne Mama ki barshi ya rik'a hukuntani kamar yarda yakeyiwa d'iyoyinsa idan sunyi masa ba dai-dai ba."
"Ke kina da bambanci da su domin bakya k'yetare umurninsa kamar yarda sauran sukeyi masa, sam ba kyayi masa laifin da zai hukuntaki dan haka bazan bari ya zakunceki ba."
"Zalinci kuma Mama?"
"Eh."
"Shifa Uba yake gareni, abin ikonsa ce ni."
"Nasan da haka amma ki sani akwai hakkin d'iyoyi akan mahaifansu dan haka yi miki hukunci batare da kin aikata laifin komi ba wannan zalinci ne kuma ba zan tab'a lamunta ba."
"Nidai Mama ki koyi hak'uri akan duk wanda ya tab'ani domin wata rana sai labari, ko ance su tab'ani bazasu iya ba."
"Allah ya kaimu wannan lokacin Uwata k'asa bai rufe idanuna ba."
"Amin Mama."
"Uwata natsu da kyau ki saurari maganar da zan sanar miki."
"To Mama ina saurarenki."
"D'azun dana fita gidan Baba Umaru naje, mun gama magana akan aurena da Malam, zan bashi sadakinsa shi kuma zai bani takardata tare da dukiyata."
"Innalillahi wa Inna ilaihin, Mama dan girman Allah ki bar maganar rabuwa da Baba domin yin hakan tamkar kin maidani marainiya ce dan na tabbata Baba ba zai barni na zauna tare da ke ba, zai gwadamiki karfin ikon da mazaje ke gwadawa matayensu da zarar sun rabu da su."
"Ki rubuta zamanmu dake aure ne kawai zai rabumu amma ba k'arfin ikon Malam ba saboda ke d'iyata ce da na ke da iko ita ko ta wani fuska."
"Mama nidai ki janye maganar rabuwan nan dan girman Allah."
"Uwata in kinga na janye sai Malam ya bani dukiyata dama Baba Umaru ya ce idan ya dank'amin hakkina in janye maganar saki idan kuma shi ya bani takardana kamar yarda yake shiri to shi kenan ba kare bin damo."
"K'alu innalillahi wa Inna ilaihin yanzu aina Baba zai samo miki kudinki alhalin kinfi kowa sanin baya da hanyarsu."
"Yana da shi Uwata, mugunta ce irin tashi ya ke son dannemin gadon da mahaifina ya barmin wanda yasha wuya wurin tarasu."
"Mama nikam ina rok'on da ki yafe masa dan girman Allah da Manzon sa."
"Uwata Malam ne ya rok'eki da ki nema masa affuwana kika amince shi ne ya ke saka miki albarka tare da yi miki alk'awarin daina hantararki."
Shiru na yi domin idan na amsa da eh, na karya alk'awarin da nayiwa Baba akan bazan bari sunarsa ya fito ba in kuma na ce a'a nayi k'arya, shirun danayi shi ne mafita."
"Uhm Uwata kenan har yanzu baki gama sanin duniya ba to bazan bar masa ba wallahi tallahi kinji na rantse to ko baya sallah sai ya biyani hak'k'ina."
Tsirawa Mama ido na yi cike da ruwan hawaye.
"Uwata kada ki sakawa kanki damuwa, zamu warware da Malam saboda yana da gidan gona wanda ya bunk'asashi da dukiyana. Kuma kema kin san sagonsa na saida kayan hatsi, yana kuma da filaye kinga kenan yana da hanyar biyana dukiyata kuma ba da jimawa ba zakiga hakan domin Baba Umaru tsohon alk'ali ne zai amsarmin kayana kamar yarda ya amsa a hannuna ya mik'a masa bisa shaidun lauya da wasu dattawa."
"Nidai Allah yasa kada kuyi rikici a binda ke tadamin da hankali kenan."
"Bazamuyi ba Uwata dan haka ki kwantar da hankalinki idan ya tambayeki yarda mukayi kice masa kin sanarmin ban amsa miki ba."
"To Mama."
"Gobe da safe zamu shiga muyiwa Alhaji Muhseen godiya."
"Tare da ke Mama?"
"Eh domin nafiki jin dad'in kyautar nan."
"Uhm Mama kenan, Allah ni kad'ai zanje in yaso idan kun had'u kyayi masa."
"Nima na ambata ne dan naji na bakinki Uwata."
Murmushi na yi ganin Mama na son maidani yarinya k'arama.
"Uwata wallahi ina farin ciki da tarayyanku da Alhaji Muhseen sama da yaron nan Aliyu da kika sanarmin."
"Mama shifa Uncle bai furta yana sona ba kawai hasa-shenki ne abinda bana fatar ya tabbata."
"To shikenan Uwata Allah ya zab'a miki mafi alkhairi cikinsu."
"Wayyo Mama shin wai da wanda ya furta da wanda bai furta ba wanne ne dahir?"
"Wanda ya furta."
"To Mama Aliyu shi ne dahir d'ina."
Kallon da Mama ke yimin yasa na tashi da gudu na fad'a d'akina. Bayana ta biyo ta zauna gefen katifa ni kuma na koma k'asa na zauna kaina sunkuye.
"Uwata dik abinda kike so shi na ke so amma ki sani ke d'in allurar cikin ruwa ce mai rabo ka d'auka dan haka na ke baki shawara idan Alhaji Muhseen ya furta miki kalman so da ki amince kada ki duba kina da Aliyu, kinji ko?"
Gyad'a kai na yi alamun amsawa amma a k'asan raina addu'ar kada Allah ya bashi damar furtamin na ke yi.
"Uwata kada kiga ina ta ambatar Alhaji Muhseen kiga kamar dan yana da kud'i ne na ke kwadayin da ki aureshi sam ba haka bane ina dai duba natsuwarsa ne tare da sanin darajar makwataka da uwa uba ilimin addini da ta zamani da ya mallaka sannan ke shaidace yana aiki da iliminsa yarda ya dace."
"Haka ne Mama."
"Da kyau sannan shi managarcin namiji ne wanda duk kan uwa ta gari zata so d'iyarta ta zamo k'ark'ashin ikonsa wato ta aureshi a game da kyautatawa iyali kuwa wannan ke ce zaki bada shaidan shi d'in jarimi ne ta kowani fuska ga iya mu'amala da mutane da sanin hak'k'in makwaftaka, kinga ko dan wad'an nan abu-buwa zanso ace ya zamo surikina, Uwata ta sami kwanciyar hankalin da na ke yi mata addu'ar samu."
"Mama dan Allah kiyi shiru haka nan wallahi kina yin maganar k'irjina na harbawa sam bana son maganar."
"Shi kenan Uwata na yi shiru amma zan cigaba da yi miki addu'ar samun miji na gari ko da kuwa ba Alhaji Muhseen ba ne ko Aliyu."
"Nagode Mamana ta kaina."
"Uwata abin alfaharin Mamanta, za'a soma soyayya."
Tura fuskata na yi tsakanin cinyoyina, ina jin ta mik'e tare da shafo kaina sannan tafice. Tashi tsaye na yi na soma kai kawo domin magan-ganun Mama sun tsayamin a rai.
"Tabbas Uncle mijin aure ne amma matarsa abar tsoro ce."
Na furta a hankali cikin jan karan hancina. Hangowa wayata na haske yasa na isa na d'auka tare da sallama muryan Aliyu Muktar ya doki kunnuwata sai na daburce domin ban saba waya da maza ba in ba Kawu Habibu ba. Dariyar da najiyo yanayi k'asa-k'asa yasa na saita kaina har da wani tsare gira tamkar yana gabana na amsa sallaman tare da tambayar shi lafiyarsa.
"Lafiyalau, alhamdulillah matar Ali."
Ware idonu na yi jin sunar da ya rad'amin, dariyarsa na kuma jiyowa amma irin mai fitowa cikin iska d'in nan.
"Ina son Nana Khadijatu ainun shi yasa na kirata da Matana kai tsaye dan inaji ajikina ke d'in mallakina ne, uwar 'ya-'yana."
"Uhm, ya su Mama da sisters."
Na samu kaina da ambatar haka duk kuwa da naji dad'in kalamansa.
"Suna lafiyalau, Salma ta ce agaisheki kafin ta zo gida."
"Wacece ita?"
"K'anwarmu ce yanzu ta shiga S S 1."
"Masha Allah ina amsawa, sai tazo ina zuba ido."
"Ai tare zamuzo gobe da hantsi insha Allah."
"Gobe!"
"Eh ko bakya nan ne?"
"Ina nan sai kunzo."
"Insha Allah kafin mu taho zan sanar miki."
"To."
Mukayi jim zuwa can ya kira sunana cikin wani siga, ban amsa ba sai gyaran murya da na yi, murshinsa najiyo nima sai na murmusa.
"Yimin hirar k'auna dan bazan tambayeki amincewa da k'auna ta ba saboda tunda kika d'auki wayar najiyo amon amincewarki na amsa kuwwa a kunnuwana da tsokar zuciyata."
Dariya ce ta kufcemin ba shiri. Shima dariyar ya sanya daga nan yasoma yimin kalaman k'auna wanda bansan da su ba a rayuwata, ni dai iyakata da shi eh, a'a, uhm domin bansan taya zan maida masa da martanin ba. Muna tsaka da wayar Beebah ta shigo da sallama yana jin na amsa sallama sai yayimin sallama, na ajiye wayar ina kallon cikin idanunta.
"Soyayya da dad'i, wata yarinya ta fad'a a cikinsa."
"Baki da dama Beebah."
"Ina da ita fa sai dai inayin dana sanin yiwa Aliyu jagora zuwa gareki."
"Ban fahimceki ba."
"Zaki fahimta tunda gida bai k'oshi ba, ba za'a bawa dawa ba."
"Matsalata da ke kenan iya salon magana wanda bancika fahimta ba."
"Kina Bahaushiya amma d'iyar Kanuri tafiki jin Hausa."
"To ya zanyi?."
"Ki koma School ki yo degree a fannin Husa."
"Aiki ja, ban iyawa kam."
Dariya muka sanya.
"Ina wayarki?"
Nuna mata na yi da yatsa, ta iso ta cirota a chargy ta sanya layukan MTN da GLO ta soma latse-latse tun ina kallonta har na gaji na kwanta barci ya d'aukeni dama shi na ke ji sosai.
Washe gari ina kammala azkar na fito waje da Baba na yi arba zaune a baranda yana jan tsarbi, gabansa na isa na gaisheshi ya amsa cikin gyaran murya na koma d'akina batare da na shiga d'akin Mama ba.
"Jiya Uncle ya kira wayarki kinyi barci."
Ware idanu na yi cikin jin fad'uwar gaba.
"Na tabbata zai kuma kira."
"Dan girman Allah ki kashe wayar."
"Saboda me?"
"Bana son na yi magana da shi ta waya ne sai bayan na yi masa godiya baki da baki."
"Kinyi magana kam amma ba za'a kashe ba, kidai hanzarta zuwa yi masa godiya kafin ya kira."
"Insha Allah zanje."
"Good."
Shiru ya ratsa wurin zuwa can na katse shirun da cewa "Kince zaki sanarmin da wani sak'o daga Uncle."
"Zan sanar miki Aunty Deejah."
"Aunty kuma?"
"Eh."
"Uhm kin fiye neman zance kam."
"Na kulle gidan ne sabida na fahimci yanzu Malam ya koma yimana lab'e."
Kauda kai gefe na yi batare da na ce komi ba.
"Uwata kinajin haushina akan lamarinmu da Malam ko?"
"A'a Mama kawai dai raina baya son tanki in tanka da kukeyi ne akaina."
"Uwata bana iya jure ganin Malam na tab'amin ke ce."
"Shi d'in mahaifina ne Mama ki barshi ya rik'a hukuntani kamar yarda yakeyiwa d'iyoyinsa idan sunyi masa ba dai-dai ba."
"Ke kina da bambanci da su domin bakya k'yetare umurninsa kamar yarda sauran sukeyi masa, sam ba kyayi masa laifin da zai hukuntaki dan haka bazan bari ya zakunceki ba."
"Zalinci kuma Mama?"
"Eh."
"Shifa Uba yake gareni, abin ikonsa ce ni."
"Nasan da haka amma ki sani akwai hakkin d'iyoyi akan mahaifansu dan haka yi miki hukunci batare da kin aikata laifin komi ba wannan zalinci ne kuma ba zan tab'a lamunta ba."
"Nidai Mama ki koyi hak'uri akan duk wanda ya tab'ani domin wata rana sai labari, ko ance su tab'ani bazasu iya ba."
"Allah ya kaimu wannan lokacin Uwata k'asa bai rufe idanuna ba."
"Amin Mama."
"Uwata natsu da kyau ki saurari maganar da zan sanar miki."
"To Mama ina saurarenki."
"D'azun dana fita gidan Baba Umaru naje, mun gama magana akan aurena da Malam, zan bashi sadakinsa shi kuma zai bani takardata tare da dukiyata."
"Innalillahi wa Inna ilaihin, Mama dan girman Allah ki bar maganar rabuwa da Baba domin yin hakan tamkar kin maidani marainiya ce dan na tabbata Baba ba zai barni na zauna tare da ke ba, zai gwadamiki karfin ikon da mazaje ke gwadawa matayensu da zarar sun rabu da su."
"Ki rubuta zamanmu dake aure ne kawai zai rabumu amma ba k'arfin ikon Malam ba saboda ke d'iyata ce da na ke da iko ita ko ta wani fuska."
"Mama nidai ki janye maganar rabuwan nan dan girman Allah."
"Uwata in kinga na janye sai Malam ya bani dukiyata dama Baba Umaru ya ce idan ya dank'amin hakkina in janye maganar saki idan kuma shi ya bani takardana kamar yarda yake shiri to shi kenan ba kare bin damo."
"K'alu innalillahi wa Inna ilaihin yanzu aina Baba zai samo miki kudinki alhalin kinfi kowa sanin baya da hanyarsu."
"Yana da shi Uwata, mugunta ce irin tashi ya ke son dannemin gadon da mahaifina ya barmin wanda yasha wuya wurin tarasu."
"Mama nikam ina rok'on da ki yafe masa dan girman Allah da Manzon sa."
"Uwata Malam ne ya rok'eki da ki nema masa affuwana kika amince shi ne ya ke saka miki albarka tare da yi miki alk'awarin daina hantararki."
Shiru na yi domin idan na amsa da eh, na karya alk'awarin da nayiwa Baba akan bazan bari sunarsa ya fito ba in kuma na ce a'a nayi k'arya, shirun danayi shi ne mafita."
"Uhm Uwata kenan har yanzu baki gama sanin duniya ba to bazan bar masa ba wallahi tallahi kinji na rantse to ko baya sallah sai ya biyani hak'k'ina."
Tsirawa Mama ido na yi cike da ruwan hawaye.
"Uwata kada ki sakawa kanki damuwa, zamu warware da Malam saboda yana da gidan gona wanda ya bunk'asashi da dukiyana. Kuma kema kin san sagonsa na saida kayan hatsi, yana kuma da filaye kinga kenan yana da hanyar biyana dukiyata kuma ba da jimawa ba zakiga hakan domin Baba Umaru tsohon alk'ali ne zai amsarmin kayana kamar yarda ya amsa a hannuna ya mik'a masa bisa shaidun lauya da wasu dattawa."
"Nidai Allah yasa kada kuyi rikici a binda ke tadamin da hankali kenan."
"Bazamuyi ba Uwata dan haka ki kwantar da hankalinki idan ya tambayeki yarda mukayi kice masa kin sanarmin ban amsa miki ba."
"To Mama."
"Gobe da safe zamu shiga muyiwa Alhaji Muhseen godiya."
"Tare da ke Mama?"
"Eh domin nafiki jin dad'in kyautar nan."
"Uhm Mama kenan, Allah ni kad'ai zanje in yaso idan kun had'u kyayi masa."
"Nima na ambata ne dan naji na bakinki Uwata."
Murmushi na yi ganin Mama na son maidani yarinya k'arama.
"Uwata wallahi ina farin ciki da tarayyanku da Alhaji Muhseen sama da yaron nan Aliyu da kika sanarmin."
"Mama shifa Uncle bai furta yana sona ba kawai hasa-shenki ne abinda bana fatar ya tabbata."
"To shikenan Uwata Allah ya zab'a miki mafi alkhairi cikinsu."
"Wayyo Mama shin wai da wanda ya furta da wanda bai furta ba wanne ne dahir?"
"Wanda ya furta."
"To Mama Aliyu shi ne dahir d'ina."
Kallon da Mama ke yimin yasa na tashi da gudu na fad'a d'akina. Bayana ta biyo ta zauna gefen katifa ni kuma na koma k'asa na zauna kaina sunkuye.
"Uwata dik abinda kike so shi na ke so amma ki sani ke d'in allurar cikin ruwa ce mai rabo ka d'auka dan haka na ke baki shawara idan Alhaji Muhseen ya furta miki kalman so da ki amince kada ki duba kina da Aliyu, kinji ko?"
Gyad'a kai na yi alamun amsawa amma a k'asan raina addu'ar kada Allah ya bashi damar furtamin na ke yi.
"Uwata kada kiga ina ta ambatar Alhaji Muhseen kiga kamar dan yana da kud'i ne na ke kwadayin da ki aureshi sam ba haka bane ina dai duba natsuwarsa ne tare da sanin darajar makwataka da uwa uba ilimin addini da ta zamani da ya mallaka sannan ke shaidace yana aiki da iliminsa yarda ya dace."
"Haka ne Mama."
"Da kyau sannan shi managarcin namiji ne wanda duk kan uwa ta gari zata so d'iyarta ta zamo k'ark'ashin ikonsa wato ta aureshi a game da kyautatawa iyali kuwa wannan ke ce zaki bada shaidan shi d'in jarimi ne ta kowani fuska ga iya mu'amala da mutane da sanin hak'k'in makwaftaka, kinga ko dan wad'an nan abu-buwa zanso ace ya zamo surikina, Uwata ta sami kwanciyar hankalin da na ke yi mata addu'ar samu."
"Mama dan Allah kiyi shiru haka nan wallahi kina yin maganar k'irjina na harbawa sam bana son maganar."
"Shi kenan Uwata na yi shiru amma zan cigaba da yi miki addu'ar samun miji na gari ko da kuwa ba Alhaji Muhseen ba ne ko Aliyu."
"Nagode Mamana ta kaina."
"Uwata abin alfaharin Mamanta, za'a soma soyayya."
Tura fuskata na yi tsakanin cinyoyina, ina jin ta mik'e tare da shafo kaina sannan tafice. Tashi tsaye na yi na soma kai kawo domin magan-ganun Mama sun tsayamin a rai.
"Tabbas Uncle mijin aure ne amma matarsa abar tsoro ce."
Na furta a hankali cikin jan karan hancina. Hangowa wayata na haske yasa na isa na d'auka tare da sallama muryan Aliyu Muktar ya doki kunnuwata sai na daburce domin ban saba waya da maza ba in ba Kawu Habibu ba. Dariyar da najiyo yanayi k'asa-k'asa yasa na saita kaina har da wani tsare gira tamkar yana gabana na amsa sallaman tare da tambayar shi lafiyarsa.
"Lafiyalau, alhamdulillah matar Ali."
Ware idonu na yi jin sunar da ya rad'amin, dariyarsa na kuma jiyowa amma irin mai fitowa cikin iska d'in nan.
"Ina son Nana Khadijatu ainun shi yasa na kirata da Matana kai tsaye dan inaji ajikina ke d'in mallakina ne, uwar 'ya-'yana."
"Uhm, ya su Mama da sisters."
Na samu kaina da ambatar haka duk kuwa da naji dad'in kalamansa.
"Suna lafiyalau, Salma ta ce agaisheki kafin ta zo gida."
"Wacece ita?"
"K'anwarmu ce yanzu ta shiga S S 1."
"Masha Allah ina amsawa, sai tazo ina zuba ido."
"Ai tare zamuzo gobe da hantsi insha Allah."
"Gobe!"
"Eh ko bakya nan ne?"
"Ina nan sai kunzo."
"Insha Allah kafin mu taho zan sanar miki."
"To."
Mukayi jim zuwa can ya kira sunana cikin wani siga, ban amsa ba sai gyaran murya da na yi, murshinsa najiyo nima sai na murmusa.
"Yimin hirar k'auna dan bazan tambayeki amincewa da k'auna ta ba saboda tunda kika d'auki wayar najiyo amon amincewarki na amsa kuwwa a kunnuwana da tsokar zuciyata."
Dariya ce ta kufcemin ba shiri. Shima dariyar ya sanya daga nan yasoma yimin kalaman k'auna wanda bansan da su ba a rayuwata, ni dai iyakata da shi eh, a'a, uhm domin bansan taya zan maida masa da martanin ba. Muna tsaka da wayar Beebah ta shigo da sallama yana jin na amsa sallama sai yayimin sallama, na ajiye wayar ina kallon cikin idanunta.
"Soyayya da dad'i, wata yarinya ta fad'a a cikinsa."
"Baki da dama Beebah."
"Ina da ita fa sai dai inayin dana sanin yiwa Aliyu jagora zuwa gareki."
"Ban fahimceki ba."
"Zaki fahimta tunda gida bai k'oshi ba, ba za'a bawa dawa ba."
"Matsalata da ke kenan iya salon magana wanda bancika fahimta ba."
"Kina Bahaushiya amma d'iyar Kanuri tafiki jin Hausa."
"To ya zanyi?."
"Ki koma School ki yo degree a fannin Husa."
"Aiki ja, ban iyawa kam."
Dariya muka sanya.
"Ina wayarki?"
Nuna mata na yi da yatsa, ta iso ta cirota a chargy ta sanya layukan MTN da GLO ta soma latse-latse tun ina kallonta har na gaji na kwanta barci ya d'aukeni dama shi na ke ji sosai.
Washe gari ina kammala azkar na fito waje da Baba na yi arba zaune a baranda yana jan tsarbi, gabansa na isa na gaisheshi ya amsa cikin gyaran murya na koma d'akina batare da na shiga d'akin Mama ba.
"Jiya Uncle ya kira wayarki kinyi barci."
Ware idanu na yi cikin jin fad'uwar gaba.
"Na tabbata zai kuma kira."
"Dan girman Allah ki kashe wayar."
"Saboda me?"
"Bana son na yi magana da shi ta waya ne sai bayan na yi masa godiya baki da baki."
"Kinyi magana kam amma ba za'a kashe ba, kidai hanzarta zuwa yi masa godiya kafin ya kira."
"Insha Allah zanje."
"Good."
Shiru ya ratsa wurin zuwa can na katse shirun da cewa "Kince zaki sanarmin da wani sak'o daga Uncle."
"Zan sanar miki Aunty Deejah."
"Aunty kuma?"
"Eh."
"Uhm kin fiye neman zance kam."