Sashe 39
Damuwata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Wannan kam ko mu biyu muka rage a duniya ba zan tab'a aurensa ba, nayiwa kaina wannan alk'awarin."
"Tsana in ya yi yawa mafi lokuta k'auna ke komawa, to dan Allah ki barwa Allah lamarin sai ya zab'a miki mari alkhairan."
"Insha Allah zan mik'a lamarin ga mai zab'awa bayi duk abinda yafi zama alkhairi a garesu."
"Da kyau tawan."
Murmushi mukayi tare da tafawa. Gyaran murya Fanta ta yi muka kalleta tsaye bakin k'ofa ta kafe Beebah da ido.
"Me ye?"
"Kin tsargu ne? To babu komi sai dai ni ce ta uku wacce ta san makauniyar soyayyar nan."
Dak'uwa ta yo mata muka fashe da dariya.
"Wallahi Aunty Beebah da a ce Yaya Mubajjal zai aureki da zance kunfi dacewa akan Aunty Hajara nan mai k'aton goshi da uban salo wai ita 'yar boko."
"To sannu 'yar son kai."
"Serious aunty Beebah, kun dace da juna kuma zan tayaki addu'ar Allah ya baki shi a matsayin miji."
"Amin 'yar uwa nagode."
"Sai dai wani hanzari ba gudu ba maganar fidda miji da Dady ya yi miki yana nan fa ba d'aga k'afa, shin ya zakiyi?."
"Ki bari kawai 'yar uwa babban DAMUWATA yanzu wannan maganar ce ga Momy ta goya masa baya shi yasa na ke jin tamkar kada in koma."
"Ga shawara ki kira Yaya Mubajjal ki sanar masa tare da neman shawararsa ko ki nuna masa ya nema miki alfarma wurin Dady da ya k'ara miki lokaci tunda kuna d'asawa ba zai juya miki baya ba."
"Good idea Aminiyata."
Na ambata cikin jinjinawa Fanta.
"Kuna ganin in aikata hakan?"
"Eh amma shawarar k'arshe na ya nema miki alfarma Dady ya k'ara miki lokaci kawai zakiyi masa. "
"Tam shi kenan, anjima zan sanar masa naji abin da zaice."
"Allah ya sa ya ce zaki aureni Habibatu."
Rungumeni ta yi cikin cewa "Da na kwana yi miki addu'ar gamawa lafiya da barin miki kyautar Umrar da Uncle ya yi min."
"Oh Aunty Beebah ba kunya."
"Amsa naki Fanta."
Ta watso mata d'ak'uwa cikin tsare gira.
Dariya muka sanya cike da nishad'i.
***
Washe gari tunda subahi kiran Uncle ya tashemu inda ya sanar da Beebah ta shirya shi zai kaisu. Ina azkar duk jikina a sanyaye na jin zasu tafi.
Sabo akace turken wawa to hakan ya faru gareni domin yinin ranar ko murmushi banjin na yi ba tun Mama da d'aukan abin da wasa har ta ga da gaske na ke sai ta koma bani baki amma duk da hakan ban dawo wal-walata ba na dai rage tsare gira. Fanta dama tunda taga ina hawaye ta fice ban sake sanyata a ido ba.
Misalin k'arfe uku na rana muna zaune saman tabarma Mama na damamin furar Tamba wanda Hajiya Inna ta aikomin da shi, muka tsinkayi sallama atare muka amsa wata Mata mai jiki tana da haske dai-dai misali ta shigo tare da matashiyar budurwa wacce kallo d'aya na yi mata na gano k'anwar Aliyu ce saboda kamarsu da juna har ya b'aci duk kuwa da tana fara shi kuwa bak'i.
Cikin girmamawa Mama ta basu wurin zama yarinyar ta zauna ta gaisar da Mama tare da yimin ya jiki na amsa cikin murmushi saboda naji dad'in ganinsu.
Matar kam tsaye ta yi k'erere tana jifana da wani kallo wanda ya saukemin kasala tare da bugun k'irji, gaisuwar da na ke nufin yi mata nakasa aiwatarwa, alokaci d'aya na nemi farin cikin ganinsu na rasa.
Mama da bata lura da kallon ba ta tafi d'auko musu abin motsa baki.
"Ina yini?"
Na furta cikin jajircewa.
"Mahaifiyar Aliyu ce dafatar ya sanar miki zuwana?"
Ta maidomin da amsar gaisuwar ta bayyanamin kanta.
"Eh, kunzo lafiya?"
"Ba damuwarki ba ne wannann."
Da sauri na kalleta ta zaromin manyan idanunta kauda kai gefe na yi ina jan addu'ar duk da yazo bakina.
"Na zo yi miki kashedi ne a kansa, ki rabumin da d'a ba zai aureki ba na zab'a masa wacce ta dace da shi domin auren zumunci zaiyi da d'iyoyin ar...
"Akul! kika nemi aibatamin d'iya akan idona Hajiya Asiya, tunda dai kin fad'i abin da ya kawoki to fice min a muhalli tun ranki baifi nawa b'aci ba."
Cikin fushi Mama ke maganar wanda na hango mamaki a idanun wacce ta kira kanta da mahaifiyar Aliyu jin kalamin Mama
"Ni kike kora a gidanki?"
"Ya wuce kokwanto, maza ficemin ko in sanya afitar da ke kuma idan kin isa da d'anki kada na sake ganinsa a k'ofar gidana balle ya shigomin muhalli."
"Haka kika ce?"
"Eh."
"Kin tabbata d'iyarki ta rabumin d'a kenan na har abada?"
"Ko a lahira bana fatar Uwata ta had'u da d'anki."
"Masha Allah, abu yazo cikin sauk'i, nabarki lafiya."
Banza Mama ta yi da ita illa nuna mata hanyar ficewa da ta yi.
"Hajiya ba haka kukayi da Yaya ba dan Allah ki ba su hak'uri dan d'anki zaifi cutuwa."
"Zaki tashi mu tafi ko sai na sab'a miki?"
Da sauri Salma ta mik'e suka fice na kalli Mama ta watsomin harara sai na tashi da sauri na shige d'akina ina jin zuciyata tamkar zata fad'o k'asa.
*Assalamu alaikum. Shahararren kamfanin nan na oriflame na yin registration kyau a wannan wata duk mai burin a dama da ita a harkan siye da siyarwa na kayan kamfanin ko yin amfani da kayan domin jin dad'inta to wannan babban damace a gareki ki garzayo ayi miki register kyauta kafin wata nan ta November ya k'are domin in ya k'are sai kin biya kusan 5k kafin ki samu damar zama 'yar kamfanin mai 'yanci dan haka ki taho ki zama .ai 'yanci a kyauta. Dan k'arin bayani ku tuntub'i wannan number 08131166848.*
[11/5, 1:15 PM] 💘: DAMUWATA (Sanin abin adona)
By Mrsjmoon
E.W.F.
https://youtu.be/v9iNYDvS8JM
Pls 'yan uwa ku dannamin subcribe a YouTube d'ina, nagode.
Page 22.
"Dan Allah ki fito waje zuciyata na koma ga mahallicina ko na huta da wannan rayuwa mai cike da damuwa kala-kala, shin wai meye dalilin zamowata mara sa'ar rayuwa ce? Ina burin gabatar da rayuwa mai cike da kwanciyar hankali tamkar sauran mutane? Wayyo ni Nana Khadijatu ina zan saka kaina? Mahaifina bai bar ruhina ya sami natsuwa daga wasi-wasin shi d'in uba na ne ko zaman agolanci na ke yi a k'ark'ashinsa ba sannan ga saurayin da na sama bayan tsawon lokacin dana kwashe ina geben samun abokin rayuwa Mahaifiyarsa ta jagoranci rabuwarmu duk da na soma fidda shi a raina amma banso rabuwarmu ya zo ta wannan sigan ba. Ina da tulin tambayoyi a gareki Mama dan Allah ki amsamin su ko natsuwar da na ke nema ya rab'eni. Ya Salam, ya rabbi ka kawomin d'auki badan halina ba. K'alu Innalillahi wa inna ilaihin raji'un, Allahumma ajirni fi masibati wa khalifni khairan minha."
Sune kalman dana rik'a ambata cikin matsanancin kuka hannayena duka biyun dafe da k'irjina wanda na tabbatar bana rabuwa da Aliyu ba ne domin ina jin wani sabon lamari na daban zai sameni wanda zanyi kukan shi yasa na bud'e baki ina yinsa tamkar wacce aka aikowa da sak'on mutuwar Mama. A k'arshe zamewa na yi na kwanta saman sallaya ina cigaba da kuka amma mara sauti saboda yin mai sautin zai janyo hankalin Mama saidai duk da rage sautin bai hanata jiyowa ba.
Ina jin shigowarta nak'i motsawa tana d'ora hannunta a gadon bayana sabon kuka ya kubcemin na fashe da mai k'arfi sosai cikin jijjiga. Hannunta ta soma yawo da shi a bayana a hankali ba tare da ta yi magana ba, ina ji a jikina itama kukan ta keyi mara sauti, d'if na d'auke nawa tare da tashi zaune da hanzari na fad'a jikinta ina cewa "Natuba Mama dan Allah ki yafemin ba burina kenan ba na sakaki kuka lamarin ne ya dameni dole saina zubda jirwaye zan sami natsuwar jiki da ruhi, dan Allah kada kiyi fushi da ni, natuba Mamana, kiyi shiru dan girman Allah, zubar hawayenki dafi ne a gareni dan Allah kibari kada wani abu mara kyau ya sameni sanadin kukan nan."
"Banyi fushi dake ba Uwata kuma ba kuka na ke yi ba fatana ki sanya salama cikin ranki dan samuwar lafiyarki sannan kada kiyi zargin na jagoranci rabaki da mosayinki ne saboda da wata manufa tawa a'a sam ba haka ba ne ina dai burin kiyi rayuwa ce mai cike da 'yanci wanda zaki sakata ki wala a gidan aurenki ba wanda zaki dawwama cikin k'unci ba bisa takurawar uwarmiji wannan dalilin yasa na datse alak'arki da Aliyu kuma idan har na isa na fad'a ki ji to daga yau babu ke babu Aliyu har abada sunarsama bana son ki sake ambata koda a cikin zuciyarki ne, burina ki kasance tamkar baki tab'a sanin shi ba balle ki tuna kun tab'a musayan kalaman k'auna."
"Mama...
"Uwata hakan na ke buk'ata da ke, hatta da makaranta da kuke had'uwa kin daina zuwarsa kenan domin na tsani mahaifiyarsa da shi kansa tunda ta sanya Uwata zubda hawaye a kan idona sannan ta nemi aibatamin ke da kalma mafi muni da natsani jinsa."
"Mama na hak'ura da shi tun kafin zuwar wannan lokaci kuma insha Allah zan ciresa a babin rayuwata sai dai ina rok'on da ki janye kalman tsana ga Aliyu saboda baiyi komi ba ko ba komi ya so Nana Khadijatunki da zuciya d'aya, ya karya bak'in tarihin nan na tana da bak'in jini ta rasa mai furta mata kalman so."
"To Uwata na jenye harma da Mahaifiyar masa duk na yi hak'uri irin wanda Allah da Manzonsa duke son mumunai nagari sunayi wato hak'uri mai kyau."
Sunkuyar da kai na yi ganin tana kallona cikin murmushi ga hawayenan cikin kwarmin idanunta suna daf da zubowa. Ban d'agoba na mik'a hannu na share mata hawayen, ta rik'e hannuna gam na d'ago da sauri ta motsa kai, matsowa jikinta na yi ta saki hannuna na samu damar shigewa na lafe, bubbugamin baya ta soma tamkar uwa na rarrashin 'yar yaye.
"Mama tun jiya na soma cire Aliyu a ruhina saboda... Na sanar da ita duk abin da ya faru zuwar matar Kawu Habibu dubani da zantukan da mukayi da Hajiya Inna.
"Alhamdulillah, Allah ya zab'a miki mafi alkhairi."
"Amin Mama."
"Tsana in ya yi yawa mafi lokuta k'auna ke komawa, to dan Allah ki barwa Allah lamarin sai ya zab'a miki mari alkhairan."
"Insha Allah zan mik'a lamarin ga mai zab'awa bayi duk abinda yafi zama alkhairi a garesu."
"Da kyau tawan."
Murmushi mukayi tare da tafawa. Gyaran murya Fanta ta yi muka kalleta tsaye bakin k'ofa ta kafe Beebah da ido.
"Me ye?"
"Kin tsargu ne? To babu komi sai dai ni ce ta uku wacce ta san makauniyar soyayyar nan."
Dak'uwa ta yo mata muka fashe da dariya.
"Wallahi Aunty Beebah da a ce Yaya Mubajjal zai aureki da zance kunfi dacewa akan Aunty Hajara nan mai k'aton goshi da uban salo wai ita 'yar boko."
"To sannu 'yar son kai."
"Serious aunty Beebah, kun dace da juna kuma zan tayaki addu'ar Allah ya baki shi a matsayin miji."
"Amin 'yar uwa nagode."
"Sai dai wani hanzari ba gudu ba maganar fidda miji da Dady ya yi miki yana nan fa ba d'aga k'afa, shin ya zakiyi?."
"Ki bari kawai 'yar uwa babban DAMUWATA yanzu wannan maganar ce ga Momy ta goya masa baya shi yasa na ke jin tamkar kada in koma."
"Ga shawara ki kira Yaya Mubajjal ki sanar masa tare da neman shawararsa ko ki nuna masa ya nema miki alfarma wurin Dady da ya k'ara miki lokaci tunda kuna d'asawa ba zai juya miki baya ba."
"Good idea Aminiyata."
Na ambata cikin jinjinawa Fanta.
"Kuna ganin in aikata hakan?"
"Eh amma shawarar k'arshe na ya nema miki alfarma Dady ya k'ara miki lokaci kawai zakiyi masa. "
"Tam shi kenan, anjima zan sanar masa naji abin da zaice."
"Allah ya sa ya ce zaki aureni Habibatu."
Rungumeni ta yi cikin cewa "Da na kwana yi miki addu'ar gamawa lafiya da barin miki kyautar Umrar da Uncle ya yi min."
"Oh Aunty Beebah ba kunya."
"Amsa naki Fanta."
Ta watso mata d'ak'uwa cikin tsare gira.
Dariya muka sanya cike da nishad'i.
***
Washe gari tunda subahi kiran Uncle ya tashemu inda ya sanar da Beebah ta shirya shi zai kaisu. Ina azkar duk jikina a sanyaye na jin zasu tafi.
Sabo akace turken wawa to hakan ya faru gareni domin yinin ranar ko murmushi banjin na yi ba tun Mama da d'aukan abin da wasa har ta ga da gaske na ke sai ta koma bani baki amma duk da hakan ban dawo wal-walata ba na dai rage tsare gira. Fanta dama tunda taga ina hawaye ta fice ban sake sanyata a ido ba.
Misalin k'arfe uku na rana muna zaune saman tabarma Mama na damamin furar Tamba wanda Hajiya Inna ta aikomin da shi, muka tsinkayi sallama atare muka amsa wata Mata mai jiki tana da haske dai-dai misali ta shigo tare da matashiyar budurwa wacce kallo d'aya na yi mata na gano k'anwar Aliyu ce saboda kamarsu da juna har ya b'aci duk kuwa da tana fara shi kuwa bak'i.
Cikin girmamawa Mama ta basu wurin zama yarinyar ta zauna ta gaisar da Mama tare da yimin ya jiki na amsa cikin murmushi saboda naji dad'in ganinsu.
Matar kam tsaye ta yi k'erere tana jifana da wani kallo wanda ya saukemin kasala tare da bugun k'irji, gaisuwar da na ke nufin yi mata nakasa aiwatarwa, alokaci d'aya na nemi farin cikin ganinsu na rasa.
Mama da bata lura da kallon ba ta tafi d'auko musu abin motsa baki.
"Ina yini?"
Na furta cikin jajircewa.
"Mahaifiyar Aliyu ce dafatar ya sanar miki zuwana?"
Ta maidomin da amsar gaisuwar ta bayyanamin kanta.
"Eh, kunzo lafiya?"
"Ba damuwarki ba ne wannann."
Da sauri na kalleta ta zaromin manyan idanunta kauda kai gefe na yi ina jan addu'ar duk da yazo bakina.
"Na zo yi miki kashedi ne a kansa, ki rabumin da d'a ba zai aureki ba na zab'a masa wacce ta dace da shi domin auren zumunci zaiyi da d'iyoyin ar...
"Akul! kika nemi aibatamin d'iya akan idona Hajiya Asiya, tunda dai kin fad'i abin da ya kawoki to fice min a muhalli tun ranki baifi nawa b'aci ba."
Cikin fushi Mama ke maganar wanda na hango mamaki a idanun wacce ta kira kanta da mahaifiyar Aliyu jin kalamin Mama
"Ni kike kora a gidanki?"
"Ya wuce kokwanto, maza ficemin ko in sanya afitar da ke kuma idan kin isa da d'anki kada na sake ganinsa a k'ofar gidana balle ya shigomin muhalli."
"Haka kika ce?"
"Eh."
"Kin tabbata d'iyarki ta rabumin d'a kenan na har abada?"
"Ko a lahira bana fatar Uwata ta had'u da d'anki."
"Masha Allah, abu yazo cikin sauk'i, nabarki lafiya."
Banza Mama ta yi da ita illa nuna mata hanyar ficewa da ta yi.
"Hajiya ba haka kukayi da Yaya ba dan Allah ki ba su hak'uri dan d'anki zaifi cutuwa."
"Zaki tashi mu tafi ko sai na sab'a miki?"
Da sauri Salma ta mik'e suka fice na kalli Mama ta watsomin harara sai na tashi da sauri na shige d'akina ina jin zuciyata tamkar zata fad'o k'asa.
*Assalamu alaikum. Shahararren kamfanin nan na oriflame na yin registration kyau a wannan wata duk mai burin a dama da ita a harkan siye da siyarwa na kayan kamfanin ko yin amfani da kayan domin jin dad'inta to wannan babban damace a gareki ki garzayo ayi miki register kyauta kafin wata nan ta November ya k'are domin in ya k'are sai kin biya kusan 5k kafin ki samu damar zama 'yar kamfanin mai 'yanci dan haka ki taho ki zama .ai 'yanci a kyauta. Dan k'arin bayani ku tuntub'i wannan number 08131166848.*
[11/5, 1:15 PM] 💘: DAMUWATA (Sanin abin adona)
By Mrsjmoon
E.W.F.
https://youtu.be/v9iNYDvS8JM
Pls 'yan uwa ku dannamin subcribe a YouTube d'ina, nagode.
Page 22.
"Dan Allah ki fito waje zuciyata na koma ga mahallicina ko na huta da wannan rayuwa mai cike da damuwa kala-kala, shin wai meye dalilin zamowata mara sa'ar rayuwa ce? Ina burin gabatar da rayuwa mai cike da kwanciyar hankali tamkar sauran mutane? Wayyo ni Nana Khadijatu ina zan saka kaina? Mahaifina bai bar ruhina ya sami natsuwa daga wasi-wasin shi d'in uba na ne ko zaman agolanci na ke yi a k'ark'ashinsa ba sannan ga saurayin da na sama bayan tsawon lokacin dana kwashe ina geben samun abokin rayuwa Mahaifiyarsa ta jagoranci rabuwarmu duk da na soma fidda shi a raina amma banso rabuwarmu ya zo ta wannan sigan ba. Ina da tulin tambayoyi a gareki Mama dan Allah ki amsamin su ko natsuwar da na ke nema ya rab'eni. Ya Salam, ya rabbi ka kawomin d'auki badan halina ba. K'alu Innalillahi wa inna ilaihin raji'un, Allahumma ajirni fi masibati wa khalifni khairan minha."
Sune kalman dana rik'a ambata cikin matsanancin kuka hannayena duka biyun dafe da k'irjina wanda na tabbatar bana rabuwa da Aliyu ba ne domin ina jin wani sabon lamari na daban zai sameni wanda zanyi kukan shi yasa na bud'e baki ina yinsa tamkar wacce aka aikowa da sak'on mutuwar Mama. A k'arshe zamewa na yi na kwanta saman sallaya ina cigaba da kuka amma mara sauti saboda yin mai sautin zai janyo hankalin Mama saidai duk da rage sautin bai hanata jiyowa ba.
Ina jin shigowarta nak'i motsawa tana d'ora hannunta a gadon bayana sabon kuka ya kubcemin na fashe da mai k'arfi sosai cikin jijjiga. Hannunta ta soma yawo da shi a bayana a hankali ba tare da ta yi magana ba, ina ji a jikina itama kukan ta keyi mara sauti, d'if na d'auke nawa tare da tashi zaune da hanzari na fad'a jikinta ina cewa "Natuba Mama dan Allah ki yafemin ba burina kenan ba na sakaki kuka lamarin ne ya dameni dole saina zubda jirwaye zan sami natsuwar jiki da ruhi, dan Allah kada kiyi fushi da ni, natuba Mamana, kiyi shiru dan girman Allah, zubar hawayenki dafi ne a gareni dan Allah kibari kada wani abu mara kyau ya sameni sanadin kukan nan."
"Banyi fushi dake ba Uwata kuma ba kuka na ke yi ba fatana ki sanya salama cikin ranki dan samuwar lafiyarki sannan kada kiyi zargin na jagoranci rabaki da mosayinki ne saboda da wata manufa tawa a'a sam ba haka ba ne ina dai burin kiyi rayuwa ce mai cike da 'yanci wanda zaki sakata ki wala a gidan aurenki ba wanda zaki dawwama cikin k'unci ba bisa takurawar uwarmiji wannan dalilin yasa na datse alak'arki da Aliyu kuma idan har na isa na fad'a ki ji to daga yau babu ke babu Aliyu har abada sunarsama bana son ki sake ambata koda a cikin zuciyarki ne, burina ki kasance tamkar baki tab'a sanin shi ba balle ki tuna kun tab'a musayan kalaman k'auna."
"Mama...
"Uwata hakan na ke buk'ata da ke, hatta da makaranta da kuke had'uwa kin daina zuwarsa kenan domin na tsani mahaifiyarsa da shi kansa tunda ta sanya Uwata zubda hawaye a kan idona sannan ta nemi aibatamin ke da kalma mafi muni da natsani jinsa."
"Mama na hak'ura da shi tun kafin zuwar wannan lokaci kuma insha Allah zan ciresa a babin rayuwata sai dai ina rok'on da ki janye kalman tsana ga Aliyu saboda baiyi komi ba ko ba komi ya so Nana Khadijatunki da zuciya d'aya, ya karya bak'in tarihin nan na tana da bak'in jini ta rasa mai furta mata kalman so."
"To Uwata na jenye harma da Mahaifiyar masa duk na yi hak'uri irin wanda Allah da Manzonsa duke son mumunai nagari sunayi wato hak'uri mai kyau."
Sunkuyar da kai na yi ganin tana kallona cikin murmushi ga hawayenan cikin kwarmin idanunta suna daf da zubowa. Ban d'agoba na mik'a hannu na share mata hawayen, ta rik'e hannuna gam na d'ago da sauri ta motsa kai, matsowa jikinta na yi ta saki hannuna na samu damar shigewa na lafe, bubbugamin baya ta soma tamkar uwa na rarrashin 'yar yaye.
"Mama tun jiya na soma cire Aliyu a ruhina saboda... Na sanar da ita duk abin da ya faru zuwar matar Kawu Habibu dubani da zantukan da mukayi da Hajiya Inna.
"Alhamdulillah, Allah ya zab'a miki mafi alkhairi."
"Amin Mama."