Sashe 40
Damuwata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Na amsa a hankali cike da kunya ta shafi sumar kaina cikin cewa "Taho muje ki tayani aiki domin zama wuri d'aya na janyo tunani mara tushe da fatan ban takura Uwata ba?"
"Mama kekoh."
Na ambata a shagwab'e.
Hanncina ta ja na d'auke numfashi cikin sigan wasa ta saki da sauri na fashe da dariya tana tayani.
"Allah ya cigaba da albarkatan rayuwarki Khadijatu."
"Amin Mamana."
Fitowa mukayi Mama ta yi ta yimin hira mai sanya mantawa da duk kan damuwa.
"Uwata yau Litini insha Allah jibi laraba zamu tafi Kwara dubo jikin Babana."
"Allah ya kaimu Mama."
"Amin."
"Gobe zamuje yi masu tsaraba da fatan zaki iya shiga kasuwa?"
"Zan iya Mama."
"Madallah, anjima Habibu zaizo muje shagunana domin ina son saidaasu na had'esu ya zama babba guda d'aya kamar super market."
"Masha Allah, Allah ya taimaka."
"Amin, zan dank'a a hannunsa dan hakan zai fi akan yawo da hankalin da masu hayan keyimin ko ba komi shi nawane, da wasu su cinyemin gara shi ya ci ya more."
"Hakan ya yi Mama, Allah ya yiwa nema albarka ya taya Kawu Habibu rik'o."
"Amin."
"Jiya an sami masalaha tsakanin Alhaji Muhseen da Malam ina fatar nadamar da na hango a idanun Malam ya zamo na gaskiya ne."
"Amin ya rabbi."
Shiru ya ratsa wurin na dubeta kad'an ta motsa kai alamun tana saurarona.
"To Mama kin hak'ura da zancen dukiyanki na wurin Baba ko?"
"A'a bazan hak'ura ba dan zaman jiya har da shi aka tsaida maganar ina dawowa daga Kwara zai dank'amin kayana domin lokacin yin amfani da su ya yi dama an bashi ne ya ajiye amatsayinsa da shugabana sai ya nemi a bashi damar ya juya zuwa sadda za'a nema to lokacin neman ya yi."
"To Mama idan baya da shi fa?"
"Na sanar miki yana da gidan gona wanda da kud'ina ya mallaka haka ya siya gonaki duk da kud'in yanzu haka takardun gonakin jiya Baba Umaru ya amsa daga hannunsa gidan gonar kuma zaiyi masa kud'i Habibu zai siya sai a had'a da gonakin a lissafa in sun kai adadin kud'ina in kuma sun wuce sai abashi ragowar hakk'insa."
"Kuma duk Baba ya amince cikin ruwan sanyi?"
"Eh saboda Baba Umaru ba sa'ar wasanshi ba ne sannan komi da akayi anyisa ne a rubuce tare da shaidu. Idan komi ya kammala filin da ke kan layin su Baba Umaru za'a siya a gina babban Mall wanda zai kasance babu ce kawai ba'a siyarwa."
Dariya na sanya cike da jin dad'i na ce "Da sai in zama shuga mai bada umurni."
"Allah dai ya cika mana burinmu Uwata domin komi da kikaga inayi to dan ingantuwar rayuwarki ne, kada k'asa ya rufe idona Malam ya handame komi ya koramin."
"Godiya na ke Mamana amma dan Allah ki kyautatawa Baba zato."
"To naji amma ki sani ba godiya a tsakanin Uwa da 'ya sai addu'ar samun babban rabo ranar lahira."
"Allah ya biyaki da gidan aljannatul firdausi."
"Amin ya rabbi."
"Yawwa Mama wai ya muke da Baba Abdul Ganiyu nan?"
Shiru ta yi har na cire rai da jin amsar tambayar sai kawai na kamo hannunta na langab'e kai cikin sanyin murya na ce "Kiyi hak'uri Mama idan sanarmin zai takuraki wallahi na fasa jin nasabanmu da shi."
"Zan sanar da ke amma a takaice domin zuwa yanzu ya kamata ki soma sanin ya ni ke da duk wanda kika ganmu tare."
"To Mama Ina saurarenki."
"Kinga Baba Abdul Ganiyu abokin mahaifina ne na k'ud da k'ud amma shi bayarbene ya yin da Mahaifina Abdullahi ya zamo Hausa Fulani d'an asalin garin sokoto. Sadda Allah ya nufa zan zo garin Kaduna da zama Baba Abdul Ganiyu ne ya had'ani da Baba Umaru wanda shi kuma ya zamo abokin kasuwancinsa daga arewa zuwa kudu. Baba Umaru ya rik'e ni tamkar shi ya haifeni dan haka wad'an nan mutanen biyu bani da kamarsu in kika cire mahaifana, Abdaullahi da Hadiza da kuma ke 'ya ta."
"Allah ya kai haske k'abarinsu."
"Amin."
"To Mama ina danginmu na Sokoto?"
"Suna nan."
"Me yasa ba...
"Uwata kada ki tsananta bincike domin na yi miki alk'awarin sanar da ke komi idan lokacin ki sani ya yi."
"To Mama na kame bakina."
"Da kyau, idan zaki sha furanki tana cikin fridge."
Murmushi na yi jin ta sauya akalan zancen.
"Ko sai zuwa dare zaki sha?"
"A'a zan sha yanzu, bari in d'ibo kad'an."
"Aha, sai ki zuba zuma zaifi dad'in d'and'ano akan saka siga."
"To Mamana."
Ina shan furar na dubi Mama wacce ke gyara zogale zata dafa mana wanda Hajiya Inna ta aikomin da shi domin na ce kwad'onsa na ke son ci da dare.
"Ya dai Uwata?"
Lashe lips na yi na amsa da "Ina burin na ganni cikin danginmu duk da bana son hayaniyar jama'a amma son ganina tsakanin kakanni, iyaye da abokanan wasa maza da mata wannan babban buri ne da ya jima a ruhina sai dai idan na nutsa cikin tunani sai wani lamari da na rasa gane kansa ya zo ya shafe burin ta hanyar jefani cikin fargaba har sai na ji ban son ganina cikin dangin baki d'aya sai na rik'a jin dama banzo duniyar ba."
Banza Mama ta yi da ni domin tunda na fara maganar bata nuna zata furta kalma ba. Na matso jikinta na jingina ina sauke numfashi, still bata kulani ba sai na gyara zama a gabanta na ce "Zanso idan mun dawo Kwara mu tsaya a Sokoto inda halima ki barni a can na zaga dangi na birni da karkara dan samun ladar zumunci."
"Allah ya kaimu lokacin amma zuwa Sokoto ba yanzu ba saboda ko wani tafiya nasa daban na ke son yi."
Jinjina kai na yi ina wasa da ganyen zogalen da ta tsinke.
"Uwata da magana a bakinki ko?"
Kallonta na yi ta waremin idanu cikin jiran abinda zan fura sai na girgiza kai tare da tashi na shige d'akina ina murmushi.
"Nana Khadijatu kenan, Uwata ta kaina, nasan damuwarki bai wuce zantukan da kika gamayi na yi banza da ke, affuwan Uwata bana da jarumtar biye miki ne."
Mama ta furta tare da mik'ewa ta shige madafi.
***
*Asabe da Hinde.*
Asabe ce zaune a k'ofarta ta tsefin kai wanda da kyar ta ke kamo bindin korar saboda tsabar tsufar da ya yi gami da datti, Hinde kuwa tana nesa da ita tana gyaran gyad'an miya.
"Hinde wallahi duk tijarar da na gani gami da iziya a hannun masu babbak'un kaya ban saduda ba ko misk'ala zarratin domin sai naga bayan Hurera kafin k'asa ya rufe idanu zanji dad'in a raina."
"Yaya tamkar kin shiga zuciyata, tunanin da na keyi kenan yanzu, wallahi da abin na ke kwana na ke tashi musanman mijin da Uwani zata aura, gashi mutumin kirki sam abinsa bai rufe masa idanu ba da ganinsa ya san abinda yakeyi, hak'ik'a zataji dad'in zama da shi, Hurera zata huta fiye da zatona, zata tabbata cikin jin dad'i mu kuma 'yan maula domin ko Malam sai yarda ta yi da shi dama ya lafiyar giwa balle ta yi hauka."
"Hinde kin sosamin inda keyimin k'aik'ayi, billahil azim ji na ke tamkar in wayi gari acemin Alhaji Muhseen ya mutu na rantse da sai na yi rawa da juyi dan Hurera taga samu taga rashi kenan a lokaci d'aya."
"Ai idan zaki bani had'in kai na rantse sai dai ya auri wata amma ba Uwani ba, domin nafi jin takaicin ni'imar da zata shiga muna kallo tamkar tumakai."
"Ina tare da ke 'yar uwa, tunda mun samu ya yi mana yayyafin naira muyi jari to mu had'esa kaf mu fantsama neman sa'ar datse wannan bak'ar alak'ar domin ba zan kirashi da fari ba."
Wata dariya Hinde ta b'arke da shi wanda ya bawa Asabe tsoro ta shige d'akinta da gudu biyo bayanta Hinde ta yi tana cigaba da dariyar tamkar ta sami tab'in hankali nanko ras ta ke tsabar jin dad'in kalaman Asabe ce.
***
"Yaya Aliyu kabi umurnin Hajiya domin ta yi rantsuwa ba zaka auri kowa ba sai Amira."
Numfashi ya sauke ya kafe Salma da ido "Me Hajiya ta aikata a gidan su Khadija wanda ya janyo ta sakani a black list ko na kirata bai shiga na ganta a online na yi mata magana ta yi blocking d'ina na sanja layi na kirata tana jin muryana ta kashe na tura sak'o ta wayar K'awarta Fanta ta k'i dawomin da amsa, maza sanarmin da abinda Hajiya ta aikata musu da ya janyo na fuskanci wannan lamarin.
"Kayi hak'uri Yaya ba zan iya sanar maka ba saboda nayiwa Hajiya alk'awarin kame bakina."
"Zanje gidan yau da kaina in yaso zanji komeye a bakinta."
"Kada kaje saboda Mamanta ta fusata zuwanka zai zamo zubewar mutuncin Hajiya ce domin ta ce idan ta isa da kai ta hanaka zuwa gidan, kenan zuwanka tamkar Hajiya bata isa da kai ba ne."
"Duk me ya kawo wannan zantukan daga zuwa dubiya?"
"Wanna tambayoyin Hajiya ke da amsoshinsu kuma ya kamata ta amsa maka domin ina zargin da abinda ta ke b'oye mana wanda ya shafi Khadija domin da kunnuwana na ji aunty Zainab na yi mata rantsuwa akan wani abu na so jin abin amma Hajiya ta sauya zancen tare da rufeni da fad'a dan na nemi k'arin bayani."
"Zainab zan sama naji munafuncin da ta k'ulla domin tunda ta gano Khadija ce wacce na ke so na hango tsanar lamarin a idanunta, kuma wallahi idan ta yi sanadin rabani da wacce na ke so rayukanmu zasu b'aci matuk'ar b'aci."
"Kabi komi a sannu Yaya amma ina ji a jikina Deejah ba matarka ba ce."
"B'acemin da gani ko in nad'a miki duka! Wawiya kawai wacce ba'ajin alkhairi abakinta sai sharri."
"Ni d'in Yaya?"
"Zaki fice ko sai na zubda miki da hak'ora?"
Cikin fushi Salma ta bar d'akin tamkar zata saka kuka.
"Ina cikin tsaka mai wuya ni Aliyu."
Ya furta tare da sake dialing number Fanta haka ya gama ringing ba'a d'aga ba, kwanciya ya yi na cigaba da kiran wayar amma baiyi dacen an d'auka ba balle ya rok'eta ta had'ashi da Deejah.
"Mama kekoh."
Na ambata a shagwab'e.
Hanncina ta ja na d'auke numfashi cikin sigan wasa ta saki da sauri na fashe da dariya tana tayani.
"Allah ya cigaba da albarkatan rayuwarki Khadijatu."
"Amin Mamana."
Fitowa mukayi Mama ta yi ta yimin hira mai sanya mantawa da duk kan damuwa.
"Uwata yau Litini insha Allah jibi laraba zamu tafi Kwara dubo jikin Babana."
"Allah ya kaimu Mama."
"Amin."
"Gobe zamuje yi masu tsaraba da fatan zaki iya shiga kasuwa?"
"Zan iya Mama."
"Madallah, anjima Habibu zaizo muje shagunana domin ina son saidaasu na had'esu ya zama babba guda d'aya kamar super market."
"Masha Allah, Allah ya taimaka."
"Amin, zan dank'a a hannunsa dan hakan zai fi akan yawo da hankalin da masu hayan keyimin ko ba komi shi nawane, da wasu su cinyemin gara shi ya ci ya more."
"Hakan ya yi Mama, Allah ya yiwa nema albarka ya taya Kawu Habibu rik'o."
"Amin."
"Jiya an sami masalaha tsakanin Alhaji Muhseen da Malam ina fatar nadamar da na hango a idanun Malam ya zamo na gaskiya ne."
"Amin ya rabbi."
Shiru ya ratsa wurin na dubeta kad'an ta motsa kai alamun tana saurarona.
"To Mama kin hak'ura da zancen dukiyanki na wurin Baba ko?"
"A'a bazan hak'ura ba dan zaman jiya har da shi aka tsaida maganar ina dawowa daga Kwara zai dank'amin kayana domin lokacin yin amfani da su ya yi dama an bashi ne ya ajiye amatsayinsa da shugabana sai ya nemi a bashi damar ya juya zuwa sadda za'a nema to lokacin neman ya yi."
"To Mama idan baya da shi fa?"
"Na sanar miki yana da gidan gona wanda da kud'ina ya mallaka haka ya siya gonaki duk da kud'in yanzu haka takardun gonakin jiya Baba Umaru ya amsa daga hannunsa gidan gonar kuma zaiyi masa kud'i Habibu zai siya sai a had'a da gonakin a lissafa in sun kai adadin kud'ina in kuma sun wuce sai abashi ragowar hakk'insa."
"Kuma duk Baba ya amince cikin ruwan sanyi?"
"Eh saboda Baba Umaru ba sa'ar wasanshi ba ne sannan komi da akayi anyisa ne a rubuce tare da shaidu. Idan komi ya kammala filin da ke kan layin su Baba Umaru za'a siya a gina babban Mall wanda zai kasance babu ce kawai ba'a siyarwa."
Dariya na sanya cike da jin dad'i na ce "Da sai in zama shuga mai bada umurni."
"Allah dai ya cika mana burinmu Uwata domin komi da kikaga inayi to dan ingantuwar rayuwarki ne, kada k'asa ya rufe idona Malam ya handame komi ya koramin."
"Godiya na ke Mamana amma dan Allah ki kyautatawa Baba zato."
"To naji amma ki sani ba godiya a tsakanin Uwa da 'ya sai addu'ar samun babban rabo ranar lahira."
"Allah ya biyaki da gidan aljannatul firdausi."
"Amin ya rabbi."
"Yawwa Mama wai ya muke da Baba Abdul Ganiyu nan?"
Shiru ta yi har na cire rai da jin amsar tambayar sai kawai na kamo hannunta na langab'e kai cikin sanyin murya na ce "Kiyi hak'uri Mama idan sanarmin zai takuraki wallahi na fasa jin nasabanmu da shi."
"Zan sanar da ke amma a takaice domin zuwa yanzu ya kamata ki soma sanin ya ni ke da duk wanda kika ganmu tare."
"To Mama Ina saurarenki."
"Kinga Baba Abdul Ganiyu abokin mahaifina ne na k'ud da k'ud amma shi bayarbene ya yin da Mahaifina Abdullahi ya zamo Hausa Fulani d'an asalin garin sokoto. Sadda Allah ya nufa zan zo garin Kaduna da zama Baba Abdul Ganiyu ne ya had'ani da Baba Umaru wanda shi kuma ya zamo abokin kasuwancinsa daga arewa zuwa kudu. Baba Umaru ya rik'e ni tamkar shi ya haifeni dan haka wad'an nan mutanen biyu bani da kamarsu in kika cire mahaifana, Abdaullahi da Hadiza da kuma ke 'ya ta."
"Allah ya kai haske k'abarinsu."
"Amin."
"To Mama ina danginmu na Sokoto?"
"Suna nan."
"Me yasa ba...
"Uwata kada ki tsananta bincike domin na yi miki alk'awarin sanar da ke komi idan lokacin ki sani ya yi."
"To Mama na kame bakina."
"Da kyau, idan zaki sha furanki tana cikin fridge."
Murmushi na yi jin ta sauya akalan zancen.
"Ko sai zuwa dare zaki sha?"
"A'a zan sha yanzu, bari in d'ibo kad'an."
"Aha, sai ki zuba zuma zaifi dad'in d'and'ano akan saka siga."
"To Mamana."
Ina shan furar na dubi Mama wacce ke gyara zogale zata dafa mana wanda Hajiya Inna ta aikomin da shi domin na ce kwad'onsa na ke son ci da dare.
"Ya dai Uwata?"
Lashe lips na yi na amsa da "Ina burin na ganni cikin danginmu duk da bana son hayaniyar jama'a amma son ganina tsakanin kakanni, iyaye da abokanan wasa maza da mata wannan babban buri ne da ya jima a ruhina sai dai idan na nutsa cikin tunani sai wani lamari da na rasa gane kansa ya zo ya shafe burin ta hanyar jefani cikin fargaba har sai na ji ban son ganina cikin dangin baki d'aya sai na rik'a jin dama banzo duniyar ba."
Banza Mama ta yi da ni domin tunda na fara maganar bata nuna zata furta kalma ba. Na matso jikinta na jingina ina sauke numfashi, still bata kulani ba sai na gyara zama a gabanta na ce "Zanso idan mun dawo Kwara mu tsaya a Sokoto inda halima ki barni a can na zaga dangi na birni da karkara dan samun ladar zumunci."
"Allah ya kaimu lokacin amma zuwa Sokoto ba yanzu ba saboda ko wani tafiya nasa daban na ke son yi."
Jinjina kai na yi ina wasa da ganyen zogalen da ta tsinke.
"Uwata da magana a bakinki ko?"
Kallonta na yi ta waremin idanu cikin jiran abinda zan fura sai na girgiza kai tare da tashi na shige d'akina ina murmushi.
"Nana Khadijatu kenan, Uwata ta kaina, nasan damuwarki bai wuce zantukan da kika gamayi na yi banza da ke, affuwan Uwata bana da jarumtar biye miki ne."
Mama ta furta tare da mik'ewa ta shige madafi.
***
*Asabe da Hinde.*
Asabe ce zaune a k'ofarta ta tsefin kai wanda da kyar ta ke kamo bindin korar saboda tsabar tsufar da ya yi gami da datti, Hinde kuwa tana nesa da ita tana gyaran gyad'an miya.
"Hinde wallahi duk tijarar da na gani gami da iziya a hannun masu babbak'un kaya ban saduda ba ko misk'ala zarratin domin sai naga bayan Hurera kafin k'asa ya rufe idanu zanji dad'in a raina."
"Yaya tamkar kin shiga zuciyata, tunanin da na keyi kenan yanzu, wallahi da abin na ke kwana na ke tashi musanman mijin da Uwani zata aura, gashi mutumin kirki sam abinsa bai rufe masa idanu ba da ganinsa ya san abinda yakeyi, hak'ik'a zataji dad'in zama da shi, Hurera zata huta fiye da zatona, zata tabbata cikin jin dad'i mu kuma 'yan maula domin ko Malam sai yarda ta yi da shi dama ya lafiyar giwa balle ta yi hauka."
"Hinde kin sosamin inda keyimin k'aik'ayi, billahil azim ji na ke tamkar in wayi gari acemin Alhaji Muhseen ya mutu na rantse da sai na yi rawa da juyi dan Hurera taga samu taga rashi kenan a lokaci d'aya."
"Ai idan zaki bani had'in kai na rantse sai dai ya auri wata amma ba Uwani ba, domin nafi jin takaicin ni'imar da zata shiga muna kallo tamkar tumakai."
"Ina tare da ke 'yar uwa, tunda mun samu ya yi mana yayyafin naira muyi jari to mu had'esa kaf mu fantsama neman sa'ar datse wannan bak'ar alak'ar domin ba zan kirashi da fari ba."
Wata dariya Hinde ta b'arke da shi wanda ya bawa Asabe tsoro ta shige d'akinta da gudu biyo bayanta Hinde ta yi tana cigaba da dariyar tamkar ta sami tab'in hankali nanko ras ta ke tsabar jin dad'in kalaman Asabe ce.
***
"Yaya Aliyu kabi umurnin Hajiya domin ta yi rantsuwa ba zaka auri kowa ba sai Amira."
Numfashi ya sauke ya kafe Salma da ido "Me Hajiya ta aikata a gidan su Khadija wanda ya janyo ta sakani a black list ko na kirata bai shiga na ganta a online na yi mata magana ta yi blocking d'ina na sanja layi na kirata tana jin muryana ta kashe na tura sak'o ta wayar K'awarta Fanta ta k'i dawomin da amsa, maza sanarmin da abinda Hajiya ta aikata musu da ya janyo na fuskanci wannan lamarin.
"Kayi hak'uri Yaya ba zan iya sanar maka ba saboda nayiwa Hajiya alk'awarin kame bakina."
"Zanje gidan yau da kaina in yaso zanji komeye a bakinta."
"Kada kaje saboda Mamanta ta fusata zuwanka zai zamo zubewar mutuncin Hajiya ce domin ta ce idan ta isa da kai ta hanaka zuwa gidan, kenan zuwanka tamkar Hajiya bata isa da kai ba ne."
"Duk me ya kawo wannan zantukan daga zuwa dubiya?"
"Wanna tambayoyin Hajiya ke da amsoshinsu kuma ya kamata ta amsa maka domin ina zargin da abinda ta ke b'oye mana wanda ya shafi Khadija domin da kunnuwana na ji aunty Zainab na yi mata rantsuwa akan wani abu na so jin abin amma Hajiya ta sauya zancen tare da rufeni da fad'a dan na nemi k'arin bayani."
"Zainab zan sama naji munafuncin da ta k'ulla domin tunda ta gano Khadija ce wacce na ke so na hango tsanar lamarin a idanunta, kuma wallahi idan ta yi sanadin rabani da wacce na ke so rayukanmu zasu b'aci matuk'ar b'aci."
"Kabi komi a sannu Yaya amma ina ji a jikina Deejah ba matarka ba ce."
"B'acemin da gani ko in nad'a miki duka! Wawiya kawai wacce ba'ajin alkhairi abakinta sai sharri."
"Ni d'in Yaya?"
"Zaki fice ko sai na zubda miki da hak'ora?"
Cikin fushi Salma ta bar d'akin tamkar zata saka kuka.
"Ina cikin tsaka mai wuya ni Aliyu."
Ya furta tare da sake dialing number Fanta haka ya gama ringing ba'a d'aga ba, kwanciya ya yi na cigaba da kiran wayar amma baiyi dacen an d'auka ba balle ya rok'eta ta had'ashi da Deejah.