← Book details Damuwata Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 36 OF 43

Sashe 36

Damuwata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

*Duk za'a samesu a farashi mai rahusa, mai buk'atar d'aya ko sari a tun-tub'emu a wad'annan numbers d'in 08132166848 ko 08147491137. Sai munjiku.*
[11/3, 11:29 PM] 💘: DAMUWATA ( Sanin abin adona)
By Mrsjmoon

E.W.F.

https://youtu.be/v9iNYDvS8JM

Pls 'yan uwa ku dannamin subcribe a YouTube d'ina, nagode.

Page 20.

Tsam na yi ina nazarin zantukansu tare da son gano abinda Mama ke b'oyemin amma iya hangena na kasa gano abin, lamarin da ya sanya sanjawan bugun numfashina ya soma fita da sauri batare da na san dalilin faruwarsa ba, na yi hanzarin kulle bakina gudun kada sautinsa ya bayyana su gano na farko har na jiyo hirarsu tunda na gano basa so inji.

Hakan danayi ya sanya na sark'e cikin fitar da tari mai k'arfi. A tare suka iso gareni, Mama ta soma shafamin baya cikin jeramin sannu Hajiya Inna kuwa ta kafamin kofin ruwa a baki, bayan tarin ya tsaya sai na tsirawa Mama ido ta ware nata na lumshe nawa tare da motsa leb'b'ana.

"Me kike son sanarmin Uwata?"

"Godiya na ke son yi muku."

Na furta duk da ba shi ne a raina ba.

"Da akayi me?"

"Kula da ni batare da gajiyawa ba."

"Wannan hakkin mu ne Uwata dan haka babu godiya a tsakaninmu, kinji ko?"

Motsa kai na yi ina saukewa Hajiya Inna murmushi wacce ke binmu da kallo cikin sigan tausayi.

'Da magana a bakinki Hajiya Inna kuma zan jiyo shi da yardan Allah.'

Na ambaci hakan a raina tare da zamewa dan in kwanta saidai Mama ta hanani hakan inda ta umurceni da in sauka in d'auro alwalla inyi Sallar Subahi. Na sakko ina cije baki saboda jirin da baigama sakina ba. Ita ta taimakamin na shiga toilet, tana tsaye na yi tsarki tare da d'auro alwalla muka fito saboda ta san halina da son wanka ina iya k'ara sanyawa jikina ruwan sanyi da zarar ta bani wuri.

A Zaune na gabatar da sallah a cikin sujata na k'arshe na rok'i Allah da ya bayyanamin abinda Mama ke b'oyemin ko da jinsa ko ganinsa zai zamo ajalina ne.

Na yi wannan addu'ar ne saboda yarda na ke son sanin lamarin.

Haka nan kawai naji b'acin rai ya kanai-naye ruhina cikin sekonni bayan na d'ago daga sujjadar, koda na sallame sallar sai na koma saman gado na kwantar tare da juyawa su baya.

"Uwata jikin ne?"

"A'a."

Na amsa a tak'aici abinda ban tab'a yi mata ba kenan bata amsa cikin rashin girmamawa.

"To tashi kisha tea kafin Likita ya shigo."

"Barci na ke ji Mama."

Wannan karan cikin rawar murya na amsa mata.

Hannunta na ji cikin sumata sai na sake lafewa batare da na juyo ba.

"Uwata na san kina tare da damuwa b'oyenmin kike yi."

Tashi zaune na yi cikin son dai-daita fuskata zuwa wal-wala.

"Kada ki wahalar da kanki Uwata wurin layancewa domin na jiyo dirin damuwarki a k'irjina, oya maza sanarmin da shi tun ban sab'a miki ba."

Dariyar dole na sanya duk dan in nuna mata ban tare da damuwar komi na d'aga yatsa na nuna Hajiya Inna wacce ta bud'e baki tare da zaro idanu jin abinda Mama ta ambata ina cewa "Kalli Hajiyarki k'uda na shirin fad'awa bakinta."

Harara ta zabgamin na kamo hannayenta na rungume a k'irjina ina doka murmushi.

"Harbawan me zuciyarki ta ke yi haka da sauri?"

"Wai tana neman ki aminta da kalaman d'iyarki ce na bata tare da damuwan komi."

"Na amince Uwata bata cikin damuwa tunda muna tare da ita a ko da yaushe kuma zamu cigaba da kasancewa da ita har zuwa sadda k'asa zai rufe idanunmu tare da burin had'uwa da juna a gidan Aljanna."

"Allahumma Amin Mamana."

"Wannan k'auna taku Hurera na bani tsoro anya lamarin nan kuwa mai b'ullewa ce?"

"Inna bakomi sai khairan, wannan shi ne ni'imar da Allah ya dasa a cikin shayar da 'ya'ya nono ko da ba...

Sai kuma ta yi shiru tare da mik'ewa ta nufi hanyar toilet.

"To Allah ya tabbatar da khairan mara iyaka Hurera."

"Amin tsohuwar su Mama."

Na amsa cikin tsokana.

"Fad'i ki k'ara da ihu tsohuwar su ce ko wani ya ce taki ce?"

"Eh kince dole sai na kiraki da Inna kinga kenan kin saka dole kin zama tsohuwata."

"Takwara ciwon nan naki yazo miki da son surutu."

Lumshe ido na yi bance komi ba itama daga haka bata sake magana ba.

Ganin Mama ta ji bata fito ba sai Hajiya Inna ta hadamin tea mai kauari ta tsareni saida na shanye. Lokacin dMama ta fito kanta k'asa dan tak'i kallona saina nuna tamkar ban lura da b'oyemin fuskanta da ta ke yi ba na d'auko apple na soma gutsira cikin zantukan zucci masu yawa a game da bak'on lamarin da na kasa gano kansa balle tushensa.

"Kunga tafiyata na koma gida na huta tunda duk kun warke."

Hajiya Inna ta ambata cikin kallon Mama wacce da alama ta yi nisa cikin tunani bata jiyo maganar ba.

"Ayya Hajiya Inna ki jira mu tafi tare tunda zamu sami sallama yau insha Allah."

"Takwarata su Malam na kan hanya dawowa to ina son zan sama musu wani abu kafin su iso."

"To tafi na baki izini tafi."

"Ja'ira kin samu lafiya fa bakin ya bud'e da tsokana kala-kala."

"Eh dai tafi sai nazo kwance jikka."

"To amma dai ki tabbatar kin maida jikinki saboda Malam bai sakewa ramamman mace fuska dan na tabbata wannan manya idanun naki da suka sake fitowa zasu firgitamin miji tsaf."

Kafin in bata amsa ta fice da sauri tana dariya Mama na tayata domin ta maido da hankalinta kanmu.

"Hajiya Inna kenan ta san kan iya tsokana."

"Uwata ke ce Inna ke sakewa irin haka duk cikin jikokinta saboda bata yarda da wasan jika da Kaka ba gudun rashin kunya irin na wasu jikokin sannan wasan kansa wasu Malaman sunce baya cikin musulinci."

"To Mama me yasa ni kad'ai takeyiwa?"

"Ita zata amsa miki wannan tambayar kam."

"Mama wai me...

Dawowar Hajiya Inna yasa ban furta abin da na yi niyya ba, muka zuba mata ido ta iso ta ja hannun Mama suka fice zuwa can ta dawo ita d'aya tare da d'aukarwa Mama hijab shima bata jima ba ta dawo ta zauna saman kujerar roba a gabana muka zubawa juna ido, numfashi ta ja ta soma magana "Nana Khadijatu Allah ya jarabceku da rayuwa k'ark'ashin baudd'en mutum sam Malam Hadi bai aiki da saninshi a matsayinsa na babban Malamin da ake ji da shi."

"Me ya faru kuma?"

"Ina fita na had'u da Alhaji Muhseen yazo tafiya da Mamanki wai ya tsayar da matarsa a waje sai sun nemi gafarar Hurera kafin kafafunsu ya shiga masa zauren gida sannan ya tara mutanen unguwa nata fesa musu lamarin da bai kamata ba domin ance duk wanda ya rufawa wani asiri to Allah zai rufa masa."

"Duk me ya janyo hakan Inna?"

Tsit na yi jin bak'in labarin abin kunyar da matar Baba tare da 'ya'yansa suka tafka.

"Dan rashin kyautawa kam sunyisa Takwarata amma ai fad'ar cikin gida ne bai kamata ya bari na waje su ji ba ko dan mumbarin da ya ke hawa bada sallah."

"Abin kunyar ce kam hakan Inna kuma ina tabbatar miki da wata manufa nasa yasa shi kiran Mama."

"Abinda itama ta ke sanarmin kenan dan ta nuna bazata je ba na bata kwarin guiwa."

"Ko me ye dai Allah na tare da masu neman taimakonsa."

"Wannan haka ya ke Khadijatu, masu neman taimakon Allah cikin lamarinsu basa tab'a ganin bak'in cikin ratuwa."

"La shakka babu Inna."

Munyi shiru zuwa can Hajiya Inna ta soma yimin hira inda yawancinsa akan yarda rayuwa ta ke juyawa al'umma ce musanman wad'anda suka d'auki duniya da fad'i. Knocking a kayi Inna ta amsa da a shigo matar Kawu Habibu ne tare da Aliyu Muktar, ware ido na yi shi kuwa ya tsaya a k'ofa yana jefomin murmushin k'auna, sunkuyar da kai na yi jin Zainab na tsokanarsa, bai kulata ba ya iso gaban Hajiya Inna ya sunkuyar har k'asa ya gaisar da ita ta amsa cikin tambayar sa mahaifiyarsa.

"Hajiya ya mai jikin?"

"Gatanan ta warke tunda bakiyi tunanin zuwa cikin lokaci ba sai da kikaji mijinki zai dawo gudun kada ya saukemiki halin nasa yasa kika zo to angode amma ki sani shi kyautatawa abune mai kyau kuma lalura na kan kowa dan Khadijatu bata zo miki barka ba bai zama hujjar da zaki riketa ba domin kinfi kowa sanin halinta na rashin son jama'a."

"To Hajiya ai duk rashin son jama'arta sai ayi mata fad'ar rik'o da zumunci tunda duk abu d'aya muka aikata har gara ni da ita."

Shiru Hajiya Inna ta yi cike da takaicin domin abinda ta tsana kenan ta nunawa mutun kurensa ya k'i amsa.

"Hajiya Inna a yi hak'uri idan na k'ara samun sauk'i zanzo ganin Baby  musanman tabbas na san ban kyautaba, Ina neman affuwan Matar babban mutum mai halin girma."

"Allah ya yi miki albarka Takwarata."

"Amin."

Muka amsa tare da Aliyu wanda ya koma gefe yana saurarenmu tunda ya gama gaisar da Inna.

"Bari in lek'a gida Takwara."

"To Inna sai kin dawo."

"Aha, ke kuma idan kinga dama ki zauna da ita kafin wani cikin ni da Hurera ya dawo."

"Agaskiya ba zan zauna ba saboda jego na keyi nadai zo  dubata kada ya zamemin abin magana wanda duk da hakan gashinan ban tsira ba saida akayimin luguden labba."

"Matar Kawu ki iya bakinki fa, Inna ba sa'ar yinki ba ce dan haka ki tauna kalaminki kafin ki furta in har kina son gamawa lafiya."

"Idan ank'i yin hakan fa?"

Bud'e baki na yi zan bata amsa Inna ta d'agamin hannu tare da komawa ta zauna.

"Zaki iya tafiya tunda kin gaisar da itan."

"Ok na barku lafiya, Allah ya k'ara affuwa."

Banza mukayi da ita ta fice abinta ba damuwar komi.

"Hajiya dan girman Allah kiyi hak'uri, halin Zainab sai ita sam bata san ya kamata ba ko a family haka ake fama da ita bata da kunyar gayawa babba duk kalamin da ya fito bakinta."

"Kada ka damu Aliyu, wannan ba sabon abu ba ne, Allah dai ya ganar da ita."

"Amin."
Chapter 36 · 0% Book details