Sashe 18
Damuwata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Nufina ban yarda kiyi masa wannan k'aunar da na gani a idanuwanki ba tun bai soma takowa k'ofar gidanku zance ba sannan bama shi ba kowaye ya furta miki kalman k'auna ban amince ki zurfafa son sa ba, kiyi masa dai-dai misali da fatan kin fahimce ni?"
"Eh Mama."
"Da kyau tashi kije wurin su Fanta kada abarsu su kad'ai."
Fitowa na yi na samu sun gyara wurin sun shige d'akina, ina shiga Fanta ta rangad'a gud'a na ja baya idanu waje suka tafa ita da Beebah, tsaki na ja cikin raina na janyo stool na zauna na zuba musu ido, iska Beebah ta huramin na kullesu da sauri.
"Wani sak'o Uncle ya sanarmiki ki fad'amin?"
"Yana muradin da ki zama matarsa ta sunnah uwar d'iyoyinsa, kin amince?"
Numfashi na sauke ahankali.
"Zanyi tunani."
"Ai baki isa ba, eh kawai na ke son ji yanzun nan ba sai anjima ba."
"Kina farin ciki da ayiwa yayarki kishiya kenan?"
"Eh."
Ta amsamin kai tsaye.
Murmushi na yi dan sam banji mamaki ba.
"To ni ina tsaron kishi da ita, ki sanarwa Uncle da haka."
"Ma'ana dai kin amince zaki auresa Aunty Nafisa ce matsalarki?"
Dan Allah Beebah ki fahimceni mana, ke fa Aliyu ya aiko amma yanzu kinayi tamkar baki san komi ba."
"Ke d'in allurar cikin ruwa ce mai rabo ka d'auka dan haka Deejah sanin mijin sai Allah, wata k'ila daga Aliyu har Uncle ba mijinki cikinsu sai dai abinda na ke son ki sani shi ne mace bata tsaida mutum d'aya ta ce shi zata aura, tana iya yin samari sama da biyar kuma sai kiga wani daban ya fito ya aureta, yanzu dai ki nemi zab'in Allah cikinsu dama wanda zasuzo nan gaba."
"Tabbas maganar Sister Beebah gaskiya ne insha Allah Deejah sai kin had'a goslow a k'ofar gidan nan masu gulman kin rasa masoyi suji kunya."
"Uhm Fanta kenan, kidai tayani addu'ar samun miji nagari kawai, masu gulma kuwa banda lokacinsu, su aiki ya sama."
"To Allah ya bamu baki d'aya."
Beebah ta ambata a hankali.
"Amin."
Muka amsa atare da Fanta.
"Deejah wallahi inajin murna ainun ganin yarda kika soma tara masoya damuwarki akan rashinsu ya zamo tarihi."
"Nagode Beebah, ni kaina ina cike da mamakin lamarin."
"Komi fa lokaci ne K'awata."
"Haka ne kam Aminiyata."
"Aha ansoma nuna wariyar ba."
Beebah ta ambata cikin zabgo musu harara.
Dariya muka sanya har ita.
"Yau su Bintu na hanya ya kamata in dafa musu abincin tarba."
"Yes Deejah tafi mu san abiyi musu dan yau Aunty Nafisa bata cikin kuzarin dafa komi shi yasama inaga Uncle ya ce kiyi masa girki."
"Sabida ta ganni tare da shi ko?"
"Oho mata dai."
Fanta ta amsamin cikin zunkud'a shoulder. Kafin in sa ke magana ta fice. Beebah na kalla ta saukemin murmushi ta ce "D'azun Aunty taga fitarku ta yi nufin zuwa ciwa Mama mutunci kafin ta iso Fanta ta kirani sai na tareta a waje na maidata gida amma dan Allah kada hakan ya baki tsoro domin hausawa sunce auren da aka soma samun rikici yafi k'wari."
"Uhm wannan kawai zance ne ba tabbas a cikinsa."
"Ni dai na rok'eki domin Allah da Manzonsa kada ki bijirewa muradin Uncle."
"Beebah na rasa gano abinda yasa kuna 'yan uwa na jini ga Aunty Nafisa amma kuke goyon bayan mijinta da yayi mata kishiya."
"Tashi muje idan su Bintu sun iso sai muyi maganar a gabansu kiji kalamin bakin kowa akai, ina ganin zakifi gamsuwa."
Tashi na yi muka fito daidai lokacin Baba na shigowa, dank'e hannuna Beebah ta yi jikinta na rawa, kallonta na yi na kuma sauke idanu kan Baba wanda ya shigo a fusace
"Innalillahi wa Inna ilaihin."
Na ambata a hankali.
"Ubanki kika tsaya kallo mai siffan aljannu?."
Na tsinkayi muryan Baba saman kaina, ja baya na yi cikin girgiza kai.
"Hurera!"
Ya kwallawa Mama kira. Bata amsa ba ya kuma kiranta, sai da Baba ya kirata sau hud'u sannan ta fito tana murza ido bisa alamu barci ta soma, kallon da Mama ta saukemin yasa na ja hannun Beebah muka shige kitchen wurin Fanta.
*TALLA.*
*Ina kuke Mata 'yan kwalisa masu bawa fatarsu 'yancinta musanman babban kadararku wato fuska. To ga dama ta zo muku cikin sauk'i wato samun kayan gyarar fuska da jiki mai inganci na organic wanda aka samar da su da abubuwa masu nagarta. Duk wacce K'uraje, Tabbai, Sunburn, kyafsi suka b'atawa fuska muna da maganin da fuskanta zai dawo fes, sumul, rangad'ad'au. Haka a fannin fatar jiki shima muna da kayan da zaiyi laushi, sulb'i tare da haske mai kyau. Ga kayan kamar haka:*
Sabulu (molato and black soap)
Scrub
Face cream
Oil
Body lotion
Shower gel
Kulachan
Humra (White and black)
Turaren tsugunon
Turaren kaya
Turaren wuta na d'aki
Garin d'a'a (domin k'an-k'aro martaban aure a turaka)
*Duk za'a samesu a farashi mai rahusa, mai buk'atar d'aya ko sari a tun-tub'emu a wad'annan numbers d'in 08132166848 ko 08147491137. Sai munjiku.*
[10/23, 2:05 PM] 💘: DAMUWATA (Sanin abin adona)
By Safiyya (Mrsjmoon)
E.W.F.
Page 11.
"Kiyi hak'uri Deejah amma mahaifinki ya cika fad'a, wallahi tsoro ya bani ganin yarda ya shigo a fusace sannan d'azun da safe na sunkuya ina gaisheshi amma ko kallo ban isheshi ba, na yarda wannan halayyan nashi ya sanya baku jituwa."
"Sister Beebah halayyan Baba halitta ce dan koni ada tsoronsa na ke ji amma tunda na fahimci haka Allah yayoshi sai na saba kamar yarda Aminiyata ya bi jikinta."
"Uhm ku mumaida hankali a kan aikinmu kunsan kowa abin da tafi so za'a dafa mata."
Na datse zancen saboda yarda na ke jin b'acin rai kuma ban son su gano hakan.
"Hakan ba zai yiwuba kawai muyi musu girki d'aya wanda zasuci baki d'ayansu."
"Nima hakan naga yafi Sister."
"Ki tafi ku huta insha Allah kafin su iso na kammala komi."
Na kuma ambata cikin tsare gira.
"Baza'ayi haka ba Fanta tafi ki d'ebo komi a gida kizo ayi amfani da shi."
"Idan ta d'ebo kada tazo dashi gidan nan, insha Allah bazamu rasa abin yin amfani ba duk da muna talakawa."
"Ya Salam, please Deejah ki fahimce ni mana."
"Beebah dan Allah kiyi shiru muyi abinda ya kamata dan banjin ina da natsuwar fahintarki ba."
"Tam na yi shiru Aunty."
"Ko ba Aunty ba."
Dariya suka kyalkyale da shi ganin yarda na tsuke fuska.
"Fushin baiyi miki kyau ba Aminiyata."
Murmusawa na yi.
"Yawwa ko ke fa sai annuri na kuma cika kyak-kyawar fuskanki."
"Ban da zagi fa Aminiyata."
"Allah ba zancen zagi domin ke kanki kinsan mai kyauce tamkar tauraruwa cikin dubbab taurari."
"Kinyi na kud'in ki wallahi."
"Ai gaskiya Fanta ke fad'a ke d'in tubarkallah masha Allah, tamkar 'yar buzaye ko Shuwa Arab."
"Eh wallahi Sister Beebah."
"Dan Allah ku barmin kunnuwa su huta."
"Ank'i sai kin sanar da mu nasabanki daga wani yare kika fito."
"Yaren Baba mana Hausa Fulani."
"Amma kinsan Allah ko a farce baki kama da Baba haka 'yan uwanki duk kinfisu kyau duk da suma da farare cikinsu amma naki hasken na dabanne."
"To ni bakuga yarda Mama ke da haske ba, ita na d'auko."
"Eh gaskiya hasken Mama kikayo aminiyata amma duk da haka kinfita fari."
"Eh nafita kam amma ai munyi kama."
Karkacewa Fanta ta yi tana k'aremin kallo na kai mata duka ta ja baya cikin cewa "Kuna kama a halittan idanunku da kyawun diri amma in banda nan ban hango ta inda kukayi kama ba."
"Kai Fanta ki duba dai da kyau hatta madai-daicin bak'insu iri d'aya ne."
"Kai Beebah a she haka kika k'arewa Mama kallo?"
"No a photonku na tantance."
Banza na yi da su ganin in na biye musu ba zamuyi abinda ke gabanmu ba.
Bintu Alale, Firdausi jelop d'in macaroni jelop sai Safina shinkafa da miya. Komi dai-dai mukayi yarda bazai zamo anyi albazaranci ba. Mun jere abincin a d'akina muka zauna muna hira Fanta ta kalli Beebah ta langab'e kai.
"Me ye malama?"
"Dan Allah Sister idan ya iso ki kulashi kinga domin ke zaizo"
"Wai Yaya Abdallah zai kawo su?"
"Eh."
Dogon tsaki Beebah ta ja tare da mik'ewa zata fice.
"Kada ki yi haka sabida ance bak'onka Annabinka."
"Fanta wallahi inda na san munafuncin da kuka k'ulla kenan tabbas da bazan jirasu ba zan wuce amma ko yanzu ba zaku sami abinda kuke so ba na rantse."
"Eh mun yarda amma dan Allah ki kulashi cikin walwala in ya wuce sai kiyi mana duk masifar da kika so."
Shiru ta yi, Fanta ta janyo hannunta ta zaunar gefen katifa tana yi mata magana a kunni, tagumi ta zabga na yi gyaran murya ta kalleni na girgiza mata kai, murmushi ta saukemin wanda a fili na dole ne saboda hakan ya bayya a saman fuskanta.
"Me ke faruwa, kuke 'yan b'oye-b'oye?"
Na cillowa Fanta tambayar duk da shiga lamarin rayuwar mutane ba halina ba ne.
"Gata nan kiyi mata nasiha ta daina wulak'anta mana Yaya, saboda shi tak'i bin su Bintu sada zumunta shi ne ya biyosu domin ya ganta dan ta yanke alak'a dashi tsawon wasu watanni, ta daina d'aukan wayarsa tayi blocking nasa a k'arshema ta saka shi a black list, in kuma ya kirata da wayar Mamansa ko k'anninsa tana jin muryansa zata kashe wayarta baki d'aya."
"Innalillahi, me ya yi zafi haka?"
"Wai bazata auri mai mata ba saboda tana tsoron jarabar matarsa mai hali irin na Aunty Nafisa sak."
Wani zabura Beebah ta yi tayo kan Fanta, ita kam ta kwasa da gudu ta fice zata rufa mata baya na rik'eta cikin tsare gira na ce "Ke kin gujewa auren tashin hankali amma ni kin dage sai na yi?"
Numfashi ta yi ta saukewa cikin alamun fushi, zuwa can ta yi gyaran murya sai lokacin na saki hannunta dana kama. Ruwa ta d'auka ta sha sosai sannan ta k'ara yin gyaran murya ta soma magana cikin natsuwa.
"Eh Mama."
"Da kyau tashi kije wurin su Fanta kada abarsu su kad'ai."
Fitowa na yi na samu sun gyara wurin sun shige d'akina, ina shiga Fanta ta rangad'a gud'a na ja baya idanu waje suka tafa ita da Beebah, tsaki na ja cikin raina na janyo stool na zauna na zuba musu ido, iska Beebah ta huramin na kullesu da sauri.
"Wani sak'o Uncle ya sanarmiki ki fad'amin?"
"Yana muradin da ki zama matarsa ta sunnah uwar d'iyoyinsa, kin amince?"
Numfashi na sauke ahankali.
"Zanyi tunani."
"Ai baki isa ba, eh kawai na ke son ji yanzun nan ba sai anjima ba."
"Kina farin ciki da ayiwa yayarki kishiya kenan?"
"Eh."
Ta amsamin kai tsaye.
Murmushi na yi dan sam banji mamaki ba.
"To ni ina tsaron kishi da ita, ki sanarwa Uncle da haka."
"Ma'ana dai kin amince zaki auresa Aunty Nafisa ce matsalarki?"
Dan Allah Beebah ki fahimceni mana, ke fa Aliyu ya aiko amma yanzu kinayi tamkar baki san komi ba."
"Ke d'in allurar cikin ruwa ce mai rabo ka d'auka dan haka Deejah sanin mijin sai Allah, wata k'ila daga Aliyu har Uncle ba mijinki cikinsu sai dai abinda na ke son ki sani shi ne mace bata tsaida mutum d'aya ta ce shi zata aura, tana iya yin samari sama da biyar kuma sai kiga wani daban ya fito ya aureta, yanzu dai ki nemi zab'in Allah cikinsu dama wanda zasuzo nan gaba."
"Tabbas maganar Sister Beebah gaskiya ne insha Allah Deejah sai kin had'a goslow a k'ofar gidan nan masu gulman kin rasa masoyi suji kunya."
"Uhm Fanta kenan, kidai tayani addu'ar samun miji nagari kawai, masu gulma kuwa banda lokacinsu, su aiki ya sama."
"To Allah ya bamu baki d'aya."
Beebah ta ambata a hankali.
"Amin."
Muka amsa atare da Fanta.
"Deejah wallahi inajin murna ainun ganin yarda kika soma tara masoya damuwarki akan rashinsu ya zamo tarihi."
"Nagode Beebah, ni kaina ina cike da mamakin lamarin."
"Komi fa lokaci ne K'awata."
"Haka ne kam Aminiyata."
"Aha ansoma nuna wariyar ba."
Beebah ta ambata cikin zabgo musu harara.
Dariya muka sanya har ita.
"Yau su Bintu na hanya ya kamata in dafa musu abincin tarba."
"Yes Deejah tafi mu san abiyi musu dan yau Aunty Nafisa bata cikin kuzarin dafa komi shi yasama inaga Uncle ya ce kiyi masa girki."
"Sabida ta ganni tare da shi ko?"
"Oho mata dai."
Fanta ta amsamin cikin zunkud'a shoulder. Kafin in sa ke magana ta fice. Beebah na kalla ta saukemin murmushi ta ce "D'azun Aunty taga fitarku ta yi nufin zuwa ciwa Mama mutunci kafin ta iso Fanta ta kirani sai na tareta a waje na maidata gida amma dan Allah kada hakan ya baki tsoro domin hausawa sunce auren da aka soma samun rikici yafi k'wari."
"Uhm wannan kawai zance ne ba tabbas a cikinsa."
"Ni dai na rok'eki domin Allah da Manzonsa kada ki bijirewa muradin Uncle."
"Beebah na rasa gano abinda yasa kuna 'yan uwa na jini ga Aunty Nafisa amma kuke goyon bayan mijinta da yayi mata kishiya."
"Tashi muje idan su Bintu sun iso sai muyi maganar a gabansu kiji kalamin bakin kowa akai, ina ganin zakifi gamsuwa."
Tashi na yi muka fito daidai lokacin Baba na shigowa, dank'e hannuna Beebah ta yi jikinta na rawa, kallonta na yi na kuma sauke idanu kan Baba wanda ya shigo a fusace
"Innalillahi wa Inna ilaihin."
Na ambata a hankali.
"Ubanki kika tsaya kallo mai siffan aljannu?."
Na tsinkayi muryan Baba saman kaina, ja baya na yi cikin girgiza kai.
"Hurera!"
Ya kwallawa Mama kira. Bata amsa ba ya kuma kiranta, sai da Baba ya kirata sau hud'u sannan ta fito tana murza ido bisa alamu barci ta soma, kallon da Mama ta saukemin yasa na ja hannun Beebah muka shige kitchen wurin Fanta.
*TALLA.*
*Ina kuke Mata 'yan kwalisa masu bawa fatarsu 'yancinta musanman babban kadararku wato fuska. To ga dama ta zo muku cikin sauk'i wato samun kayan gyarar fuska da jiki mai inganci na organic wanda aka samar da su da abubuwa masu nagarta. Duk wacce K'uraje, Tabbai, Sunburn, kyafsi suka b'atawa fuska muna da maganin da fuskanta zai dawo fes, sumul, rangad'ad'au. Haka a fannin fatar jiki shima muna da kayan da zaiyi laushi, sulb'i tare da haske mai kyau. Ga kayan kamar haka:*
Sabulu (molato and black soap)
Scrub
Face cream
Oil
Body lotion
Shower gel
Kulachan
Humra (White and black)
Turaren tsugunon
Turaren kaya
Turaren wuta na d'aki
Garin d'a'a (domin k'an-k'aro martaban aure a turaka)
*Duk za'a samesu a farashi mai rahusa, mai buk'atar d'aya ko sari a tun-tub'emu a wad'annan numbers d'in 08132166848 ko 08147491137. Sai munjiku.*
[10/23, 2:05 PM] 💘: DAMUWATA (Sanin abin adona)
By Safiyya (Mrsjmoon)
E.W.F.
Page 11.
"Kiyi hak'uri Deejah amma mahaifinki ya cika fad'a, wallahi tsoro ya bani ganin yarda ya shigo a fusace sannan d'azun da safe na sunkuya ina gaisheshi amma ko kallo ban isheshi ba, na yarda wannan halayyan nashi ya sanya baku jituwa."
"Sister Beebah halayyan Baba halitta ce dan koni ada tsoronsa na ke ji amma tunda na fahimci haka Allah yayoshi sai na saba kamar yarda Aminiyata ya bi jikinta."
"Uhm ku mumaida hankali a kan aikinmu kunsan kowa abin da tafi so za'a dafa mata."
Na datse zancen saboda yarda na ke jin b'acin rai kuma ban son su gano hakan.
"Hakan ba zai yiwuba kawai muyi musu girki d'aya wanda zasuci baki d'ayansu."
"Nima hakan naga yafi Sister."
"Ki tafi ku huta insha Allah kafin su iso na kammala komi."
Na kuma ambata cikin tsare gira.
"Baza'ayi haka ba Fanta tafi ki d'ebo komi a gida kizo ayi amfani da shi."
"Idan ta d'ebo kada tazo dashi gidan nan, insha Allah bazamu rasa abin yin amfani ba duk da muna talakawa."
"Ya Salam, please Deejah ki fahimce ni mana."
"Beebah dan Allah kiyi shiru muyi abinda ya kamata dan banjin ina da natsuwar fahintarki ba."
"Tam na yi shiru Aunty."
"Ko ba Aunty ba."
Dariya suka kyalkyale da shi ganin yarda na tsuke fuska.
"Fushin baiyi miki kyau ba Aminiyata."
Murmusawa na yi.
"Yawwa ko ke fa sai annuri na kuma cika kyak-kyawar fuskanki."
"Ban da zagi fa Aminiyata."
"Allah ba zancen zagi domin ke kanki kinsan mai kyauce tamkar tauraruwa cikin dubbab taurari."
"Kinyi na kud'in ki wallahi."
"Ai gaskiya Fanta ke fad'a ke d'in tubarkallah masha Allah, tamkar 'yar buzaye ko Shuwa Arab."
"Eh wallahi Sister Beebah."
"Dan Allah ku barmin kunnuwa su huta."
"Ank'i sai kin sanar da mu nasabanki daga wani yare kika fito."
"Yaren Baba mana Hausa Fulani."
"Amma kinsan Allah ko a farce baki kama da Baba haka 'yan uwanki duk kinfisu kyau duk da suma da farare cikinsu amma naki hasken na dabanne."
"To ni bakuga yarda Mama ke da haske ba, ita na d'auko."
"Eh gaskiya hasken Mama kikayo aminiyata amma duk da haka kinfita fari."
"Eh nafita kam amma ai munyi kama."
Karkacewa Fanta ta yi tana k'aremin kallo na kai mata duka ta ja baya cikin cewa "Kuna kama a halittan idanunku da kyawun diri amma in banda nan ban hango ta inda kukayi kama ba."
"Kai Fanta ki duba dai da kyau hatta madai-daicin bak'insu iri d'aya ne."
"Kai Beebah a she haka kika k'arewa Mama kallo?"
"No a photonku na tantance."
Banza na yi da su ganin in na biye musu ba zamuyi abinda ke gabanmu ba.
Bintu Alale, Firdausi jelop d'in macaroni jelop sai Safina shinkafa da miya. Komi dai-dai mukayi yarda bazai zamo anyi albazaranci ba. Mun jere abincin a d'akina muka zauna muna hira Fanta ta kalli Beebah ta langab'e kai.
"Me ye malama?"
"Dan Allah Sister idan ya iso ki kulashi kinga domin ke zaizo"
"Wai Yaya Abdallah zai kawo su?"
"Eh."
Dogon tsaki Beebah ta ja tare da mik'ewa zata fice.
"Kada ki yi haka sabida ance bak'onka Annabinka."
"Fanta wallahi inda na san munafuncin da kuka k'ulla kenan tabbas da bazan jirasu ba zan wuce amma ko yanzu ba zaku sami abinda kuke so ba na rantse."
"Eh mun yarda amma dan Allah ki kulashi cikin walwala in ya wuce sai kiyi mana duk masifar da kika so."
Shiru ta yi, Fanta ta janyo hannunta ta zaunar gefen katifa tana yi mata magana a kunni, tagumi ta zabga na yi gyaran murya ta kalleni na girgiza mata kai, murmushi ta saukemin wanda a fili na dole ne saboda hakan ya bayya a saman fuskanta.
"Me ke faruwa, kuke 'yan b'oye-b'oye?"
Na cillowa Fanta tambayar duk da shiga lamarin rayuwar mutane ba halina ba ne.
"Gata nan kiyi mata nasiha ta daina wulak'anta mana Yaya, saboda shi tak'i bin su Bintu sada zumunta shi ne ya biyosu domin ya ganta dan ta yanke alak'a dashi tsawon wasu watanni, ta daina d'aukan wayarsa tayi blocking nasa a k'arshema ta saka shi a black list, in kuma ya kirata da wayar Mamansa ko k'anninsa tana jin muryansa zata kashe wayarta baki d'aya."
"Innalillahi, me ya yi zafi haka?"
"Wai bazata auri mai mata ba saboda tana tsoron jarabar matarsa mai hali irin na Aunty Nafisa sak."
Wani zabura Beebah ta yi tayo kan Fanta, ita kam ta kwasa da gudu ta fice zata rufa mata baya na rik'eta cikin tsare gira na ce "Ke kin gujewa auren tashin hankali amma ni kin dage sai na yi?"
Numfashi ta yi ta saukewa cikin alamun fushi, zuwa can ta yi gyaran murya sai lokacin na saki hannunta dana kama. Ruwa ta d'auka ta sha sosai sannan ta k'ara yin gyaran murya ta soma magana cikin natsuwa.