← Book details Damuwata Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 38 OF 43

Sashe 38

Damuwata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Mama dan girman Allah kiyi ta hak'uri da Baba insha Allah hakurinki babban riba ne saboda halinsa ba ke kad'ai yake yimawa ba, na fahimci haka Allah ya yo shi mafad'aci ga saurin hasala akan abin da bai kai ya kawo ba."

"To Alhaji Allah ya k'ara mana hak'urin baki d'aya."

"Amin."

Muka amsa.

Wayar Bintu na amsa na turawa Aliyu sak'o. Ina kallon Uncle na hararan hannuna ta gefen ido sai lamarin yabani dariya na murmusa har sautin na fitowa ya kalleni ido cikin ido na lumshe nawa.

"Ina wayarki?"

Ya furta cikin rad'a.

"An sace wayar."

"Inji wa?"

Wannan karan ya bud'e murya.

"To Uncle nazo da ita Asibiti ba'a ganta ba."

"Ok za'a siya wani."

"A'a kada a siya tana wurin Baba Umaru, Habibu ya sanarmin da sun dawo daga tafiya za'a kawo mata."

"To Mama."

Ya amsa cikin girmamawa.

Wayar hannuna ta yi k'ara number Aliyu ya baiyana sai na maida silent tare da maidawa gefe na ajiye, ina kallo kira ya yi ta shigowa ban d'auka ba saboda idanun Uncle wanda yanzu k'imarsa ya kuma ninkuwa a gare ni ainun.

"Ki d'auka wulak'anci bai da kyau Khadijatu."

Cikin rad'a ya ambatamin haka, kallonsa na yi ya jinjinamin kai maida kai gefe na yi batare da na bi umurninsa ba.

Muna isa gida su Beebah suka gyaramin d'akina dana Mama cikin a binda baifi awa d'aya da dawowarmu ba gidan ya koma fes har girki sun d'ora, wanka na yi muka zauna a baranda saman babban tabarma Fanta na yi min fifita sakamakon zafin da na ce yana damuna, shi yasa na sanya riga mai yankakken hannu da siket mara nauyi sai na sanya k'aramin hijab wanda ya tsayamin iya wuya.

Aunty Nafisa ce tare da yaranta suka shigo mun gaisa cikin mutunci Mama ta sake yi mata godiya akan d'awainiyar da Uncle ke kanyi mana. Muna tare da ita har dare sannan tsawon lokacin ban hango tijara a idanunta ba domin duk had'a idanun da zamuyi bata yimin mugun kallon da ta ke bina da shi a tun sanina da ita. Sai bayan isha'i ta wuce tare da su Bintu, su kabar Beebah da Fanta.

Ina sallah na jiyo shigowar Baba Umaru Ina idarwa na tafi muka gaisa sai tsokanata ya keyi da gawa tak'i rami, Kawu Habibu na taremin. Shigowar Baba yasa na bar wurin da sauri ina jin Kawu Habibu na k'orafin sababin Baba dan ganin yarda na tsorata da shigowarsa. Ba jimawa na jiyo muryan Uncle inda na fahimci masalaha akazo samu bisa jagorancin Baba Umaru.

"Aliyu ya na k'ofar gida fa."

Idanu na zubawa Beebah, ta gyadamin kai "Tun kina wanka ya zo kuma ya kamata ki fita."

"A gaban su Baba Umaru zan fita zance?"

"To me ye? Kinga ba sai Baba ya gane muna da masun-sunar da ya yi mana gorinsu ba."

Sunkuyar da kai na yi saboda yarda ta yi maganar na gano zagin da Baba ya yi musu d'azun ya b'ata ranta.

"Uhm wallahi badan mahaifinki ba ne Deejah na rantse da d'azun bansan kalan maganar da zanyi masa ba dan har zagi zai iya masa amma sai ya zamo ya haifeki 'yar albarka."

"Aunty Beebah ba Uncle ya ce maganar ta wuce ba."

"Ya wuce Fanta kawai dai har yanzu haushi lamarin ya ke bani barinma dana jiyo muryansa yanzu."

"Kiyi hak'uri nima d'iyarsa bai bari ba, kin dai gani da idanunki."

"Ya wuce yanzu tashi ki tafi wurin masoyinki."

"Dan Allah ku fita ku wakilceni domin bazan iya tsallake taron can ba."

"Fanta tafi ki sanarmasa tasha magani jiri ta ke gani ya shigo su gaisa."

"A'a kada ya shigo."

"Me kike nufi?"

"Ya tafi sai da safe ya dawo."

"To baki isa ba sai ya shigo tunda dubiya yazo ba soyayya ba."

Tab'e baki na yi jin abinda ta ce idanu ta zaro na zabga mata harara tare da hayewa saman doguwar kujera na kwanta. Fita sukayi tare da Fanta zuwa can na jiyo sallamar Aliyu da sauri na tashi na jira hijab na cure wuri d'aya. Duk Ina jin sadda ya gama gaida kowa su Beebah suka yi masa jagora zuwa d'akina na sha mamaki da banji Baba ya yi sababi ba amma tuno da Baba Umaru a wurin sai na barshi saboda ganinsa sa ne ya tsuke baki.

Tashi zaune na yi muka gaisa daga nan shiru ya biyo baya, su Beebah dai na zaune saman gado kowacce na latsa wayarta basu da niyya bamu wuri sai hakan ya yimin dad'i saboda har cikin raina banda kalman furta masa..

"Allah ya k'ara lafiya."

"Amin, nagode."

"Bakomi ke matar Ali ce insha Allah."

Da sauri na kalleshi ya dokamin murmushi sunkuyar da kai na yi.

"In Allah ya kaimu gobe Hajiyana tare da Salma zasu zo dubaki."

"Ok Allah ya kaimu."

"Amin."

Ya mik'e ya fice Fanta ta rufa masa baya.

"Ke matar Muhammad Muhseen ne ba Ali ba."

"Uhm Beebah hoo naga dai ke ce duk kikayi kid'a da rawar nan fa."

"Shi yasa na ke son goge zunubina."

Dariya ta bani sosai na dara tana tayani.

"Allah Deejah kafin in bar garin nan sai kin rabu da Aliyu."

"Saboda me?"

"Haka nan naga yanzu baku dace da juna ba, farar mace sai farin namiji kamar Uncle zubin labarawa."

"Kinyi kuskuren fad'ar karin.maganar Malama cewa akayi farar mace sai bakin namiji, farin namiji kuwa sai farar mace tamkar yarda Uncle suke da Aunty Nafisa ita chocolate shi fari, my Ali baki ni 'yar fara kad'an."

"Ko ba 'yar fara kad'an ba."

Ta furta cikin kawomin duka na gofce tare da komawa serious na ce "Bazan auri Aliyu ba saboda da wasu manyan dalilai wanda zan sanar da ke kafin ku tafi."

"Zanso jinsu yanzu saboda tafiyarmu zai iya yiwuwa gobe ne."

"Gobe kuma?"

"Eh saboda Aunty Nafisa ta had'a mana gurmi wurin tsoho mai ran k'arfe ya kira Uncle lallai mu taho gobe ko ya iso garin Kaduna da kansa ya d'aukemu musanman ni da ke aikin taimakon al'umma."

"Wayyo zansha kewa."

"Muma haka amma tafiyar banda Fanta saboda muna da biki watan gobe zasuzo da fatan zakiyi mana kara kizo?"

"Insha Allah zanzo duk da muma zamuyi tafiya amma nasan kafin bikin mundawo."

"Dan Allah kizo."

"Insha Allah."

"Ok."

"Bikin na miji ko mace?"

"Babban yayarmu baki d'aya shi ne zaiyi aure."

"Masha Allah."

"K'aton tazuru ne fa duk k'anninsa sunyi aure da 'ya'yanzu shi kuwa ya tsaya bautawa boko, da kiranye ya dawo Nigeria, baki gansa ba tamkar bature."

"Ikon Allah, lokacin auren nasa ne baiyi ba sai yanzu."

K'asa ta yi da murya sannan ta ce "Ina son shi fa insha Allah zanzo a ta biyu shi yasa na yakice Yaya Abdul da k'arfi da ya ji."

"To wata sabuwa inji 'yan ca-ca."

"Ki bari kawai dear ni kad'ai na ke kidana da rawana sannan in banda ke ba wanda ya sani."

"To ta ya za'a yi auren kenan?"

"Ta yarda akeyi."

"Zanso ganin wannan soyayya wacce ta ke ma kauniya."

"Ki bari kawai Deejah ni kaina na bata wannan sunar amma ina fatar ta sami ido bada jimawa ba domin ba zan iya bawa kowa ruhina ba sai Yaya Mubajjal."

"Wow suna mai dad'i ga tarin ma'ana."

"Duk mai sunar ya tarasu wallahi ya san kansa baruwansa kowa na sa ne, kinga tunda ya dawo duk jikokin gidan shi ke d'awainiyar karatunsu hatta da mu da muke jikokin d'iyoyi mata ya d'auki nauyi sai d'an abin da ba'arasa ba iyayenmu keyi mana, kud'i ya ke samu tamkar yana hak'osu a k'asa saboda a can turai ya ginu har kamfanoni ya ke da su tare da turawa."

"Masha Allah, matarsa ta yi dacen miji mai son zumunci."

"Wallahi fa ta yi dace kuma ta tsinci dami akala domin d'iyar kawunsa zai aura itama yar boko ce lecturer ce sai dai yafita kyau da aji nesa ba kusa ba."

"To ke Beebah ba sai ki cire kanki a lamarinsa ba ki fidda masu sonki tunda shi ya sami mata."

"Bazaki gane wani kalan so na keyi masa ba wallahi ba dan kudi da kyawunsa ba ne na kamu da k'aunarsa, tun ranar da nagansa naji fad'uwar gaba kuma tundaga ranar duk in mun had'u sai na shiga yanayin daburcewa, tun ban gano dalilin ba har nagano sonsa na ke yi."

"Ikon Allah sai ji da gani."

"Kin nan me?"

"Sai kin fad'a."

"Duk cikinmu yafi yimin magana ko yanzu mafi yawancin shirye-shiryen bikin shi Momynmu zatayi wanda ni ya d'ora a kai na nemi shawararta ta ce in bar mata komi a hannunta daga nan fa ya maida gidanmu wurin zuwarsa ni kuma anan na kuma kamuwa da kaunarsa matsananci saboda yarda ya ke shigemin ko nak'i fitowa idan ya zo sai yanemi izinin momy ya biyoni d'akina shi yasa na daina gudu duk in ya zo sannan gashi ya iya tsokana irin ta abokannan wasa sai dai in yana yimin daburcewa na keyi sam ban iya maida masa da martani inda zai ta kirana da 'yar k'auye mai kunyar maza, wani zubin Momy ce zatayi ta taremin."

"To shima yana sonki kenan?"

"Ko d'aya, haka yakeyiwa dukkanmu sai dai kafin ya kirasu ne ya kirani sau ba adadi."

"Amma naga ko sau d'aya banga kunyi wayata ba."

Nunomin wayarta ta yi naga Miss call barkatai.

"Kullum sai ya kirani wani in amsa wani in share saboda haushin auren da zaiyi."

Dariya na kyale-kyale da shi ta tale baki tamkar zata fashe da kuka.

"Sorry dear in baki shawara?"

"Eh."

"Ki rik'a amsa kiransa inda hali ke ce zaki soma kiransa sannan ki b'oye kishin nan ta gaibu domin wanda kikeyi bai sani ba, ki nemi zab'in Allah ba son zuciyarki ba, in har mijinki ne da kansa zai furta miki k'auna."

"Nagode da shawara amma da kamar wuya hakan ya faru kawai ni ce zan ambatawa Kaka ina son shi na tabbata aurenmu zai k'ullu cikin ruwan sanyi "

"Ban amince kiyi haka ba saboda naji masu iya magana sunce matar shige bata daraja, gara ya furta da kansa."

"D'an boko ne da makar wuya ya zauna da mata biyu."

"To ki hak'ura da shi mana ki rik'e Yaya Abdul."
Chapter 38 · 0% Book details