Sashe 13
Damuwata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da kallo na rakashi har ya fice, cikin tutani na shiga sai kuma na murmusa cikin jin natsuwar ruhi.
"A yau ranace da bazan manta da ita ba, Aliyu ya aikomin da sak'on yana so na, Baba yayimin magana cikin lumana har da sanyamin albarka, tabbas gobe zan tashi da azumi domin nuna godiyata ga Allah akan wannan rana da ya nufeni da ji tare da ganinsa"
Da sauri na tashi na soma gyara d'akin Mama duk da baya da datti. Ina gamawa na fito waje nanma na gyarasa tsaf sannan na shiga kitchen na d'ora girkin dare. Ina kammala zuba a bincin a kula na tsinkayi sallaman Fanta cikin karad'inta na fama, da sauri na fito muka rungume juna cike da murna, idanu muka had'a da Beebah na saki Fanta da sauri na nufeta ina doka murmushi.
"Ke dai tafi ku gama ganin juna da aminiyarki tunda abin 'yar wariya ce."
"Affuwan my Beebah."
Na furta cikin rungumota.
"Uhm ni sakeni ki tafi wurin Fanta ta baki sak'on farko daga Uncle wanda ya ce tukuici ne kafin ni kuma na baki ta biyu wacce tafi na farkon muhinmanci."
Kallon Fanta na yi ta zira hannu cikin hand bag ta fiddo leda fara sol ta mik'omin amsa na yi batare da na fidda abinda ke cikin ledar ba.
"Ciro da bissmillah Aminiyata domin mallakinki ne."
Fanta ta Umurceni.
"Tura hannu na yi na ciro abin da ke ciki d'auke da basmallah, ware ido na yi suka sanya dariya, bud'e kwalin dana ciro nasomayi jikina na rawa na cikaro da dalleliyar waya k'iran sumsung, takardan da ke d'auke da kudin wayar na kalla sai na ajiye wayar a k'asa ina kallon su Beebah idanu waje hannayena dafe a k'irjina.
"Ba'a maida hannun kyauta baya, ki amsa tare da godiya domin mallakan waya mai daraja irin wannan rabonki ne ya tsaga."
"Amma Fanta wayar sama da dubu d'ari tafi k'arfina."
"Idan ta million ce batafi k'arfinki ba Deejah domin na tabbata in kika ce kina so Mama zata siya miki dan haka ina had'aki da Allah ki amshi kyautar nan tare da yiwa Uncle godiya, ya tabbatar min ke tamkar ni ya d'aukeki kinga kenan shi yasa ya siyo mana wayoyi iri d'aya illa bambancin kala."
"To Fanta nagode sosai kuma a mik'amin godiya a garesa kafin inzo da kaina."
"Masha Allah, zaiji K'awata."
"Uhm!."
Beebah tayi gyaran murya, muka maida hankalin gareta, ta rausayar sa kai cikin kashe min ido d'aya sannan ta ce "Sak'on Uncle na biyu ita ce samun wuri na musanman a ruhinki."
"Banfahinceki ba."
"Zanyi miki dala-dala k'awar Fanta, ke dai bini a sannu kawai.
Zama na yi suma suka zauna, sallaman Mama ya dakatar da zancen sa Beebah ke shirin sanar da ji, mukayi mata sannu da zuwa ta amsa a hankali tare da shigewa cikin d'aki.
"Mama bata da lafiya ce?"
"Eh "
Na amsawa Fanta domin bana da amsar da tafi wannan."
"Allah ya bata lafiya."
"Amin."
Bari mu tafi zuwa anjima zan dawo sai muyi maganar amma kafin nan zan turo miki sak'o domin ki soma shirin burge Uncle d'inmu."
Tagumi na zabga saboda zantukan sun jefani cikin tunani, aikam a tare suka kyalkyale da dariya ganin yarda na yi tamkar mara lafiya, harara na cilla musu suka sake kwashewa da dariya tare da nufar hanyar fita gidan, ina kallonsu suka tafi na tashi jikina a mace na shiga kitchen na d'auko abincin, ina fitowa Mama na sanyo kai kitchen d'in sai na koma da baya ta shigo ta kama kafad'una ta rik'e gam, na rintse ido ina karanto addu'an samun kariya daga musiba sabida yarda naga idanun Mama ya tsoratani.
"Uwata kiyi hak'uri da rayuwa domin kowa da kika gani da abinda ya zame masa k'alubale duk kuwa muk'aminsa ko sarautarsa."
"Haka ne Mama shi yasa Annabi S.A.W ya umurcemu da mu zamo masu yarda da k'addara ta khairan ko kishiyarta."
Rungumeni Mama ta yi tana sauke ajiyar zuciya, mun jima a haka kafin da sakeni tare da rik'o hannuna muka fito na ajiye kulan abincin, zama mukayi a shinfid'ar da na yi domin cin abinci, sai lokacin idanunta ya sauka kan kwalin waya tare da wayar da suke a jiye gefe.
"Wa ya baki?"
"Uncle Muhseen ya aiko su Fanta su kawomin wai tukuicin dafawa abokansa abinci da na yi ranar Dana k'one."
"Allah ya biyasa da dubun alkhairori."
"Amin."
"A she abinda zai siya miki kenan d'azun ya shigo neman izini."
"Ya shigo wurinki Mama?"
"Eh ya zo shida Fanta ya sake bani hak'uri akan abinda ya faru sadda zai tafi sai ya ce yana neman izinin da in bashi dama ya rik'a kula da lamuranki kamar yarda yakeyiwa Fanta, na kuma bashi dama saboda na hango gaskiya a tare da shi gami da uwa uba natsuwa."
"Ikon Allah Uncle na da abin mamaki, a da fa ko na gaisheshi bai amsawa sai yaga dama amma daga jiya zuwa yau ya sanjamin matuk'a."
"Uwata hoo, to kika sani ko yana ciki ne?"
"Cikin me Mama?"
"Manema aurenki mana."
"Innalillahi! Bana fatan faruwan hakan Mama, dan Allah ki daina zancen nan bana so, wallahi bazan iya zama da matarsa ba."
"Uwata natsu dan Allah, nifa hasashe na ke yi ba zahiri ba ne da zaki rud'e haka kamar zaki zauna da mala'ikan d'aukan rai."
Mik'ewa na yi nufin yi dan gujewa zancen, Mama ta maidani na koma zaune ba shiri, cikin tsare gira ta dubeni na sunkuyar da kai.
*TALLA.*
*Ina kuke Mata 'yan kwalisa masu bawa fatarsu 'yancinta musanman babban kadararku wato fuska. To ga dama ta zo muku cikin sauk'i wato samun kayan gyarar fuska da jiki mai inganci na organic wanda aka samar da su da abubuwa masu nagarta. Duk wacce K'uraje, Tabbai, Sunburn, kyafsi suka b'atawa fuska muna da maganin da fuskanta zai dawo fes, sumul, rangad'ad'au. Haka a fannin fatar jiki shima muna da kayan da zaiyi laushi, sulb'i tare da haske mai kyau. Ga kayan kamar haka:*
Sabulu (molato and black soap)
Scrub
Face cream
Oil
Body lotion
Shower gel
Kulachan
Humra (White and black)
Turaren tsugunon
Turaren kaya
Turaren wuta na d'aki
Garin d'a'a (domin k'an-k'aro martaban aure a turaka)
*Duk za'a samesu a farashi mai rahusa, mai buk'atar d'aya ko sari a tun-tub'emu a wad'annan numbers d'in 08132166848 ko 08147491137. Sai munjiku.*
[10/19, 4:58 PM] 💘: DAMUWATA (Sanin abin adona)
By Mrsjmoon
E.W.F
*Shafin na ku ne 'yan uwa rabin jikina, Yaya Sadiya (Mmn Ihsan) tare da Yaya Amina (Mmn Ganar) Alkhairori marasa iyaka su dawwama a gareku bi jahiy Nabiy S A W. Amin.*
Page 08.
"Uwata me ke damunki? Da kike son maida wata d'abi'a mara kyau ya zamo naki. Ni ce fa na ke yi miki magana amma kikayi nufin tashi ki bani wuri, innalillahi wa Inna ilaihin raji'un, yau wacce kalan rana ce tazo gareni ni Hurera."
"Rabbi igfirli. Na tuba Mamana kiyi hak'uri bazan sake aikata makamancin haka gareki ba."
Na ambata cikin rawar murya.
"Uwa banyi fushi da ke ba kuma da yardan Allah bazan tab'ayi ba."
Fad'awa jikinta na yi ta rungume ni, a hankali take shafan suman kaina zuwa bayana, nayi lamo ina jan hailalah domin samun nutsuwar ruhi.
"Uwata."
"Na'am Mama."
"Shi me ya kamata kiyi a daren wannan ranar wanda kika tsinci kanki da d'a namiji ya aiko miki da kyau mai matuk'ar amfani?"
"Zan rayata da nafilfili sannan na wayi gari da Azimi domin nunawa Allah godiyata akan faruwar hakan."
"Masha Allah, Uwata tafi na kowa hangen nesa."
Murmusawa na yi tare da sark'e tafin hannunta cikin nawa na ce ,"Mamana a yau abubuwa uku sun riskeni kuma dik a kusan lokaci d'aya, dan haka kema ki tayani nuna farin cikin ta hanyar raya daren da salloli tare da tashi da Azimin nafila."
"Wannan a rubuce ya ke Uwata amma zanso sannin ragowar abubuwa biyun dan nasan na farkon dai kyautar waya ce daga makwafcin arziki."
"A'a kyautar waya ita ce cikon na ukun."
"To ina saurarenki Uwata kuma Aminiyar Mamanta."
Manna jikina na sake na yi da nata sannan na sunkuyar da kai domin ina jin kunyar zancen farko, a hankali na ce "Mama a yau abokin karatuna ya aikomin da sak'on yana sona ta bakin Beebah haka a yau Baba ya... Hamdalah da Mama ta sanya mai k'arfi ya sanya na dakata da zancen na kamo hannunta na kife fuskata a kai ina dariya k'asa-k'asa.
"Uwata insha Allah sai kin tara masoya masu yawa, kin zab'a kin darje, ina fatan ki samu nagari maiyi miki k'auna ta hak'ik'a,."
"Allah ya nufa hakan Mamana."
"Amin, ai ina jiyo jinkirin nan naki alkhairi ne."
Ina kallon idanunta na cigaba da cewa "Mamana abu na biyu shi ne Baba ya sanya min albarka ya sanarmin ni d'in yarinyar arziki ce kuma haskenku ce ni, ya amince shi abin adona ne, ya tabbatar min bazai sake hantarata ba, mu'amalar arziki zai kasance tsakaninmu."
Kallon da Mama ke bina dashi yasa jikina ya yi sanyi sai na kamo hannunta na rik'e gam na ce "Dan Allah Mama ki yafe masa du...
"Uwata tashi muyi haraman sallah idan mun idar ina son yin magana dake sannan ina tayaki murnan abinda Malam ya ambata miki na albarka, ina addu'ar yasa har cikin ransa haka zancen yake ba don cikar wani buri nasa ya sanya shi yin furucin ba."
Kasa amsawa na yi da Amin sabida yarda jikina ya yi lakwas jin Mama ta harbo jirgin.
"Uwata ko har yanzu yatsun suna yi miki ciwo ne naga fuskanki ya sanja?"
Kallon yatsun k'afata na yi sannan na girgiza kai. "Sun k'ame banjin ciwo sosai sai abinda ba'arasa ba kamar k'ai-k'ayi na warkewa."
"Hakan na ke son ji, maza tashi muyi sallah a cikin lokacinta."
Mik'ewa na yi na shige d'akina. Saida na saka sabuwar wayata a chargy sannan na fad'a toilet. Ko da na idar da sallah sai na koma na yi suddaja na rok'awa Uncle Muhseen rahamar Allah tare da neman alkhairi a lamarina da Aliyu a k'arshe na rok'i Allah ya sanyawa Mama sanyi da ta yafewa Baba dukiyanta kamar yarda ya ke buri.
"A yau ranace da bazan manta da ita ba, Aliyu ya aikomin da sak'on yana so na, Baba yayimin magana cikin lumana har da sanyamin albarka, tabbas gobe zan tashi da azumi domin nuna godiyata ga Allah akan wannan rana da ya nufeni da ji tare da ganinsa"
Da sauri na tashi na soma gyara d'akin Mama duk da baya da datti. Ina gamawa na fito waje nanma na gyarasa tsaf sannan na shiga kitchen na d'ora girkin dare. Ina kammala zuba a bincin a kula na tsinkayi sallaman Fanta cikin karad'inta na fama, da sauri na fito muka rungume juna cike da murna, idanu muka had'a da Beebah na saki Fanta da sauri na nufeta ina doka murmushi.
"Ke dai tafi ku gama ganin juna da aminiyarki tunda abin 'yar wariya ce."
"Affuwan my Beebah."
Na furta cikin rungumota.
"Uhm ni sakeni ki tafi wurin Fanta ta baki sak'on farko daga Uncle wanda ya ce tukuici ne kafin ni kuma na baki ta biyu wacce tafi na farkon muhinmanci."
Kallon Fanta na yi ta zira hannu cikin hand bag ta fiddo leda fara sol ta mik'omin amsa na yi batare da na fidda abinda ke cikin ledar ba.
"Ciro da bissmillah Aminiyata domin mallakinki ne."
Fanta ta Umurceni.
"Tura hannu na yi na ciro abin da ke ciki d'auke da basmallah, ware ido na yi suka sanya dariya, bud'e kwalin dana ciro nasomayi jikina na rawa na cikaro da dalleliyar waya k'iran sumsung, takardan da ke d'auke da kudin wayar na kalla sai na ajiye wayar a k'asa ina kallon su Beebah idanu waje hannayena dafe a k'irjina.
"Ba'a maida hannun kyauta baya, ki amsa tare da godiya domin mallakan waya mai daraja irin wannan rabonki ne ya tsaga."
"Amma Fanta wayar sama da dubu d'ari tafi k'arfina."
"Idan ta million ce batafi k'arfinki ba Deejah domin na tabbata in kika ce kina so Mama zata siya miki dan haka ina had'aki da Allah ki amshi kyautar nan tare da yiwa Uncle godiya, ya tabbatar min ke tamkar ni ya d'aukeki kinga kenan shi yasa ya siyo mana wayoyi iri d'aya illa bambancin kala."
"To Fanta nagode sosai kuma a mik'amin godiya a garesa kafin inzo da kaina."
"Masha Allah, zaiji K'awata."
"Uhm!."
Beebah tayi gyaran murya, muka maida hankalin gareta, ta rausayar sa kai cikin kashe min ido d'aya sannan ta ce "Sak'on Uncle na biyu ita ce samun wuri na musanman a ruhinki."
"Banfahinceki ba."
"Zanyi miki dala-dala k'awar Fanta, ke dai bini a sannu kawai.
Zama na yi suma suka zauna, sallaman Mama ya dakatar da zancen sa Beebah ke shirin sanar da ji, mukayi mata sannu da zuwa ta amsa a hankali tare da shigewa cikin d'aki.
"Mama bata da lafiya ce?"
"Eh "
Na amsawa Fanta domin bana da amsar da tafi wannan."
"Allah ya bata lafiya."
"Amin."
Bari mu tafi zuwa anjima zan dawo sai muyi maganar amma kafin nan zan turo miki sak'o domin ki soma shirin burge Uncle d'inmu."
Tagumi na zabga saboda zantukan sun jefani cikin tunani, aikam a tare suka kyalkyale da dariya ganin yarda na yi tamkar mara lafiya, harara na cilla musu suka sake kwashewa da dariya tare da nufar hanyar fita gidan, ina kallonsu suka tafi na tashi jikina a mace na shiga kitchen na d'auko abincin, ina fitowa Mama na sanyo kai kitchen d'in sai na koma da baya ta shigo ta kama kafad'una ta rik'e gam, na rintse ido ina karanto addu'an samun kariya daga musiba sabida yarda naga idanun Mama ya tsoratani.
"Uwata kiyi hak'uri da rayuwa domin kowa da kika gani da abinda ya zame masa k'alubale duk kuwa muk'aminsa ko sarautarsa."
"Haka ne Mama shi yasa Annabi S.A.W ya umurcemu da mu zamo masu yarda da k'addara ta khairan ko kishiyarta."
Rungumeni Mama ta yi tana sauke ajiyar zuciya, mun jima a haka kafin da sakeni tare da rik'o hannuna muka fito na ajiye kulan abincin, zama mukayi a shinfid'ar da na yi domin cin abinci, sai lokacin idanunta ya sauka kan kwalin waya tare da wayar da suke a jiye gefe.
"Wa ya baki?"
"Uncle Muhseen ya aiko su Fanta su kawomin wai tukuicin dafawa abokansa abinci da na yi ranar Dana k'one."
"Allah ya biyasa da dubun alkhairori."
"Amin."
"A she abinda zai siya miki kenan d'azun ya shigo neman izini."
"Ya shigo wurinki Mama?"
"Eh ya zo shida Fanta ya sake bani hak'uri akan abinda ya faru sadda zai tafi sai ya ce yana neman izinin da in bashi dama ya rik'a kula da lamuranki kamar yarda yakeyiwa Fanta, na kuma bashi dama saboda na hango gaskiya a tare da shi gami da uwa uba natsuwa."
"Ikon Allah Uncle na da abin mamaki, a da fa ko na gaisheshi bai amsawa sai yaga dama amma daga jiya zuwa yau ya sanjamin matuk'a."
"Uwata hoo, to kika sani ko yana ciki ne?"
"Cikin me Mama?"
"Manema aurenki mana."
"Innalillahi! Bana fatan faruwan hakan Mama, dan Allah ki daina zancen nan bana so, wallahi bazan iya zama da matarsa ba."
"Uwata natsu dan Allah, nifa hasashe na ke yi ba zahiri ba ne da zaki rud'e haka kamar zaki zauna da mala'ikan d'aukan rai."
Mik'ewa na yi nufin yi dan gujewa zancen, Mama ta maidani na koma zaune ba shiri, cikin tsare gira ta dubeni na sunkuyar da kai.
*TALLA.*
*Ina kuke Mata 'yan kwalisa masu bawa fatarsu 'yancinta musanman babban kadararku wato fuska. To ga dama ta zo muku cikin sauk'i wato samun kayan gyarar fuska da jiki mai inganci na organic wanda aka samar da su da abubuwa masu nagarta. Duk wacce K'uraje, Tabbai, Sunburn, kyafsi suka b'atawa fuska muna da maganin da fuskanta zai dawo fes, sumul, rangad'ad'au. Haka a fannin fatar jiki shima muna da kayan da zaiyi laushi, sulb'i tare da haske mai kyau. Ga kayan kamar haka:*
Sabulu (molato and black soap)
Scrub
Face cream
Oil
Body lotion
Shower gel
Kulachan
Humra (White and black)
Turaren tsugunon
Turaren kaya
Turaren wuta na d'aki
Garin d'a'a (domin k'an-k'aro martaban aure a turaka)
*Duk za'a samesu a farashi mai rahusa, mai buk'atar d'aya ko sari a tun-tub'emu a wad'annan numbers d'in 08132166848 ko 08147491137. Sai munjiku.*
[10/19, 4:58 PM] 💘: DAMUWATA (Sanin abin adona)
By Mrsjmoon
E.W.F
*Shafin na ku ne 'yan uwa rabin jikina, Yaya Sadiya (Mmn Ihsan) tare da Yaya Amina (Mmn Ganar) Alkhairori marasa iyaka su dawwama a gareku bi jahiy Nabiy S A W. Amin.*
Page 08.
"Uwata me ke damunki? Da kike son maida wata d'abi'a mara kyau ya zamo naki. Ni ce fa na ke yi miki magana amma kikayi nufin tashi ki bani wuri, innalillahi wa Inna ilaihin raji'un, yau wacce kalan rana ce tazo gareni ni Hurera."
"Rabbi igfirli. Na tuba Mamana kiyi hak'uri bazan sake aikata makamancin haka gareki ba."
Na ambata cikin rawar murya.
"Uwa banyi fushi da ke ba kuma da yardan Allah bazan tab'ayi ba."
Fad'awa jikinta na yi ta rungume ni, a hankali take shafan suman kaina zuwa bayana, nayi lamo ina jan hailalah domin samun nutsuwar ruhi.
"Uwata."
"Na'am Mama."
"Shi me ya kamata kiyi a daren wannan ranar wanda kika tsinci kanki da d'a namiji ya aiko miki da kyau mai matuk'ar amfani?"
"Zan rayata da nafilfili sannan na wayi gari da Azimi domin nunawa Allah godiyata akan faruwar hakan."
"Masha Allah, Uwata tafi na kowa hangen nesa."
Murmusawa na yi tare da sark'e tafin hannunta cikin nawa na ce ,"Mamana a yau abubuwa uku sun riskeni kuma dik a kusan lokaci d'aya, dan haka kema ki tayani nuna farin cikin ta hanyar raya daren da salloli tare da tashi da Azimin nafila."
"Wannan a rubuce ya ke Uwata amma zanso sannin ragowar abubuwa biyun dan nasan na farkon dai kyautar waya ce daga makwafcin arziki."
"A'a kyautar waya ita ce cikon na ukun."
"To ina saurarenki Uwata kuma Aminiyar Mamanta."
Manna jikina na sake na yi da nata sannan na sunkuyar da kai domin ina jin kunyar zancen farko, a hankali na ce "Mama a yau abokin karatuna ya aikomin da sak'on yana sona ta bakin Beebah haka a yau Baba ya... Hamdalah da Mama ta sanya mai k'arfi ya sanya na dakata da zancen na kamo hannunta na kife fuskata a kai ina dariya k'asa-k'asa.
"Uwata insha Allah sai kin tara masoya masu yawa, kin zab'a kin darje, ina fatan ki samu nagari maiyi miki k'auna ta hak'ik'a,."
"Allah ya nufa hakan Mamana."
"Amin, ai ina jiyo jinkirin nan naki alkhairi ne."
Ina kallon idanunta na cigaba da cewa "Mamana abu na biyu shi ne Baba ya sanya min albarka ya sanarmin ni d'in yarinyar arziki ce kuma haskenku ce ni, ya amince shi abin adona ne, ya tabbatar min bazai sake hantarata ba, mu'amalar arziki zai kasance tsakaninmu."
Kallon da Mama ke bina dashi yasa jikina ya yi sanyi sai na kamo hannunta na rik'e gam na ce "Dan Allah Mama ki yafe masa du...
"Uwata tashi muyi haraman sallah idan mun idar ina son yin magana dake sannan ina tayaki murnan abinda Malam ya ambata miki na albarka, ina addu'ar yasa har cikin ransa haka zancen yake ba don cikar wani buri nasa ya sanya shi yin furucin ba."
Kasa amsawa na yi da Amin sabida yarda jikina ya yi lakwas jin Mama ta harbo jirgin.
"Uwata ko har yanzu yatsun suna yi miki ciwo ne naga fuskanki ya sanja?"
Kallon yatsun k'afata na yi sannan na girgiza kai. "Sun k'ame banjin ciwo sosai sai abinda ba'arasa ba kamar k'ai-k'ayi na warkewa."
"Hakan na ke son ji, maza tashi muyi sallah a cikin lokacinta."
Mik'ewa na yi na shige d'akina. Saida na saka sabuwar wayata a chargy sannan na fad'a toilet. Ko da na idar da sallah sai na koma na yi suddaja na rok'awa Uncle Muhseen rahamar Allah tare da neman alkhairi a lamarina da Aliyu a k'arshe na rok'i Allah ya sanyawa Mama sanyi da ta yafewa Baba dukiyanta kamar yarda ya ke buri.