Sashe 37
Damuwata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ya matso daf da gadon ya ce min "Na yi kewarki, Allah yasa kaffara ce."
"Amin."
Kud'i mai yawa ya ciro yan dari bibiyu sabbi fil ya ajimin saman cinya sannan ya fice bayan ya sake bawa Hajiya Inna hak'uri.
"Me ke tsakaninku da shi Takwarata?"
Shiru na yi tare da kulle fuska da tafukan hannayena.
"Oh na fahimta, to ba damuwa za'a kuma yayibo irin rashin d'a'a ba."
"Hajiya Inna me ya yi?"
"Jinin Zainab basu k'ara shigomin ahali da yardan Allah dan haka tun kafin ki haukace a shiriritan so dinan ki koreshi."
Idanu na zare ta zabgomin harara.
"Inna wai ya suke da matar Kawu?"
"Abokik wasanta ne domin da babanshi da Mamanta uwarsu d'aya ubansu d'aya kuma yayarshi wanda suke uba d'aya abokin Habibu ne, agidansu Habibu ya had'u da ita dan Mamanshi ita ta rik'eta har zuwa aurenta."
"Ikon Allah amma duk shekarun da muka kwashe da Aliyu ban tab'a sanin hakan ba."
"To ina kike zuwa balle ki had'u da 'yan uwansa sannan shima Aliyun bai zuwa gidan Habibu sai hab'o."
Shiru na yi ina nazarin wannan lamari, ta ke naji duk damuwar da na ke ciki ya koma ba komi ba saboda tuno mugun halin Zainab da tasha gwadamin wanda nashajin Hajiya Inna na cewa d'aukosa ta yi wurin uwar goyonta.
'Wato mahaifiyar Aliyu bata da kirki kenan? Aikam na hak'ura da kai domin ina burin aure na ke inda Zan sami kwanciyar hankali ba kishiyarta ba.'
"Ban son shiga dogon tunani saboda lalurarki."
Na tsinkayi muryan Hajiya Inna daf da ni. Kallonta na yi har lokacin bata cikin walwala.
"Kiyi hak'uri Inna."
"Ya zamamin dole Khadijatu sai dai DAMUWATA shi ne na yarda surikata gudan jinina d'aya tilo zata zamemin abokiyar gaba."
"Ban gane ba Inna? Kina nufin su Mama Indo ba surukanki ba ne?"
"Surukaina ne amma duk kan mazajensu 'ya'yan uwar gidan Alhaji ce wacce ta rasu ta barmin su duk suna k'ananu, Habibu shi ne yarona na shida kuma shi ne ya rayu har naga aurensa domin yayunsa da k'anninsa daga sun taso suke mutuwa domin babban yayarsa na daf da yin aure ya sami hatsarin mota ya mutu nasan kin tuna lokacin."
Eh na tuna da kawu Hamza, Allah ya ji kansu da Rahma "
"Amin.
"To yau kinji yarda na ke da su Balarabe."
"Allahu albar, sannu Inna, lallai ke ta daban ce, Allah ya biyaki da khairan."
"Amin ya rabbi."
"A gaskiya su Mama Indo nada ladabi sama da Zainab sam ba wanda zaice ba ke ce kika haifi mazajensu ba."
"D'iyoyin tarbiyya kenan, sannan sun samu mazaje tsayayyu masu jajircewa akan abin da suke so dole abi ba irin Habibu ba da gata ya yiwa yawo ya ke ganin matarsa ba komi ta ke yimin ba saima ganin ni ce nacika fad'a da saka ido."
"Shi Kawun ke kallonki da hakan?"
"Ya wuce kokwanto Khadijatu domin yanzu indan da gabansa hakan ya faru wallahi tsaf bayar matarsa zaibi ya yi ta k'unci na tozarta masa iyali gaban mutane."
"In haka ne kam da sake wallahi, ai lamarin uwa sama da komi ya ke, gashi wayayye da ilimi amma bai aiki da shi."
"Ki bari kawai Khadijatu, shi yasa na kance da shi halinsa d'aya da Hadi."
Kulle baki na yi idanu waje na ke girgiza mata kai murmushi ta yi kad'an ta ce "Na tabbata ko halinsu bai zo d'aya ba a wani abin zaizo domin ya yi nisa akan lamarin figaggiyar matarsa mai zubin zabbin daji da kanta kamar k'ullin maganin sanyi."
Dariya na kyale-kyale da shi tana tayani. Daga haka muka saki zancen domin nagano ta sanyo mana raha ne saboda bata son acigaba da zancen.
***
Ina cin abincin rana faten Irish ne ya ji hanta da ganyen ugun wanda su Fanta suka kawomin, sai hira mukeyi hankali kwance domin Hajiya Inna ta sami wucewa gida tunda ta ga isowarsu.
Mama ce ta shigo Uncle na biye da ita tare da Baba a bayansu. K'irjina ne ya harba ganin Baba domin na tabbata sai ya b'atamin rai kafin ya tafi.
"Kai dalla! Ku fice ku bata wuri ta sha iska, kunzo kun nanuk'eta da tik'a-tik'an jikinku ba mijin kwasa ko da ya ke duk jirgi d'aya ya kwasoku da ita ga kyau da wayewa ba mashin-shini, kai tir muku!."
Tashi su Fanta sukayi duk suka fice jikinsu a sanyaye, na kalli Uncle wanda na hango b'acin rai a idanunsa kwance sai kawai na fashe da kuka mai sauti ina kaiwa k'arfe gadon duka wanda ke nuni da takaicin da na ke ciki.
*TALLA.*
*Ina kuke Mata 'yan kwalisa masu bawa fatarsu 'yancinta musanman babban kadararku wato fuska. To ga dama ta zo muku cikin sauk'i wato samun kayan gyarar fuska da jiki mai inganci na organic wanda aka samar da su da abubuwa masu nagarta. Duk wacce K'uraje, Tabbai, Sunburn, kyafsi suka b'atawa fuska muna da maganin da fuskanta zai dawo fes, sumul, rangad'ad'au. Haka a fannin fatar jiki shima muna da kayan da zaiyi laushi, sulb'i tare da haske mai kyau. Ga kayan kamar haka:*
Sabulu (molato and black soap)
Scrub
Face cream
Oil
Body lotion
Shower gel
Kulachan
Humra (White and black)
Turaren tsugunon
Turaren kaya
Turaren wuta na d'aki
Garin d'a'a (domin k'an-k'aro martaban aure a turaka)
*Duk za'a samesu a farashi mai rahusa, mai buk'atar d'aya ko sari a tun-tub'emu a wad'annan numbers d'in 08132166848 ko 08147491137. Sai munjiku.*
[11/4, 5:42 PM] 💘: DAMUWATA (Sanin abin adona)
By Mrsjmoon
E.W.F.
https://youtu.be/v9iNYDvS8JM
Pls 'yan uwa ku dannamin subcribe a YouTube d'ina, nagode.
Page 21.
"Ke! Kuma me akayi miki kika b'are baki kamar faranti kina kukan iyashege, to maza ki rufe mana baki ko ingamu da ke ba ciwo ba ko mutuwa kikeyi zan iya taka gawarki na wuce ta kai ba ruwana."
Shiru na yi amma badan tsoron dukansa ba sai dan takaicin halinsa tare da tunanin yin kukana baida amfani.
"Dan an kira k'awayenki tik'a-tik'a shi ne abin yin kuka saboda Hurera ta gama sangartaki, ke yanzu dan Allah ko kunya bakiji kamarki kina kuka, inda a k'auye kike da yanzu kina da 'yay'ya bakwai zuwa goma amma dubeki zaune makar gar, to wallahi ki sani kwanaki kad'an ya rage in zar...
"Dan Allah Malam kayi shiru haka ban muji da abinda ya damemu tunda kai haka Allah ya yika baka gajiya da sababi mara ma'ana da ke janyo jin kunya."
"Hurera ni...
"Dan soyayyarka da mahaliccinmu ka daina fad'ar nan haka, haba dan Allah kai ko gajiya bakyayi da zance a gaban idanun kunya."
Tsuke baki ya yi yana aunawa Mama mugun kallo, kunya ce ta rufeni ganin yarda Uncle ya ke binsa da kallon banza, tabbas kallon ya haskomin karatun ruhinsa wato takaicin Baba mai jin tamkar a rufe rufeshi da duka.
"Uncle nagode da tarin d'awainiya Allah ya jik'an mahaifa ya kuma shirya maka zuri'a tare da gamawa lafiya cikin samuwar babban rabo ranar lahira."
Sai da ya yi gyaran murya sannan ya amsa lokacin har Mama ta amsa ya yin da Baba ya tsare giran sama da k'asa yana zabgomin harara.
"Bari inga Dr. Jalal."
Uncle ya furta batare da ya jira amsawarmu ba ya fice.
"Munafukin banza wai shi nan ya ji haushi na kori k'aninsa, to an koresun in zai iya ya rufeni da duka yaga inda tsiya ke zamaninta wallahi."
"Allah ya yi mana tsari da ganin tsiya."
"Amin."
Na amsa da sauri.
"Ya jikin naki?"
Baba ya ambata cikin taushin murya. Ban dauka da ni ta keyi ba shi yasa bance komi ba.
"Au dan kin samu na tambayi ciwon karyan da kikayi shi ne zaki maidani sokon banza?"
Kafin inyi magana Mama ta rigani da cewa "Gata nan ta warke ganin idanunka sai kuma me uban 'yan sababi."
"Hurera me yasa sam baki san darajar aure ba ne?"
"Sabon karatun sanin darajojin aure zamu koma makaranta muyo tare da kai domin kome ka kirani kaine malamina."
"Zan sab'a miki fa Hurera ba ruwana da Asibiti ne nan."
"Maza aikata abin yamad'i-d'i karo na biyu a safiyar nan a samu masu d'oraka a yanar gizo da bugawa a jaridu kaga ka zama dan wasan kwai-kwayo na zahiri kamar yarda sabon sunarka ya koma a unguwarka yanzu."
"Ni Malam Hadi kike kira da d'an drama?"
Banza Mama ta yi da shi, nikam tuni na juya baya tare da tura yatsuna cikim kunnuwana saboda na gaji da sauraren sababin Baba.
"Sai mun had'u a gida zan nuna miki nafi gaban iskancinki sannan kada kiga na d'aga darajarki a gaban abokan zamanki d'azun ki d'auka kin sameni ne a'a biyana zakiyi dan wallahi sai naci buhunar wake biyar domin na saka buri akan wanda sukayi satan sai reshe ya juye da mujiya dan haka sai ki shirya bi...
"Allah ya ganar da kai hanyar gaskiya."
Mama ta ambata tare da shigewa toilet ta barshi tsaye da baki bud'e, dariya ce ya zomin na kife fuska gudun kada ya jigoni na shiga uku
K'aran buga k'ofar ya sanarmin da Baba ya fice, numfashi na sauke ina auna lamuran Baba wanda na yanzu na ke d'orasu a mizanin rashin hankali.
"Astagafirullah."
Na ambata a hankali.
Shigowar Doctor, Uncle da su Beebah biye da su ya yi daidai da fitowar Mama daga toilet. Ya bani sallama tare da shawarwari agame da daina barin damuwa ko tunani na takuramu ni da Mama saboda su ne babban matsalolinmu.
Sosai Mama ta yi masa godiya, su Fanta suka tattara mana kaya muka fito. Ni da Mama tare da Bintu motar Uncle muka shiga ya yin da su Fiddausi suka shiga wanda suka zo a ciki Beebah ta ja, ta yi gaba Uncle ya rufa mata baya, akan hanya ya kira Hajiya Inna ya sanar mata da an sallamemu.
"Yawwa Alhaji sanar da Malam kada ya zama abin laifi duk da yasan za'ayi sallaman."
"To Mama."
Ni ya mik'owa wayar batare da ya furta kalma ba.
Sunar da naga an sanya Baban Nana na kira har ta tsinke ba'a d'auka ba, haka na yi ta kira sau ba adadi a k'arshe sai aka kashe wayar.
Mik'awa Uncle wayarsa na yi ya amsa batare da ya cemin uffan ba haka nima ban tofa ba.
"Amin."
Kud'i mai yawa ya ciro yan dari bibiyu sabbi fil ya ajimin saman cinya sannan ya fice bayan ya sake bawa Hajiya Inna hak'uri.
"Me ke tsakaninku da shi Takwarata?"
Shiru na yi tare da kulle fuska da tafukan hannayena.
"Oh na fahimta, to ba damuwa za'a kuma yayibo irin rashin d'a'a ba."
"Hajiya Inna me ya yi?"
"Jinin Zainab basu k'ara shigomin ahali da yardan Allah dan haka tun kafin ki haukace a shiriritan so dinan ki koreshi."
Idanu na zare ta zabgomin harara.
"Inna wai ya suke da matar Kawu?"
"Abokik wasanta ne domin da babanshi da Mamanta uwarsu d'aya ubansu d'aya kuma yayarshi wanda suke uba d'aya abokin Habibu ne, agidansu Habibu ya had'u da ita dan Mamanshi ita ta rik'eta har zuwa aurenta."
"Ikon Allah amma duk shekarun da muka kwashe da Aliyu ban tab'a sanin hakan ba."
"To ina kike zuwa balle ki had'u da 'yan uwansa sannan shima Aliyun bai zuwa gidan Habibu sai hab'o."
Shiru na yi ina nazarin wannan lamari, ta ke naji duk damuwar da na ke ciki ya koma ba komi ba saboda tuno mugun halin Zainab da tasha gwadamin wanda nashajin Hajiya Inna na cewa d'aukosa ta yi wurin uwar goyonta.
'Wato mahaifiyar Aliyu bata da kirki kenan? Aikam na hak'ura da kai domin ina burin aure na ke inda Zan sami kwanciyar hankali ba kishiyarta ba.'
"Ban son shiga dogon tunani saboda lalurarki."
Na tsinkayi muryan Hajiya Inna daf da ni. Kallonta na yi har lokacin bata cikin walwala.
"Kiyi hak'uri Inna."
"Ya zamamin dole Khadijatu sai dai DAMUWATA shi ne na yarda surikata gudan jinina d'aya tilo zata zamemin abokiyar gaba."
"Ban gane ba Inna? Kina nufin su Mama Indo ba surukanki ba ne?"
"Surukaina ne amma duk kan mazajensu 'ya'yan uwar gidan Alhaji ce wacce ta rasu ta barmin su duk suna k'ananu, Habibu shi ne yarona na shida kuma shi ne ya rayu har naga aurensa domin yayunsa da k'anninsa daga sun taso suke mutuwa domin babban yayarsa na daf da yin aure ya sami hatsarin mota ya mutu nasan kin tuna lokacin."
Eh na tuna da kawu Hamza, Allah ya ji kansu da Rahma "
"Amin.
"To yau kinji yarda na ke da su Balarabe."
"Allahu albar, sannu Inna, lallai ke ta daban ce, Allah ya biyaki da khairan."
"Amin ya rabbi."
"A gaskiya su Mama Indo nada ladabi sama da Zainab sam ba wanda zaice ba ke ce kika haifi mazajensu ba."
"D'iyoyin tarbiyya kenan, sannan sun samu mazaje tsayayyu masu jajircewa akan abin da suke so dole abi ba irin Habibu ba da gata ya yiwa yawo ya ke ganin matarsa ba komi ta ke yimin ba saima ganin ni ce nacika fad'a da saka ido."
"Shi Kawun ke kallonki da hakan?"
"Ya wuce kokwanto Khadijatu domin yanzu indan da gabansa hakan ya faru wallahi tsaf bayar matarsa zaibi ya yi ta k'unci na tozarta masa iyali gaban mutane."
"In haka ne kam da sake wallahi, ai lamarin uwa sama da komi ya ke, gashi wayayye da ilimi amma bai aiki da shi."
"Ki bari kawai Khadijatu, shi yasa na kance da shi halinsa d'aya da Hadi."
Kulle baki na yi idanu waje na ke girgiza mata kai murmushi ta yi kad'an ta ce "Na tabbata ko halinsu bai zo d'aya ba a wani abin zaizo domin ya yi nisa akan lamarin figaggiyar matarsa mai zubin zabbin daji da kanta kamar k'ullin maganin sanyi."
Dariya na kyale-kyale da shi tana tayani. Daga haka muka saki zancen domin nagano ta sanyo mana raha ne saboda bata son acigaba da zancen.
***
Ina cin abincin rana faten Irish ne ya ji hanta da ganyen ugun wanda su Fanta suka kawomin, sai hira mukeyi hankali kwance domin Hajiya Inna ta sami wucewa gida tunda ta ga isowarsu.
Mama ce ta shigo Uncle na biye da ita tare da Baba a bayansu. K'irjina ne ya harba ganin Baba domin na tabbata sai ya b'atamin rai kafin ya tafi.
"Kai dalla! Ku fice ku bata wuri ta sha iska, kunzo kun nanuk'eta da tik'a-tik'an jikinku ba mijin kwasa ko da ya ke duk jirgi d'aya ya kwasoku da ita ga kyau da wayewa ba mashin-shini, kai tir muku!."
Tashi su Fanta sukayi duk suka fice jikinsu a sanyaye, na kalli Uncle wanda na hango b'acin rai a idanunsa kwance sai kawai na fashe da kuka mai sauti ina kaiwa k'arfe gadon duka wanda ke nuni da takaicin da na ke ciki.
*TALLA.*
*Ina kuke Mata 'yan kwalisa masu bawa fatarsu 'yancinta musanman babban kadararku wato fuska. To ga dama ta zo muku cikin sauk'i wato samun kayan gyarar fuska da jiki mai inganci na organic wanda aka samar da su da abubuwa masu nagarta. Duk wacce K'uraje, Tabbai, Sunburn, kyafsi suka b'atawa fuska muna da maganin da fuskanta zai dawo fes, sumul, rangad'ad'au. Haka a fannin fatar jiki shima muna da kayan da zaiyi laushi, sulb'i tare da haske mai kyau. Ga kayan kamar haka:*
Sabulu (molato and black soap)
Scrub
Face cream
Oil
Body lotion
Shower gel
Kulachan
Humra (White and black)
Turaren tsugunon
Turaren kaya
Turaren wuta na d'aki
Garin d'a'a (domin k'an-k'aro martaban aure a turaka)
*Duk za'a samesu a farashi mai rahusa, mai buk'atar d'aya ko sari a tun-tub'emu a wad'annan numbers d'in 08132166848 ko 08147491137. Sai munjiku.*
[11/4, 5:42 PM] 💘: DAMUWATA (Sanin abin adona)
By Mrsjmoon
E.W.F.
https://youtu.be/v9iNYDvS8JM
Pls 'yan uwa ku dannamin subcribe a YouTube d'ina, nagode.
Page 21.
"Ke! Kuma me akayi miki kika b'are baki kamar faranti kina kukan iyashege, to maza ki rufe mana baki ko ingamu da ke ba ciwo ba ko mutuwa kikeyi zan iya taka gawarki na wuce ta kai ba ruwana."
Shiru na yi amma badan tsoron dukansa ba sai dan takaicin halinsa tare da tunanin yin kukana baida amfani.
"Dan an kira k'awayenki tik'a-tik'a shi ne abin yin kuka saboda Hurera ta gama sangartaki, ke yanzu dan Allah ko kunya bakiji kamarki kina kuka, inda a k'auye kike da yanzu kina da 'yay'ya bakwai zuwa goma amma dubeki zaune makar gar, to wallahi ki sani kwanaki kad'an ya rage in zar...
"Dan Allah Malam kayi shiru haka ban muji da abinda ya damemu tunda kai haka Allah ya yika baka gajiya da sababi mara ma'ana da ke janyo jin kunya."
"Hurera ni...
"Dan soyayyarka da mahaliccinmu ka daina fad'ar nan haka, haba dan Allah kai ko gajiya bakyayi da zance a gaban idanun kunya."
Tsuke baki ya yi yana aunawa Mama mugun kallo, kunya ce ta rufeni ganin yarda Uncle ya ke binsa da kallon banza, tabbas kallon ya haskomin karatun ruhinsa wato takaicin Baba mai jin tamkar a rufe rufeshi da duka.
"Uncle nagode da tarin d'awainiya Allah ya jik'an mahaifa ya kuma shirya maka zuri'a tare da gamawa lafiya cikin samuwar babban rabo ranar lahira."
Sai da ya yi gyaran murya sannan ya amsa lokacin har Mama ta amsa ya yin da Baba ya tsare giran sama da k'asa yana zabgomin harara.
"Bari inga Dr. Jalal."
Uncle ya furta batare da ya jira amsawarmu ba ya fice.
"Munafukin banza wai shi nan ya ji haushi na kori k'aninsa, to an koresun in zai iya ya rufeni da duka yaga inda tsiya ke zamaninta wallahi."
"Allah ya yi mana tsari da ganin tsiya."
"Amin."
Na amsa da sauri.
"Ya jikin naki?"
Baba ya ambata cikin taushin murya. Ban dauka da ni ta keyi ba shi yasa bance komi ba.
"Au dan kin samu na tambayi ciwon karyan da kikayi shi ne zaki maidani sokon banza?"
Kafin inyi magana Mama ta rigani da cewa "Gata nan ta warke ganin idanunka sai kuma me uban 'yan sababi."
"Hurera me yasa sam baki san darajar aure ba ne?"
"Sabon karatun sanin darajojin aure zamu koma makaranta muyo tare da kai domin kome ka kirani kaine malamina."
"Zan sab'a miki fa Hurera ba ruwana da Asibiti ne nan."
"Maza aikata abin yamad'i-d'i karo na biyu a safiyar nan a samu masu d'oraka a yanar gizo da bugawa a jaridu kaga ka zama dan wasan kwai-kwayo na zahiri kamar yarda sabon sunarka ya koma a unguwarka yanzu."
"Ni Malam Hadi kike kira da d'an drama?"
Banza Mama ta yi da shi, nikam tuni na juya baya tare da tura yatsuna cikim kunnuwana saboda na gaji da sauraren sababin Baba.
"Sai mun had'u a gida zan nuna miki nafi gaban iskancinki sannan kada kiga na d'aga darajarki a gaban abokan zamanki d'azun ki d'auka kin sameni ne a'a biyana zakiyi dan wallahi sai naci buhunar wake biyar domin na saka buri akan wanda sukayi satan sai reshe ya juye da mujiya dan haka sai ki shirya bi...
"Allah ya ganar da kai hanyar gaskiya."
Mama ta ambata tare da shigewa toilet ta barshi tsaye da baki bud'e, dariya ce ya zomin na kife fuska gudun kada ya jigoni na shiga uku
K'aran buga k'ofar ya sanarmin da Baba ya fice, numfashi na sauke ina auna lamuran Baba wanda na yanzu na ke d'orasu a mizanin rashin hankali.
"Astagafirullah."
Na ambata a hankali.
Shigowar Doctor, Uncle da su Beebah biye da su ya yi daidai da fitowar Mama daga toilet. Ya bani sallama tare da shawarwari agame da daina barin damuwa ko tunani na takuramu ni da Mama saboda su ne babban matsalolinmu.
Sosai Mama ta yi masa godiya, su Fanta suka tattara mana kaya muka fito. Ni da Mama tare da Bintu motar Uncle muka shiga ya yin da su Fiddausi suka shiga wanda suka zo a ciki Beebah ta ja, ta yi gaba Uncle ya rufa mata baya, akan hanya ya kira Hajiya Inna ya sanar mata da an sallamemu.
"Yawwa Alhaji sanar da Malam kada ya zama abin laifi duk da yasan za'ayi sallaman."
"To Mama."
Ni ya mik'owa wayar batare da ya furta kalma ba.
Sunar da naga an sanya Baban Nana na kira har ta tsinke ba'a d'auka ba, haka na yi ta kira sau ba adadi a k'arshe sai aka kashe wayar.
Mik'awa Uncle wayarsa na yi ya amsa batare da ya cemin uffan ba haka nima ban tofa ba.