Sashe 28
Damuwata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Fanta ta ambata tare da sake k'amk'ame Mama, lamarin da yaso karyamata zuciya amma sai ta soma addu'a cikin fitar sauti a hankali.
"To zaki wuce gida kuwa in har kuka zakizo kina sanya mutane."
"Uncle na kasa daurewa ne."
"Ki cigaba da ambatar addu'ar da kika sanarwa da Mama har ta sami jarumta."
Motsa kai ta yi tare da janye jikinta ta koma gefen Deejah ta wurin kanta ta zauna bakinta na motsi alamun addu'ar ta ke yi hannunta na yawo saman sumar Deejah.
***
"Yaya ka kwatantamin gidansu sai inje na dubo maka ita."
"K'anwata kinfi kowa sanin tsaron Hajiya."
"Zance mata zani gidan Aunty Zainab ce."
"Tsakanin gidan su Deejah da gidan Zainab da tazara mai nisa kafin kije ki dawo na tabbata Hajiya zata kira taji idan kinje kuma in kika soma zuwa gidan Zainab kina fita zata kira Hajiya ta sanar mata da kin fito kinga kenan lamarin ba mai sauki ba ne."
"Yaya yanzu ya za'ayi?"
"Bari ruwan ya kare sai in lallab'a na tafi da kaina."
"Bazaka iya ba Yaya, jikinka bai warke ba, kallifa yarda kake magana kana hutawa."
"Buguwar da na yi a hakarkari na ne keyimin zafi amma banjin ciwon komi bayan shi."
"Ka dai samo wani dibaran domin kaima na tabbata Hajiya baza ta barka ka fita a haka ba."
"Bari in sake kiran K'awarta ko zanyi dacen ta d'auka tunda ita nata wayar a kashe ya ke."
"Ok jaraba mugani "
Cikin jan tsaki ya jefar da wayar gefe.
"Bata dauka ba ko?"
"Ina cikin damuwa wallahi, narasa wanda zan kira na sami labarin Khadija."
"Mijin Aunty Zainab mana tunda kace, ka ganinsu tare."
"Kuma hakan ya kamata, nagode k'anwata."
Kiran number ya yi aka d'auka bayan gaisuwa sai ya rasa abinda zaice masa.
"Ya dai Aliyu?"
"Yallab'ai dama zance ya wurin su d'iyarka?"
"Oh Khadija?"
"Eh."
"Wallahi yanzu Baba ke sanarmin Mamanta bata da lafiya tana Asibiti."
"Ya rabbi, shiya ban samun wayarta kenan?"
"Eh zaiyiwu hakan ne."
"Allah yabata lafiya."
"Amin."
"Wani Asibiti ne?"
"Ban sani ba dan nima yanzu zan tafi na d'auki Baba mu tafi amma in na isa zan kiraka."
"To nahode."
Ok bakomi."
Sauke wayar ya yi tare da lumshe ido.
"Itama bata da lafiya ne ?"
"Mamanta ne a ka kwantar."
"Ayya Allah ya sa kaffara ce."
"Amin."
"Amma Yaya kana son janyowa kanka ruwa fa."
"Kinga kada ki sake maganar sokuwar nan ya hadamu."
"To ai bance komi ba "
"Gara dai haka."
"Salma fito hakanan ki barsa ya huta."
"To Hajiya."
Gyad'a mata kai ya yi ta fice tana murmushi.
***
Habibu ya cika fam da takaicin Baba akan zagin dake da durawa Uncle duk kuwa da bai sanshi ba amma ji yake tamkar d'an uwansa ake zagi ga shi Baba Umaru na ji amma bai ce kanzil ba hasalima wani littafin addu'o'i ya bud'e yana bita. Zuwa can Habibu ya ce "Haba Malam Hadi kana Malami amma ake jin wannan ashariyar abakinka dan kawai makwafci ya nuna kulawa ga iyalinka abinda na yi imani kai bazaka iya yimusu ba."
"Kai Habibu ban son rashin ta ido kaji ko? Shin kasan muhinmancin iyali kuwa?"
"A'a sai ka koyar da ni irin yarda ka san naka."
"Akul Habibu, kada na kuma jin bakinka."
"To Baba."
"Baba wallahi mutumin nan ya rainani, dan Allah kayi masa iyaka da iyalina, kwata-kwata ban son su sake mu'amala da shi domin ina jin ana maganar arzikinsa bana halas ba ce wata kilama so ya ke ya shanyemin jininsu, ya kaini ya baro."
"A'uzubillahi! Me ya kawo wannan maganar kuma Hadi?"
"Baba wallahi lamarin ne ya kasa kwantamin dubi da yarda yake kashewa Uwani kud'i duba fa ka ga wayar dubbunnan kud'ad'e da ya mallaka mata tamkar bai san zafin nemansu ba."
Mik'a hannu Baba Umaru ya yi ya amsa wayar ya jefa a aljihu batare da ya duba ba.
Hararan gefen ido Baba ya maka masa domin yaso saida wayarce shi yasa ya d'auke amma azal ya sanyashi yin maganarta ta zamo haramiyarsa.
"Hadi duk yarda makwafci ya ce shi d'in d'an uwa ne saboda shaidansa kad'ai zai iya kaika gidan Aljanna, ina tunasar da kai abinda ka sani kake takewa shi ne ka kyautatawa makwafci zato tare da rufa masa asiri musanman ga wanda ya bada kula ga iyalinka."
"To Baba amma ai musulinci bai bashi damar shigamin gida lokacin da bana nan ba, ko dan gudun gudun zargin mutane."
"Abinda na ke tunasar da kai kenan cewa ka kyautata masa zato kuma zanyiwa tufka hanci akan irin haka bazai sake faruwa ba tunda ya wuce iyaka, shiga gida yana baligi."
"Yawwa Baba kaima dai kagani."
"Zan bincika lamarin tundaga farko kafin in yanke hukunci."
"Ai wallahi ko da ka ja masa kunni sai na makashi a kotu."
"Kotu!?"
Habibu ya amtaba batare da ya sani ba.
"Eh can zan kaishi kuma sai ya gane shayi ruwa ne, dani yake zancen."
"Wato in na fahinceka dama can kuna da jika'kkiya kenan?"
Baba Umaru ya furta cikin shakewar murya domin ya soma gajiya da rashin kangadon Baba.
"A'a kawai shiga lamarin iyalinsa da ya yi na ke son ayi masa iyaka da su."
"To ba amfanin sakani cikin lamarin da kayi kenan?"
"Da shi mana Baba, kawai rubdugu zanyi masa ya gane ba da wasa na ke yi ba."
"Hadi in kanayiwa Allah da mahaifanka ka janye maganar kai makwafcinka kotu."
"Baba ka...
"In har na isa da in sanya baki cikin lamarin to ka janye."
"Shi kenan amma wallahi sai ya fita harkan iyalina."
"Naji zai fita."
Daga haka shiru ya ziyarci motar, Habibu ya ja tsaki kad'an cikin zabgowa Baba harara ta mirror, dak'uwa Baba ya auno masa batare da ya bari Baba Umaru ya gani ba, wani hararan Habibu ta bunko masa tare da cije lips.
"Kayi koyin halin girma tamkar mahaifinka."
"Kafi kowa sanin hakinsa kaf na kafe saidai kayiwa kanka wa'azin kula da iyali."
"Baba yaushe Habibu ya koma mara kunya haka?"
"Habibu ban son na sake jin amonka."
"To Baba."
Ga masifa a bakin Baba amma Baba Umaru ya katange damar amayosu saboda bakin rijiya ba wurin wasan makaho ba ne.
Koda suka isa Asibitin Uncle ya koma gida Baba ya yi ta hura hanci Baba domin bai so hakan ba, Baba Umaru dai na kallonsa cikin nazari ya yin da Habibu ke ta zabga masa harara cike da takaicin hanashi maganar da Baba ya yi da sai ya wanke Baba tas da ruwan kalamai.
Abin mamaki ko sannu da jiki Baba baiyiwa Mama ba da ya iso ya sameta cikin k'oshin lafiya sama da d'azun da ya barta cikin godiyan Allah, balle kuma ya yiwa Deejah da ke kwance tamkar gawa. Halin ko in kulan da ya nuna ya tab'a zuciyar Mama amma ganin su Baba Umaru sai ta kauda duk bacin ranta saboda matsayin su na da banne.
Addu'a Baba Umaru ya ke ta tofawa Deejah yana rik'e da hannunta na dama cike da tarin damuwa zuwa can ya juyo ya tambayi Mama yarda lamarin ya kasance.
Abinda Likitoci suka sanar mata ta fad'a masa ya jinjina kai ya sake tambayarta yarda ita kuma ciwonta ya sameta nanma abinda ta sani da wanda Uncle ya bata labari ta fad'a masa tare da taimakon Malamin nan duk ta sanar da shi sai dai bata tona tijarar da Baba ya yi ba.
"Alhamdulillah zanje gidan Malamin na yi masa godiya domin ya taimakeni wurin bawa amanata kariya, Allah ya biyashi da gidan Aljanna."
"Amin ya rabbi."
Habibu ya amsa da sauri yana aunawa Baba wani kallo.
K'ara hade rai Baba ya yi tamkar wanda aka aikowa da sak'on mutuwa.
Kallonsa Mama ta yi ta ce "Kaima Malam ka je ka gode masa domin ya taimakemu iya taimako."
"Zanje, ko ba Malam Isuhu mai gudun duniya ba?."
"Eh, haka fa sunarsa ya ke."
"Au a shema d'ana ne, kai masha Allah, ai ya yo gadon sanin lak'anin korar shed'anu wurin mahaifinsa Malam Hassan, madallah da d'an arziki irin albarka."
"Baba ka sanshi kenan?"
"Eh na sanshi Hurera, mahaifinsa mutumina ne kafin Allah ya yi masa rasuwa."
"Allah sarki gaskiya ya zamo Malami na gari."
Da sauri Baba ya kalleta ta sauke masa murmushi ya kauda kai yana tsinewa Uncle da Malam Isuhu cikin ransa.
Ni zan koma na aiko Habibu da sak'o wanda idan ta farka shi zata soma sha, insha Allah jikinta zai dawo dai-dai batare da firgicin komi ba balle kufcewar tunani."
"To Baba, nagode."
"Ke ma ki sha idan ya kawo sannan Hajiya zata zo bayan sallar magriba ta kwana da ku saboda kema ba lafiyar ce ta wadaceki ba."
"To Baba, Allah ya k'ara girma."
"Amin, Allah yasa kaffara ce."
"Amin."
"Hadi zamu barka a nan ne?"
"Eh Baba."
"To ayi ta hak'uri kada ka tada zancen nan a Asibiti saboda jama'a, idan sun dawo gida zanzo da kaina mu zauna kuma ka tabbatar ka bawa Malam Isuhu hadin kai anyiwa gidan nan addu'o'in da ya kamata dan na fahimce akwai damuwa cikinsa."
"To, za'ayi."
"Madallah, nabarku lafiya."
Suka fice da Habibu Baba ya rakasu da mugun kallo tamkar zai cinyesu da idanu.
"Malam uban nawa kake harara?"
"Kinga Hurera ki fita idona in rufe."
"Allah baka hak'uri amma ka sani ba zan tab'a hararan naka mahaifan ba."
Tana ambatar haka ta juya masa baya tana mai ambaton sunar Allah dan samun rinjaye akan zuciyarta domin kallon da ya raka Baba Umaru da shi ya sosa ranta.
"Ke! fice ki bamu wuri munafuka banza kawai, 'yar rahoto."
Da sauri Fanta ta fice tana sharan hawaye dan tana kwance gefen Deejah.
"Hurera kin san Allah na kara ganin Alhaji Muhseen a Asibitin nan sai ranki ya b'aci."
"Malam wai me kake nufi ne? Yanzu Uwata na kwance tamkar gawa amma ka kasa yi mata sannu da jiki balle addu'a amatsayinka na Malamin addini?"
"Uwanki kika ce ko uwata?"
"Tawa ce ba taka ba."
"To sai ki tsukemin bakinki mai kama da Asusu ki saurari kashedina wanda ke makwafin wajibi a bishi in ana son ganin dai-dai."
"Malam dan Allah ka tafi kaina ya somin ciwo."
"Yanzu kika soma ganin ciwon kai in dai bazaki bi abinda na ke so ba."
"Me kake nufi?"
"To zaki wuce gida kuwa in har kuka zakizo kina sanya mutane."
"Uncle na kasa daurewa ne."
"Ki cigaba da ambatar addu'ar da kika sanarwa da Mama har ta sami jarumta."
Motsa kai ta yi tare da janye jikinta ta koma gefen Deejah ta wurin kanta ta zauna bakinta na motsi alamun addu'ar ta ke yi hannunta na yawo saman sumar Deejah.
***
"Yaya ka kwatantamin gidansu sai inje na dubo maka ita."
"K'anwata kinfi kowa sanin tsaron Hajiya."
"Zance mata zani gidan Aunty Zainab ce."
"Tsakanin gidan su Deejah da gidan Zainab da tazara mai nisa kafin kije ki dawo na tabbata Hajiya zata kira taji idan kinje kuma in kika soma zuwa gidan Zainab kina fita zata kira Hajiya ta sanar mata da kin fito kinga kenan lamarin ba mai sauki ba ne."
"Yaya yanzu ya za'ayi?"
"Bari ruwan ya kare sai in lallab'a na tafi da kaina."
"Bazaka iya ba Yaya, jikinka bai warke ba, kallifa yarda kake magana kana hutawa."
"Buguwar da na yi a hakarkari na ne keyimin zafi amma banjin ciwon komi bayan shi."
"Ka dai samo wani dibaran domin kaima na tabbata Hajiya baza ta barka ka fita a haka ba."
"Bari in sake kiran K'awarta ko zanyi dacen ta d'auka tunda ita nata wayar a kashe ya ke."
"Ok jaraba mugani "
Cikin jan tsaki ya jefar da wayar gefe.
"Bata dauka ba ko?"
"Ina cikin damuwa wallahi, narasa wanda zan kira na sami labarin Khadija."
"Mijin Aunty Zainab mana tunda kace, ka ganinsu tare."
"Kuma hakan ya kamata, nagode k'anwata."
Kiran number ya yi aka d'auka bayan gaisuwa sai ya rasa abinda zaice masa.
"Ya dai Aliyu?"
"Yallab'ai dama zance ya wurin su d'iyarka?"
"Oh Khadija?"
"Eh."
"Wallahi yanzu Baba ke sanarmin Mamanta bata da lafiya tana Asibiti."
"Ya rabbi, shiya ban samun wayarta kenan?"
"Eh zaiyiwu hakan ne."
"Allah yabata lafiya."
"Amin."
"Wani Asibiti ne?"
"Ban sani ba dan nima yanzu zan tafi na d'auki Baba mu tafi amma in na isa zan kiraka."
"To nahode."
Ok bakomi."
Sauke wayar ya yi tare da lumshe ido.
"Itama bata da lafiya ne ?"
"Mamanta ne a ka kwantar."
"Ayya Allah ya sa kaffara ce."
"Amin."
"Amma Yaya kana son janyowa kanka ruwa fa."
"Kinga kada ki sake maganar sokuwar nan ya hadamu."
"To ai bance komi ba "
"Gara dai haka."
"Salma fito hakanan ki barsa ya huta."
"To Hajiya."
Gyad'a mata kai ya yi ta fice tana murmushi.
***
Habibu ya cika fam da takaicin Baba akan zagin dake da durawa Uncle duk kuwa da bai sanshi ba amma ji yake tamkar d'an uwansa ake zagi ga shi Baba Umaru na ji amma bai ce kanzil ba hasalima wani littafin addu'o'i ya bud'e yana bita. Zuwa can Habibu ya ce "Haba Malam Hadi kana Malami amma ake jin wannan ashariyar abakinka dan kawai makwafci ya nuna kulawa ga iyalinka abinda na yi imani kai bazaka iya yimusu ba."
"Kai Habibu ban son rashin ta ido kaji ko? Shin kasan muhinmancin iyali kuwa?"
"A'a sai ka koyar da ni irin yarda ka san naka."
"Akul Habibu, kada na kuma jin bakinka."
"To Baba."
"Baba wallahi mutumin nan ya rainani, dan Allah kayi masa iyaka da iyalina, kwata-kwata ban son su sake mu'amala da shi domin ina jin ana maganar arzikinsa bana halas ba ce wata kilama so ya ke ya shanyemin jininsu, ya kaini ya baro."
"A'uzubillahi! Me ya kawo wannan maganar kuma Hadi?"
"Baba wallahi lamarin ne ya kasa kwantamin dubi da yarda yake kashewa Uwani kud'i duba fa ka ga wayar dubbunnan kud'ad'e da ya mallaka mata tamkar bai san zafin nemansu ba."
Mik'a hannu Baba Umaru ya yi ya amsa wayar ya jefa a aljihu batare da ya duba ba.
Hararan gefen ido Baba ya maka masa domin yaso saida wayarce shi yasa ya d'auke amma azal ya sanyashi yin maganarta ta zamo haramiyarsa.
"Hadi duk yarda makwafci ya ce shi d'in d'an uwa ne saboda shaidansa kad'ai zai iya kaika gidan Aljanna, ina tunasar da kai abinda ka sani kake takewa shi ne ka kyautatawa makwafci zato tare da rufa masa asiri musanman ga wanda ya bada kula ga iyalinka."
"To Baba amma ai musulinci bai bashi damar shigamin gida lokacin da bana nan ba, ko dan gudun gudun zargin mutane."
"Abinda na ke tunasar da kai kenan cewa ka kyautata masa zato kuma zanyiwa tufka hanci akan irin haka bazai sake faruwa ba tunda ya wuce iyaka, shiga gida yana baligi."
"Yawwa Baba kaima dai kagani."
"Zan bincika lamarin tundaga farko kafin in yanke hukunci."
"Ai wallahi ko da ka ja masa kunni sai na makashi a kotu."
"Kotu!?"
Habibu ya amtaba batare da ya sani ba.
"Eh can zan kaishi kuma sai ya gane shayi ruwa ne, dani yake zancen."
"Wato in na fahinceka dama can kuna da jika'kkiya kenan?"
Baba Umaru ya furta cikin shakewar murya domin ya soma gajiya da rashin kangadon Baba.
"A'a kawai shiga lamarin iyalinsa da ya yi na ke son ayi masa iyaka da su."
"To ba amfanin sakani cikin lamarin da kayi kenan?"
"Da shi mana Baba, kawai rubdugu zanyi masa ya gane ba da wasa na ke yi ba."
"Hadi in kanayiwa Allah da mahaifanka ka janye maganar kai makwafcinka kotu."
"Baba ka...
"In har na isa da in sanya baki cikin lamarin to ka janye."
"Shi kenan amma wallahi sai ya fita harkan iyalina."
"Naji zai fita."
Daga haka shiru ya ziyarci motar, Habibu ya ja tsaki kad'an cikin zabgowa Baba harara ta mirror, dak'uwa Baba ya auno masa batare da ya bari Baba Umaru ya gani ba, wani hararan Habibu ta bunko masa tare da cije lips.
"Kayi koyin halin girma tamkar mahaifinka."
"Kafi kowa sanin hakinsa kaf na kafe saidai kayiwa kanka wa'azin kula da iyali."
"Baba yaushe Habibu ya koma mara kunya haka?"
"Habibu ban son na sake jin amonka."
"To Baba."
Ga masifa a bakin Baba amma Baba Umaru ya katange damar amayosu saboda bakin rijiya ba wurin wasan makaho ba ne.
Koda suka isa Asibitin Uncle ya koma gida Baba ya yi ta hura hanci Baba domin bai so hakan ba, Baba Umaru dai na kallonsa cikin nazari ya yin da Habibu ke ta zabga masa harara cike da takaicin hanashi maganar da Baba ya yi da sai ya wanke Baba tas da ruwan kalamai.
Abin mamaki ko sannu da jiki Baba baiyiwa Mama ba da ya iso ya sameta cikin k'oshin lafiya sama da d'azun da ya barta cikin godiyan Allah, balle kuma ya yiwa Deejah da ke kwance tamkar gawa. Halin ko in kulan da ya nuna ya tab'a zuciyar Mama amma ganin su Baba Umaru sai ta kauda duk bacin ranta saboda matsayin su na da banne.
Addu'a Baba Umaru ya ke ta tofawa Deejah yana rik'e da hannunta na dama cike da tarin damuwa zuwa can ya juyo ya tambayi Mama yarda lamarin ya kasance.
Abinda Likitoci suka sanar mata ta fad'a masa ya jinjina kai ya sake tambayarta yarda ita kuma ciwonta ya sameta nanma abinda ta sani da wanda Uncle ya bata labari ta fad'a masa tare da taimakon Malamin nan duk ta sanar da shi sai dai bata tona tijarar da Baba ya yi ba.
"Alhamdulillah zanje gidan Malamin na yi masa godiya domin ya taimakeni wurin bawa amanata kariya, Allah ya biyashi da gidan Aljanna."
"Amin ya rabbi."
Habibu ya amsa da sauri yana aunawa Baba wani kallo.
K'ara hade rai Baba ya yi tamkar wanda aka aikowa da sak'on mutuwa.
Kallonsa Mama ta yi ta ce "Kaima Malam ka je ka gode masa domin ya taimakemu iya taimako."
"Zanje, ko ba Malam Isuhu mai gudun duniya ba?."
"Eh, haka fa sunarsa ya ke."
"Au a shema d'ana ne, kai masha Allah, ai ya yo gadon sanin lak'anin korar shed'anu wurin mahaifinsa Malam Hassan, madallah da d'an arziki irin albarka."
"Baba ka sanshi kenan?"
"Eh na sanshi Hurera, mahaifinsa mutumina ne kafin Allah ya yi masa rasuwa."
"Allah sarki gaskiya ya zamo Malami na gari."
Da sauri Baba ya kalleta ta sauke masa murmushi ya kauda kai yana tsinewa Uncle da Malam Isuhu cikin ransa.
Ni zan koma na aiko Habibu da sak'o wanda idan ta farka shi zata soma sha, insha Allah jikinta zai dawo dai-dai batare da firgicin komi ba balle kufcewar tunani."
"To Baba, nagode."
"Ke ma ki sha idan ya kawo sannan Hajiya zata zo bayan sallar magriba ta kwana da ku saboda kema ba lafiyar ce ta wadaceki ba."
"To Baba, Allah ya k'ara girma."
"Amin, Allah yasa kaffara ce."
"Amin."
"Hadi zamu barka a nan ne?"
"Eh Baba."
"To ayi ta hak'uri kada ka tada zancen nan a Asibiti saboda jama'a, idan sun dawo gida zanzo da kaina mu zauna kuma ka tabbatar ka bawa Malam Isuhu hadin kai anyiwa gidan nan addu'o'in da ya kamata dan na fahimce akwai damuwa cikinsa."
"To, za'ayi."
"Madallah, nabarku lafiya."
Suka fice da Habibu Baba ya rakasu da mugun kallo tamkar zai cinyesu da idanu.
"Malam uban nawa kake harara?"
"Kinga Hurera ki fita idona in rufe."
"Allah baka hak'uri amma ka sani ba zan tab'a hararan naka mahaifan ba."
Tana ambatar haka ta juya masa baya tana mai ambaton sunar Allah dan samun rinjaye akan zuciyarta domin kallon da ya raka Baba Umaru da shi ya sosa ranta.
"Ke! fice ki bamu wuri munafuka banza kawai, 'yar rahoto."
Da sauri Fanta ta fice tana sharan hawaye dan tana kwance gefen Deejah.
"Hurera kin san Allah na kara ganin Alhaji Muhseen a Asibitin nan sai ranki ya b'aci."
"Malam wai me kake nufi ne? Yanzu Uwata na kwance tamkar gawa amma ka kasa yi mata sannu da jiki balle addu'a amatsayinka na Malamin addini?"
"Uwanki kika ce ko uwata?"
"Tawa ce ba taka ba."
"To sai ki tsukemin bakinki mai kama da Asusu ki saurari kashedina wanda ke makwafin wajibi a bishi in ana son ganin dai-dai."
"Malam dan Allah ka tafi kaina ya somin ciwo."
"Yanzu kika soma ganin ciwon kai in dai bazaki bi abinda na ke so ba."
"Me kake nufi?"