Sashe 29
Damuwata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Abin da tunaninki ya baki."
"Kai ne sanadin ciwo na kenan?"
"Wannan kuma kanki akeji nidai na sanar miki kada Alhaji Muhseen ya sake shigamin lamarin iyali."
"Yanzu kuwa yasoma shiga saboda wata rana surukinka ne shi."
"Au Allah?"
"Insha Allah."
"Zamuga ni."
"Insha Allah khairan gamu gani."
"Shi kenan Hurera ki nunawa duniya ban isa da ke ba kinji?"
"Malam kayi nazari domin wallahi Alhaji Muhseen mutumin kirki ne, kai shaida ne domin kafin zuwar lokacin nan kasha sanarmin da cewa baka tab'a ganin mai kud'i mara girman kai da sanin darajan makwafci irin shi ba."
"Au saboda yana da arziki shi yasa kike son ya auri Uwani?"
Shiru Mama ta yi bata amsa ba.
"Shi ne irin mijin da kikeyi mata addu'ar samu kenan?"
Ya furta cikin cillowa Mama kallon banza.
"Eh."
Ta ambata kai tsaye.
"To ina tayata murna."
Kafin Mama ta san abin cewa ya buga babban rigarsa ya fice.
Dafe goshinta ta yi saboda jiri da ta soma gani. Ba dan Fanta ta shigo ba tabbas da fad'owa k'asa zatayi daga saman kujerar da ta ke zaune. Cikin sa'a Nurse ta shigo ita ta taimwa Fanta suka dorata gefen gadon Deejah, cikin gaggawa aka kawo wani dago d'akin aka maidata kansa, Likitoci biyu suka rufu kanta, cikin mintoci da basu gaza goma ba ta samu barci.
Fad'a Dr. jalal ke yi tamkar zai ari baki a k'arshe ya bada umurnin kada a sake barin Baba shigo masa Asibiti, har masu gadi ya sanarwa wannan kashedi.
***
Kamar yarda Malam Isuhu ya ambata bayan sallar la'asar ya iso gidan Uncle ya fito suka shiga cikin gidan su Deejah suka raba Qur'ani har da Uncle suka soma karatu da ya ke suna da yawa awa d'aya da rabi suka kammala suka soma jero addu'a d'aya bayan d'aya suna daf da kammalawa Baba ya fad'o gidan afujan-jan. Duk yarda yaso yin tijara kasawa ya yi darajar gamin Al-qur'ani sai ya sami kansa da zama aka shafa addu'ar da shi. Kallon da Malam Isuhu keyi masa ne ya yasa jikinsa k'ara yin sanyi.
Uncle ne ya mik'awa Malam hannu sukayi musabaha tare da mik'a godiya, ya dubi Baba ya russuna cikin ban girma ya gaisar da shi ganin karramashin da Uncle ya yi sai ya saki rai ya soma washe bakin dole.
Haka d'aliban suka soma gaisar junarsu ta hanyar musabaha daga k'arshe suka russunawa suka gaida Malaminsu da su Uncle, daga nan suka fice gidan ya rage saura su uku.
"Malam Yusuf ga mai gidan nan ni albarkacin makwaftaka ya sa na jagoranci lamarin."
"Malam Hadi kai ne maigidan Hajiya?"
"Eh, Hurera ba, ai bataje Hajji ba Malam."
"Inda rai da rabo Baba."
Uncle ya mabata cikin murmushi.
Tsaki Baba ya ja ya juya zai fice sai dai maganar Malam Isuhu ya dakatar da shi ya juyo a hanzarce.
"Me ka ce?"
"Cewa na yi na kudiri aniyar maidawa wanda ke son cutar da Hajiya aniyarsa."
"Haba Malam Isuhu kana masanin addini amma kana son saka sharri da sharri, ka da fa kamanta yin hakan d'aukan zunubi ne domin ba lallai ne ya sauka kan wanda ya aikata d'in ba."
"Idan na aikata tabbas sai ya sauka kan wanda ya yi tare da wanda ya yi sanadiin aiki."
"Kuma dai?"
"Eh, saboda rama mugunta ga macuci ba laifi ba ne."
"Kagane Malam Isuhu mubar maganar zanzo gida na sameka sai muyi maganar anatse mai cike da fahimtar juna."
Kallon k'urillah Malam Isuhu ya kafeshi da shi sai kuma ya murmusa tare da motsa kai ya kalli Uncle ya ce "Insha Allah sauka na k'arshe Malam Hadi zai jagoranta shi da d'alibansa."
"Malam da ka cikashe aikinka kawai."
"Alhaji ai tare dani za'a yi har da kai tamkar dai yarda mukayi wannan tare manufata shima Malam Hadi ya kamata ya taimaka da irin nasa baiwar tunda shi ne jigon gidan."
"Haka ne, to Allah ya kaimu lokacin."
"Amin."
Uncle ya amsa Baba kam kai ya wuya gefe zuciyarsa tamkar wuta saboda takaicin ya sa tijarar da ya zo da shi.
Sake yin musabaha da Baba Malam Isuhu ya yi Uncle ya rufa masa baya suka bar Baba tsaye tamkar an dasashi.
"Ya kamata in san inda kaina keyimin ciwo tun kafin gwad'o ya yi min k'afa."
Baba ya ambata cikin zare idanu, ganin Uncle ya dawo sai ya dai-daita natsuwarsa tare dajin wani kalan tak'ama ya ziyarce shi.
"Baba dan Allah kayi hak'uri akan laifin dana aikata maka na shiga lamarin iyalinka kai tsaye batare da na nemi izininka ba, hakan ya faru ne saboda halin dana ganta a ciki wanda tunanin nemanka ya b'acemin sai bayan na kaita Asibiti amma insha Allah hakan ba zai sake faruba, ka ya femin dan Allah."
Shiru ya yi yana kallon Uncle a d'age cikin hura hanci.
"Ni makwafci na gari ne ban aikata hakan don muzguna maka ba sai dan taimako irin ta makwafci na kwarai."
Ya sake ambatar haka a ladafce.
"Shi kenan ya wuce amma ka sani daga yau ban amince na sake ganin kafafunka a cikin gidan iyalina ba tunda ba gidan gala ba ne."
"Insha Allah zan kiyaye."
Tsaki ya ja, Uncle ya kalle shi da sauri domin tsaki nadaga cikin abinda ke fusatashi.
"Tunda kai kayi kid'an to kai zakayi rawar ba ruwan Hadi ciki."
"Ban fahinceka ba Baba?"
"Munufata tunda kai ka kaisu Asibiti ba zanyi asarar ko taro ba, kai da kaja ruwar kai zai duka."
Murmushi Uncle ya yi cikin jinjina halin Baba wanda samuwar lamarin yasa shi ganewa.
"Wannan ba komi ba ne Baba ai yiwa wani aka ce yiwa kai ne."
"To madallah, zaka iya ficemin a gida."
Wani murmushin Uncle ya kuma yi, ya karkace a ya tura hannu a aljihu ya ciro kud'i yan dari biyar biyar masu yawa ya russuna ya mik'awa Baba, wani kallon banza ya saukewa kudin amma a zahiri godiya ya ke gabga masa cikin ransa ya yi hakan ne dan kare marbata.
"Na me ye wannan?"
"Ihisanin dai dana saba yi maka ne na aiwatar amma ba dan wani manufa na daban ba."
"Nagode, Allah ya rubuce "
Ya furta cikin damk'e kud'in.
"Amin Baba."
Sukayi sallama cikin wal-wala lamarin da ya yi ta bawa Uncle dariya.
'Wato kudi masu sayo martaba da k'arfi da yaji.'
Cikin ransa ya ambata yana kuma murmusawa.
"Halayyan Baban Khadijatu nada ban mamaki, gashi dai masanin ilimin addini amma in ya kwab'a wani abin tamkar bai tab'a zuwa makaranta ba balle ace yana koyarwa."
Ya furta cikin ransa. Su Bintu ya gani suna shiga mota wanda ya tabbatar Asibiti zasu, ya k'arasa wurin cikin wal-wala amma ganin yarda fuskansu ya ke cikin rashin wal-wala sai ya tsare gira, duk suka fito suna gaisar da shi bai amsaba sai idanu da ya zubawa Nafisa wacce ke hakimce a gidan baya bata fito ba.
"Ina zaki je?"
Ya jefo mata tambayar.
"Asibiti."
"Kai waye ba lafiya?"
Ya maido da tambayarsa kan su Beebah da ke tsai-tsaye
"Mama da Deejah."
Safina ta amsa masa.
Ya juyo kan Nafisa kafin ya bud'e baki ta rigashi cewa "Makwafci ko me ya yi maka na aibu ya kamata ka saka masa da khairan dan koyi da halin Manzon Allah."
"Sallallahu Alaihi Wasallam."
Ya ambata tare da su Beebah.
"Abban Hafiz ina fatar daga yau fushin ya k'are?"
Ta ambata a hankali wanda da alama shi kad'ai ya jiyo saboda ya matso jikin motar ya bawa su Bintu baya.
"Allah ya kiyaye hanya."
Ya ambata tare da mik'a mata kudi "Ku saya musu kayan marmari."
"Ok."
Ta amsa tana kallon cikin idanunsa, murmushi ya sauke mata ta maida masa da martani. Yana tsaye suka fice inda Beebah ce ke jan motar.
"Allah yasa tuban gaskiya kikayi dan na san waye ke Nafisat idan kin so shirya tsiya."
"Alhaji gashi inji wani mutum ya ce abaka idan ka dawo."
Mai gadi ya ambata cikin miko masa Emblem.
Amsa yi ya ya nufi cikin gida yana kallon agogon da ke d'aure a tsin-tsiyar hannunsa na hagu.
*TALLA.*
*Ina kuke Mata 'yan kwalisa masu bawa fatarsu 'yancinta musanman babban kadararku wato fuska. To ga dama ta zo muku cikin sauk'i wato samun kayan gyarar fuska da jiki mai inganci na organic wanda aka samar da su da abubuwa masu nagarta. Duk wacce K'uraje, Tabbai, Sunburn, kyafsi suka b'atawa fuska muna da maganin da fuskanta zai dawo fes, sumul, rangad'ad'au. Haka a fannin fatar jiki shima muna da kayan da zaiyi laushi, sulb'i tare da haske mai kyau. Ga kayan kamar haka:*
Sabulu (molato and black soap)
Scrub
Face cream
Oil
Body lotion
Shower gel
Kulachan
Humra (White and black)
Turaren tsugunon
Turaren kaya
Turaren wuta na d'aki
Garin d'a'a (domin k'an-k'aro martaban aure a turaka)
*Duk za'a samesu a farashi mai rahusa, mai buk'atar d'aya ko sari a tun-tub'emu a wad'annan numbers d'in 08132166848 ko 08147491137. Sai munjiku.*
[10/30, 9:42 PM] 💘: DAMUWATA (Sanin abin adona)
By Mrsjmoon.
E.W.F.
https://youtu.be/v9iNYDvS8JM
Pls ku dannamin subcribe a YouTube chennel d'ina.🖕
*Alhamdulillah. Masha Allah. Congratulations Sister Aisha (Neesha). A yau Asabar anshiga daga cikin, matakin cikar kamala ya kammalu tsaf, Allah ya sanya khairan tare da dauwaman zaman lafiya, samuwar albarkan zuri'a d'ayyiba tare da so da k'auna mara iyaka, Allahumma Amin🤲.* Shafin na ki ne baki d'ayan shi, Amarya 'yar shagali😍.
Page 17.
*Aliyu.*
"Yaya kayi kyau."
"Wani kyau ga bak'in fata."
"Ai su ne asalin kyawa-wa."
"Fad'arki ba."
"Da gaske Yaya bak'in fata na da kyau kuma ina son bak'in mutum."
"Saboda kinganki fara ba."
"Allah ba haka ne, nidai ina son bak'in abu shi yasa ko a kala ne nafi zab'an bak'i."
"Ke ni rabani da surutu, sanarmin da gaisuwarki zuwa ga My Deejah."
"Au batare zamu tafi ba?"
"Ki rufamin asiri kada Hajiya ta hana fitar baki d'aya."
"Kasan Allah Yaya yau sai naga Khadija ido da ido."
Zama ya yi gefen gado ya tsira mata ido.
"Zan fita yanzu a cewar zani gidan su Alawiyya amso Note book d'ina sai ka fito mu wuce."
Kallonta dai ya ke yi batare da ya yi magana ba, ganin haka sai ta fice tana dariya.
"Salma matsala in ban barta taje ba bazata barni na huta da uban mitaba."
"Kai ne sanadin ciwo na kenan?"
"Wannan kuma kanki akeji nidai na sanar miki kada Alhaji Muhseen ya sake shigamin lamarin iyali."
"Yanzu kuwa yasoma shiga saboda wata rana surukinka ne shi."
"Au Allah?"
"Insha Allah."
"Zamuga ni."
"Insha Allah khairan gamu gani."
"Shi kenan Hurera ki nunawa duniya ban isa da ke ba kinji?"
"Malam kayi nazari domin wallahi Alhaji Muhseen mutumin kirki ne, kai shaida ne domin kafin zuwar lokacin nan kasha sanarmin da cewa baka tab'a ganin mai kud'i mara girman kai da sanin darajan makwafci irin shi ba."
"Au saboda yana da arziki shi yasa kike son ya auri Uwani?"
Shiru Mama ta yi bata amsa ba.
"Shi ne irin mijin da kikeyi mata addu'ar samu kenan?"
Ya furta cikin cillowa Mama kallon banza.
"Eh."
Ta ambata kai tsaye.
"To ina tayata murna."
Kafin Mama ta san abin cewa ya buga babban rigarsa ya fice.
Dafe goshinta ta yi saboda jiri da ta soma gani. Ba dan Fanta ta shigo ba tabbas da fad'owa k'asa zatayi daga saman kujerar da ta ke zaune. Cikin sa'a Nurse ta shigo ita ta taimwa Fanta suka dorata gefen gadon Deejah, cikin gaggawa aka kawo wani dago d'akin aka maidata kansa, Likitoci biyu suka rufu kanta, cikin mintoci da basu gaza goma ba ta samu barci.
Fad'a Dr. jalal ke yi tamkar zai ari baki a k'arshe ya bada umurnin kada a sake barin Baba shigo masa Asibiti, har masu gadi ya sanarwa wannan kashedi.
***
Kamar yarda Malam Isuhu ya ambata bayan sallar la'asar ya iso gidan Uncle ya fito suka shiga cikin gidan su Deejah suka raba Qur'ani har da Uncle suka soma karatu da ya ke suna da yawa awa d'aya da rabi suka kammala suka soma jero addu'a d'aya bayan d'aya suna daf da kammalawa Baba ya fad'o gidan afujan-jan. Duk yarda yaso yin tijara kasawa ya yi darajar gamin Al-qur'ani sai ya sami kansa da zama aka shafa addu'ar da shi. Kallon da Malam Isuhu keyi masa ne ya yasa jikinsa k'ara yin sanyi.
Uncle ne ya mik'awa Malam hannu sukayi musabaha tare da mik'a godiya, ya dubi Baba ya russuna cikin ban girma ya gaisar da shi ganin karramashin da Uncle ya yi sai ya saki rai ya soma washe bakin dole.
Haka d'aliban suka soma gaisar junarsu ta hanyar musabaha daga k'arshe suka russunawa suka gaida Malaminsu da su Uncle, daga nan suka fice gidan ya rage saura su uku.
"Malam Yusuf ga mai gidan nan ni albarkacin makwaftaka ya sa na jagoranci lamarin."
"Malam Hadi kai ne maigidan Hajiya?"
"Eh, Hurera ba, ai bataje Hajji ba Malam."
"Inda rai da rabo Baba."
Uncle ya mabata cikin murmushi.
Tsaki Baba ya ja ya juya zai fice sai dai maganar Malam Isuhu ya dakatar da shi ya juyo a hanzarce.
"Me ka ce?"
"Cewa na yi na kudiri aniyar maidawa wanda ke son cutar da Hajiya aniyarsa."
"Haba Malam Isuhu kana masanin addini amma kana son saka sharri da sharri, ka da fa kamanta yin hakan d'aukan zunubi ne domin ba lallai ne ya sauka kan wanda ya aikata d'in ba."
"Idan na aikata tabbas sai ya sauka kan wanda ya yi tare da wanda ya yi sanadiin aiki."
"Kuma dai?"
"Eh, saboda rama mugunta ga macuci ba laifi ba ne."
"Kagane Malam Isuhu mubar maganar zanzo gida na sameka sai muyi maganar anatse mai cike da fahimtar juna."
Kallon k'urillah Malam Isuhu ya kafeshi da shi sai kuma ya murmusa tare da motsa kai ya kalli Uncle ya ce "Insha Allah sauka na k'arshe Malam Hadi zai jagoranta shi da d'alibansa."
"Malam da ka cikashe aikinka kawai."
"Alhaji ai tare dani za'a yi har da kai tamkar dai yarda mukayi wannan tare manufata shima Malam Hadi ya kamata ya taimaka da irin nasa baiwar tunda shi ne jigon gidan."
"Haka ne, to Allah ya kaimu lokacin."
"Amin."
Uncle ya amsa Baba kam kai ya wuya gefe zuciyarsa tamkar wuta saboda takaicin ya sa tijarar da ya zo da shi.
Sake yin musabaha da Baba Malam Isuhu ya yi Uncle ya rufa masa baya suka bar Baba tsaye tamkar an dasashi.
"Ya kamata in san inda kaina keyimin ciwo tun kafin gwad'o ya yi min k'afa."
Baba ya ambata cikin zare idanu, ganin Uncle ya dawo sai ya dai-daita natsuwarsa tare dajin wani kalan tak'ama ya ziyarce shi.
"Baba dan Allah kayi hak'uri akan laifin dana aikata maka na shiga lamarin iyalinka kai tsaye batare da na nemi izininka ba, hakan ya faru ne saboda halin dana ganta a ciki wanda tunanin nemanka ya b'acemin sai bayan na kaita Asibiti amma insha Allah hakan ba zai sake faruba, ka ya femin dan Allah."
Shiru ya yi yana kallon Uncle a d'age cikin hura hanci.
"Ni makwafci na gari ne ban aikata hakan don muzguna maka ba sai dan taimako irin ta makwafci na kwarai."
Ya sake ambatar haka a ladafce.
"Shi kenan ya wuce amma ka sani daga yau ban amince na sake ganin kafafunka a cikin gidan iyalina ba tunda ba gidan gala ba ne."
"Insha Allah zan kiyaye."
Tsaki ya ja, Uncle ya kalle shi da sauri domin tsaki nadaga cikin abinda ke fusatashi.
"Tunda kai kayi kid'an to kai zakayi rawar ba ruwan Hadi ciki."
"Ban fahinceka ba Baba?"
"Munufata tunda kai ka kaisu Asibiti ba zanyi asarar ko taro ba, kai da kaja ruwar kai zai duka."
Murmushi Uncle ya yi cikin jinjina halin Baba wanda samuwar lamarin yasa shi ganewa.
"Wannan ba komi ba ne Baba ai yiwa wani aka ce yiwa kai ne."
"To madallah, zaka iya ficemin a gida."
Wani murmushin Uncle ya kuma yi, ya karkace a ya tura hannu a aljihu ya ciro kud'i yan dari biyar biyar masu yawa ya russuna ya mik'awa Baba, wani kallon banza ya saukewa kudin amma a zahiri godiya ya ke gabga masa cikin ransa ya yi hakan ne dan kare marbata.
"Na me ye wannan?"
"Ihisanin dai dana saba yi maka ne na aiwatar amma ba dan wani manufa na daban ba."
"Nagode, Allah ya rubuce "
Ya furta cikin damk'e kud'in.
"Amin Baba."
Sukayi sallama cikin wal-wala lamarin da ya yi ta bawa Uncle dariya.
'Wato kudi masu sayo martaba da k'arfi da yaji.'
Cikin ransa ya ambata yana kuma murmusawa.
"Halayyan Baban Khadijatu nada ban mamaki, gashi dai masanin ilimin addini amma in ya kwab'a wani abin tamkar bai tab'a zuwa makaranta ba balle ace yana koyarwa."
Ya furta cikin ransa. Su Bintu ya gani suna shiga mota wanda ya tabbatar Asibiti zasu, ya k'arasa wurin cikin wal-wala amma ganin yarda fuskansu ya ke cikin rashin wal-wala sai ya tsare gira, duk suka fito suna gaisar da shi bai amsaba sai idanu da ya zubawa Nafisa wacce ke hakimce a gidan baya bata fito ba.
"Ina zaki je?"
Ya jefo mata tambayar.
"Asibiti."
"Kai waye ba lafiya?"
Ya maido da tambayarsa kan su Beebah da ke tsai-tsaye
"Mama da Deejah."
Safina ta amsa masa.
Ya juyo kan Nafisa kafin ya bud'e baki ta rigashi cewa "Makwafci ko me ya yi maka na aibu ya kamata ka saka masa da khairan dan koyi da halin Manzon Allah."
"Sallallahu Alaihi Wasallam."
Ya ambata tare da su Beebah.
"Abban Hafiz ina fatar daga yau fushin ya k'are?"
Ta ambata a hankali wanda da alama shi kad'ai ya jiyo saboda ya matso jikin motar ya bawa su Bintu baya.
"Allah ya kiyaye hanya."
Ya ambata tare da mik'a mata kudi "Ku saya musu kayan marmari."
"Ok."
Ta amsa tana kallon cikin idanunsa, murmushi ya sauke mata ta maida masa da martani. Yana tsaye suka fice inda Beebah ce ke jan motar.
"Allah yasa tuban gaskiya kikayi dan na san waye ke Nafisat idan kin so shirya tsiya."
"Alhaji gashi inji wani mutum ya ce abaka idan ka dawo."
Mai gadi ya ambata cikin miko masa Emblem.
Amsa yi ya ya nufi cikin gida yana kallon agogon da ke d'aure a tsin-tsiyar hannunsa na hagu.
*TALLA.*
*Ina kuke Mata 'yan kwalisa masu bawa fatarsu 'yancinta musanman babban kadararku wato fuska. To ga dama ta zo muku cikin sauk'i wato samun kayan gyarar fuska da jiki mai inganci na organic wanda aka samar da su da abubuwa masu nagarta. Duk wacce K'uraje, Tabbai, Sunburn, kyafsi suka b'atawa fuska muna da maganin da fuskanta zai dawo fes, sumul, rangad'ad'au. Haka a fannin fatar jiki shima muna da kayan da zaiyi laushi, sulb'i tare da haske mai kyau. Ga kayan kamar haka:*
Sabulu (molato and black soap)
Scrub
Face cream
Oil
Body lotion
Shower gel
Kulachan
Humra (White and black)
Turaren tsugunon
Turaren kaya
Turaren wuta na d'aki
Garin d'a'a (domin k'an-k'aro martaban aure a turaka)
*Duk za'a samesu a farashi mai rahusa, mai buk'atar d'aya ko sari a tun-tub'emu a wad'annan numbers d'in 08132166848 ko 08147491137. Sai munjiku.*
[10/30, 9:42 PM] 💘: DAMUWATA (Sanin abin adona)
By Mrsjmoon.
E.W.F.
https://youtu.be/v9iNYDvS8JM
Pls ku dannamin subcribe a YouTube chennel d'ina.🖕
*Alhamdulillah. Masha Allah. Congratulations Sister Aisha (Neesha). A yau Asabar anshiga daga cikin, matakin cikar kamala ya kammalu tsaf, Allah ya sanya khairan tare da dauwaman zaman lafiya, samuwar albarkan zuri'a d'ayyiba tare da so da k'auna mara iyaka, Allahumma Amin🤲.* Shafin na ki ne baki d'ayan shi, Amarya 'yar shagali😍.
Page 17.
*Aliyu.*
"Yaya kayi kyau."
"Wani kyau ga bak'in fata."
"Ai su ne asalin kyawa-wa."
"Fad'arki ba."
"Da gaske Yaya bak'in fata na da kyau kuma ina son bak'in mutum."
"Saboda kinganki fara ba."
"Allah ba haka ne, nidai ina son bak'in abu shi yasa ko a kala ne nafi zab'an bak'i."
"Ke ni rabani da surutu, sanarmin da gaisuwarki zuwa ga My Deejah."
"Au batare zamu tafi ba?"
"Ki rufamin asiri kada Hajiya ta hana fitar baki d'aya."
"Kasan Allah Yaya yau sai naga Khadija ido da ido."
Zama ya yi gefen gado ya tsira mata ido.
"Zan fita yanzu a cewar zani gidan su Alawiyya amso Note book d'ina sai ka fito mu wuce."
Kallonta dai ya ke yi batare da ya yi magana ba, ganin haka sai ta fice tana dariya.
"Salma matsala in ban barta taje ba bazata barni na huta da uban mitaba."