Sashe 32
Damuwata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
*Ina kuke Mata 'yan kwalisa masu bawa fatarsu 'yancinta musanman babban kadararku wato fuska. To ga dama ta zo muku cikin sauk'i wato samun kayan gyarar fuska da jiki mai inganci na organic wanda aka samar da su da abubuwa masu nagarta. Duk wacce K'uraje, Tabbai, Sunburn, kyafsi suka b'atawa fuska muna da maganin da fuskanta zai dawo fes, sumul, rangad'ad'au. Haka a fannin fatar jiki shima muna da kayan da zaiyi laushi, sulb'i tare da haske mai kyau. Ga kayan kamar haka:*
Sabulu (molato and black soap)
Scrub
Face cream
Oil
Body lotion
Shower gel
Kulachan
Humra (White and black)
Turaren tsugunon
Turaren kaya
Turaren wuta na d'aki
Garin d'a'a (domin k'an-k'aro martaban aure.)
*Duk za'a samesu a farashi mai rahusa, mai buk'atar d'aya ko sari a tun-tub'emu a wad'annan numbers 08132166848 ko 08147491137. Sai munjiku.*
[10/31, 9:28 PM] 💘: DAMUWATA. (Sanin abin adona)
By Mrsjmoon.
E.W..F.
Page 18.
K'arar na'urar da ke nuna Deejah na da rai shi ne ya tashi su Mama barci a dai-dai lokacin kuma anata kiraye-kirayen sallar subahi. Dr. Jalal tare da Nurses ne suka shigo a hanzarce sakamakon jiyo k'aran na'urar. Fita su Mama sukayi suka tsaya bakin k'ofar cikin jan addu'o'i nasara.
Bayan wucewar wani lokaci Doctor ya fito da sauri Mama ta sha gabansa murmushi ya sauke mata ya nuna mata d'akin da hannu.
"Tafi ta ganki dan itama ke ta ke ta ambata."
"Da gaske Likita?"
"Eh Mama."
Cikin rawar jiki Mama ta fad'a d'akin ta yi ido biyu da Deejah jingine da gado Nurse na wanke mata baki.
Kulle ido na yi na bud'esu kan Mama wacce ke tsaye hawaye na bin kumatunta.
"Mamana kina raye dama ban saraki ba?"
"Alhamdulillah."
Shi ne abinda Mama ta furta a maimakon bani amsa.
"Gawa ta k'i rami ya jikin naki?"
"Hajiya Inna taho taji d'uminku."
Da sauri suka iso tare da rungumeni. Murna kam naganshi wurin Mama, ni kaina farin cikin da na samu kaina ciki na ganin Mama a raye ba mai misaltuwa ba ne.
"Ina Baba Umaru?"
Ta ambata saboda shi kawai na ke son sanyawa a ido.
"Yana Jigawa."
"Lafiya ko?"
Mamata ta ambata cikin sauri idanunta zube kan Hajiya Inna.
"Sai ya dawo muji saboda bayan na taho Habibu ke sanarmin sun tafi."
"Allah yasa dai lafiya wannan irin tafiya cikin dare."
"Amin."
"Mama muma mutafi dan Allah naga Dattijon kirki wanda bakya gajiya da bani labarin karamcinsa gareki."
"Uwata insha Allah kina warkewa zan shirya mana tafiya."
"Da fatan har Sokoto zakuje?"
"A'a Inna kowanne tafiyarsa daban zan shirya masa da yarda Allah."
"Allah ya amince."
"Amin."
"Mama ki saka mana ranar zuwa dan Allah, ina son ga nina cikin dangi masu yawa, naje can gidan naje can."
"Kin ganki Takwara da salo tamkar abin da kike ambata zaki iya aikatawa, ke da kike kifin rijiya sam ba kya son jama'a."
"Allah Hajiya Inna ina son ganina cikin dangi irin masu yawan nan."
"Uwata bari in had'o miki tea ki Sha."
Mama ta kauda maganar.
"To amma wanda na ke son yi jikina duk ciwo keyimin."
"Ai kam dole ki jiki ba dai-dai ba, kwanaki biyu a kwance ba motsi dole gab'b'ai su amsa."
"Hajiya Inna wai dogon suma na yi ko me?"
"Eh fa, irin wanda ke kama, coma inji turawa."
Shiru na yi ina tuno kalaman da suka shigo kunnuwana lokacin.
"Uwata sannu kinji? Allah kada ya k'ara nuna mana irin wannan lamari."
"Amin Mamana."
"Hajiya Likita ya ce abata abu mai d'umi sai ta sha magani kada abarta ta yi tafiya ita d'aya saboda jikinta ba kwari."
"To nurse zamu kiyaye."
"Nikam wanka na ke sonyi in rama sallolin da ke kaina."
"Ki bari ki warware ai ya shigo babin lalura Takwara."
"Hajiya Inna to a barni inyi wanka na sanja tufafi."
"Anfa samu lafiya kenan agwa-gwa sarkin wanka."
Murmushi na yi tare da komawa na kwanta. Duk yarda su Mama suka so nasha tea na kafe sai na yi wanka.
"To ki jira gari ya gama wayewa sai su Fanta su d'auko miki kayan da zaki sanja."
"To zanyi fitsari."
"Sakko na rik'eki Uwata."
"A'a yi zamanki Hurera, ke da baki da k'oshin lafiya."
"Hajiya Inna ce ta rakani, ina jin fitarta na tub'e kayan jikina na hau watsa ruwan sanyi, ba sabulu na yibta tirje jikina dukbda jirin da na ke gani haka kan na dafa bango ya kammala wankan na d'auro zani na fito sumata na d'igan ruwa, baki suka bud'e ganin wayon da na yi musu.
"Uwata halinki sai ke, narasa inda kika samo wannan tsafta."
"Wurin Kawu Habibu."
"Aikam sai wurin d'an ka iya."
"Zanyi sallah Mama."
"To cire ganin jikinki ga wankakke da Hijab."
Sanjawa na yi na hau sallaya saidai nakasa tsayuwa sakamakon rawar sanyin da na ke yi. Ai kam Hajiya Inna ta balbaleni da fad'a tamkar zata ari baki ya yin da Mama ta ruga kiran Likita. Kafin likita ya iso Hajiya Inna ta cic-cib'eni ta d'ora a gado ta rufeni da bargo tana ta tofamin addu'a sai duk suka bani tausayi na soma nadamar yin wanka da ruwan sanyin.
Ina jin Likita ya shigo ya dubani tare da yimin allura wanda ban jima ba na mance abinda ke faruwa sakamakon barcin da ya d'auke ni.
***
Kamar yarda Uncle ya k'udurta yana idar da sallah ya nufi masallacin da Baba ke bada sallah. Na'ibinsa ya samu bayan sun gaisa ya tambayesa Baba ya sanar masa baizo sallah ba, cike da mamaki ya juya sai ya tsinkayi muryan Na'ibin.
"Amma ga babban d'ansa nan ka sanar masa da sak'on insha Allah zai isar zuwa ga reshi."
Kallon wanda aka kira babban d'an Baba ya yi a ta ke ya aminta saboda kamannin da ya gani.
"Biyoni."
Abinda Uncle ya furta kenan tare da yin gaba.
"Bishi Auwalu kaji da abinda yazo."
"To Baba."
Uncle Bai sanar da Auwalu komi ba har saida suka iso k'ofar gidan su Deejah sannan ya dakata ya kalle shi a natse ya labarta masa abin da ke faruwa.
"Innalillahi wa Inna ilaihin raji'un."
Auwalu ya ambata cikin sanyin murya wanda ya ja hankalin Uncle har ya zuba masa ido yana mamakin sanyinsa tamkar ba jinin Baba mai zafi ba.
'Tabbas su Kamalu ne da wannan aikin bisa hud'ubar su Inna, da gaske kenan Baba ya sha furan mai maganin barci? In ko haka ne Innar su Anas bata kyautawa Baba ba.'
"Malam Auwalu tunda kaine magajin Baba zuwa anjima kazo muje police station d'in ka gansu tare da bayanin dalilin zuwarsu yin sata."
"Alhaji Baba yana cikin gidan nan, maganin mura ya sha barci mai nauyi na daukesa shi ne suka sami nasarar aikata satan."
Ya ambaci haka saboda kunyar tonawa Matar Babansa asiri.
"Me ye hujarka?"
"Jiya da dare ni na kawosa gida kuma ya sanarmin zaisha maganin mura."
"Ok bari mu dubashi."
Suna shiga da Baba sukayi arba zaune saman buzu ganinsu yasa shi sallame lazimin ya nuna Auwalu da yatsa "Uban wa kabarwa tsaron tsangayar?"
"Antashi lafiya Baba?"
"Ban sani ba, amsamin tambayata kafin gaisuwa ya biyo baya."
"Baba Na'ibi zai kula da su."
"To lafiyalau, me kazo yi?"
"Alhaji zai sanarma, nabarka lafiya, Alhaji sai wani lokacin."
"To Malam Auwalu ga wanna ka hau abin hawa."
"Hannu ya mik'a ya amshi kudin tare da yin godiya, suna had'a ido da Baba ya girgiza masa kai tare da cije leb'en k'asa, murmushi ya yi kawai ya fice yana tir da halin mayintar kud'i irin na Baba.
"Halin Baba sai shi, sam ba'a yiwa mutum kyauta ya kauda idonsa a kai."
Ya furta a hankali.
"Alhaji me ke faruwa?"
Gyarar murya Uncle ya yi sannan ya jero masa duk abinda ya faru.
"Wallahi saina shukawa Hinde rashin mutunci saboda ita ta bani fura mai kayan maye na yi ta shek'a barci wanda ya janyomin asarar sallah cikin Jam'i, ga shi har b'arayi sun shigomin gidan iyali."
"Baba ko dai maganin muran da ka sha ne ya haifar da nauyin barcin?"
"Uban wa ya sanarma na sha maganin mura?"
"Auwalu ne."
"Oh yanzu na gane daga inda iskanci ya fito wato shima ya lalace kenan shi yasa ya siyamin lemu ya zuba kwayoyi shi ne zai ce maka ina mura to billahil azim sai na...
"A'a Baba banda saurin rantsuwa a matsayinka na shugaba kuma jagorar dubannin al'umma."
"Allah ya yi maka albarka Abdul Muhseen dan ka tunasar dani kiyaye harshena."
"Amin Baba."
"Yanzu zamu tafi naga shegun ne ko ya?"
"Sai zuwa hantsi zamuje, insha Allah."
"To amma ka sanar da a sanja musu kamannin ko?"
"Eh, dan yanzu haka ance sun sanar da wanda suka turosu, kafin mu isa za'a kamosu."
"Yawwa hakan ya kamata a had'asu a ci k'aniyarsu yarda gaba ko sunar b'arawo aka kira zasu bar wurin a guje."
Murmushi Uncle ya yi yana k'ara yabawa fitinar Baba.
Bayan tafiyar Uncle Baba ya nufi kitchen yana surutai zuwa can kuna ya soma yabon Mama.
"Allah ya biyaki da khairan Hurera da kina nan sai abinda na so ci zaki dafamin, ina ci ina tura mikin masifa amma bazaki d'aga kai ba saboda sanin darajar aure, shi yasa duk rintsi ba zan rabu da ke ba sai na binne gawarki da hannayena biyu kafin nan tuni Uwani ta dad'e da zama yar gari a barzahu domin wannan sumar batashi zatayi ba."
Shi kad'ai ya yi ta zuba surutu har ya samu ya gama soya kwai tare dadafa ruwan zafi ya had'a tea mai kauri ya tafi ya kulle k'ofar gida ya dawo ya zauna saman buzunsa ya korawa hakali kwance.
"A she ban manta rayuwar almajiranci ba inda muke satar kwan kajin Malam dana makwafta mu tafi bayan gari mu d'iba girki mai rai da lafiya. Ya Allah ka yafe mana laifukanmu domin munyi cuta iya cuta na cinyewa kaji kwai da zabbi."
Sabulu (molato and black soap)
Scrub
Face cream
Oil
Body lotion
Shower gel
Kulachan
Humra (White and black)
Turaren tsugunon
Turaren kaya
Turaren wuta na d'aki
Garin d'a'a (domin k'an-k'aro martaban aure.)
*Duk za'a samesu a farashi mai rahusa, mai buk'atar d'aya ko sari a tun-tub'emu a wad'annan numbers 08132166848 ko 08147491137. Sai munjiku.*
[10/31, 9:28 PM] 💘: DAMUWATA. (Sanin abin adona)
By Mrsjmoon.
E.W..F.
Page 18.
K'arar na'urar da ke nuna Deejah na da rai shi ne ya tashi su Mama barci a dai-dai lokacin kuma anata kiraye-kirayen sallar subahi. Dr. Jalal tare da Nurses ne suka shigo a hanzarce sakamakon jiyo k'aran na'urar. Fita su Mama sukayi suka tsaya bakin k'ofar cikin jan addu'o'i nasara.
Bayan wucewar wani lokaci Doctor ya fito da sauri Mama ta sha gabansa murmushi ya sauke mata ya nuna mata d'akin da hannu.
"Tafi ta ganki dan itama ke ta ke ta ambata."
"Da gaske Likita?"
"Eh Mama."
Cikin rawar jiki Mama ta fad'a d'akin ta yi ido biyu da Deejah jingine da gado Nurse na wanke mata baki.
Kulle ido na yi na bud'esu kan Mama wacce ke tsaye hawaye na bin kumatunta.
"Mamana kina raye dama ban saraki ba?"
"Alhamdulillah."
Shi ne abinda Mama ta furta a maimakon bani amsa.
"Gawa ta k'i rami ya jikin naki?"
"Hajiya Inna taho taji d'uminku."
Da sauri suka iso tare da rungumeni. Murna kam naganshi wurin Mama, ni kaina farin cikin da na samu kaina ciki na ganin Mama a raye ba mai misaltuwa ba ne.
"Ina Baba Umaru?"
Ta ambata saboda shi kawai na ke son sanyawa a ido.
"Yana Jigawa."
"Lafiya ko?"
Mamata ta ambata cikin sauri idanunta zube kan Hajiya Inna.
"Sai ya dawo muji saboda bayan na taho Habibu ke sanarmin sun tafi."
"Allah yasa dai lafiya wannan irin tafiya cikin dare."
"Amin."
"Mama muma mutafi dan Allah naga Dattijon kirki wanda bakya gajiya da bani labarin karamcinsa gareki."
"Uwata insha Allah kina warkewa zan shirya mana tafiya."
"Da fatan har Sokoto zakuje?"
"A'a Inna kowanne tafiyarsa daban zan shirya masa da yarda Allah."
"Allah ya amince."
"Amin."
"Mama ki saka mana ranar zuwa dan Allah, ina son ga nina cikin dangi masu yawa, naje can gidan naje can."
"Kin ganki Takwara da salo tamkar abin da kike ambata zaki iya aikatawa, ke da kike kifin rijiya sam ba kya son jama'a."
"Allah Hajiya Inna ina son ganina cikin dangi irin masu yawan nan."
"Uwata bari in had'o miki tea ki Sha."
Mama ta kauda maganar.
"To amma wanda na ke son yi jikina duk ciwo keyimin."
"Ai kam dole ki jiki ba dai-dai ba, kwanaki biyu a kwance ba motsi dole gab'b'ai su amsa."
"Hajiya Inna wai dogon suma na yi ko me?"
"Eh fa, irin wanda ke kama, coma inji turawa."
Shiru na yi ina tuno kalaman da suka shigo kunnuwana lokacin.
"Uwata sannu kinji? Allah kada ya k'ara nuna mana irin wannan lamari."
"Amin Mamana."
"Hajiya Likita ya ce abata abu mai d'umi sai ta sha magani kada abarta ta yi tafiya ita d'aya saboda jikinta ba kwari."
"To nurse zamu kiyaye."
"Nikam wanka na ke sonyi in rama sallolin da ke kaina."
"Ki bari ki warware ai ya shigo babin lalura Takwara."
"Hajiya Inna to a barni inyi wanka na sanja tufafi."
"Anfa samu lafiya kenan agwa-gwa sarkin wanka."
Murmushi na yi tare da komawa na kwanta. Duk yarda su Mama suka so nasha tea na kafe sai na yi wanka.
"To ki jira gari ya gama wayewa sai su Fanta su d'auko miki kayan da zaki sanja."
"To zanyi fitsari."
"Sakko na rik'eki Uwata."
"A'a yi zamanki Hurera, ke da baki da k'oshin lafiya."
"Hajiya Inna ce ta rakani, ina jin fitarta na tub'e kayan jikina na hau watsa ruwan sanyi, ba sabulu na yibta tirje jikina dukbda jirin da na ke gani haka kan na dafa bango ya kammala wankan na d'auro zani na fito sumata na d'igan ruwa, baki suka bud'e ganin wayon da na yi musu.
"Uwata halinki sai ke, narasa inda kika samo wannan tsafta."
"Wurin Kawu Habibu."
"Aikam sai wurin d'an ka iya."
"Zanyi sallah Mama."
"To cire ganin jikinki ga wankakke da Hijab."
Sanjawa na yi na hau sallaya saidai nakasa tsayuwa sakamakon rawar sanyin da na ke yi. Ai kam Hajiya Inna ta balbaleni da fad'a tamkar zata ari baki ya yin da Mama ta ruga kiran Likita. Kafin likita ya iso Hajiya Inna ta cic-cib'eni ta d'ora a gado ta rufeni da bargo tana ta tofamin addu'a sai duk suka bani tausayi na soma nadamar yin wanka da ruwan sanyin.
Ina jin Likita ya shigo ya dubani tare da yimin allura wanda ban jima ba na mance abinda ke faruwa sakamakon barcin da ya d'auke ni.
***
Kamar yarda Uncle ya k'udurta yana idar da sallah ya nufi masallacin da Baba ke bada sallah. Na'ibinsa ya samu bayan sun gaisa ya tambayesa Baba ya sanar masa baizo sallah ba, cike da mamaki ya juya sai ya tsinkayi muryan Na'ibin.
"Amma ga babban d'ansa nan ka sanar masa da sak'on insha Allah zai isar zuwa ga reshi."
Kallon wanda aka kira babban d'an Baba ya yi a ta ke ya aminta saboda kamannin da ya gani.
"Biyoni."
Abinda Uncle ya furta kenan tare da yin gaba.
"Bishi Auwalu kaji da abinda yazo."
"To Baba."
Uncle Bai sanar da Auwalu komi ba har saida suka iso k'ofar gidan su Deejah sannan ya dakata ya kalle shi a natse ya labarta masa abin da ke faruwa.
"Innalillahi wa Inna ilaihin raji'un."
Auwalu ya ambata cikin sanyin murya wanda ya ja hankalin Uncle har ya zuba masa ido yana mamakin sanyinsa tamkar ba jinin Baba mai zafi ba.
'Tabbas su Kamalu ne da wannan aikin bisa hud'ubar su Inna, da gaske kenan Baba ya sha furan mai maganin barci? In ko haka ne Innar su Anas bata kyautawa Baba ba.'
"Malam Auwalu tunda kaine magajin Baba zuwa anjima kazo muje police station d'in ka gansu tare da bayanin dalilin zuwarsu yin sata."
"Alhaji Baba yana cikin gidan nan, maganin mura ya sha barci mai nauyi na daukesa shi ne suka sami nasarar aikata satan."
Ya ambaci haka saboda kunyar tonawa Matar Babansa asiri.
"Me ye hujarka?"
"Jiya da dare ni na kawosa gida kuma ya sanarmin zaisha maganin mura."
"Ok bari mu dubashi."
Suna shiga da Baba sukayi arba zaune saman buzu ganinsu yasa shi sallame lazimin ya nuna Auwalu da yatsa "Uban wa kabarwa tsaron tsangayar?"
"Antashi lafiya Baba?"
"Ban sani ba, amsamin tambayata kafin gaisuwa ya biyo baya."
"Baba Na'ibi zai kula da su."
"To lafiyalau, me kazo yi?"
"Alhaji zai sanarma, nabarka lafiya, Alhaji sai wani lokacin."
"To Malam Auwalu ga wanna ka hau abin hawa."
"Hannu ya mik'a ya amshi kudin tare da yin godiya, suna had'a ido da Baba ya girgiza masa kai tare da cije leb'en k'asa, murmushi ya yi kawai ya fice yana tir da halin mayintar kud'i irin na Baba.
"Halin Baba sai shi, sam ba'a yiwa mutum kyauta ya kauda idonsa a kai."
Ya furta a hankali.
"Alhaji me ke faruwa?"
Gyarar murya Uncle ya yi sannan ya jero masa duk abinda ya faru.
"Wallahi saina shukawa Hinde rashin mutunci saboda ita ta bani fura mai kayan maye na yi ta shek'a barci wanda ya janyomin asarar sallah cikin Jam'i, ga shi har b'arayi sun shigomin gidan iyali."
"Baba ko dai maganin muran da ka sha ne ya haifar da nauyin barcin?"
"Uban wa ya sanarma na sha maganin mura?"
"Auwalu ne."
"Oh yanzu na gane daga inda iskanci ya fito wato shima ya lalace kenan shi yasa ya siyamin lemu ya zuba kwayoyi shi ne zai ce maka ina mura to billahil azim sai na...
"A'a Baba banda saurin rantsuwa a matsayinka na shugaba kuma jagorar dubannin al'umma."
"Allah ya yi maka albarka Abdul Muhseen dan ka tunasar dani kiyaye harshena."
"Amin Baba."
"Yanzu zamu tafi naga shegun ne ko ya?"
"Sai zuwa hantsi zamuje, insha Allah."
"To amma ka sanar da a sanja musu kamannin ko?"
"Eh, dan yanzu haka ance sun sanar da wanda suka turosu, kafin mu isa za'a kamosu."
"Yawwa hakan ya kamata a had'asu a ci k'aniyarsu yarda gaba ko sunar b'arawo aka kira zasu bar wurin a guje."
Murmushi Uncle ya yi yana k'ara yabawa fitinar Baba.
Bayan tafiyar Uncle Baba ya nufi kitchen yana surutai zuwa can kuna ya soma yabon Mama.
"Allah ya biyaki da khairan Hurera da kina nan sai abinda na so ci zaki dafamin, ina ci ina tura mikin masifa amma bazaki d'aga kai ba saboda sanin darajar aure, shi yasa duk rintsi ba zan rabu da ke ba sai na binne gawarki da hannayena biyu kafin nan tuni Uwani ta dad'e da zama yar gari a barzahu domin wannan sumar batashi zatayi ba."
Shi kad'ai ya yi ta zuba surutu har ya samu ya gama soya kwai tare dadafa ruwan zafi ya had'a tea mai kauri ya tafi ya kulle k'ofar gida ya dawo ya zauna saman buzunsa ya korawa hakali kwance.
"A she ban manta rayuwar almajiranci ba inda muke satar kwan kajin Malam dana makwafta mu tafi bayan gari mu d'iba girki mai rai da lafiya. Ya Allah ka yafe mana laifukanmu domin munyi cuta iya cuta na cinyewa kaji kwai da zabbi."