← Book details Damuwata Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 6 OF 43

Sashe 6

Damuwata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Mama ce ta ke tambayana yarda na isa na tabbatar mata da lafiyalau. Ina sauke wayar a kunnina idanunmu ya had'u dana Uncle samun kaina na yi da kallon cikin idanunsa tamkar yarda ya ke kallon nawa, musmushi ya yi tare da juyowa ya kalleni sosai na yi hanzarin sunkuyar da kai ina latsa gidan layina fad'in Fanta.

"Nafisat dama k'anwar taki bata da waya baki sanarmin ba?"

Yarda ya yi maganar ba wanda zaice shi ne ke fad'a d'azun.

"Wa kenan?

Ta ambata a dak'ile hankalinta na kan wayarta.

"Nana Khadijatu."

"Yau she na ke da k'anwa mai wannan sunar Abban Hafiz?"

"Oh ya rabbi, a gaskiya baki da kirki Nafisat, yanzu k'awar Fanta ai k'anwarki ce inda kara."

"Idan kuma babu karan fa?"

Kafin ya bata amsa Abokinsa da ya kira ya iso dan haka sai ya bud'e k'ofar ya fice sun sami mintoci biyu zuwa uku sannan Uncle ya umurcemu da mu fito inda muna fitowa sukayi gaba muka rufa musu baya. Wannan damar Aunty Nafisat ta samu ta yi min gargad'i akan fita harkan mijinta. Ni sai lamarin ya zamomin wani kala domin tun tasowata bantab'a cin karo da wata nayimin gargad'i akan mijinta ba ko saurayinta. Haka nan kawai naji wani nishad'i na ratsamin ruhi a maimakon shiga k'unci domin Aunty Nafisat ta sokamin maganganu masu zafi wanda zasu k'ona min rai ta hanyar kiran Baba da Boka abin da ta hango na tsani jin kalman shi yasa a zantukan nata ta yi ta kiran Bokan Ubanki, amma sam basu k'onamin rai ba kamar yarda ta ke da buri.

Daf da zamu isa wurin muta be na kalleta cikin murmushi mai sauti ta ware ido na kuma murmusawa tamkar zanyi magana sai kuma na tsuke baki hakan kuwa ya b'ata mata rai dan hannu ta d'aga zata zabgamin mari na yi saurin sunkuyawa ta sami iska wanda ya jata ta tafi zata fad'i na yi hanzarin tareta cikin ambatar sunar Allah RAHMAN. Da sauri Uncle ya juyo tare da abokinsa.

"Lafiya?"

"Normal Dear kawai d'an tuntub'e naji."

Ta bawa Uncle amsa cikin tureni daga rik'on da nayi mata.

"Allah ya kara kiyayewa."

Abokin Uncle ya ambata.

"Amin."

Na amsa tare da gaisar da shi ya amsa cikin kauda kai gefe yana mai gaisar da Aunty Nafisat. Tamkar mai ciwon hak'ori haka ta amsa Uncle ya ja dogon tsaki ya yi gaba dan yaji haushin abinda tayiwa abokin nasa.

Wuri na musanman Malamin ya kaimu wanda baida nisa da inda ya ajiye Uncle domin wurin maza daban mata daban. Hak'ik'a wurin ya tsaru matuk'a dan wurin manyan bak'i ne, lumshe ido na yi ina hasko sadda na zauna a cikin taro irin haka.

"Alhamdulillah, ya Allah da ka bani ilimin addini da na zamani dai-dai misali, Ya rabbi ka bani ikon aiki da su ta hanya na gari."

Na furta a hankali.

Tsakin da Aunty Nafisat ta ja yasa na bud'e ido duk sai naji na takura sabida yarda Aunty Nafisat ke zabgomin harara da kuma idanun mutane da ya dawo kaina, murmushin yak'e na yi ta yi ina kallon idanunta ta kuma jan tsaki mai sauti sama da na farko sai na kauda fuska na yi kamar badani ta ke yi ba zuwa can na fakaici idanun Uncle na sulale zuwa wurin su Bintu wanda tun ganina suke ta d'agomin hannu.

"Ayya Deejah kinyi kyau sosai."

Suka ambata a tare.

"Nagode, kuma kunyi kyau."

"Deejah k'awarki tayi fushi da ke."

"Safeena a tayani bata hak'uri, jiya na raya daren ne da yiwa Annabi salati shi yasa na tashi a makare."

"Masha Allah, rayuwarki na kan burgeni matuk'a."

"Uhm."

Na ambata cikin sosa gefen idona.

Haka suka yita min hira ina biye musu cikin jin dad'in kulawar da suke bani.

'Karfe goma dai-dai aka soma kiran masu saukan suna yin karatu. Masha Allah shi ne abin ambata domin kowa a ka kira zaiyi karatu cike da kwarewa, Fanta harda kuka sadda akazo kanta lamarin da ya ja hankalin mutane sukayi ta sanya mata albarka tare da yi mata lik'in kud'i ciki har da ni da su Bintu, Uncle kam mu da muka rufeta ya yi ta zubawa 'yar dari biyar-biyar sabbi fil.

'Karfe biyu da mintoci goma sha biyar aka tashi taron cike da farin ciki.

Muna isa gida sallar azuhur mukayi. Ni da Beebah muka hau hidima da tulin 'kawayen Fanta zuwa la'asar dik sunka watse, muna zaune a d'akin Fanta sai hayaniya sukeyi na koma gefe na sami gefen gadon Fanta na zauna ina duba wayarta domin soma gane yarda ta ke saboda daga jiya zuwa yau na ji son rik'e babban waya. Maganar Aunty Nafisat na tsinkaya cikin hargajinta na fama.

"Ke! dalla ta so ki dafamin abinci."

Tsit d'akin ya d'auka na d'ago na bi su da kallo sai naga ni suke kallo sai na maida kai ga abinda na ke yi.

"A haka Abban Hafiz ke ambatarki da k'anwata, inayi miki magana kin bawa banza ajiyata, uhm yayi miki kyau, labari zai isa kunninsa domin na san ke ba K'awata ba ce."

Da sauri na d'ago har ta juya zata bud'e k'ofa na ce "Ayya Aunty ban san dani kikeyi ba, kiyi hak'uri muje na dafa."

Batare da ta juyo ba ta amsa "Ban son gulma kawai in zakizo kizo ba sai kin cikamin kunni da karad'i ba."

Baki bud'e na raka bayarta da ido cike da mamakin k'arfin halinta tare da nunan iko alhalin bai zama dole inyi mata aikin ba.

Tsaki Beebah ta doka ta fice fuww, Bintu ta rufa mata baya Fanta ta janyo hannuna cikin cewa "Ba girkin da zakiyi mata dan ke ba 'yar aikinta bace."

"Wallahi Deejah kada kiyi tunda bata san yarda zata nemi arzikin ayi mata abu ba."

Fiddausi ta furta cikin fad'a.

"Uhm nikam na tafi gidan Mama nasha kunun aya.

" Safeena ta ambata tare da ficewa.

"Jirani mu tafi dan nasan halin k'awata sai tayi girkin ni kuma ban shirya ta yata ba."

Rik'o hannun Fanta na yi ta fizge ta fice da gudu Fiddausi ta rufa mata baya da gudu itana. Girgiza kai na yi na fito zuwa d'akin Aunty Nafisat hayaniyarta najiyo cikin muryan fad'a sai ban shiga ba na juyo zuwa kitchen na samu ta fitarmin da dik abinda zan buk'ata. Aiki na somayi cikin kwarewa domin amfani da kayan wutar baizamemin abin wuya ba dan nasaba taya Fanta girki da su sannan girki wani sashi ne na rayuwata domin idan ina yinsa har wani nishad'i na ke samun kaina ciki, lokuta da mada Mama kan kirani da Uwata sarauniyar girki, jin hakan na k'aramin k'aimi wurin ganin na dafa abinci mai rai da lafiya.

A cikin awa biyu na kammala dafa jelop rice wacce ta ji kayan lambu da yankakkun Hanta tare da had'in zobo drink. Ina goge hannuna da towel najiyo k'amshi wani turare mai shegen k'amshi, juyowa na yi cikin lumshe ido sakamakon kasancewata mai son k'amshi,

"Sannu da Aiki."

Na bud'e idanu da sauri jin muryan Uncle wanda ke tsaye a bakin kofar kitchen hannayensa zube cikin aljihunsa.

Kunya ce ta ziyarceni ganin ya ganni babu hijab, kai na sunkuye na ce

"Yawwa, barka da yammaci."

Banji ya amsa ba kuma ina ji ajikina kallona ya ke cigaba da yi sai na janyo hijab d'ina dake rataye saman k'ofa na sanya na d'ago muka had'a ido ya murmusa kad'an tare da shigowa ya nufi wormers dana zuba abincin ya bud'esu ya maida ya kulle ya d'auki cup k'arami ya zuba zobo drink dana  jefa k'an-k'ara cikinsa, ya d'auki sanyi.

Gyashi na ji ya yi tare da hamdala duk a lokaci d'aya.

"Dama ke Nafisat ta saka aikin dana sanyata?"

Ban amsa ba sabida ban san amsar sa zan bashi ba sabida kada na ambata eh ya zamo na yi laifi a wurin aunty Nafisa.

"Thank you Khadijatu, me kike so na baki amatsayin tukuici? Saboda kin farantamin rai ta hanyar fitar da ni jin kunyar abokan kasuwancina."

Still ban ce komi ba dan wani yanayi na fad'a domin wannan shi ne karo na biyu tun zamowata budurwa da namiji ya tab'a yabamin har da neman zab'ina akan wani abu da zaiyimin na farantawa.

"Uhm ina saurarenki."

Muryansa ya katsemin tunanin dana fad'a.

Kallonsa na yi kad'an sai naga ya cikamin ido kuma na kasa furta kalma.

"Bakiji maganar da nasanar miki d'azun ba ko Khadijatu?"

"Kayi hak'uri Uncle."

"Oya na ji sarkin tuba, zama sanar da ni abin da kike so."

Motsa yatsuna nayi cikin saita harshena na ce...

*TALLA.*

*Ina kuke Mata 'yan kwalisa masu bawa fatarsu 'yancinta musanman babban kadararku wato fuska. To ga dama ta zo muku cikin sauk'i wato samun kayan gyarar fuska da jiki mai inganci na organic wanda aka samar da su da abubuwa masu nagarta. Duk wacce K'uraje, Tabbai, Sunburn, kyafsi suka b'atawa fuska muna da maganin da fuskanta zai dawo fes, sumul, rangad'ad'au. Haka a fannin fatar jiki shima muna da kayan da zaiyi laushi, sulb'i tare da haske mai kyau. Ga kayan kamar haka:*

Sabulu (molato and black soap)
Scrub
Face cream
Oil
Body lotion
Shower gel
Kulachan
Humra (White and black)
Turaren tsugunon
Turaren kaya
Turaren wuta na d'aki
Garin d'a'a (domin k'an-k'aro martaban aure.)

*Duk za'a samesu a farashi mai rahusa, mai buk'atar d'aya ko sari a tun-tub'emu a wad'annan numbers 08132166848 ko 08147491137. Sai munjiku.*
[10/14, 2:40 PM] 💘: DAMUWATA (Sanin abin adona)
By Mrsjmoon.

EWF.

*Shafin sadaukarwa ne ga Ramlat Mai Dambu (Mom muwaddat) Allah ya yi wayuwa albarka tare da raya zuri'a cike da ni'imominsa. Amin.*

Page 04.

"Babu tukuici a tsakaninmu Uncle, dan kawai na yi aikin da ya zamamemin abin alfahari, Ni tamkar d'iya ce ko ince k'anwa a gareka."

"Nasan da wannan just ina son jin ra'ayinki akan abinda na k'udurta yi miki ne sabida yarda kika farantamin ta hanyar fitar da ni kunya da abinda na nemi alfarma matana da ta yimin amma tak'i sai ta sanyaki gashi kinyi abinda nasan bazata iya shi ba, kinga kin cancanci a faranta miki ta hanyar rukuici."

"Uncle ka gama faranta min tunda ka ya bi aikina."

Na amsa cikin fitar da siririyar dariya domin ainun naji dad'in yabon da ya yi min.

"Wato bazaki fad'aba kenan ko?"
Chapter 6 · 0% Book details