Sashe 22
Damuwata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Uhm nidai dan girman Allah ku barni da Fanta."
"Kiyi hak'uri itama tana son kai ziyara taga dangi."
"Shi kenan Allah ya dawo da ita lafiya."
"Amin."
Wanka na shiga na d'auro alwallah na sallaci shafa'i da wutri na yi shirin barci. Kwanciya na yi cike da sake-saken yarda al'amuran rayuwata yasoma sauyawa da salo mai cike a bababen mamaki.
'Wai ni ce wacce ada maza ke k'in kulawa amma yanzu sun soma cajamin kwakwalwa.'
"Inkon Allah kenan."
Na ambata a fili.
"Sai ji da gani ba"
Na tsinkayi muryan Beebah ta amsamin.
Sai da safe na yi mata, itama ta shiga toilet tajima sannan ta fito bisa alamu wanka ta yi.
Tsakiyar dare na farka sakamakon jin motsin ana tab'amin k'ofa, gabana ya fad'i tuno rayuwata na baya wanda na ke gadin kaina a duk tsakiyar dare. Addu'a na soma ja inda ya taimakamin na samu kuzarin mik'ewa na nufi k'ofar.
Ina bud'ewa Mama ta fad'omin a jiki tana nunfarfashi tare da nunamin hanyar k'ofar d'akinta da yatsa dan takasa yin magana.
*TALLA.*
*Ina kuke Mata 'yan kwalisa masu bawa fatarsu 'yancinta musanman babban kadararku wato fuska. To ga dama ta zo muku cikin sauk'i wato samun kayan gyarar fuska da jiki mai inganci na organic wanda aka samar da su da abubuwa masu nagarta. Duk wacce K'uraje, Tabbai, Sunburn, kyafsi suka b'atawa fuska muna da maganin da fuskanta zai dawo fes, sumul, rangad'ad'au. Haka a fannin fatar jiki shima muna da kayan da zaiyi laushi, sulb'i tare da haske mai kyau. Ga kayan kamar haka:*
Sabulu (molato and black soap)
Scrub
Face cream
Oil
Body lotion
Shower gel
Kulachan
Humra (White and black)
Turaren tsugunon
Turaren kaya
Turaren wuta na d'aki
Garin d'a'a (domin k'an-k'aro martaban aure a turaka)
*Duk za'a samesu a farashi mai rahusa, mai buk'atar d'aya ko sari a tun-tub'emu a wad'annan numbers d'in 08132166848 ko 08147491137. Sai munjiku.*
[10/25, 11:01 PM] 💘: DAMUWATA (Sanin abin adona)
By Safiyya (Mrsjmoon)
E.W.F.
Page 13.
Rungumota na yi ina salati tare da janyota ciki na maida k'ofar na rufe, addu'a na soma tofa mata hankalina a tashe. Saukan fitar numfashinta da sauri da sauri ya tashi Beebah daga barci ta iso gabana tana jeromin tambayoyi ganin ban amsa mata ba sai addu'a na ke aikin tofawa Mama cikin sauri-sauri sai ta zubo ruwa a kofi ta zauna ta rik'e babban yatsar k'afar Mama da kyau ta soma tofa addu'a a ruwan hannunta, tana gama tofawa sai ta guntsa da fesa aikam ta ke Mama ta ja numfashi mai k'arfi, Beebah ta k'ara guntsan ruwan sai dai kafin ta fesa mata akaro da biyu tari ya sark'eta kofin da ruwan addu'ar ke ciki ya kufce a hannunta ya zube a k'asa. Sannu na yi ta jera mata har zuwa sadda tarin ya lafa ta matso muka cigaba da tofawa Mama addu'a. Tsawon rabin awa muna fama da Mama kafin mu samu ta dawo hayyacinta ta soma ambatar Hasbunallahu wal ni'imal wakil, da k'arfi ganin haka muma muka somabinta, zuwa wani lokaci sai ta rufe da salati. Gumi sai b'ulb'ulowa ya keyi daga sassan jikinta, gamin haka sai muka samu madai-daitan towel muka soma goge mata, lumshe idanu ta yi tana mai ambatar albarka a garemu. Bayan munga ta sani natsuwa sai muka kamata zuwa saman katifa, ta dubeni cikin tarin rauni ta ce "Uwata akwai damuwa a gidan nan, hak'ik'a da idanuna naga wani halitta mai kama da maciji na son hayomin gado shi ne ya firgitani wallahi ji na yi kamar zuciyata zata fito sabida tsoron halittar, tabbas da yazo da ajali da yanzu zuciyana ta buga na zamo gawa, kin koma marainiya na hak'ik'a."
"Mama kwanta ki huta gobe da safe sai muyi maganar kuma in Allah yaso kinfi k'arfi dik kan abin sharri daga jinsin mutum da aljan, insha Allah burinki sai ya cika a kaina k'asa bai rufe idanunki ba."
"Allah yaso hakan Uwata."
"Amin."
Muka amsa tare da Beebah.
Maganin ciwon kai ta nemi in bata ta sha, Beebah ta b'allo Boska d'aya Sudrex d'aya ta bata, tana sha bajimawa barci ya d'auketa cikin fitar murmushi mai cike da natsuwa.
Kasa komawa barci na yi sai na d'auro alwallah nasoma jera nafil-fili cikin kaiwa Allah kukana da ya karemu daga dukkan sharrin abin cutarwa na fili da b'oye, Beebah itama maramin baya ta yi, haka muka kwana addu'o'i. Bayan mun idar da sallar Subahi muka shiga d'akin Mama a tsorace bakinmu d'auke da addu'a, bamuga komi ba, Beebah ta ce mu bincika ko ina amma Mama ta hana ta ce mai cire maciji zaizo ya cire shi.
Hak'ik'a abin ya tab'a min zuciya ganin yarda Mama ta koma kamar yarinya domin da taji motsi zata zabura ta k'ank'ameni ko Beebah, sukalewa na yi na shiga bayin waje na kulle kaina na yi ta kuka cikin rashin fitar sauti, bayan na rar-rashi kaina na fito cikin k'ok'arin sanya wal-wala a fusakata gudun sake dagulawa Mama lissafi. Ko abinci ba wanda ya ci dan ko abin karyawa bamu sami damar had'awa ba saboda halin da mukaga Mama ya gama kashe Mana jiki domin da gari ya yi haske ta garas sai ta rik'a sunbatu tamkar wacce brain d'inta ya ke son tab'uwa, da mun had'a ido hawaye ke zubomin amma bana bari ta gani Beebah ce ta fahimta tasoma yimin nasiha a hankali gudun kada Mama taji ta k'ara bircikewa. Haka muka kasance da Mama mun kasa dawo da ita asalin natsuwarta.
Da hantsi mai cire maciji yazo ya gama hayak'insa da bincikensa baiga komi ba ya tafi, Beebah ce ta sanarwa da Uncle halin da ake ciki yana zuwa bai jira komi ba ya kira wani Malami da d'alibansa suka zauna danyin saukan alqur'anin a gidan, mu kuma ya ce mu tafi da Mama asibiti ganin yarda ta ke yin abun tamkar rud'ad'd'iyar tsohuwa, shima lamarin ya firgitashi.
Kwatanta damuwan dana shiga ba mai misaltuwa ba ce, na yi kuka har na ji zuciyata na son samun matsala ta hanyar jin ina fizgar numfashi da kyar tare da jin tanayimin zugi, kan dole na rarrashi kaina da kaina tunda nak'i jin ban bakin su Beebah.
Babban DAMUWATA shi ne na rashin sanin halin da Mamana ke ciki tsawon awanni shida da muka kawaota domin mun kawota da mintoci goma sha biyar Likitoci suka shige da ita wani d'aki sai dai inga sun fito sun shiga ba labarin komi, lamarin ya k'ara d'agamin hankali kenan nakasa sauraren ban bakin kowa hatta kuwa da Uncle domin gani na ke basu san kalan damuwarta da na ke ciki ba ne shi yasa suke cewa na daina kuka dan inda banyi kukan ba tabbas da nima ina kwance a gadon majinyata.
Bayan na gabatar da sallar magriba na dawo bak'in k'ofar da ka saka Mama na kife fuskata a jikin bangon na kuma fashewa da kuka mara sauti saboda tuni muryata ta dushe.
"Dan girman Allah kiyi hak'uri Aminiyata, ki tuna falalar mai yarda da k'addara ta khairan ko kishiyarta, kina da sani akansa shin me yasa bazaki zamo cikin masu mik'a lamuransu ga Ubangijin da baya barci balle gyan-gyad'i ba? Ki yi hak'uri irin wacce Allah ya umurci bayinsa mumunai da su aikata idan jarabawar rayuwa ta riskesu, ki sani Allah da ya jarabci Mama da lalura nan ya fiki sonta sannan faruwan hakan alamun tana cikin bayinsa salihai ne wanda ke dorawa cuta domin gwada imaninsu tare da shafewar zunubai."
Rungume Fanta ya yi tsan-tsan ina kuka mai ciccira.
"Insha Allah Mama zata warke jinkirin bayyanar halin da ta ke ciki alkhairi zai zamo biy jahiy Nabiyyi S.A.W."
"Allah ya so hakan, nagode sosai Aminiyata."
Na ambata batare da tunanin tajiyoni ba saboda yarda muryan ke fita can a mak'oshina.
"Ku tafi da ita gida ta huta."
Na tsinkayi muryan Uncle daf da ni.
Da sauri na juyo na rik'o hannunsa batare da tunanin komi ba saboda natsuwana ya yi balaguro.
"A'a Uncle ba zan iya hutawa ba alhalin Mamana na cikin wannan halin, ka barni har zuwa sadda zan san halin da ta ke ciki."
"Wani hali ta ke ciki?"
Ya cillomin tambayar tamkar bai san komi da ke faruwa ba.
Maimakon amsa masa sai na saki hannunsa na koma jikin Beebah na kwantar da kaina a kafad'arta na fashewa da sabon kuka.
"Beebah ku tafi da ita gida na ce."
"Ba zanje ba!."
Na furta da k'arfi.
"A haka kike son Mama ta yi ido biyu da ke? Kin koma tamkar wacce ta yi amai da zawo, oya ki tafi gida ki huta wannan shi ne umurnina na k'arshe akanki."
Ban sa ke magana ba kuma ban daina kuka ba, hawaye na bin cheek d'ina tamkar an bud'e famfo na motsa masa kai alamun cika umurninsa. Jan hannuna Bintu ta yi na kalleta naga itama kukan ta ke yi.
"Kunga idan kuka zaku koma kunayi banga amfanin had'aku da ita ba."
"Sorry Uncle mun bari."
Fanta ta ambata cikin muryan kuka.
"Ku tabbatar da ta ci abincin kafin in iso."
"To."
Beebah ta amsa a hankali.
"Yaya me yasa bazaka barta ta shiga ta ganta ba? Tana fa cikin yanayi mai kyau itama burinta ta sanya d'iyarta a ido."
Wata murya mai sanyi naji ya ambaci haka, ai banjira amsawan Uncle ba na juyo da gudu caraf Uncle ya kamani ya matse hannuna gam.
Runtse ido na yi saboda da yarda rik'on ya ratsa sassan jikina.
"Ki tafi gida idan kin dawo zaki ganta."
"Dan soyayyarka da Ma'aikin Allah ka barni inga halin da Mamana ke ciki kafin in tafi."
Sakina ya yi wani hannu mai mugun d'umi sama dana Uncle ya kamani haka nasoma binsa tamkar jela a k'ofar wani d'aki ya tsaya ya juyamin baya dama banga fuskansa ba, ban kuma damu da sai nagani ba.
"Ki shiga tana ciki amma idan kika d'aga mata hankali da wannan kukan naki tabbas da kaina zan fito da ke."
Motsa kai na yi tare da tura k'ofar d'akin na fad'a ciki da sauri dan gani na ke tamkar Uncle zai hanani duk da baibiyo bayanmu ba.
"Kiyi hak'uri itama tana son kai ziyara taga dangi."
"Shi kenan Allah ya dawo da ita lafiya."
"Amin."
Wanka na shiga na d'auro alwallah na sallaci shafa'i da wutri na yi shirin barci. Kwanciya na yi cike da sake-saken yarda al'amuran rayuwata yasoma sauyawa da salo mai cike a bababen mamaki.
'Wai ni ce wacce ada maza ke k'in kulawa amma yanzu sun soma cajamin kwakwalwa.'
"Inkon Allah kenan."
Na ambata a fili.
"Sai ji da gani ba"
Na tsinkayi muryan Beebah ta amsamin.
Sai da safe na yi mata, itama ta shiga toilet tajima sannan ta fito bisa alamu wanka ta yi.
Tsakiyar dare na farka sakamakon jin motsin ana tab'amin k'ofa, gabana ya fad'i tuno rayuwata na baya wanda na ke gadin kaina a duk tsakiyar dare. Addu'a na soma ja inda ya taimakamin na samu kuzarin mik'ewa na nufi k'ofar.
Ina bud'ewa Mama ta fad'omin a jiki tana nunfarfashi tare da nunamin hanyar k'ofar d'akinta da yatsa dan takasa yin magana.
*TALLA.*
*Ina kuke Mata 'yan kwalisa masu bawa fatarsu 'yancinta musanman babban kadararku wato fuska. To ga dama ta zo muku cikin sauk'i wato samun kayan gyarar fuska da jiki mai inganci na organic wanda aka samar da su da abubuwa masu nagarta. Duk wacce K'uraje, Tabbai, Sunburn, kyafsi suka b'atawa fuska muna da maganin da fuskanta zai dawo fes, sumul, rangad'ad'au. Haka a fannin fatar jiki shima muna da kayan da zaiyi laushi, sulb'i tare da haske mai kyau. Ga kayan kamar haka:*
Sabulu (molato and black soap)
Scrub
Face cream
Oil
Body lotion
Shower gel
Kulachan
Humra (White and black)
Turaren tsugunon
Turaren kaya
Turaren wuta na d'aki
Garin d'a'a (domin k'an-k'aro martaban aure a turaka)
*Duk za'a samesu a farashi mai rahusa, mai buk'atar d'aya ko sari a tun-tub'emu a wad'annan numbers d'in 08132166848 ko 08147491137. Sai munjiku.*
[10/25, 11:01 PM] 💘: DAMUWATA (Sanin abin adona)
By Safiyya (Mrsjmoon)
E.W.F.
Page 13.
Rungumota na yi ina salati tare da janyota ciki na maida k'ofar na rufe, addu'a na soma tofa mata hankalina a tashe. Saukan fitar numfashinta da sauri da sauri ya tashi Beebah daga barci ta iso gabana tana jeromin tambayoyi ganin ban amsa mata ba sai addu'a na ke aikin tofawa Mama cikin sauri-sauri sai ta zubo ruwa a kofi ta zauna ta rik'e babban yatsar k'afar Mama da kyau ta soma tofa addu'a a ruwan hannunta, tana gama tofawa sai ta guntsa da fesa aikam ta ke Mama ta ja numfashi mai k'arfi, Beebah ta k'ara guntsan ruwan sai dai kafin ta fesa mata akaro da biyu tari ya sark'eta kofin da ruwan addu'ar ke ciki ya kufce a hannunta ya zube a k'asa. Sannu na yi ta jera mata har zuwa sadda tarin ya lafa ta matso muka cigaba da tofawa Mama addu'a. Tsawon rabin awa muna fama da Mama kafin mu samu ta dawo hayyacinta ta soma ambatar Hasbunallahu wal ni'imal wakil, da k'arfi ganin haka muma muka somabinta, zuwa wani lokaci sai ta rufe da salati. Gumi sai b'ulb'ulowa ya keyi daga sassan jikinta, gamin haka sai muka samu madai-daitan towel muka soma goge mata, lumshe idanu ta yi tana mai ambatar albarka a garemu. Bayan munga ta sani natsuwa sai muka kamata zuwa saman katifa, ta dubeni cikin tarin rauni ta ce "Uwata akwai damuwa a gidan nan, hak'ik'a da idanuna naga wani halitta mai kama da maciji na son hayomin gado shi ne ya firgitani wallahi ji na yi kamar zuciyata zata fito sabida tsoron halittar, tabbas da yazo da ajali da yanzu zuciyana ta buga na zamo gawa, kin koma marainiya na hak'ik'a."
"Mama kwanta ki huta gobe da safe sai muyi maganar kuma in Allah yaso kinfi k'arfi dik kan abin sharri daga jinsin mutum da aljan, insha Allah burinki sai ya cika a kaina k'asa bai rufe idanunki ba."
"Allah yaso hakan Uwata."
"Amin."
Muka amsa tare da Beebah.
Maganin ciwon kai ta nemi in bata ta sha, Beebah ta b'allo Boska d'aya Sudrex d'aya ta bata, tana sha bajimawa barci ya d'auketa cikin fitar murmushi mai cike da natsuwa.
Kasa komawa barci na yi sai na d'auro alwallah nasoma jera nafil-fili cikin kaiwa Allah kukana da ya karemu daga dukkan sharrin abin cutarwa na fili da b'oye, Beebah itama maramin baya ta yi, haka muka kwana addu'o'i. Bayan mun idar da sallar Subahi muka shiga d'akin Mama a tsorace bakinmu d'auke da addu'a, bamuga komi ba, Beebah ta ce mu bincika ko ina amma Mama ta hana ta ce mai cire maciji zaizo ya cire shi.
Hak'ik'a abin ya tab'a min zuciya ganin yarda Mama ta koma kamar yarinya domin da taji motsi zata zabura ta k'ank'ameni ko Beebah, sukalewa na yi na shiga bayin waje na kulle kaina na yi ta kuka cikin rashin fitar sauti, bayan na rar-rashi kaina na fito cikin k'ok'arin sanya wal-wala a fusakata gudun sake dagulawa Mama lissafi. Ko abinci ba wanda ya ci dan ko abin karyawa bamu sami damar had'awa ba saboda halin da mukaga Mama ya gama kashe Mana jiki domin da gari ya yi haske ta garas sai ta rik'a sunbatu tamkar wacce brain d'inta ya ke son tab'uwa, da mun had'a ido hawaye ke zubomin amma bana bari ta gani Beebah ce ta fahimta tasoma yimin nasiha a hankali gudun kada Mama taji ta k'ara bircikewa. Haka muka kasance da Mama mun kasa dawo da ita asalin natsuwarta.
Da hantsi mai cire maciji yazo ya gama hayak'insa da bincikensa baiga komi ba ya tafi, Beebah ce ta sanarwa da Uncle halin da ake ciki yana zuwa bai jira komi ba ya kira wani Malami da d'alibansa suka zauna danyin saukan alqur'anin a gidan, mu kuma ya ce mu tafi da Mama asibiti ganin yarda ta ke yin abun tamkar rud'ad'd'iyar tsohuwa, shima lamarin ya firgitashi.
Kwatanta damuwan dana shiga ba mai misaltuwa ba ce, na yi kuka har na ji zuciyata na son samun matsala ta hanyar jin ina fizgar numfashi da kyar tare da jin tanayimin zugi, kan dole na rarrashi kaina da kaina tunda nak'i jin ban bakin su Beebah.
Babban DAMUWATA shi ne na rashin sanin halin da Mamana ke ciki tsawon awanni shida da muka kawaota domin mun kawota da mintoci goma sha biyar Likitoci suka shige da ita wani d'aki sai dai inga sun fito sun shiga ba labarin komi, lamarin ya k'ara d'agamin hankali kenan nakasa sauraren ban bakin kowa hatta kuwa da Uncle domin gani na ke basu san kalan damuwarta da na ke ciki ba ne shi yasa suke cewa na daina kuka dan inda banyi kukan ba tabbas da nima ina kwance a gadon majinyata.
Bayan na gabatar da sallar magriba na dawo bak'in k'ofar da ka saka Mama na kife fuskata a jikin bangon na kuma fashewa da kuka mara sauti saboda tuni muryata ta dushe.
"Dan girman Allah kiyi hak'uri Aminiyata, ki tuna falalar mai yarda da k'addara ta khairan ko kishiyarta, kina da sani akansa shin me yasa bazaki zamo cikin masu mik'a lamuransu ga Ubangijin da baya barci balle gyan-gyad'i ba? Ki yi hak'uri irin wacce Allah ya umurci bayinsa mumunai da su aikata idan jarabawar rayuwa ta riskesu, ki sani Allah da ya jarabci Mama da lalura nan ya fiki sonta sannan faruwan hakan alamun tana cikin bayinsa salihai ne wanda ke dorawa cuta domin gwada imaninsu tare da shafewar zunubai."
Rungume Fanta ya yi tsan-tsan ina kuka mai ciccira.
"Insha Allah Mama zata warke jinkirin bayyanar halin da ta ke ciki alkhairi zai zamo biy jahiy Nabiyyi S.A.W."
"Allah ya so hakan, nagode sosai Aminiyata."
Na ambata batare da tunanin tajiyoni ba saboda yarda muryan ke fita can a mak'oshina.
"Ku tafi da ita gida ta huta."
Na tsinkayi muryan Uncle daf da ni.
Da sauri na juyo na rik'o hannunsa batare da tunanin komi ba saboda natsuwana ya yi balaguro.
"A'a Uncle ba zan iya hutawa ba alhalin Mamana na cikin wannan halin, ka barni har zuwa sadda zan san halin da ta ke ciki."
"Wani hali ta ke ciki?"
Ya cillomin tambayar tamkar bai san komi da ke faruwa ba.
Maimakon amsa masa sai na saki hannunsa na koma jikin Beebah na kwantar da kaina a kafad'arta na fashewa da sabon kuka.
"Beebah ku tafi da ita gida na ce."
"Ba zanje ba!."
Na furta da k'arfi.
"A haka kike son Mama ta yi ido biyu da ke? Kin koma tamkar wacce ta yi amai da zawo, oya ki tafi gida ki huta wannan shi ne umurnina na k'arshe akanki."
Ban sa ke magana ba kuma ban daina kuka ba, hawaye na bin cheek d'ina tamkar an bud'e famfo na motsa masa kai alamun cika umurninsa. Jan hannuna Bintu ta yi na kalleta naga itama kukan ta ke yi.
"Kunga idan kuka zaku koma kunayi banga amfanin had'aku da ita ba."
"Sorry Uncle mun bari."
Fanta ta ambata cikin muryan kuka.
"Ku tabbatar da ta ci abincin kafin in iso."
"To."
Beebah ta amsa a hankali.
"Yaya me yasa bazaka barta ta shiga ta ganta ba? Tana fa cikin yanayi mai kyau itama burinta ta sanya d'iyarta a ido."
Wata murya mai sanyi naji ya ambaci haka, ai banjira amsawan Uncle ba na juyo da gudu caraf Uncle ya kamani ya matse hannuna gam.
Runtse ido na yi saboda da yarda rik'on ya ratsa sassan jikina.
"Ki tafi gida idan kin dawo zaki ganta."
"Dan soyayyarka da Ma'aikin Allah ka barni inga halin da Mamana ke ciki kafin in tafi."
Sakina ya yi wani hannu mai mugun d'umi sama dana Uncle ya kamani haka nasoma binsa tamkar jela a k'ofar wani d'aki ya tsaya ya juyamin baya dama banga fuskansa ba, ban kuma damu da sai nagani ba.
"Ki shiga tana ciki amma idan kika d'aga mata hankali da wannan kukan naki tabbas da kaina zan fito da ke."
Motsa kai na yi tare da tura k'ofar d'akin na fad'a ciki da sauri dan gani na ke tamkar Uncle zai hanani duk da baibiyo bayanmu ba.