Sashe 12
Damuwata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Kibar zancen Uwata wata rana ba sai kin tambayeni ba zan sanar miki."
"Mama dan Allah ki fitar da ni a duhu game da lamurana da Baba."
"Uwata kinsan na sanar miki zan baki labarin kaina ko?"
"Eh Mama."
"To mafarin tare suke da labarina"
Shiru na yi alamun ina son sani na dai k'yale ne kawai saboda bana cikin masu naci akan abu.
"Ina rok'onki Uwata ba dan ni sai dan wanda ya yi halittarmu cikin isa da mulkinsa wato Allah S.A.W da ki bar zancen nan in lokacin ki sani ya yi zansanar miki batare da kin nemi sani ba, ko d'azun natsuwarki na ke son gani shi yasa na ce ki taho kiji amma ba manufata na sanar da ke abin da kike burin sani ba, dafatan zakiyi hak'urin zuwar lokacin dana d'iba?"
"Shikenan Mama abin da kikace shi zanbi kuma zan dakaci zuwan lokacin da yarda Allah."
"Da kyau Uwata alfaharin Mamanta."
Murmushin na yi ganin yarda Mama ta yi maganar ta sigan wayon da ake yiwa yara dan su manta da abu.
Dik yarda ran Mama ya b'aci haka nan ta danne ta soma yimin hira mai sanya nishad'i, nima ganin hakan sai na sake na nuna mata bana tare da damuwar komi sannan wannan damar nabi na sanar da ita abin da ya faru game da buk'atar malamai na son in koma koyarwa kullum amaimakon a sati sau biyu dana ke zuwa.
"Uwata inaga ki sanar da su kin k'ara kwana d'aya akan kwanaki biyun da kikeyi sai ki koma shiga sau uku a sati Asabar, Litini da Laraba."
"Wallahi nima hakan na raya a raina Mama."
"To kingani, dama na hango rashin son hayaniyar da bakiso ne, haka zanso ki huta ba wai ace kullum kina zaryan fita ba."
"Mamana ta kaina, kina son Deejah ta huta alhalin itad'in ba 'yar hutu ba ce."
"Inji wa ya ce miki ke ba 'yar hutu ba ce?"
"Ni na fad'awa kaina."
"To ki sanar da kanki ke 'yar hutu ce domin baki nemi komi kin rasa ba."
"Haka ne Mama, a kullum Ina alfahari da samunki a matsayin mahifiya domin kin gama sharemin hawayen babu akan duk kan komi, wallahi sosai nake sonki Mamana."
"Ina godiya Uwata. Allah ya nunamin aurenki k'asa bai rufe idanuna ba."
Sunkuyar da kaina nayi ina murmushi tare da amsawa da Amin a cikin raina. So na ke na sanar da ita yau wani ya furtamin kalman so amma inajin nauyin ambata.
"Duk ranar da za'a kaiki gidan miji a ranar zan sanar dake abinda ya shige miki duhu Uwata, kada ki saka damuwa akan lamarin ked'in d'iyarmu ce abin alfaharinmu."
"Allah ya kaimu lokacin lafiya Mama, nima ina alfahari da ku."
"Muna godiya da hakan."
"Mamana kiyi hak'uri dan Allah ki sanarmin laifin da nayiwa Baba yau har ya tunzurashi yazo dukana dan in kiyaye sake aita laifin."
"Uhm Uwata bakiyi masa komi ba fad'ar ni da shi ne, to ganin ban kulashi mun raba hali ba shi ne ya d'auko doriga ya huce akanki tunda ni bazan doku masa ba sannan ya tabbatar in ya tab'aki zan kulashi."
"Mama kema kiyi ta hak'uri da lamuran Baba insha Allah watarana sai labari."
"To Uwata Allah ya cigaba da bamu hak'uri."
"Amin."
"Mamana wai meye abin adona?"
"Uwata baki san abin adonki ba?"
Shiru nayi zuwa can na amsa "Na sani kawai ina son k'arin baya ni ne."
"To sanarmin inji in kinsani."
"Ke ce abin adona Mamana domin hakan d'azun na sanarwa da Malam Hassan da ya sanarmin cewa wai Baba ne abin adona sannan naji d'azun kin ce shi ba abin adona ba ne sai na k'ara tabbatarwa da ke d'ince abin adona."
"Eh gaskiya Malam Hassan ya fad'a miki, Uba shi ne abin ado Uwata, daga yau duk wanda ya tambayeki abin adonki ki sanar masa da cewa Mahaifinki shi ne abin adonki, saboda duk tink'ahon 'ya ko d'a to da Uba suke ado domin shi ne haskensu a idanun al'umma ko da aya suke kuwa sune dai tink'ahonsu domin baki tab'a jin ance Mace ta zamo waliyyiya a wurin d'aurin aure ba sannan zancena na d'azun bacin rai ne ya sa na furta hakan amma Babanki shi ne abin adonki ta ko wani fuska."
Idanu na tsira mata ina auna zantukan saman harshenta zuwa cikin ruhinta sai na ji baya rasa nak'asu ganin a yarda ta dage tana mai-maita zantukan tamkar wacce aka tursasa.
"Ki cire shakku Uwata haka zancen ya ke har zu...
"Kina nufin duk takun sak'an dake tsakanina da Baba shi ne abin adona ba ke ba?"
Na katse mata abin da ta yi niyyar ambata.
"Tabbas Malam abin adonki ne Uwata haka nima abin adonki ce."
"Shi kenan Mama na amince zan rik'esa na d'an lokaci zuwa sadda zanyi aure amma ke zan rik'eki na har abada."
"A'a Uwata ki rik'emu abin adonki na har abada kinji."
"Kiyi hak'uri Mamana haka nan kawai na ji zuciyata takasa amincewa da in rik'e Baba na har abada kamar yarda na aminta na rik'eki."
"Lallai zuciyarki ta sanar miki da karatun gaskiya Uwani, kada ki sake ki rik'e ni abin adonki koda na minti daya ne domin bazan rufe miki cinya ba yayin da kika zo d'aura zani."
Idanu na zubawa Baba dake tsaye bakin k'ofar shigowa d'akin barcin Mama. Sai na sami kaina da jin fad'uwar gaba duk da ban gama fahimtar zancensa ba amma na hasko har cikin ruhinsa zancen ya fito. Motsa min kai ya yi alamun tabbatar da kalamansa fuskan nan nasa kamar dare saboda yarda ya d'aureta babu alamun rahma.
"Ki rik'eni ayar zuciyarki ta amince miki Uwani domin bazata sanar dake k'arya ba."
Ya furta cikin halin ko in kula.
Lumshe ido na yi ina hasko Baba a wani muhalli na daban wanda ya haddasa k'arin bugun zuciyana.
"Hurera ina son yau ayita ta k'are tsakanina da ke."
Jin abinda ya furta yasa na bud'e ido da sauri na sauke kan Mama wacce tayi k'asa da kai hakan danagani ya kuma jefa zuciyata cikin rud'ani matsananci.
"Kin amince na baki takardan sakin da kika nema yanzu?"
Da sauri na kalli Baba ya watsomin harara da jajayen idanunsa. Girgiza masa kai na yi cikin zubar hawaye na isa gabansa, ina bud'e baki zanyi magana kuka ya kufcemin sai na kife fuskata a saman k'afafunsa na soma rerawa cikin fitar sauti. Na sami wasu mintoci inayin kukan wanda bai k'areni da komi ba sai janyomin k'arin k'unci a zuciya zuwa can na tsagaita, cikin rawar murya na d'ago na kalli Baba na ce "Ba dan na isa ba sai dan martaban Manzon Allah S.A.W kada ka saki Mamana, ta tuba ga dukkan laifin da ta aikata maka cikin sani da rashinsa kuma bazata sake aikata abinda zai sosa maka raiba insha Allah. Ka hukuntani Baba idan yin hakan zai wanke maka b'acin ran da kake ciki, ka dukeni iya yarda ranka yaso ni d'in abar ikonka ce amma kada ka saki Mamana dan girman Allah."
Tsit d'akin yayi sai sautin kukana kawai ke tashi.
"Kinji abinda Uwani ta rok'a miki ko Hurera? Shin kin amince bazaki sake yimin rashin d'a'a ba tare da nunan iko akanta?"
"Eh na amince amma bisa sharad'in zaka dawonin da dukiyata da ke hannunka kafataninsu."
"Me ye! haka kikeyi Hurera!? Shin soyayyar d'iyarmu har ya kai wannan matakin ban sani ba?"
"Kafi kowa sanin abinda na keyi Malam kuma daga yau zuwa gobe na baka dan ina son ganin dukiyata a kammale tamkar yarda ka amsa domin kwandala ban amince ta yi ciwon kai ba, sannan ka aikata duk abin da kake ganin ruhinka na k'issima maka akan ni da Uwata ban hanaka ba amma ka sani ka tab'amin shaksiyyanta billahil azim sai na yi shari'a da kai wannan a rubuce ya ke bazan d'aga maka k'afa ba a game da dagulawa Nana Khadijatu lissafi, dafatan ka tuna zantukanmu na gaban Baba Umaru?"
Mama na gama ambatar haka ta mik'e ta janyo hijab d'inta ta zira ta fice batare da ta bari idanunmu ya had'u ba gudun kada in hanata aikata k'udirinta.
Kallona na maida kan Baba wanda zufa ke ta tsats-tsafo masa a saman goshi.
"Me ke faruwa Baba? Fitar da ni a duhu dan Allah."
Na jero masa tambayar jikina na rawa.
Abin maamki sai naga Baba ya sunkuyo gabana ya kamo hannuna ya matse gam a cikin nasa, ya yi k'asa da murya cikin cewa "Uwani ki taimaka ki bawa Mamanki baki da tabar maganar dukiyan nan sabida wallahi bani da hanyar samosu."
Shiru na yi ina cigaba kallonsa, sake yin k'asa da murya ya yi ya ce "Idan kika sanya baki nasan zata hak'ura bazata kuma tada zancen ba sannan kin taimaki Mahaifinki ga kub'uta daga tozarcin duniya idan mamanki ta k'wace dukiyanta da ya zamo rufin asirinsa."
"Baba idan na yi hakan zaka dawo yin mu'amala dani mai kyau kuma zaka amince kai d'in abin adona ne?"
"Zan daina hantararki Uwani idan kin cika alk'awari."
"Zamowa abin ado fa?"
"Kada ki damu Uwani aike d'iyata ce, ni dai burina ki tursasa Hurera data ya femin dukiyanta dake kaina yafiya kuma na har abada."
"To zaka janye zancen sakinta har abada kaima?"
"Wannan zancen an barshi Uwani, ni da Hurera aurenmu mutu ka raba takalmin kaza sunarsa da yardan Allah."
"Ina godiya Baba."
"Bakomi Uwani fatana dai ki cika alk'awari."
"To Baba amma shin kud'in ya kai...
"Uwani ke yarinyar kirkice mai hankali gami da natsuwa, Allah yayi miki albarka."
Shiru na yi ganin ya datsemin abinda zan furta da yimin yabo abinda ya zamemin sabon abu daga gareshi.
"Uwani ke haske ce a rayuwarmu ni da Hurera dan haka ki kuma zamowa haske wanda bai yankewa a gareni ta hanyar yimin wannan alfarman."
"To Baba amma ka amsa...
"A'a Uwani kada ki yimin tambaya wanda samo amsarta zai zamemin babban aiki."
"Shikenan Baba na bar tambayar, insha Allah Mama zata mallaka maka."
"Da kyau Uwani, Allah ya rayaki rayuwa mai albarka."
"Amin ya rabbi Baba."
"Zan tafi amma dan Allah kada ki muna mata ni na tursasaki da ki rok'armin yafiyanta, kawai ki nuna mata ra'ayinki ne aikata hakan."
"Zan kiyaye baiyanar sunarka Baba."
"Madallah d'iyar arziki."
"Mama dan Allah ki fitar da ni a duhu game da lamurana da Baba."
"Uwata kinsan na sanar miki zan baki labarin kaina ko?"
"Eh Mama."
"To mafarin tare suke da labarina"
Shiru na yi alamun ina son sani na dai k'yale ne kawai saboda bana cikin masu naci akan abu.
"Ina rok'onki Uwata ba dan ni sai dan wanda ya yi halittarmu cikin isa da mulkinsa wato Allah S.A.W da ki bar zancen nan in lokacin ki sani ya yi zansanar miki batare da kin nemi sani ba, ko d'azun natsuwarki na ke son gani shi yasa na ce ki taho kiji amma ba manufata na sanar da ke abin da kike burin sani ba, dafatan zakiyi hak'urin zuwar lokacin dana d'iba?"
"Shikenan Mama abin da kikace shi zanbi kuma zan dakaci zuwan lokacin da yarda Allah."
"Da kyau Uwata alfaharin Mamanta."
Murmushin na yi ganin yarda Mama ta yi maganar ta sigan wayon da ake yiwa yara dan su manta da abu.
Dik yarda ran Mama ya b'aci haka nan ta danne ta soma yimin hira mai sanya nishad'i, nima ganin hakan sai na sake na nuna mata bana tare da damuwar komi sannan wannan damar nabi na sanar da ita abin da ya faru game da buk'atar malamai na son in koma koyarwa kullum amaimakon a sati sau biyu dana ke zuwa.
"Uwata inaga ki sanar da su kin k'ara kwana d'aya akan kwanaki biyun da kikeyi sai ki koma shiga sau uku a sati Asabar, Litini da Laraba."
"Wallahi nima hakan na raya a raina Mama."
"To kingani, dama na hango rashin son hayaniyar da bakiso ne, haka zanso ki huta ba wai ace kullum kina zaryan fita ba."
"Mamana ta kaina, kina son Deejah ta huta alhalin itad'in ba 'yar hutu ba ce."
"Inji wa ya ce miki ke ba 'yar hutu ba ce?"
"Ni na fad'awa kaina."
"To ki sanar da kanki ke 'yar hutu ce domin baki nemi komi kin rasa ba."
"Haka ne Mama, a kullum Ina alfahari da samunki a matsayin mahifiya domin kin gama sharemin hawayen babu akan duk kan komi, wallahi sosai nake sonki Mamana."
"Ina godiya Uwata. Allah ya nunamin aurenki k'asa bai rufe idanuna ba."
Sunkuyar da kaina nayi ina murmushi tare da amsawa da Amin a cikin raina. So na ke na sanar da ita yau wani ya furtamin kalman so amma inajin nauyin ambata.
"Duk ranar da za'a kaiki gidan miji a ranar zan sanar dake abinda ya shige miki duhu Uwata, kada ki saka damuwa akan lamarin ked'in d'iyarmu ce abin alfaharinmu."
"Allah ya kaimu lokacin lafiya Mama, nima ina alfahari da ku."
"Muna godiya da hakan."
"Mamana kiyi hak'uri dan Allah ki sanarmin laifin da nayiwa Baba yau har ya tunzurashi yazo dukana dan in kiyaye sake aita laifin."
"Uhm Uwata bakiyi masa komi ba fad'ar ni da shi ne, to ganin ban kulashi mun raba hali ba shi ne ya d'auko doriga ya huce akanki tunda ni bazan doku masa ba sannan ya tabbatar in ya tab'aki zan kulashi."
"Mama kema kiyi ta hak'uri da lamuran Baba insha Allah watarana sai labari."
"To Uwata Allah ya cigaba da bamu hak'uri."
"Amin."
"Mamana wai meye abin adona?"
"Uwata baki san abin adonki ba?"
Shiru nayi zuwa can na amsa "Na sani kawai ina son k'arin baya ni ne."
"To sanarmin inji in kinsani."
"Ke ce abin adona Mamana domin hakan d'azun na sanarwa da Malam Hassan da ya sanarmin cewa wai Baba ne abin adona sannan naji d'azun kin ce shi ba abin adona ba ne sai na k'ara tabbatarwa da ke d'ince abin adona."
"Eh gaskiya Malam Hassan ya fad'a miki, Uba shi ne abin ado Uwata, daga yau duk wanda ya tambayeki abin adonki ki sanar masa da cewa Mahaifinki shi ne abin adonki, saboda duk tink'ahon 'ya ko d'a to da Uba suke ado domin shi ne haskensu a idanun al'umma ko da aya suke kuwa sune dai tink'ahonsu domin baki tab'a jin ance Mace ta zamo waliyyiya a wurin d'aurin aure ba sannan zancena na d'azun bacin rai ne ya sa na furta hakan amma Babanki shi ne abin adonki ta ko wani fuska."
Idanu na tsira mata ina auna zantukan saman harshenta zuwa cikin ruhinta sai na ji baya rasa nak'asu ganin a yarda ta dage tana mai-maita zantukan tamkar wacce aka tursasa.
"Ki cire shakku Uwata haka zancen ya ke har zu...
"Kina nufin duk takun sak'an dake tsakanina da Baba shi ne abin adona ba ke ba?"
Na katse mata abin da ta yi niyyar ambata.
"Tabbas Malam abin adonki ne Uwata haka nima abin adonki ce."
"Shi kenan Mama na amince zan rik'esa na d'an lokaci zuwa sadda zanyi aure amma ke zan rik'eki na har abada."
"A'a Uwata ki rik'emu abin adonki na har abada kinji."
"Kiyi hak'uri Mamana haka nan kawai na ji zuciyata takasa amincewa da in rik'e Baba na har abada kamar yarda na aminta na rik'eki."
"Lallai zuciyarki ta sanar miki da karatun gaskiya Uwani, kada ki sake ki rik'e ni abin adonki koda na minti daya ne domin bazan rufe miki cinya ba yayin da kika zo d'aura zani."
Idanu na zubawa Baba dake tsaye bakin k'ofar shigowa d'akin barcin Mama. Sai na sami kaina da jin fad'uwar gaba duk da ban gama fahimtar zancensa ba amma na hasko har cikin ruhinsa zancen ya fito. Motsa min kai ya yi alamun tabbatar da kalamansa fuskan nan nasa kamar dare saboda yarda ya d'aureta babu alamun rahma.
"Ki rik'eni ayar zuciyarki ta amince miki Uwani domin bazata sanar dake k'arya ba."
Ya furta cikin halin ko in kula.
Lumshe ido na yi ina hasko Baba a wani muhalli na daban wanda ya haddasa k'arin bugun zuciyana.
"Hurera ina son yau ayita ta k'are tsakanina da ke."
Jin abinda ya furta yasa na bud'e ido da sauri na sauke kan Mama wacce tayi k'asa da kai hakan danagani ya kuma jefa zuciyata cikin rud'ani matsananci.
"Kin amince na baki takardan sakin da kika nema yanzu?"
Da sauri na kalli Baba ya watsomin harara da jajayen idanunsa. Girgiza masa kai na yi cikin zubar hawaye na isa gabansa, ina bud'e baki zanyi magana kuka ya kufcemin sai na kife fuskata a saman k'afafunsa na soma rerawa cikin fitar sauti. Na sami wasu mintoci inayin kukan wanda bai k'areni da komi ba sai janyomin k'arin k'unci a zuciya zuwa can na tsagaita, cikin rawar murya na d'ago na kalli Baba na ce "Ba dan na isa ba sai dan martaban Manzon Allah S.A.W kada ka saki Mamana, ta tuba ga dukkan laifin da ta aikata maka cikin sani da rashinsa kuma bazata sake aikata abinda zai sosa maka raiba insha Allah. Ka hukuntani Baba idan yin hakan zai wanke maka b'acin ran da kake ciki, ka dukeni iya yarda ranka yaso ni d'in abar ikonka ce amma kada ka saki Mamana dan girman Allah."
Tsit d'akin yayi sai sautin kukana kawai ke tashi.
"Kinji abinda Uwani ta rok'a miki ko Hurera? Shin kin amince bazaki sake yimin rashin d'a'a ba tare da nunan iko akanta?"
"Eh na amince amma bisa sharad'in zaka dawonin da dukiyata da ke hannunka kafataninsu."
"Me ye! haka kikeyi Hurera!? Shin soyayyar d'iyarmu har ya kai wannan matakin ban sani ba?"
"Kafi kowa sanin abinda na keyi Malam kuma daga yau zuwa gobe na baka dan ina son ganin dukiyata a kammale tamkar yarda ka amsa domin kwandala ban amince ta yi ciwon kai ba, sannan ka aikata duk abin da kake ganin ruhinka na k'issima maka akan ni da Uwata ban hanaka ba amma ka sani ka tab'amin shaksiyyanta billahil azim sai na yi shari'a da kai wannan a rubuce ya ke bazan d'aga maka k'afa ba a game da dagulawa Nana Khadijatu lissafi, dafatan ka tuna zantukanmu na gaban Baba Umaru?"
Mama na gama ambatar haka ta mik'e ta janyo hijab d'inta ta zira ta fice batare da ta bari idanunmu ya had'u ba gudun kada in hanata aikata k'udirinta.
Kallona na maida kan Baba wanda zufa ke ta tsats-tsafo masa a saman goshi.
"Me ke faruwa Baba? Fitar da ni a duhu dan Allah."
Na jero masa tambayar jikina na rawa.
Abin maamki sai naga Baba ya sunkuyo gabana ya kamo hannuna ya matse gam a cikin nasa, ya yi k'asa da murya cikin cewa "Uwani ki taimaka ki bawa Mamanki baki da tabar maganar dukiyan nan sabida wallahi bani da hanyar samosu."
Shiru na yi ina cigaba kallonsa, sake yin k'asa da murya ya yi ya ce "Idan kika sanya baki nasan zata hak'ura bazata kuma tada zancen ba sannan kin taimaki Mahaifinki ga kub'uta daga tozarcin duniya idan mamanki ta k'wace dukiyanta da ya zamo rufin asirinsa."
"Baba idan na yi hakan zaka dawo yin mu'amala dani mai kyau kuma zaka amince kai d'in abin adona ne?"
"Zan daina hantararki Uwani idan kin cika alk'awari."
"Zamowa abin ado fa?"
"Kada ki damu Uwani aike d'iyata ce, ni dai burina ki tursasa Hurera data ya femin dukiyanta dake kaina yafiya kuma na har abada."
"To zaka janye zancen sakinta har abada kaima?"
"Wannan zancen an barshi Uwani, ni da Hurera aurenmu mutu ka raba takalmin kaza sunarsa da yardan Allah."
"Ina godiya Baba."
"Bakomi Uwani fatana dai ki cika alk'awari."
"To Baba amma shin kud'in ya kai...
"Uwani ke yarinyar kirkice mai hankali gami da natsuwa, Allah yayi miki albarka."
Shiru na yi ganin ya datsemin abinda zan furta da yimin yabo abinda ya zamemin sabon abu daga gareshi.
"Uwani ke haske ce a rayuwarmu ni da Hurera dan haka ki kuma zamowa haske wanda bai yankewa a gareni ta hanyar yimin wannan alfarman."
"To Baba amma ka amsa...
"A'a Uwani kada ki yimin tambaya wanda samo amsarta zai zamemin babban aiki."
"Shikenan Baba na bar tambayar, insha Allah Mama zata mallaka maka."
"Da kyau Uwani, Allah ya rayaki rayuwa mai albarka."
"Amin ya rabbi Baba."
"Zan tafi amma dan Allah kada ki muna mata ni na tursasaki da ki rok'armin yafiyanta, kawai ki nuna mata ra'ayinki ne aikata hakan."
"Zan kiyaye baiyanar sunarka Baba."
"Madallah d'iyar arziki."