Sashe 3
Damuwata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
*Ina kuke Mata 'yan kwalisa masu bawa fatarsu 'yancinta musanman babban kadararku wato fuska. To ga dama ta zo muku cikin sauk'i wato samun kayan gyarar fuska da jiki mai inganci na organic wanda aka samar da su da abubuwa masu nagarta. Duk wacce K'uraje, Tabbai, Sunburn, kyafsi suka b'atawa fuska muna da maganin da fuskanta zai dawo fes, sumul, rangad'ad'au. Haka a fannin fatar jiki shima muna da kayan da zaiyi laushi, sulb'i tare da haske mai kyau. Ga kayan kamar haka:*
Sabulu (molato and black soap)
Scrub
Face cream
Oil
Body lotion
Shower gel
Kulachan
Humra (White and black)
Turaren tsugunon
Turaren kaya
Turaren wuta na d'aki
Garin d'a (domin k'an-k'aro martaban aure.)
*Duk za'a samesu a farashi mai rahusa, mai buk'atar d'aya ko sari a tun-tub'emu a wad'annan numbers 08132166848 ko 08147491137. Sai munjiku.*
[10/11, 11:39 AM] 💘: DAMUWANA (Sanin abin adona)
By Mrsjmoon.
EWF.
*Shafin sadaukarwa ne ga Zarah d'ansauka (Mom Jasrah) Allah ya yiwa rayuwa albarka.*
Page 02.
"Malam ya isheka! Wallahi Allah kana daf da kaini bango wanda zan ajiye komi a gefe na kwatarmana 'yancinmu dan haka ka bari kawai cikin girma da arziki ko in shayar da kai ruwan mamaki, Uwata tawa ce ni kad'ai, eh na amince hakan sai ka barmin d'iya ta shak'i iskan 'yanci kamar ko wani yaro tunda ka nesanta kanka da ita."
Dafa bago na yi idanu waje domin jin yarda Mama ke magana ya jefani cikin rud'ani.
"Kingama d'iban albarka naki?"
Na jiyo Baba ya furta a hankali wanda na shiga cikin mamakin jin muryan nasa cikin sanyi tamkar banasa ba, domin zan iya cewa tunda na taso ban tab'a jin maganarsa a hankali irin wannan ba.
"Da saurana"
Mama ta ambata muryanta na rawa alamun ta soma kuka. Dafe goshina na yi cike da damuwa domin wata rana bana jin dad'in yarda Mama ke amsawa Baba zantuka kai tsaye ba ladabi irin na Mata zuwa ga Mijinta.
"Ina saurarenki isash-shiya."
Wannan karan cikin masifa Baba ya ambata lamarin da ya kuma sanyamin jiki kenan na sake lafewa sosai dan in jiyo zantukan da kyau, zuciyana sai harbawa ta ke yi tamkar zata fito daga ma'ajiyarta.
"Malam kaji tsoron Allah wallahi saninka bai amfana maka komi ba tunda kake kan cutar da mutanen da basu san ta ina aka hau ba balle su san inda za'a sauka, kafi kowa sanin li'irabi akan k'addararren al'amari amma saboda son zuciya irin naka ka bi ka ta ke ka juya masa baya to wallahi ka sani laifi kake aikatawa mai girma wanda Allah sai ya tambayeka kiwon mu da ya baka a matsayinka na shigabanmu kuma Malami wanda ke koyar da mutane bin haryar sanin Allah da Manzonsa."
Lumshe ido na yi cikin jin k'arin mutuwar jiki, kalamn Mama suna amsa kuwwa a cikin kunnuwana.
'Uwata ta wace ni kad'ai' shi ne kalman da ke maimaita kansa a cikin brain d'ina. Gyara tsayuwa na yi cike da burin sanin fassaran kalman. Shiru ban sa ke jin motsin komi ba dan ko tari ban jiyo Baba ya yi ba haka Mama ta daina shesshekan kukan, jikina ya sake macewa, kwakwalwata ta d'auki zafi ainun, kukan da najiyo Mama ta fashe da shi mai sauti kamkar wacce aka duka yasa na zabura kamar zan shiga cikin d'akin sai kuma na tsaya cak ina jan numfashi sai nima na fashe da kukan cikin rashin fitar sauti, jikina sai rawa yakeyi. Jin alamun tafiya za'a fito sai na koma mazaunin da Mama ta tashi da sauri na soma juya kunun ayar tare da sauke kaina k'asa hawaye na d'iga saman zanin jikina.
Inaji a jikina kallona Baba ke yi sadda ya fito, ban d'ago ba balle in gaishesa kamar yarda nasaba, kimanin mintoci biyu zuwa uku ya bar wurin batare da yaja min tsakinsa da ya saba ba. D'agowa na yi na rakashi da ido daf da zai shiga zauren ya waigo muka had'a ido ya juya da sauri ya fice na sake ware manyan idanuna da sukayimin nauyi, cike na ke da mamakin sauyawarsa lokaci d'aya daga mai sababi zuwa mai sanyi domin tunda na mallaki hankalina Baba bai tab'a shigowa ya fice batare da ya zagi Uwana da Ubana ba ko da kuwa barci na ke yi ya shigo gidan tabbas kafin yafita sai ya zo inda na ke ya zunbud'amin zagi sannan zai tafi, abin har ya zamemin jiki shi yasa yau da baiyi sabon nashi ba na shiga mamaki.
Da tunanin sauyin nasa na tashi na shiga d'akin Mama bata a falo kai tsaye na shiga uwar d'aka na hangota kwance saman gado ta juyawa k'ofar shigowa baya tana kuka cikin k'aramin sauti a sanyaye na hau gadon na kwanta a jikinta na fashe da kuka mai k'arfi, a rud'e ta juyo ta rungume ni tana shanye kukanta amma yak'i shanyuwa ba yarda ta iya dole ta biyemin muka cigaba da kuka tamkar wad'anda aka yiwa dukan tsiya. Zuwa wani lokaci Mama ta tsaida kukan ta soma shafamin baya alamun rarrashi amma ban san tanayi ba sabida a lokacin ma naji wani sabon kuka na zuwamin, na ko b'are baki na yi ta yi cikin sark'ewar tari.
"Ya isa haka nan Uwata, bakiga nima da kike tayawa na hak'ura ba, bakomi haka Allah ya nufemu da zama a k'asan jagora mara fahimta kinga kenan hak'uri ya zame mana dole."
"Mama ba rashin fahimta ba ne tsabar rashin adalci ne a matsayinsa na Malami amma sam bai aiki da saninsa, wallahi wani zubin in ya aikata abu tamkar ba mai koyar da d'aliba ilimi ba."
"Uwata kalamanki akan hanya suke Malam baiyi mana adalci ko kad'an, bai aiki da sanin da Allah ya hore masa haka bai duba sadaukarwan da muke kanyi masa domin hakkinmu da ya rataya a wuyarsa bai saukewa, ban tab'a damuwa ba saboda ina da rufin asirina wanda har wasu na ke taimakawa amma a hakan ban tsiraba saima biyoni da tijara da ke kanyi akan abinda yasan rayuwa ce ba wanda yafi k'arfin fuskantan irinta."
"Mama muyi ta hak'uri wata rana sai labari."
"Shi ne abinda na ke nusar da ke amma ki sani da gajiya fa."
"To ya zamuyi da shi?"
"Uhm a kwai Allah ai kuma kinsan dan yasan ke ce lagona shi yasa ya ke b'ata miki domin raina ya b'aci, tun kina k'ara yake min wannan d'abi'ar amma zuwa sadda kika girma sai ya sanja salo da yawan ambatarki da sunar asara alhalin ke d'in arziki ce mai tarin yawa domin wani daga cikin dukiyar da na ke tak'ama da shi har shima ya ke cin moriyarta ke ce silar albarkansu."
"Ni kuma Mama?"
"Eh ke ce Uwata domin bayan na sayi idan nan mun tare sai b'arayi suka shigo suka sacemin abinda ya ragemin na kudi wanda na b'oye zanyi jari, anyi abin da kwana biyu kika shigo da kaza budurwa makwafciyata marigayiya Iya Mai Kunu ta baki dan kiyi kiwo to itace tayi ta zuba mana 'ya'ya na saidasu ma siya miki tunkiya da matashin rago wanda Hajiya Inna ta cika kud'in domin ita ta siyo a k'auye da haka suka cigaba da hayayyafa ta hanyar saida raguna ina k'aro tumakai, kajin suma ina saidawa tare da tara kudad'en cikin amincin Allah a shekaru uku zuwa hud'u nasiya firjin wanda yanzu muke kan samun abin rufin asiri da shi."
"Ikon Allah Mama a she ina da k'ashin arziki haka amma Baba ke kirata da suna mara albarka?"
"Uwata kenan wannan halin Malam ne tijara dik wanda ya tsana ko da kuwa kullum zai kwanta ya bi ta kansa ya wuce ba zai daina aibatashi ba, ni kaina bai barni ba duk da ranar da na yi masa wanda ya ke fankama shi mai dukiya ne yafi k'arfi wulak'anci."
"Mama wai me yasa ya tsaneni to?"
Shiru Mama bata amsamin ba sai na Kuma jefo mata tambayar da ke cimin rai.
"To Mama ko dai nid'in ba d'iyarsa ba ce kamar yarda Maman su Khamila ta ke ambatamin kalman karere?"
"Yau she ta kiraki da wannan sunar?"
"Tunda nayi hankali ta ke ambatamin sunar shi yasa bana son zuwa gidan ke kuma sai ki matsamin akan sai naje munyi zumunci da 'yan uwana."
Shiru Mama ta yi na zuba mata ido cikin fad'uwar gaba.
"Mama gaskiya ta ke fad'a ko?"
"Uwata ke d'in ba karere ba ce domin ita da d'iyoyinta arzikinki suke kan ci dan da kud'inki mijinta ya sami bud'i har ta zama haka ta sami bakin kiranki da sunar banza amma zanyiwa tufkan hanci daga yau bata sake ambatamin ki sunar."
"Mama wai kina nufin Baba Usman ke ce kika ranta masa kud'in da keyin sana'a shi ne dalilin da dik sati ke kawo miki riba?"
"Eh, jari na bashi dik in aka sami riban sati sai ya raba uku ya bani kaso d'aya ya rik'e kaso biyu."
"Ikon Allah Mama kina da hali mai kyau shi yasa muke ganin haske a lamuranmu."
"Dik ke ce sila Uwata."
"Uhm Mamana ta kaina."
Na ambata cikin murmushi domin labarin ya farantamin rai ainun.
"Uwata in har ina numfashi bazakiyi kukan damuwa ba sai bisa rubutaccen al'amari."
"Allah ya amince hakan Mamana."
"Amin."
"Yawwa Mama wai me a baya jama'a sun nunamin kulawa da k'auna kamar yarda na ke gani anayiwa yara?"
"Sosai kuwa an nuna miki k'auna Uwata, dan a yarintarki ke d'in mai masoya ne domin Allah ya hore miki farin jini na ban mamaki, ga samun kyauta a wurare da dama."
"To Mama me yasa yanzu sai naga kamar suna k'yamata?"
Na cillo Mata tambayar cikin tsareta da idanu. Kauda kai naga ta yi zuwa can najiyo muryanta cikin rawa.
"Uwata kinfi gaban a k'yamaceki duk da ta...
"Duk da me ne Mama?"
"Tashi muje mu kammala aikinmu tambayoyin sun isa haka Uwata."
"To Mama amma dan Allah kidaina yiwa Baba kuka sabida yanajin dad'in ganin hawayenki abin da na lura da shi kenan."
"Na bari Uwata, taso muje muna aiki kina bani labarin yarda d'alibanki ke amsan karatu."
Mike'ewa na yi ina maijin natsuwar ruhi ganin Mama tana walwala.
"Ina sonki Mamana."
Sabulu (molato and black soap)
Scrub
Face cream
Oil
Body lotion
Shower gel
Kulachan
Humra (White and black)
Turaren tsugunon
Turaren kaya
Turaren wuta na d'aki
Garin d'a (domin k'an-k'aro martaban aure.)
*Duk za'a samesu a farashi mai rahusa, mai buk'atar d'aya ko sari a tun-tub'emu a wad'annan numbers 08132166848 ko 08147491137. Sai munjiku.*
[10/11, 11:39 AM] 💘: DAMUWANA (Sanin abin adona)
By Mrsjmoon.
EWF.
*Shafin sadaukarwa ne ga Zarah d'ansauka (Mom Jasrah) Allah ya yiwa rayuwa albarka.*
Page 02.
"Malam ya isheka! Wallahi Allah kana daf da kaini bango wanda zan ajiye komi a gefe na kwatarmana 'yancinmu dan haka ka bari kawai cikin girma da arziki ko in shayar da kai ruwan mamaki, Uwata tawa ce ni kad'ai, eh na amince hakan sai ka barmin d'iya ta shak'i iskan 'yanci kamar ko wani yaro tunda ka nesanta kanka da ita."
Dafa bago na yi idanu waje domin jin yarda Mama ke magana ya jefani cikin rud'ani.
"Kingama d'iban albarka naki?"
Na jiyo Baba ya furta a hankali wanda na shiga cikin mamakin jin muryan nasa cikin sanyi tamkar banasa ba, domin zan iya cewa tunda na taso ban tab'a jin maganarsa a hankali irin wannan ba.
"Da saurana"
Mama ta ambata muryanta na rawa alamun ta soma kuka. Dafe goshina na yi cike da damuwa domin wata rana bana jin dad'in yarda Mama ke amsawa Baba zantuka kai tsaye ba ladabi irin na Mata zuwa ga Mijinta.
"Ina saurarenki isash-shiya."
Wannan karan cikin masifa Baba ya ambata lamarin da ya kuma sanyamin jiki kenan na sake lafewa sosai dan in jiyo zantukan da kyau, zuciyana sai harbawa ta ke yi tamkar zata fito daga ma'ajiyarta.
"Malam kaji tsoron Allah wallahi saninka bai amfana maka komi ba tunda kake kan cutar da mutanen da basu san ta ina aka hau ba balle su san inda za'a sauka, kafi kowa sanin li'irabi akan k'addararren al'amari amma saboda son zuciya irin naka ka bi ka ta ke ka juya masa baya to wallahi ka sani laifi kake aikatawa mai girma wanda Allah sai ya tambayeka kiwon mu da ya baka a matsayinka na shigabanmu kuma Malami wanda ke koyar da mutane bin haryar sanin Allah da Manzonsa."
Lumshe ido na yi cikin jin k'arin mutuwar jiki, kalamn Mama suna amsa kuwwa a cikin kunnuwana.
'Uwata ta wace ni kad'ai' shi ne kalman da ke maimaita kansa a cikin brain d'ina. Gyara tsayuwa na yi cike da burin sanin fassaran kalman. Shiru ban sa ke jin motsin komi ba dan ko tari ban jiyo Baba ya yi ba haka Mama ta daina shesshekan kukan, jikina ya sake macewa, kwakwalwata ta d'auki zafi ainun, kukan da najiyo Mama ta fashe da shi mai sauti kamkar wacce aka duka yasa na zabura kamar zan shiga cikin d'akin sai kuma na tsaya cak ina jan numfashi sai nima na fashe da kukan cikin rashin fitar sauti, jikina sai rawa yakeyi. Jin alamun tafiya za'a fito sai na koma mazaunin da Mama ta tashi da sauri na soma juya kunun ayar tare da sauke kaina k'asa hawaye na d'iga saman zanin jikina.
Inaji a jikina kallona Baba ke yi sadda ya fito, ban d'ago ba balle in gaishesa kamar yarda nasaba, kimanin mintoci biyu zuwa uku ya bar wurin batare da yaja min tsakinsa da ya saba ba. D'agowa na yi na rakashi da ido daf da zai shiga zauren ya waigo muka had'a ido ya juya da sauri ya fice na sake ware manyan idanuna da sukayimin nauyi, cike na ke da mamakin sauyawarsa lokaci d'aya daga mai sababi zuwa mai sanyi domin tunda na mallaki hankalina Baba bai tab'a shigowa ya fice batare da ya zagi Uwana da Ubana ba ko da kuwa barci na ke yi ya shigo gidan tabbas kafin yafita sai ya zo inda na ke ya zunbud'amin zagi sannan zai tafi, abin har ya zamemin jiki shi yasa yau da baiyi sabon nashi ba na shiga mamaki.
Da tunanin sauyin nasa na tashi na shiga d'akin Mama bata a falo kai tsaye na shiga uwar d'aka na hangota kwance saman gado ta juyawa k'ofar shigowa baya tana kuka cikin k'aramin sauti a sanyaye na hau gadon na kwanta a jikinta na fashe da kuka mai k'arfi, a rud'e ta juyo ta rungume ni tana shanye kukanta amma yak'i shanyuwa ba yarda ta iya dole ta biyemin muka cigaba da kuka tamkar wad'anda aka yiwa dukan tsiya. Zuwa wani lokaci Mama ta tsaida kukan ta soma shafamin baya alamun rarrashi amma ban san tanayi ba sabida a lokacin ma naji wani sabon kuka na zuwamin, na ko b'are baki na yi ta yi cikin sark'ewar tari.
"Ya isa haka nan Uwata, bakiga nima da kike tayawa na hak'ura ba, bakomi haka Allah ya nufemu da zama a k'asan jagora mara fahimta kinga kenan hak'uri ya zame mana dole."
"Mama ba rashin fahimta ba ne tsabar rashin adalci ne a matsayinsa na Malami amma sam bai aiki da saninsa, wallahi wani zubin in ya aikata abu tamkar ba mai koyar da d'aliba ilimi ba."
"Uwata kalamanki akan hanya suke Malam baiyi mana adalci ko kad'an, bai aiki da sanin da Allah ya hore masa haka bai duba sadaukarwan da muke kanyi masa domin hakkinmu da ya rataya a wuyarsa bai saukewa, ban tab'a damuwa ba saboda ina da rufin asirina wanda har wasu na ke taimakawa amma a hakan ban tsiraba saima biyoni da tijara da ke kanyi akan abinda yasan rayuwa ce ba wanda yafi k'arfin fuskantan irinta."
"Mama muyi ta hak'uri wata rana sai labari."
"Shi ne abinda na ke nusar da ke amma ki sani da gajiya fa."
"To ya zamuyi da shi?"
"Uhm a kwai Allah ai kuma kinsan dan yasan ke ce lagona shi yasa ya ke b'ata miki domin raina ya b'aci, tun kina k'ara yake min wannan d'abi'ar amma zuwa sadda kika girma sai ya sanja salo da yawan ambatarki da sunar asara alhalin ke d'in arziki ce mai tarin yawa domin wani daga cikin dukiyar da na ke tak'ama da shi har shima ya ke cin moriyarta ke ce silar albarkansu."
"Ni kuma Mama?"
"Eh ke ce Uwata domin bayan na sayi idan nan mun tare sai b'arayi suka shigo suka sacemin abinda ya ragemin na kudi wanda na b'oye zanyi jari, anyi abin da kwana biyu kika shigo da kaza budurwa makwafciyata marigayiya Iya Mai Kunu ta baki dan kiyi kiwo to itace tayi ta zuba mana 'ya'ya na saidasu ma siya miki tunkiya da matashin rago wanda Hajiya Inna ta cika kud'in domin ita ta siyo a k'auye da haka suka cigaba da hayayyafa ta hanyar saida raguna ina k'aro tumakai, kajin suma ina saidawa tare da tara kudad'en cikin amincin Allah a shekaru uku zuwa hud'u nasiya firjin wanda yanzu muke kan samun abin rufin asiri da shi."
"Ikon Allah Mama a she ina da k'ashin arziki haka amma Baba ke kirata da suna mara albarka?"
"Uwata kenan wannan halin Malam ne tijara dik wanda ya tsana ko da kuwa kullum zai kwanta ya bi ta kansa ya wuce ba zai daina aibatashi ba, ni kaina bai barni ba duk da ranar da na yi masa wanda ya ke fankama shi mai dukiya ne yafi k'arfi wulak'anci."
"Mama wai me yasa ya tsaneni to?"
Shiru Mama bata amsamin ba sai na Kuma jefo mata tambayar da ke cimin rai.
"To Mama ko dai nid'in ba d'iyarsa ba ce kamar yarda Maman su Khamila ta ke ambatamin kalman karere?"
"Yau she ta kiraki da wannan sunar?"
"Tunda nayi hankali ta ke ambatamin sunar shi yasa bana son zuwa gidan ke kuma sai ki matsamin akan sai naje munyi zumunci da 'yan uwana."
Shiru Mama ta yi na zuba mata ido cikin fad'uwar gaba.
"Mama gaskiya ta ke fad'a ko?"
"Uwata ke d'in ba karere ba ce domin ita da d'iyoyinta arzikinki suke kan ci dan da kud'inki mijinta ya sami bud'i har ta zama haka ta sami bakin kiranki da sunar banza amma zanyiwa tufkan hanci daga yau bata sake ambatamin ki sunar."
"Mama wai kina nufin Baba Usman ke ce kika ranta masa kud'in da keyin sana'a shi ne dalilin da dik sati ke kawo miki riba?"
"Eh, jari na bashi dik in aka sami riban sati sai ya raba uku ya bani kaso d'aya ya rik'e kaso biyu."
"Ikon Allah Mama kina da hali mai kyau shi yasa muke ganin haske a lamuranmu."
"Dik ke ce sila Uwata."
"Uhm Mamana ta kaina."
Na ambata cikin murmushi domin labarin ya farantamin rai ainun.
"Uwata in har ina numfashi bazakiyi kukan damuwa ba sai bisa rubutaccen al'amari."
"Allah ya amince hakan Mamana."
"Amin."
"Yawwa Mama wai me a baya jama'a sun nunamin kulawa da k'auna kamar yarda na ke gani anayiwa yara?"
"Sosai kuwa an nuna miki k'auna Uwata, dan a yarintarki ke d'in mai masoya ne domin Allah ya hore miki farin jini na ban mamaki, ga samun kyauta a wurare da dama."
"To Mama me yasa yanzu sai naga kamar suna k'yamata?"
Na cillo Mata tambayar cikin tsareta da idanu. Kauda kai naga ta yi zuwa can najiyo muryanta cikin rawa.
"Uwata kinfi gaban a k'yamaceki duk da ta...
"Duk da me ne Mama?"
"Tashi muje mu kammala aikinmu tambayoyin sun isa haka Uwata."
"To Mama amma dan Allah kidaina yiwa Baba kuka sabida yanajin dad'in ganin hawayenki abin da na lura da shi kenan."
"Na bari Uwata, taso muje muna aiki kina bani labarin yarda d'alibanki ke amsan karatu."
Mike'ewa na yi ina maijin natsuwar ruhi ganin Mama tana walwala.
"Ina sonki Mamana."