Sashe 35
Damuwata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ba musu Mama ta kwanta gefena sai na kwanto rabin jikina a saman nata na lumshe ido ina mik'a godiya ga Allah da ya bani mahaifiya irin Mama mai damuwa da dukkan DAMUWATA.
Karatun Qur'ani Hajiya Inna ta soma cikin harshen karatun zaure saboda shi ta iya, na yi tsam ina saurarenta domin naji dadinsa har ina burin iyashi, natsuwar huri ya wadacemu baki d'aya barci ya daukemu batare da mun sani ba. Hak'ik'a samun ilimim addani musanman na Alqur'ani babban falala ce, gashi haske ne ga dukkanin duhu.
***
Baba gidan ya koma cike da fushin yarda Mama tak'i yi masa magana tunda ta kulashi sau d'aya bata sake nuna tana wurin ba wannan abu da ta yi ya k'ona masa rai. Wanka ya yi da ruwan sanyi saboda ranar da ya kwaso tare da tiri-rin da zuciyarsa keyi masa. A baranda ya zauna yana bincikensa, sai tsaki ya ke ta dokawa saboda ya kasa gane komi, zuwa can ya ture mazubin k'asar gefe ya zabga tagumi.
K'arar da wayarsa ta yi ne ya katse masa tunani ya d'auka da hanzari ganin sunar Babban yaronsa Auwalu ya bayyana. Sallamarsa ya amsa bai tsaya amsa gaisuwarsa ba ya rufeshi da fad'a akan kiransa da ya yi.
"Kayi hak'uri Baba matsala ce babban yasa dole sai na kiraka."
"Me ye shi?"
"Innar su Kamalu da Innar su Anas na wurin 'yan sanda."
Tsaye Baba ya mik'e yana cewa "Me! suka janyowa kansu ni Hadi?"
"Wallahi Baba ban san ainihin abinda ya faru ba amma dai Baba Usman ya sanarmin wai Innar su Kamalu ce ta jefa 'yar sanda a rijiya daga tazo da K'asimu cikin ankwa."
"Innalillahi! Yau na shiga uku da wad'an nan matan jaraba, to yanzu anciro 'yar sandan ko kuwa?"
"Eh ancirota amma da wuya ta rayu saboda ance bata motsi yanzu dai an wuce da ita Asibiti dan a tabbatar da rayuwarta."
"Kai kana ina ne yanzu?"
"Ina bawa d'alibai karatu."
"To ka sallamesu ka tafi ofishin 'yan sanda idan an tamabayeka inda na ke ka ce na yi tafiya yau da subahi ban san komi akai ba saboda ba a gidan na kwana ba."
Jim Auwalu ya yi amma tsawar da Baba ya daka masa sai ya amsa jikinsa na rawa. Ka she kiran ya yi yana share gumi.
"Amma anyi shegun nata masu janyomin bala'i ina zaman lafiyana, wallahi ba mai kaini belinsu, su da suka janyo masifar ya k'are akansu, yanzu bari in nemi Alhaji Muhseen muje wurin 'yan banzan yaran can a zabgawa iyayensu tara na samu na sakawa a aljihu domin walalhi cewa zanyi sun kwashe rabin waken sun siyar sun dawo kwashe sauran ne Allah ya toni asirinsu aka kamasu kuma sai anbiya ninkin kud'in, duk buhu d'aya a sittin da biyu zai tashi na ce buhu ashirin da biyar suka sace, iyayensu sayi maganin shed'ancinsu domin sunji a jikinsu."
Murmushi ya yi jiyo k'amshin zuwar kud'ad'e a bulus.
Cikin gaggawa ya shirya ya fito yana sab'a babban riga ya doshi gidan Uncle dan ya tabbatar zuwa yanzu ya baro Asibitin. Mai gadi ya aika ba jimawa sai Uncle ya fito cikin shigar kamala sai k'amshi ya ke bugawa. gaisar da shi Uncle ya yi amkar wani abu mara dad'i bai faru ba. Suna tafiya cikin mota Baba na sanar da shi yarda yatsara za'a amsa wurin iyayen yaran shi dai Uncle baice uffanba saboda ya san darace zataci gida domin tuni ya sami labarin 'ya'yan Baba ne b'arayin. Suna isa 'yan sanda suka kewaye Baba zasuyi masa tijara, Uncle ne ya yi musu magana tare da tunasar da su girman rawanin da ke kansa. Baba kam sai zare ido ya ke yi jin abin da 'yan sandan ke fad'a.
' Yanzu b'arayin nan ashe su Kamalu ne? Iyayensu suka turo su? Kenan na shigo hannu duk boren danayi bazanyi asarar kud'i ba a she sai na yi dai, kai anyi sokayen mata marasa sanin ciwon kai, inbanda b'atan basira ta ya zasu shigo sata gidan Hurera, gidan da akayi saukan Alqur'ani mai girma cikinsa, to wallahi zanyi belin ku amma zan baku mamaki matuk'ar mamaki, zaku san kun zubdamin da martaba.'
"Baba muje ciki."
Ya tsinkayi muryan Uncle daf da shi wanda ya taimaka wurin katse masa zantukan zuccin da ya ke yi. Wani kallo ya saukewa Uncle tare da girgiza kai.
'Kome ya faru kai ne sanadi da baka kira masu babbak'un kaya ba da banga zubewar mutunci ba, wallahi ni kad'ai nasan tsiyar da zan shuka maka.'
"Baba ka natsu ba wanda ya isa ya kulleka tunda ina wurin kuma belin matarka zanyi shi insha Allah tunda anyi sa'a 'yar sanda da ta jefa rijiya bata mutu ba haka bataji babban ciwo ba balle buguwa mai wuyar magani firgicin ne ya sanyata dogon suma amma yaran sai sunje gidan yari domin gaba suji tsoron aikata sata."
"Nagode Alhaji."
Abinda Baba ya iya ambata kenan shima jin ba shi ne zai kashe kud'in belinsu Asabe ba amma ba dan ya daina jin haushin Uncle ba
Duk wani kace na ce Uncle ne ya shige gaba har aka basu belin su Hinde wanda suka sha dukan tsiya fuskansu dik ya bumbure sakamakon sanadin jefa 'yar sanda rijiya da Asabe ta yi shi yasa ana kawosu 'yan uwan aikinta mata suka rufesu da dukan kawo wuk'a. Hinde kam ta tsinewa Asabe ba iyaka ya yin da Asaben ke saurarenta ta kasa ramawa saboda tafi buguwa.
Kallonsu Baba ke yi a tsiyace ba d'igon tausayin halin da suke ciki ya yin da su kam sun kasa had'a ido da shi, ko wacce cike ta ke da farban makoman aurenta domin sunfi kowa sanin masifar Baba barinma da duka zubar masa da mutunci aka kawosu gidan masu babbak'un kaya, gidan da keyiwa tofin Allah tsine ba gaira ba dalili.
***
Sadda na farko gari ya yi haske, Mama na hango rik'e da Alqur'ani tana bita a sirrance, ban nuna mata na tashi ba sai na lafe tare da lumshe ido ina kallonta ta k'asar gashin idanu cike da k'auna mara misaltuwa.
Hajiya Inna ce ta matso kusa da Mama ta yi k'asa da murya bayan ta saukemin kallo na seconni. Samun kaina na yi da bud'e kunnuwa da kyau domin jiyo zancen da zatayi wanda na raya a kaina ne sai dai sab'anin zargina sai na ji ta soma cewa "Hurera su Babanki zasu dawo gobe insha Allah sannan ya ce in sanar miki da ki zauna cikin shiri na tafiya duba Alhaji Abdul ganiyu domin tafiyar gaggawan da ya yi sanar masa akayi ya rasu shi ne ya tafi domin ya sami jana'iza sai ya samu dogon suma ya yi."
"Innalillahi wa inna ilaihin raji'un, Insha Allah da Uwata ta sami sauk'i zamu tafi Inna, dama ina shirin tafiyar ne lalura ta samemu."
"Hakan ya kamata, sannan Alhaji ya sanarmin shi Alhaji Abdul ganiyu na son magana da ke baki da baki."
"Ayya Baba ai da ya sanarwa da Baba Umaru sai ya sanarmin."
"Ba zai rasa sanar da shi ba amma dai yafi buk'atar ya yi maganar da ke ido da ido."
"To ina nan tafe da yardan Allah."
"Madallah, sannan ina baki shawara idan kun baro kwara to ku sauka a Sokoto sada zumunta, ki watsar da duk abinda ya faru abaya inda hali ki yafe musu domin kema Allah ya yafe miki."
"Inna ban jin zan iya yafewa dangin mahaifina, sannan bazan tab'a waiwayansu ba, yarda suka bawa Duniya ni to zan tabbatar musu ni d'in ta Duniya ce domin na gamu da ku masu karamci fiye da su marasa adalci."
"A'a Hurera ki zamo mai yafiya sannan idan kika aikata haka mahaifinki ba zaiji dad'i ba domin duk tunk'ahon d'a ko 'ya da asalinsu suke tutiya ko da kuwa a ya suke su ne dai ababen adonta duniya da hahira"
"Allah sarki Babana mai sona tare da damuwa da duk abinda ya shafeni, da shi na saba saboda mahaifiyata banyi wayon saninta ba amma yarda ya ke bani labarinta sai na ke ji tamkar na rayu da ita sannan indai sune zanyi tink'ahon da su wallahi gara na dauwama ba dangi tunda ina da sanyin idaniyata Nana Khadijatu."
"Allah ya gafarta musu da Rahma, amma Hurera ya kamata ki rage zafin nan da kika d'auka ki tuna bawa bai tsallake zanen k'addararsa domin lamari ne da Allah ya samar da shi tun kafin tsiron halittar bayi."
"To Hajiya Inna zan duba."
"Hakan na ke son ji domin rik'o bai da kyau."
"Nagode Inna."
"Bakomi, sannan abu na gaba dole ki sanar da Khadija...
"Dan girman Allah Inna mu bar wannan maganar."
"Saboda me kike b'oye gaskiyan alhalin lokacin abayyana ya yi?"
"Bana son damuwarta saboda DAMUWATA ce."
"Wannan ba hujja ba ce Hurera."
"Hajiya Inna dan girman Allah na ce ki bar magana zamuyita gaba."
"To ai shi kenan tunda kinga hakan yafi miki."
"Dan Allah kiyi hak'uri Inna."
"Bakiyimin komi ba Hurera dama shawara ce na kawo tunda kince sai nan gaba ina yi miki fatar kaiwa lokacin cikin rayuwa."
"Allah ya amince."
"Amin."
Daga haka suka sanja labari zuwa zancen mugun halin Baba wanda banso hakan ba.
"Bisa alamu Mama na da babban damuwar da ta ke b'oyemin."
Na furta hakan wanda fitar sautinsu suka tsaya a iyaka saman lab'b'ana.
*Munata gangara izuwa k'arshen free pages dai.*😍 Pay 300 to 0468069082 Haruna Safiyya GTbank. Send the evidence to WhatsApp number 08132166848.
*TALLA.*
*Ina kuke Mata 'yan kwalisa masu bawa fatarsu 'yancinta musanman babban kadararku wato fuska. To ga dama ta zo muku cikin sauk'i wato samun kayan gyarar fuska da jiki mai inganci na organic wanda aka samar da su da abubuwa masu nagarta. Duk wacce K'uraje, Tabbai, Sunburn, kyafsi suka b'atawa fuska muna da maganin da fuskanta zai dawo fes, sumul, rangad'ad'au. Haka a fannin fatar jiki shima muna da kayan da zaiyi laushi, sulb'i tare da haske mai kyau. Ga kayan kamar haka:*
Sabulu (molato and black soap)
Scrub
Face cream
Oil
Body lotion
Shower gel
Kulachan
Humra (White and black)
Turaren tsugunon
Turaren kaya
Turaren wuta na d'aki
Garin d'a'a (domin k'an-k'aro martaban aure a turaka)
Karatun Qur'ani Hajiya Inna ta soma cikin harshen karatun zaure saboda shi ta iya, na yi tsam ina saurarenta domin naji dadinsa har ina burin iyashi, natsuwar huri ya wadacemu baki d'aya barci ya daukemu batare da mun sani ba. Hak'ik'a samun ilimim addani musanman na Alqur'ani babban falala ce, gashi haske ne ga dukkanin duhu.
***
Baba gidan ya koma cike da fushin yarda Mama tak'i yi masa magana tunda ta kulashi sau d'aya bata sake nuna tana wurin ba wannan abu da ta yi ya k'ona masa rai. Wanka ya yi da ruwan sanyi saboda ranar da ya kwaso tare da tiri-rin da zuciyarsa keyi masa. A baranda ya zauna yana bincikensa, sai tsaki ya ke ta dokawa saboda ya kasa gane komi, zuwa can ya ture mazubin k'asar gefe ya zabga tagumi.
K'arar da wayarsa ta yi ne ya katse masa tunani ya d'auka da hanzari ganin sunar Babban yaronsa Auwalu ya bayyana. Sallamarsa ya amsa bai tsaya amsa gaisuwarsa ba ya rufeshi da fad'a akan kiransa da ya yi.
"Kayi hak'uri Baba matsala ce babban yasa dole sai na kiraka."
"Me ye shi?"
"Innar su Kamalu da Innar su Anas na wurin 'yan sanda."
Tsaye Baba ya mik'e yana cewa "Me! suka janyowa kansu ni Hadi?"
"Wallahi Baba ban san ainihin abinda ya faru ba amma dai Baba Usman ya sanarmin wai Innar su Kamalu ce ta jefa 'yar sanda a rijiya daga tazo da K'asimu cikin ankwa."
"Innalillahi! Yau na shiga uku da wad'an nan matan jaraba, to yanzu anciro 'yar sandan ko kuwa?"
"Eh ancirota amma da wuya ta rayu saboda ance bata motsi yanzu dai an wuce da ita Asibiti dan a tabbatar da rayuwarta."
"Kai kana ina ne yanzu?"
"Ina bawa d'alibai karatu."
"To ka sallamesu ka tafi ofishin 'yan sanda idan an tamabayeka inda na ke ka ce na yi tafiya yau da subahi ban san komi akai ba saboda ba a gidan na kwana ba."
Jim Auwalu ya yi amma tsawar da Baba ya daka masa sai ya amsa jikinsa na rawa. Ka she kiran ya yi yana share gumi.
"Amma anyi shegun nata masu janyomin bala'i ina zaman lafiyana, wallahi ba mai kaini belinsu, su da suka janyo masifar ya k'are akansu, yanzu bari in nemi Alhaji Muhseen muje wurin 'yan banzan yaran can a zabgawa iyayensu tara na samu na sakawa a aljihu domin walalhi cewa zanyi sun kwashe rabin waken sun siyar sun dawo kwashe sauran ne Allah ya toni asirinsu aka kamasu kuma sai anbiya ninkin kud'in, duk buhu d'aya a sittin da biyu zai tashi na ce buhu ashirin da biyar suka sace, iyayensu sayi maganin shed'ancinsu domin sunji a jikinsu."
Murmushi ya yi jiyo k'amshin zuwar kud'ad'e a bulus.
Cikin gaggawa ya shirya ya fito yana sab'a babban riga ya doshi gidan Uncle dan ya tabbatar zuwa yanzu ya baro Asibitin. Mai gadi ya aika ba jimawa sai Uncle ya fito cikin shigar kamala sai k'amshi ya ke bugawa. gaisar da shi Uncle ya yi amkar wani abu mara dad'i bai faru ba. Suna tafiya cikin mota Baba na sanar da shi yarda yatsara za'a amsa wurin iyayen yaran shi dai Uncle baice uffanba saboda ya san darace zataci gida domin tuni ya sami labarin 'ya'yan Baba ne b'arayin. Suna isa 'yan sanda suka kewaye Baba zasuyi masa tijara, Uncle ne ya yi musu magana tare da tunasar da su girman rawanin da ke kansa. Baba kam sai zare ido ya ke yi jin abin da 'yan sandan ke fad'a.
' Yanzu b'arayin nan ashe su Kamalu ne? Iyayensu suka turo su? Kenan na shigo hannu duk boren danayi bazanyi asarar kud'i ba a she sai na yi dai, kai anyi sokayen mata marasa sanin ciwon kai, inbanda b'atan basira ta ya zasu shigo sata gidan Hurera, gidan da akayi saukan Alqur'ani mai girma cikinsa, to wallahi zanyi belin ku amma zan baku mamaki matuk'ar mamaki, zaku san kun zubdamin da martaba.'
"Baba muje ciki."
Ya tsinkayi muryan Uncle daf da shi wanda ya taimaka wurin katse masa zantukan zuccin da ya ke yi. Wani kallo ya saukewa Uncle tare da girgiza kai.
'Kome ya faru kai ne sanadi da baka kira masu babbak'un kaya ba da banga zubewar mutunci ba, wallahi ni kad'ai nasan tsiyar da zan shuka maka.'
"Baba ka natsu ba wanda ya isa ya kulleka tunda ina wurin kuma belin matarka zanyi shi insha Allah tunda anyi sa'a 'yar sanda da ta jefa rijiya bata mutu ba haka bataji babban ciwo ba balle buguwa mai wuyar magani firgicin ne ya sanyata dogon suma amma yaran sai sunje gidan yari domin gaba suji tsoron aikata sata."
"Nagode Alhaji."
Abinda Baba ya iya ambata kenan shima jin ba shi ne zai kashe kud'in belinsu Asabe ba amma ba dan ya daina jin haushin Uncle ba
Duk wani kace na ce Uncle ne ya shige gaba har aka basu belin su Hinde wanda suka sha dukan tsiya fuskansu dik ya bumbure sakamakon sanadin jefa 'yar sanda rijiya da Asabe ta yi shi yasa ana kawosu 'yan uwan aikinta mata suka rufesu da dukan kawo wuk'a. Hinde kam ta tsinewa Asabe ba iyaka ya yin da Asaben ke saurarenta ta kasa ramawa saboda tafi buguwa.
Kallonsu Baba ke yi a tsiyace ba d'igon tausayin halin da suke ciki ya yin da su kam sun kasa had'a ido da shi, ko wacce cike ta ke da farban makoman aurenta domin sunfi kowa sanin masifar Baba barinma da duka zubar masa da mutunci aka kawosu gidan masu babbak'un kaya, gidan da keyiwa tofin Allah tsine ba gaira ba dalili.
***
Sadda na farko gari ya yi haske, Mama na hango rik'e da Alqur'ani tana bita a sirrance, ban nuna mata na tashi ba sai na lafe tare da lumshe ido ina kallonta ta k'asar gashin idanu cike da k'auna mara misaltuwa.
Hajiya Inna ce ta matso kusa da Mama ta yi k'asa da murya bayan ta saukemin kallo na seconni. Samun kaina na yi da bud'e kunnuwa da kyau domin jiyo zancen da zatayi wanda na raya a kaina ne sai dai sab'anin zargina sai na ji ta soma cewa "Hurera su Babanki zasu dawo gobe insha Allah sannan ya ce in sanar miki da ki zauna cikin shiri na tafiya duba Alhaji Abdul ganiyu domin tafiyar gaggawan da ya yi sanar masa akayi ya rasu shi ne ya tafi domin ya sami jana'iza sai ya samu dogon suma ya yi."
"Innalillahi wa inna ilaihin raji'un, Insha Allah da Uwata ta sami sauk'i zamu tafi Inna, dama ina shirin tafiyar ne lalura ta samemu."
"Hakan ya kamata, sannan Alhaji ya sanarmin shi Alhaji Abdul ganiyu na son magana da ke baki da baki."
"Ayya Baba ai da ya sanarwa da Baba Umaru sai ya sanarmin."
"Ba zai rasa sanar da shi ba amma dai yafi buk'atar ya yi maganar da ke ido da ido."
"To ina nan tafe da yardan Allah."
"Madallah, sannan ina baki shawara idan kun baro kwara to ku sauka a Sokoto sada zumunta, ki watsar da duk abinda ya faru abaya inda hali ki yafe musu domin kema Allah ya yafe miki."
"Inna ban jin zan iya yafewa dangin mahaifina, sannan bazan tab'a waiwayansu ba, yarda suka bawa Duniya ni to zan tabbatar musu ni d'in ta Duniya ce domin na gamu da ku masu karamci fiye da su marasa adalci."
"A'a Hurera ki zamo mai yafiya sannan idan kika aikata haka mahaifinki ba zaiji dad'i ba domin duk tunk'ahon d'a ko 'ya da asalinsu suke tutiya ko da kuwa a ya suke su ne dai ababen adonta duniya da hahira"
"Allah sarki Babana mai sona tare da damuwa da duk abinda ya shafeni, da shi na saba saboda mahaifiyata banyi wayon saninta ba amma yarda ya ke bani labarinta sai na ke ji tamkar na rayu da ita sannan indai sune zanyi tink'ahon da su wallahi gara na dauwama ba dangi tunda ina da sanyin idaniyata Nana Khadijatu."
"Allah ya gafarta musu da Rahma, amma Hurera ya kamata ki rage zafin nan da kika d'auka ki tuna bawa bai tsallake zanen k'addararsa domin lamari ne da Allah ya samar da shi tun kafin tsiron halittar bayi."
"To Hajiya Inna zan duba."
"Hakan na ke son ji domin rik'o bai da kyau."
"Nagode Inna."
"Bakomi, sannan abu na gaba dole ki sanar da Khadija...
"Dan girman Allah Inna mu bar wannan maganar."
"Saboda me kike b'oye gaskiyan alhalin lokacin abayyana ya yi?"
"Bana son damuwarta saboda DAMUWATA ce."
"Wannan ba hujja ba ce Hurera."
"Hajiya Inna dan girman Allah na ce ki bar magana zamuyita gaba."
"To ai shi kenan tunda kinga hakan yafi miki."
"Dan Allah kiyi hak'uri Inna."
"Bakiyimin komi ba Hurera dama shawara ce na kawo tunda kince sai nan gaba ina yi miki fatar kaiwa lokacin cikin rayuwa."
"Allah ya amince."
"Amin."
Daga haka suka sanja labari zuwa zancen mugun halin Baba wanda banso hakan ba.
"Bisa alamu Mama na da babban damuwar da ta ke b'oyemin."
Na furta hakan wanda fitar sautinsu suka tsaya a iyaka saman lab'b'ana.
*Munata gangara izuwa k'arshen free pages dai.*😍 Pay 300 to 0468069082 Haruna Safiyya GTbank. Send the evidence to WhatsApp number 08132166848.
*TALLA.*
*Ina kuke Mata 'yan kwalisa masu bawa fatarsu 'yancinta musanman babban kadararku wato fuska. To ga dama ta zo muku cikin sauk'i wato samun kayan gyarar fuska da jiki mai inganci na organic wanda aka samar da su da abubuwa masu nagarta. Duk wacce K'uraje, Tabbai, Sunburn, kyafsi suka b'atawa fuska muna da maganin da fuskanta zai dawo fes, sumul, rangad'ad'au. Haka a fannin fatar jiki shima muna da kayan da zaiyi laushi, sulb'i tare da haske mai kyau. Ga kayan kamar haka:*
Sabulu (molato and black soap)
Scrub
Face cream
Oil
Body lotion
Shower gel
Kulachan
Humra (White and black)
Turaren tsugunon
Turaren kaya
Turaren wuta na d'aki
Garin d'a'a (domin k'an-k'aro martaban aure a turaka)