Sashe 1
Damuwata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
[10/10, 2:55 PM] 💘: DAMUWATA. (Sanin abin adona)
By Mrsjmoon
*EXQUISITE WRITER'S FORUM ( EWF).*
Da sunan Allah mai Rahma mai jin kai. Allahumma salli ala sayyidina Muhammadu wa ala alihi ada-da mafi ilmi salatin da'imatan bi du'a'un Janna. S.A.W.
*Sharhi.*
Labarin (DAMUWATA) hak'k'ina ne ban yarda a juyamin shi ta wani siga ba ko yimin iko da shi ta hanyar had'a document ko makamancin haka sannan ba kyauta ba ne amma da pages masu zuwa domin farin cikinku masoya. Allah ya sa mu amfana da darasoshin da ke cikinsa na khairan, muyi watsi da kishiyar shi Allahumma amin.
*Jimlar littafan marubuciyar:*
Free books.
Mabrukha
Ra'ayi
Rayuwar Bahijja.
A tunanina
Ruwan dare.
Paid books.
Bak'on lamari
Rashin jituwa
Banyi zato ba
Rabi'atul Addawiyya
Rumasa'u
Mutunci Madara ne
Doctor Laylah.
*Baki d'aya shafin sadaukarwa ne ga Aunty Maijidda Musa (Aunty Jidda) Allah ya albarkaci rayuwarta tare da zuri'arta biy jahiy Nabiy S A.W.*
Page 01.
Cikin talatainin dare wanda masu iya magana kan kirasa da suna mahutar bawa. Ni kam a gareni kiran shi na yi da lokacin gadin kaina domin zaune na ke a gefen katifana ba komi ke damuna ba sai barci wanda yake d'ibana ina korarsa da k'arfi da yaji domin bazanyi sakaci ya d'auke ni ba ya zamo rayuwata ta shiga garari. Abinda na kasa fahimta a rud'ad'd'en lamarin shi ne saceni ake sonyi ko kuwa b'atamin rayuwa.
'Sai dai b'ata miki rayuwa domin alamu sun nuna hakan.'
Sosa gefen wuyana na yi cikin aminta da amsan da zuciyata ta bani.
"Oh ni Deejah me ke shirin faruwa da ni ne? Waye wannan mutumin dake son dasamin bak'in tabbo mara b'acewa a jiki da ruhi? Ya Allah ga baiwarka Nana Khadijatu ka dubeni duban da batasan ya yake ba sai kai da ka halicceni, d'aukinka ya zamo jagoran yayewar duhun nan da na ke ciki."
Ruwan dake d'iga a bayan hannayena ya ankarad da ni kuka na ke yi mara sauti.
" Hak'ik'a DAMUWATA na dabanne da sauran mutane. Shin wai ahaka zan cigaba da rayuwa ban samun barci?"
Amsan da ban samoshi ba kenan tun soma fuskantan barazanar shigomin d'aki cikin dare har zuwa yanzu da na ke mai-maita shi.
Sake sosa wuyana na yi cike da tausayin kaina.
"A kwanaki biyun nan har na rame, samun barci alamun natsuwa ne dan haka rashinsa dole ya sakawa mutum ciwo, ya Rabbi ka bayyanamin abinda ke cikin duhun nan batare da hankalin Mamana ya tashi ba."
Motsin da na jiyo a bakin k'ofa yasa na zabura na koma bayan k'ofar na manne, jikina na mazari cikin bugawar k'irji, ina jin ana kici kicin bud'e k'ofar, ba jimawa akayi nasarar bud'ewa tare da turota a hankali, na d'auke numfashi ina kallon inuwar mugun sadda ya doshi saman katifana a cikin d'an hasken da ya shigo d'akin ta glob din waje, sam ban tsaya tantance ko waye ba duk da burina kenan gano shed'anin da ke lalibeni idan ina barci wanda na ke kwatar kaina da k'yar.
Ganin ya dage da neman inda na ke sai na silale cikin sand'a na fice daga d'akin zuwa mafakana wato d'akin tumakan Mama, wurin dana gyara tun da yamma dan b'oyewa saboda shigana makewayi ya sakani jin tsoro.
Na tsuguna a cikin dabbobi jikina na cigaba da rawa, damuwa ya kuma lullub'eni, sai lokacin naji dama na tsaya na kunna wutan d'akin naga fuskan mugun.
"A sannu zan gano ko waye insha Allah."
Na furta cikin matse gefen wuyana cikin nauyin idanu alamun kwanciya kawai na ke muradi.
'Deejah zurfin ciki banaki ba ne ki sanarwa Mama kada ya sami nasara akanki ya kaiki ya baro, ki jefa Mamanki cikin damuwa da ke kanki.'
"A'a ba zan iya wannan zancen da Mama ba, ina jin nauyin furta shi ga wanima balle Mamana."
'Zurfin ciki nan sam baiyi ba Deejah.'
"Na san da haka amma to ya zanyi?"
'Ki koreshi domin samun 'yancin furta matsalarki gudun cutuwa.'
Jinjina kai na yi domin na amince da wannan shawarar da zuciyata ta bani.
Na jima tsugune zuwan na ji wani abu mai sanyi na bin k'afana ya sa na mik'e, na kuma jin ya nad'emin dika k'afafun, aikam na daka uban tsalle na fad'a cikin tumakai, atake suka soma ihu sabida na firgitasu, bashiri nayo waje a guje na shige makewayi ina haki, muryan Mama da Baba na jiyo suna salati na fito da gudu a rud'e na rungume Mama ina mai danne kukana kada ya baiyana ta ritsani da tambayoyin dalilin yinsa alhali bani da amsa, sai na matse bakina da hannu d'aya ina lek'en abinda sukagani suke yiwa salati.
Maciji ne k'ato ya nad'e k'aramar tunkiya zare idanu na yi jikina na kuma d'aukan rawa ganin tunkiyar a wurin dana tsugunna d'azun ta ke kwance.
'Wato shi ne abinda d'azun ya nad'emin k'afafu?'
Tuno hakan ya sa na kwalla ihu ina tsalle tamkar macijin ne yazo ya sake nad'eni, a rud'e Mama ta kamani ta soma tofamin addu'a. Tsaki Baba ya ja yasoma fad'a.
"Ga Tunkiyanki nan cikin hatsari kin biyewa wannan sokuwan da batasan komi ba sai janyo miki asara."
"Uwata tafi min dik abinda na mallaka Malam dan haka bai dace ka had'ata da dabba ba domin darajar bil'adam mai girma ne sama da dukkan halittun duniya sannan Uwata kam bazata tab'a janyomin asara ba sai alkhairi, nasha sanar da kai wannan zancen amma ka kasa daina jinginamin ita da kalman k'an-k'anci."
Wani tsakin ya kuma ja tare da cewa "Ai sai ta korar miki macijin in gani tunda tafi ni amfani da daraja."
"Ni da kaina zan koreshi Malam domin lafiyar Uwata yafi nawa muhinmanci a yanzu kuma ni bance tafika amfani ba, dan Allah ka rika fahimtana."
"Ai sai kiyi tunda d'iyar t...
"A kul! Malam ka tsaya daganan kada ka furta abinda zai zamo sanadin rabuwarmu, da fatan ka tuna me na ke nufi?"
"Ke! Hurera kifita idanuna in rufe wallahi akan wannan yarinyar mai bak'i jini zan ci miki mutunci matuk'a."
Ina gani Mama zata sake magana na kulle mata baki ta kalleni na girgiza mata kai. Shiru ta yi ranta amugun b'ace, Baba ya buga babban rigarsa a fusace ya koma d'aki. Da kallo Mama ta raka shi zuwa can ta janye jikinta zuwa cikin dak'in tumakan, na biyo bayanta cikin rik'o hannunta ina cewa "Dawo Mama kada ya illamin ke na shiga uku na lalace."
"Insha Allah bake ba shiga uku Uwata balle lalacewa indai ina numfashi "
"Mama to ki...
Maganar ta mak'alemin ganin babu macijin ba sanmatarshi sai tunkiyan kwance ta mik'e bisa alamu ta mutu.
"Muje ki kwanta zuwa gobe mai cire maciji zaizo a fidda shi a inda ya b'oye."
"Mama ina ya je?"
"Ai dama ba zai tsaya ba tunda yaji motsin mutane."
"Mama kada yazo ya cutar damu muna barci."
"Wanda ya dogara ga Allah to Allah zai bashi kariya batare da saninsa ba, ki dage da mik'a lamuranki gare shi domin shi mai amsa buk'atun bayi ne."
Motsa kai nayi alamun gamsuwa da zancen.
Har d'akina ta kawoni wanda ta kunna fitillar dana kashe ina ganin zata fita na rik'ota bance komi ba kaina sunkuye motsa kai ta yi cikin fitar murmushi ta je ta kulle k'ofa tare da zubawa wurin da aka jijjije da k'arfi ido."
"Waye gwanin lalata miki k'ofa Uwata?"
"Nima ban sani ba Mama."
Na ambata cikin rawar murya.
"Uwata sanarmin da damuwanki."
"Lafiyalau na ke Mama."
"Ban yarda ba maza sanarmin kinsan ina jin dirin Damuwarki a k'irjina ko da baki furtamin ba wanda na tabbata kwanaki biyu nan duk kinyisu cikin damuwa ce musanman cikin dare kamar bakya samun ishashshen barci dubi da yarda kike tashi amakare kuma idanu kumbure."
"Kiyimin addu'a kawai Mama wata k'ila wasi-wasin shed'an ne ke hasko miki ina cikin damuwa."
'Uwata na san zurfin cikin ki dan Allah ki sanarmin da abinda ke damunki inyi maganinsa tun bai girma ba."
"Mama ki amince ina cikin walwalata ba abinda ke damuna."
"To Allah ya sa hakan ne dan nasan zurfin cikinki yafi k'arfinki Uwata, abinda na ke nusar da ke aitaka hakan ba abu mai kyau ba, dan Allah ki gyara kada wata rana ya cutarmin da lafiyarki."
Bance komi ba illa na kuma narkewa a kafad'arta ina lumshe ido alamun jin barci.
"Ina jin b'arayi sun soma harin gidan nan dan ko jiya najiyo motsi kamar ana gudu ko da na fito sai na samu Malam na dubawa, wata k'ila waken suyar da na yi cikonsa sukeyiwa fako."
"Allah ba zai basu sa'ar d'aukan komi ba."
"To Allah ya sa hakan."
"Amin."
"Mama kada ki tafi tsoro nakeji."
Na furta da sauri ganin ta janye jikinta daga nawa.
"Ba zan tafi ba Uwata mu kwanta a nan, Allah ya tsaremu da mugun ji da gani."
"Amin Mamana."
Na amsa cikin k'an-k'ameta domin a zahiri tsoron maciji ya danne bargaban da na ke ciki na azzalimin da ke kawomin hari a cikin gidanmu ba tsoron Allah.
Washe gari bayan na kammala tilawar karatun qur'ani kamar yarda na saba na fito na isa k'ofar Mama dan gaisar da ita domin tunda subahi ta koma d'akinta, sai dai kafin inyi sallama najiyo maganar Baba cikin d'aga harshe.
"Wallahi Hurera duk ranar da kika kuma zuwa d'akin Uwani kika kwana sai na sab'a miki kuma in had'aki da mai sakamako wato Allah."
Banjiyo me Mama ta ce ba sabida muryanta ya yi k'asa.
"Na dai sanar miki in har ina gidan nan ban yafe ba kika kuma kwana da baliga alhalin ga mijinki na buk'atarki dan kuyi aikin lada amma sabida rashin hankali kikayi watsi da shi kika manne a jikin 'yar...
Ban tsaya jiyo k'arshen kalaman Baba ba na bar k'ofar jikina na rawa domin na san k'arshen kalman yafi duk kan kalamansa muni. D'akina na koma na tura k'ofar da ta kusa fad'i k'asa na zauna gefen katifa cike da damuwa hawaye na bin kumatuna.
'Anya Baba shi yayi sanadin kawoni duniya kuwa? Ko dai da gaske ne da Maman su Khamila ke ambatamin 'yar karere? kai ban amince ba kawai salon kishinta ne na fitina ke kaita da yin kalamin wanda ko su Maman Anas bata bari ba.'
"Uwani!."
By Mrsjmoon
*EXQUISITE WRITER'S FORUM ( EWF).*
Da sunan Allah mai Rahma mai jin kai. Allahumma salli ala sayyidina Muhammadu wa ala alihi ada-da mafi ilmi salatin da'imatan bi du'a'un Janna. S.A.W.
*Sharhi.*
Labarin (DAMUWATA) hak'k'ina ne ban yarda a juyamin shi ta wani siga ba ko yimin iko da shi ta hanyar had'a document ko makamancin haka sannan ba kyauta ba ne amma da pages masu zuwa domin farin cikinku masoya. Allah ya sa mu amfana da darasoshin da ke cikinsa na khairan, muyi watsi da kishiyar shi Allahumma amin.
*Jimlar littafan marubuciyar:*
Free books.
Mabrukha
Ra'ayi
Rayuwar Bahijja.
A tunanina
Ruwan dare.
Paid books.
Bak'on lamari
Rashin jituwa
Banyi zato ba
Rabi'atul Addawiyya
Rumasa'u
Mutunci Madara ne
Doctor Laylah.
*Baki d'aya shafin sadaukarwa ne ga Aunty Maijidda Musa (Aunty Jidda) Allah ya albarkaci rayuwarta tare da zuri'arta biy jahiy Nabiy S A.W.*
Page 01.
Cikin talatainin dare wanda masu iya magana kan kirasa da suna mahutar bawa. Ni kam a gareni kiran shi na yi da lokacin gadin kaina domin zaune na ke a gefen katifana ba komi ke damuna ba sai barci wanda yake d'ibana ina korarsa da k'arfi da yaji domin bazanyi sakaci ya d'auke ni ba ya zamo rayuwata ta shiga garari. Abinda na kasa fahimta a rud'ad'd'en lamarin shi ne saceni ake sonyi ko kuwa b'atamin rayuwa.
'Sai dai b'ata miki rayuwa domin alamu sun nuna hakan.'
Sosa gefen wuyana na yi cikin aminta da amsan da zuciyata ta bani.
"Oh ni Deejah me ke shirin faruwa da ni ne? Waye wannan mutumin dake son dasamin bak'in tabbo mara b'acewa a jiki da ruhi? Ya Allah ga baiwarka Nana Khadijatu ka dubeni duban da batasan ya yake ba sai kai da ka halicceni, d'aukinka ya zamo jagoran yayewar duhun nan da na ke ciki."
Ruwan dake d'iga a bayan hannayena ya ankarad da ni kuka na ke yi mara sauti.
" Hak'ik'a DAMUWATA na dabanne da sauran mutane. Shin wai ahaka zan cigaba da rayuwa ban samun barci?"
Amsan da ban samoshi ba kenan tun soma fuskantan barazanar shigomin d'aki cikin dare har zuwa yanzu da na ke mai-maita shi.
Sake sosa wuyana na yi cike da tausayin kaina.
"A kwanaki biyun nan har na rame, samun barci alamun natsuwa ne dan haka rashinsa dole ya sakawa mutum ciwo, ya Rabbi ka bayyanamin abinda ke cikin duhun nan batare da hankalin Mamana ya tashi ba."
Motsin da na jiyo a bakin k'ofa yasa na zabura na koma bayan k'ofar na manne, jikina na mazari cikin bugawar k'irji, ina jin ana kici kicin bud'e k'ofar, ba jimawa akayi nasarar bud'ewa tare da turota a hankali, na d'auke numfashi ina kallon inuwar mugun sadda ya doshi saman katifana a cikin d'an hasken da ya shigo d'akin ta glob din waje, sam ban tsaya tantance ko waye ba duk da burina kenan gano shed'anin da ke lalibeni idan ina barci wanda na ke kwatar kaina da k'yar.
Ganin ya dage da neman inda na ke sai na silale cikin sand'a na fice daga d'akin zuwa mafakana wato d'akin tumakan Mama, wurin dana gyara tun da yamma dan b'oyewa saboda shigana makewayi ya sakani jin tsoro.
Na tsuguna a cikin dabbobi jikina na cigaba da rawa, damuwa ya kuma lullub'eni, sai lokacin naji dama na tsaya na kunna wutan d'akin naga fuskan mugun.
"A sannu zan gano ko waye insha Allah."
Na furta cikin matse gefen wuyana cikin nauyin idanu alamun kwanciya kawai na ke muradi.
'Deejah zurfin ciki banaki ba ne ki sanarwa Mama kada ya sami nasara akanki ya kaiki ya baro, ki jefa Mamanki cikin damuwa da ke kanki.'
"A'a ba zan iya wannan zancen da Mama ba, ina jin nauyin furta shi ga wanima balle Mamana."
'Zurfin ciki nan sam baiyi ba Deejah.'
"Na san da haka amma to ya zanyi?"
'Ki koreshi domin samun 'yancin furta matsalarki gudun cutuwa.'
Jinjina kai na yi domin na amince da wannan shawarar da zuciyata ta bani.
Na jima tsugune zuwan na ji wani abu mai sanyi na bin k'afana ya sa na mik'e, na kuma jin ya nad'emin dika k'afafun, aikam na daka uban tsalle na fad'a cikin tumakai, atake suka soma ihu sabida na firgitasu, bashiri nayo waje a guje na shige makewayi ina haki, muryan Mama da Baba na jiyo suna salati na fito da gudu a rud'e na rungume Mama ina mai danne kukana kada ya baiyana ta ritsani da tambayoyin dalilin yinsa alhali bani da amsa, sai na matse bakina da hannu d'aya ina lek'en abinda sukagani suke yiwa salati.
Maciji ne k'ato ya nad'e k'aramar tunkiya zare idanu na yi jikina na kuma d'aukan rawa ganin tunkiyar a wurin dana tsugunna d'azun ta ke kwance.
'Wato shi ne abinda d'azun ya nad'emin k'afafu?'
Tuno hakan ya sa na kwalla ihu ina tsalle tamkar macijin ne yazo ya sake nad'eni, a rud'e Mama ta kamani ta soma tofamin addu'a. Tsaki Baba ya ja yasoma fad'a.
"Ga Tunkiyanki nan cikin hatsari kin biyewa wannan sokuwan da batasan komi ba sai janyo miki asara."
"Uwata tafi min dik abinda na mallaka Malam dan haka bai dace ka had'ata da dabba ba domin darajar bil'adam mai girma ne sama da dukkan halittun duniya sannan Uwata kam bazata tab'a janyomin asara ba sai alkhairi, nasha sanar da kai wannan zancen amma ka kasa daina jinginamin ita da kalman k'an-k'anci."
Wani tsakin ya kuma ja tare da cewa "Ai sai ta korar miki macijin in gani tunda tafi ni amfani da daraja."
"Ni da kaina zan koreshi Malam domin lafiyar Uwata yafi nawa muhinmanci a yanzu kuma ni bance tafika amfani ba, dan Allah ka rika fahimtana."
"Ai sai kiyi tunda d'iyar t...
"A kul! Malam ka tsaya daganan kada ka furta abinda zai zamo sanadin rabuwarmu, da fatan ka tuna me na ke nufi?"
"Ke! Hurera kifita idanuna in rufe wallahi akan wannan yarinyar mai bak'i jini zan ci miki mutunci matuk'a."
Ina gani Mama zata sake magana na kulle mata baki ta kalleni na girgiza mata kai. Shiru ta yi ranta amugun b'ace, Baba ya buga babban rigarsa a fusace ya koma d'aki. Da kallo Mama ta raka shi zuwa can ta janye jikinta zuwa cikin dak'in tumakan, na biyo bayanta cikin rik'o hannunta ina cewa "Dawo Mama kada ya illamin ke na shiga uku na lalace."
"Insha Allah bake ba shiga uku Uwata balle lalacewa indai ina numfashi "
"Mama to ki...
Maganar ta mak'alemin ganin babu macijin ba sanmatarshi sai tunkiyan kwance ta mik'e bisa alamu ta mutu.
"Muje ki kwanta zuwa gobe mai cire maciji zaizo a fidda shi a inda ya b'oye."
"Mama ina ya je?"
"Ai dama ba zai tsaya ba tunda yaji motsin mutane."
"Mama kada yazo ya cutar damu muna barci."
"Wanda ya dogara ga Allah to Allah zai bashi kariya batare da saninsa ba, ki dage da mik'a lamuranki gare shi domin shi mai amsa buk'atun bayi ne."
Motsa kai nayi alamun gamsuwa da zancen.
Har d'akina ta kawoni wanda ta kunna fitillar dana kashe ina ganin zata fita na rik'ota bance komi ba kaina sunkuye motsa kai ta yi cikin fitar murmushi ta je ta kulle k'ofa tare da zubawa wurin da aka jijjije da k'arfi ido."
"Waye gwanin lalata miki k'ofa Uwata?"
"Nima ban sani ba Mama."
Na ambata cikin rawar murya.
"Uwata sanarmin da damuwanki."
"Lafiyalau na ke Mama."
"Ban yarda ba maza sanarmin kinsan ina jin dirin Damuwarki a k'irjina ko da baki furtamin ba wanda na tabbata kwanaki biyu nan duk kinyisu cikin damuwa ce musanman cikin dare kamar bakya samun ishashshen barci dubi da yarda kike tashi amakare kuma idanu kumbure."
"Kiyimin addu'a kawai Mama wata k'ila wasi-wasin shed'an ne ke hasko miki ina cikin damuwa."
'Uwata na san zurfin cikin ki dan Allah ki sanarmin da abinda ke damunki inyi maganinsa tun bai girma ba."
"Mama ki amince ina cikin walwalata ba abinda ke damuna."
"To Allah ya sa hakan ne dan nasan zurfin cikinki yafi k'arfinki Uwata, abinda na ke nusar da ke aitaka hakan ba abu mai kyau ba, dan Allah ki gyara kada wata rana ya cutarmin da lafiyarki."
Bance komi ba illa na kuma narkewa a kafad'arta ina lumshe ido alamun jin barci.
"Ina jin b'arayi sun soma harin gidan nan dan ko jiya najiyo motsi kamar ana gudu ko da na fito sai na samu Malam na dubawa, wata k'ila waken suyar da na yi cikonsa sukeyiwa fako."
"Allah ba zai basu sa'ar d'aukan komi ba."
"To Allah ya sa hakan."
"Amin."
"Mama kada ki tafi tsoro nakeji."
Na furta da sauri ganin ta janye jikinta daga nawa.
"Ba zan tafi ba Uwata mu kwanta a nan, Allah ya tsaremu da mugun ji da gani."
"Amin Mamana."
Na amsa cikin k'an-k'ameta domin a zahiri tsoron maciji ya danne bargaban da na ke ciki na azzalimin da ke kawomin hari a cikin gidanmu ba tsoron Allah.
Washe gari bayan na kammala tilawar karatun qur'ani kamar yarda na saba na fito na isa k'ofar Mama dan gaisar da ita domin tunda subahi ta koma d'akinta, sai dai kafin inyi sallama najiyo maganar Baba cikin d'aga harshe.
"Wallahi Hurera duk ranar da kika kuma zuwa d'akin Uwani kika kwana sai na sab'a miki kuma in had'aki da mai sakamako wato Allah."
Banjiyo me Mama ta ce ba sabida muryanta ya yi k'asa.
"Na dai sanar miki in har ina gidan nan ban yafe ba kika kuma kwana da baliga alhalin ga mijinki na buk'atarki dan kuyi aikin lada amma sabida rashin hankali kikayi watsi da shi kika manne a jikin 'yar...
Ban tsaya jiyo k'arshen kalaman Baba ba na bar k'ofar jikina na rawa domin na san k'arshen kalman yafi duk kan kalamansa muni. D'akina na koma na tura k'ofar da ta kusa fad'i k'asa na zauna gefen katifa cike da damuwa hawaye na bin kumatuna.
'Anya Baba shi yayi sanadin kawoni duniya kuwa? Ko dai da gaske ne da Maman su Khamila ke ambatamin 'yar karere? kai ban amince ba kawai salon kishinta ne na fitina ke kaita da yin kalamin wanda ko su Maman Anas bata bari ba.'
"Uwani!."