Sashe 4
Abbana Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Abba Kuma kallan mahaifiyarsa ya yi ya ce "Mama, dan Allah ki yi hakuri idan na saba miki na korar yarinyar nan da na yi."A'a Abbana, baka saba min ba, ni kaina zaman yarinyar ma na naiman samin damuwa, in da dai ita har yanzu taki fada Mana ita wacece, daga sunanta bamu san komai ba game da ita, garama ta tafi, ita wannan uwar masu tausayin na samu in samu kanta."
Haka dai Abba suka kare fira da mahaifiyarsa da sunan washegari za a kuri Mansura.
Washegari Amina da wuri ta tashi ta yi masu abin breakfast, ta kawo ma bakuwarta nata.
Mansura tea din tasha kadan, bread din ko ko kallansa ba ta yi ba. Amina na gamawa ta sa Mansura ta yi wanka bayan ta bata kaya ta sa, Amina ta kalleta ta ce, "Mansura, yanzu zan kaiki tasha ki shiga motar Kaduna ki tafi garinku, za ki gane in da zaki ko?." Mansura mai makon taba Amina amsa sai ta fashe ma Amina da kuka. Sosai ta ba Amina tausayi. Amina dafa ta yi ta ce "Baki son tafiya gidan ne?." Kai Mansura ta daga ma Amina. "Me ya sa biki son tafiya?." Amina ta tambayeta tana mai kureta da ido. Nan Kuma Mansura shiru ta yi bata tanka ma Amina ba. Amina hannun Mansura ta kama tana ja alamar ta zo ta rakata tasha ta sa ta a mota, Amma Mansura taki ta cije tana kuka. Amina babu yadda ba ta yi da Mansura ba ta tashi su tafi amma taki tashi karshe daga zata kama hanunta ita Kuma ta make hannunta taki yadda ta kama. Amina ganin haka wajan mahaifiyarta ta je, cikin damuwa ta labarta Mata abin da ke faruwa. Mahaifiyar Amina da mamaki ta ce "Ka ji min yarinyar, to mu ya za mu yi da ita, yanda Abba ya nuna damuwarsa da zamanta gidan nan ai ba zai yuwu ba, dole za ta yi hakuri ta tafi. Mu je in yi magana da ita."
Mahaifiyar Amina ta dade tana kallan Mansura da ke uban kuka har da majina. Cikin sanyin murya mahaifiyar Amina ta ce "Yata, ki yi hakuri kin ji, Amina ta je ta saki a mota ki tafi gidanku."
Mansura dai babu abin da take sai kuka sosai take kuka har da Majinarta. Amina da babu wuyar kuka ganin haka itama sai ta fashe da kuka. Mahaifiyar Amina Kuma duk sai ta shiga damuwa yadda ta ga Mansura na kuka, hakan ya nuna mata bata son tafiya ne. Mahaifiyar Amina cikin sanyi ta kalli Mansura tana mai dafata ta ce "Shi kenan, ya isa, ki yi shiru, fada min me ya sa biki son tafiyar?." Nan na Maimakon Mansura ta bata amsa sai kuka. Mahaifiyar Amina ta ce "Ai kin ji abinda ke hada ni da ke, ki yi shiru ki fada min me ya sa baki son tafiyar?."
Babu yadda mahaifiyar Amina ba su yi da Mansura ba amma taki Magana sai kuka.
Mahaifiyar Amina hannun Mansura ta kama ita kanta sai ta ji duk ba dadi ta mika ma Amina ta ce "Amina maza ku je ki sata a mota ta tafi."
Amina kama hanun Mansura ta yi suka fita. Suna fita gidan, Mansura ta tsugunna kusa da get din gidan ta tusa kanta a tsakankanin kafafunta tana kuka. Babu yadda Amina ba ta yi da ita ba ta tashi su tafi amma taki, dole Amina ta gaji ta rabu da ita ta koma gida, ta sanar da mahaifiyarta abin da ke faruwa.
Ajiyar zuciya mahaifiyar Amina ta sauke ta ce "Amina kin ga dai in da mun samu ta fita daga gidan nan shi kenan, duk da Wallahi duk na ji babu dadi kukan nata, ta bani tausayi sosai, to Amina rayuwarce sai a hankali Kai kanka ba ka gama maganin kukanka ba bare ka yi ma wani."
Amina dai bata ce komai ba ta nufi bedroom dinta ta kwanta, saboda kanta dake Mata ciwo, dan tun jiya ba wani barci tayi ba, kwana ta yi tunanin Mansura. Kasan cewar Amina jiya ba wani barcin kirki ta yi ba, hakan ya sa tana kwanciya barci ya dauketa.
Amina ba ita ta farka ba sai 1:50Pm, ana ta kiraye-kiran Sallah. Tashi ta yi ta fara gabatar da Sallah, sannan ta nufi hanyar fita gidan. Mahaifiyar Amina da ke kitchen Kiran Amina ta yi ta ce "Ina zaki kike sauri haka?." Mama, lekawa zan yi in ga Mansura na nan ko ta tafi."
Shiru mahaifiyar Amina ta yi tana kallan Amina, ta san indai ta je ta Kuma ganin Mansura ba ta tafi ba za ta zo ne ta sa kanta cikin wata damuwar, hakan ya sa ta ce "Bana son shirme me za ta tsayayi tun dazu, ga abincinki can ki je ki ci."
Amina cikin sanyi ta juya ta koma, in da ko tana nan ma babu wani abu da za ta iya Mata, tasan ita ta jawo ma kanta, kila da ta fada masu ita ko wacece ba ta jin yayanta ma zai koreta.
Misalin 80:00PM Abba ya dawo wajan aiki, kamar yadda ya saba dawowa kusan kullum. Da mamaki ya ke kallan Mansura da bai gane kowacece ba, ya ga dai mutum a zaune ta tusa kanta a tsakankanin cinyoyinta. Abba fita ya yi daga motar daboda da kansa ya ke bude ma kansa get ya shiga da motarsa. Da mamaki ya ce "Ke! Lafiya? Me kike yi a nan?." Ya fadi maganar da karfi.
Mansura ko da tun maganar farko ta gane muryarsa cikin tsoro ta tashi ta matsa da sauri ta bar wajan get din nasu.
Abba da mamaki ya bita da kallo dan ya ganeta. Kallo daya ya yi Mata ya fahimci tsoran da ta shiga na ganinshi din da ta yi. Abba Matsawa ya yi har inda Mansura take, tsugunnawa ya yi ya na kallanta, Wanda ita Kuma Bata san yana yi ba, saboda ta tusa kanta a tsakankanin cinyoyinta. Cikin mamaki ko dare bata tsoro Abba ya ce "Me kike yi anan? Biki ji saukona bane ba, na ce Amina ta kaiki tasha ki shiga mota ki tafi garinku ba?."
Mansura cikin tsoro ta ce "Zan tafi." Tana fadin haka ta tashi ta tafi✍🏻
Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/LGosWoHsPkj3rhf9EbKjrK
⭐ABBANA⭐
🔔📚
*JARUMAI WRITER'S ASSOCIATION📚*
Daga Marubuciyar 👇🏻
*Meenalyn Daddy
*Oga Habib
*Fadeela
*In da rai
*Abdurrahim
*Daga Allah ko d'ora ma Kai
*So ne sila
*Rayuwar Haidar
*Bakin kishi
Follow the ABBANA channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaYZGsNEFeXsr1CKQl3r
P 5-6
Abba tsugunnawa ya yi kusa da Mansura ,ya ce "Me kike yi a nan, baki ji saukona bane ba, na ce Amina ta kaiki tasha ki shiga mota ki tafi garinku ba?."
Mansura cikin tsoro ta tashi ta ce "Zan tafi." Tana fadin haka ta tafi..
Abba tsayawa ya yi yana kallanta, so yake ya juya ya tafi amma Kuma ya kasa, ganin dare ne, gashi ba garinsu ba ina zata yanzu, hakan ya sa Abba ya bi Mansurar, wadda daga gani tafiya kawai take amma ba ta san inda zata ba. Abba shan gabanta ya yi ya ce, "Muje." Mansura juyawa ta yi ta bi bayan Abba.
Abba da sallama ya shiga falon mahaifiyarshi, inda ya iske mahaifiyarshi da Amina zaune. Amina da Mahaifiyar Amina da mamaki suka bi Mansura da kallo. Abba zama ya yi ya nuna ma Mansura kuda da Amina ya ce "Zauna." Zama Mansura ta yi gefan Amina tana zare ido.
Abba kallan Amina ya yi ya ce ,"Amina me ya sa baki kaita tasha ba kamar yadda nace?."
Amina cikin raurau da fuska ta ce "Yaya Abba, Wallahi ka tambayi mama shirya zan rakata muna fita ta takure a bakin get taki tafiya."
Abba mai da kallanshi ga Mansura ya yi ya ce "Wacece ke? Kuma me ya baro da ke daga gidan iyayanki?."
Mansura kuka ta fara har tana shashsheka. mahaifiyar Amina dafa Mansura ta yi ta ce "Ki yi shiru Yata, ki fada Mana wacece ke?" Mansura dai ba ta ce komai ba, ta ci gaba da kukanta.
Abba ransa fara baci ya yi, ganin kamar tana so ta raina masu wayau, daga tambayeta wacece ita sai kuka, hakan ya sa ya daka mata tsawa ya ce "Wacece ke nace? Ba kuka aka tambayeki ba."
Ba Mansura ba hatta Amina sai da ta tsorata da tsawar da Abba ya yi ma Mansura.
Mansura take jikinta ya fara rawa ta kasa magana, Wanda ita kanta tsoran shirun nata take ji.
Amina a hankali ta ce "Mansura dan Allah ki natsu ki yi magana, Kinga ke Yaya Abba ke saurare. Shirun naki zai jawo ya yi miki wani zargin wajan Yaya Abba, ki yi magana dan Allah."
Mansura cikin sarkewar harshe ta ce"Sunana Mansura, mamana da babana sun yi accident ne suka mutu." Mansura ta idasa maganar tana Kuma rushewa da kuka. Amina sarkin tausayi itama kukan ta fara.
Abba shiru ya yi, kafin zuwa can ya ce "A'ina dangin baban naki suke."
"Ba nida su, babana gudin hijira ya yi, a hanyarmu ta zuwa Kaduna ne muka yi accident din."
Abba kwatakwata zuciyarsa ba ta gamsu da maganar Mansura ba. Amma ganin yadda mahaifiyarsa da Amina suka yadda ya sa bai ce komai ba.
Mahaifiyar Amina cikin tausayin Mansura ta ce "Ki yi hakuri kin ji ba kuka za ki yi ba Addu'a za ki yi musu, Allah ya jikansu, Amina kamaya ku shiga ciki."
Amina hannun Mansura ta kama suka shiga tafi.
Haka dai Abba suka kare fira da mahaifiyarsa da sunan washegari za a kuri Mansura.
Washegari Amina da wuri ta tashi ta yi masu abin breakfast, ta kawo ma bakuwarta nata.
Mansura tea din tasha kadan, bread din ko ko kallansa ba ta yi ba. Amina na gamawa ta sa Mansura ta yi wanka bayan ta bata kaya ta sa, Amina ta kalleta ta ce, "Mansura, yanzu zan kaiki tasha ki shiga motar Kaduna ki tafi garinku, za ki gane in da zaki ko?." Mansura mai makon taba Amina amsa sai ta fashe ma Amina da kuka. Sosai ta ba Amina tausayi. Amina dafa ta yi ta ce "Baki son tafiya gidan ne?." Kai Mansura ta daga ma Amina. "Me ya sa biki son tafiya?." Amina ta tambayeta tana mai kureta da ido. Nan Kuma Mansura shiru ta yi bata tanka ma Amina ba. Amina hannun Mansura ta kama tana ja alamar ta zo ta rakata tasha ta sa ta a mota, Amma Mansura taki ta cije tana kuka. Amina babu yadda ba ta yi da Mansura ba ta tashi su tafi amma taki tashi karshe daga zata kama hanunta ita Kuma ta make hannunta taki yadda ta kama. Amina ganin haka wajan mahaifiyarta ta je, cikin damuwa ta labarta Mata abin da ke faruwa. Mahaifiyar Amina da mamaki ta ce "Ka ji min yarinyar, to mu ya za mu yi da ita, yanda Abba ya nuna damuwarsa da zamanta gidan nan ai ba zai yuwu ba, dole za ta yi hakuri ta tafi. Mu je in yi magana da ita."
Mahaifiyar Amina ta dade tana kallan Mansura da ke uban kuka har da majina. Cikin sanyin murya mahaifiyar Amina ta ce "Yata, ki yi hakuri kin ji, Amina ta je ta saki a mota ki tafi gidanku."
Mansura dai babu abin da take sai kuka sosai take kuka har da Majinarta. Amina da babu wuyar kuka ganin haka itama sai ta fashe da kuka. Mahaifiyar Amina Kuma duk sai ta shiga damuwa yadda ta ga Mansura na kuka, hakan ya nuna mata bata son tafiya ne. Mahaifiyar Amina cikin sanyi ta kalli Mansura tana mai dafata ta ce "Shi kenan, ya isa, ki yi shiru, fada min me ya sa biki son tafiyar?." Nan na Maimakon Mansura ta bata amsa sai kuka. Mahaifiyar Amina ta ce "Ai kin ji abinda ke hada ni da ke, ki yi shiru ki fada min me ya sa baki son tafiyar?."
Babu yadda mahaifiyar Amina ba su yi da Mansura ba amma taki Magana sai kuka.
Mahaifiyar Amina hannun Mansura ta kama ita kanta sai ta ji duk ba dadi ta mika ma Amina ta ce "Amina maza ku je ki sata a mota ta tafi."
Amina kama hanun Mansura ta yi suka fita. Suna fita gidan, Mansura ta tsugunna kusa da get din gidan ta tusa kanta a tsakankanin kafafunta tana kuka. Babu yadda Amina ba ta yi da ita ba ta tashi su tafi amma taki, dole Amina ta gaji ta rabu da ita ta koma gida, ta sanar da mahaifiyarta abin da ke faruwa.
Ajiyar zuciya mahaifiyar Amina ta sauke ta ce "Amina kin ga dai in da mun samu ta fita daga gidan nan shi kenan, duk da Wallahi duk na ji babu dadi kukan nata, ta bani tausayi sosai, to Amina rayuwarce sai a hankali Kai kanka ba ka gama maganin kukanka ba bare ka yi ma wani."
Amina dai bata ce komai ba ta nufi bedroom dinta ta kwanta, saboda kanta dake Mata ciwo, dan tun jiya ba wani barci tayi ba, kwana ta yi tunanin Mansura. Kasan cewar Amina jiya ba wani barcin kirki ta yi ba, hakan ya sa tana kwanciya barci ya dauketa.
Amina ba ita ta farka ba sai 1:50Pm, ana ta kiraye-kiran Sallah. Tashi ta yi ta fara gabatar da Sallah, sannan ta nufi hanyar fita gidan. Mahaifiyar Amina da ke kitchen Kiran Amina ta yi ta ce "Ina zaki kike sauri haka?." Mama, lekawa zan yi in ga Mansura na nan ko ta tafi."
Shiru mahaifiyar Amina ta yi tana kallan Amina, ta san indai ta je ta Kuma ganin Mansura ba ta tafi ba za ta zo ne ta sa kanta cikin wata damuwar, hakan ya sa ta ce "Bana son shirme me za ta tsayayi tun dazu, ga abincinki can ki je ki ci."
Amina cikin sanyi ta juya ta koma, in da ko tana nan ma babu wani abu da za ta iya Mata, tasan ita ta jawo ma kanta, kila da ta fada masu ita ko wacece ba ta jin yayanta ma zai koreta.
Misalin 80:00PM Abba ya dawo wajan aiki, kamar yadda ya saba dawowa kusan kullum. Da mamaki ya ke kallan Mansura da bai gane kowacece ba, ya ga dai mutum a zaune ta tusa kanta a tsakankanin cinyoyinta. Abba fita ya yi daga motar daboda da kansa ya ke bude ma kansa get ya shiga da motarsa. Da mamaki ya ce "Ke! Lafiya? Me kike yi a nan?." Ya fadi maganar da karfi.
Mansura ko da tun maganar farko ta gane muryarsa cikin tsoro ta tashi ta matsa da sauri ta bar wajan get din nasu.
Abba da mamaki ya bita da kallo dan ya ganeta. Kallo daya ya yi Mata ya fahimci tsoran da ta shiga na ganinshi din da ta yi. Abba Matsawa ya yi har inda Mansura take, tsugunnawa ya yi ya na kallanta, Wanda ita Kuma Bata san yana yi ba, saboda ta tusa kanta a tsakankanin cinyoyinta. Cikin mamaki ko dare bata tsoro Abba ya ce "Me kike yi anan? Biki ji saukona bane ba, na ce Amina ta kaiki tasha ki shiga mota ki tafi garinku ba?."
Mansura cikin tsoro ta ce "Zan tafi." Tana fadin haka ta tashi ta tafi✍🏻
Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/LGosWoHsPkj3rhf9EbKjrK
⭐ABBANA⭐
🔔📚
*JARUMAI WRITER'S ASSOCIATION📚*
Daga Marubuciyar 👇🏻
*Meenalyn Daddy
*Oga Habib
*Fadeela
*In da rai
*Abdurrahim
*Daga Allah ko d'ora ma Kai
*So ne sila
*Rayuwar Haidar
*Bakin kishi
Follow the ABBANA channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaYZGsNEFeXsr1CKQl3r
P 5-6
Abba tsugunnawa ya yi kusa da Mansura ,ya ce "Me kike yi a nan, baki ji saukona bane ba, na ce Amina ta kaiki tasha ki shiga mota ki tafi garinku ba?."
Mansura cikin tsoro ta tashi ta ce "Zan tafi." Tana fadin haka ta tafi..
Abba tsayawa ya yi yana kallanta, so yake ya juya ya tafi amma Kuma ya kasa, ganin dare ne, gashi ba garinsu ba ina zata yanzu, hakan ya sa Abba ya bi Mansurar, wadda daga gani tafiya kawai take amma ba ta san inda zata ba. Abba shan gabanta ya yi ya ce, "Muje." Mansura juyawa ta yi ta bi bayan Abba.
Abba da sallama ya shiga falon mahaifiyarshi, inda ya iske mahaifiyarshi da Amina zaune. Amina da Mahaifiyar Amina da mamaki suka bi Mansura da kallo. Abba zama ya yi ya nuna ma Mansura kuda da Amina ya ce "Zauna." Zama Mansura ta yi gefan Amina tana zare ido.
Abba kallan Amina ya yi ya ce ,"Amina me ya sa baki kaita tasha ba kamar yadda nace?."
Amina cikin raurau da fuska ta ce "Yaya Abba, Wallahi ka tambayi mama shirya zan rakata muna fita ta takure a bakin get taki tafiya."
Abba mai da kallanshi ga Mansura ya yi ya ce "Wacece ke? Kuma me ya baro da ke daga gidan iyayanki?."
Mansura kuka ta fara har tana shashsheka. mahaifiyar Amina dafa Mansura ta yi ta ce "Ki yi shiru Yata, ki fada Mana wacece ke?" Mansura dai ba ta ce komai ba, ta ci gaba da kukanta.
Abba ransa fara baci ya yi, ganin kamar tana so ta raina masu wayau, daga tambayeta wacece ita sai kuka, hakan ya sa ya daka mata tsawa ya ce "Wacece ke nace? Ba kuka aka tambayeki ba."
Ba Mansura ba hatta Amina sai da ta tsorata da tsawar da Abba ya yi ma Mansura.
Mansura take jikinta ya fara rawa ta kasa magana, Wanda ita kanta tsoran shirun nata take ji.
Amina a hankali ta ce "Mansura dan Allah ki natsu ki yi magana, Kinga ke Yaya Abba ke saurare. Shirun naki zai jawo ya yi miki wani zargin wajan Yaya Abba, ki yi magana dan Allah."
Mansura cikin sarkewar harshe ta ce"Sunana Mansura, mamana da babana sun yi accident ne suka mutu." Mansura ta idasa maganar tana Kuma rushewa da kuka. Amina sarkin tausayi itama kukan ta fara.
Abba shiru ya yi, kafin zuwa can ya ce "A'ina dangin baban naki suke."
"Ba nida su, babana gudin hijira ya yi, a hanyarmu ta zuwa Kaduna ne muka yi accident din."
Abba kwatakwata zuciyarsa ba ta gamsu da maganar Mansura ba. Amma ganin yadda mahaifiyarsa da Amina suka yadda ya sa bai ce komai ba.
Mahaifiyar Amina cikin tausayin Mansura ta ce "Ki yi hakuri kin ji ba kuka za ki yi ba Addu'a za ki yi musu, Allah ya jikansu, Amina kamaya ku shiga ciki."
Amina hannun Mansura ta kama suka shiga tafi.