Sashe 32
Abbana Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Mahaifiyar Abba har ta shiga bedroom dinta tana mita akan halin mansura na tunane-tunane da tasa ma ranta.
Mansura tarasa dalilin rikicewarta akan maganar ankon bikin Abba da mahaifiyar Abba ta yi.
Gaba daya wunin yau haka Mansura ta yi sa wani iri, ga damuwar auran da Abba daya dora Mata ga Kuma maganar auransa dake gabatowa.
Abba bayan magariba ya dawo gidan ya nufi bangaran mahaifiyarsa, yau Abba ya dage sai ziba yake ma mahaifiyarsa, mahaifiyar Abba kallan Abba ta yi tana murmushi ta ce "Abba wannan fara'a haka, fada min wana albishir din akai ma?." Abba dariya ya yi yana kallan mahaifiyarsa ya ce "Mama Wallahi haka na tsinci kaina nima cikin farin ciki." Tom Allah ya daurar da shi, ya maganar lefan Aisha." Kai Abba ya sosa dan yama manta da maganar laife ya ce "Mama akwai wata Mata a asibitinmu sanarta kenan hada lefi, ita ta hadama Aminu abokina, zan mata magana gobe."Bana son shiririta kaga saura kwana 33 yau bikin, ya kamata ace ka gama hada komai."
Abba sun jima suna fira da mahaifiyarsa kafin ya fita ya nufi bangaransa, wanka Abba ya shiga, bayan ya fito ya shirya cikin wasu k'ananan kaya masu kyau ya dauki key din motarsa ya fita, baidade sosai ba ya dawo. Abba rufe motarsa ya yi ya fita rike da leda ahanunsa ya nufi bangaran mahaifiyarsa yana addu'ar Allah ya sa bata falon. Abba na zuwa ya tura kofar falon rufe ya jita alamun ansa Mata key, Abba Mansura ya Kira a waya da tundazu take tsimayinsa, ta ji an daura auran nasu ko a'a.
Hakan ya sa Mansura na ganin kiran Abba ta daga. Abba cikin kasa da murya ya ce "Zo ki bude min kofar falo, amma fa ki yi a hankali Kar mama ta ji." Abba na fadin haka ya kashe wayarsa.
Mansura lallabawa ta yi a hankali ta bude kofar falon kamar yadda Abba ya naima. Tana budewa Abba ya maida kofar ya rufe, Mansura magana za ta yi ganin Abba ya rufe kofar amma sai ya yi Mata nuna da hannu akan su shiga ciki."
Mansura na biye da Abba har bedroom dinta. Abba zama ya yi gefan bed din Mansura. Mansura Kuma kanta a kasa daga gani dai tana jira ne daga Abban.
Abba gyaran murya ya yi kafin ya ce "Mansura Kinga yadda kaddarar auranmu mukuma ta kasance ko? Dazu bayan na dawo dake gida na koma malam ya yi jagoranci aka Daura Mana aure bayan fitowa daga massalaci bayan sallar azahar. Ga sadakinki." Abba ya ciro kudi masu yawa daga cikin ajjihunsa ya aje a cinyar Mansura ya ce "Dubu dari da biyu ne kamar yadda na biya na Aisha, ina fatan za ki ci gaba da rufa asirin auranmu har ranar da Allah zai da mama ta amince da auranmu?."
Mansura dago idanunta ta yi da suka cika da hawaye ta kalli Abba, amma bata ce komai ba, ta maida kanta kasa.
Abba cikin sanyi ya ce "Mansura kuka baya maganin komai, duk da soyayyarki ita ta fara zama silar kulla wannan auran namu, amma abu na biyu har da fatan waraka daga zubar hawayanki na kulla Mana wannan auran Mansura."
Mansura fashewa ta yi da kuka jin abinda Abba ya ce ta ce tana kuka "Yaya Abba, hawaye ba za su taba gushewa daga fuskataba har ranar da zan yi bankwana da rayuwa, na aikata kuskure mafi muni a rayuwata, na aikata kuskure Yaya Abba." Mansura ta yi maganar cikin tsantsar kuka.
Abba kallan Mansura ya yi da ya kasa hanata daina kukanta cikin sanyi da rauni ya ce "Wana kuskure ki aikata Mansura? Fada min me kika aikata?."
Mansura kuka take sosai wanda Abba bai taba ganin ta yi irinsa ba, Abba bai hanata ba sai da ya ji tana yi da karfi gudin Kar mahaifiyarsa ta jiyo ya sa Abba ya matso kusa da Mansura ya kwantar da kanta kan kafadarsa yana shafa bayanta, shi kansa ya kasa magana. Sun dauki shawan lokaci a haka. Sauke ajiyar zuciyar Mansura ya ji wanda ya tabbatar mai da ta yi barci, Abba dago kan Mansura ya yi da mamaki yaga barci take, hakan ya sa Abba ya matsar da Mansurar tsakiyar gadon ya kwantar da ita a hankali yana tsoran ta tashi.
Abba bin ledar da ya shigo da ita ya yi da kallo ta kaza da Yoghurt ya mamanta da ita gashi wadda ya siyo mawa din ta yi barci.
Abba tashi ya yi ya shiga toilet din Mansura kafin ya zo ya kwanta gefan Mansurar Yana tofe su da addu'a.
4:00AM Abba ya farka rike da kansa saboda wani mummunin mafarkin da ya yi, Abba sauka ya yi daga kan gadon ya je ya doro Alwallah ya yi nafila da naiman tsari akan mafarkin da ya yi, Abba nanan zaune kan abin sallah yana lazimi Mansura ma ta farka a firgice tana ihu tana Kiran "Abbana."
Abba da sauri ya je ya rirrike Mansura Yana tofa mata addu'a ganin yadda ta firgice har yanzu Kuma Bata bar Kiran "Abbana." ba din da take yi.
Abba rungume Mansura ya yi ajikinsa yana shafa kanta Yana Kuma tofa Mata addu'a.
Mansura jinta jikin mutum da ta yi ya sa ta dawo natsuwarta, dago Kai ta yi suka hada ido da Abba. Mansura zaro ido ta yi tana ƙoƙarin tashi daga jikin Abba .
Abba a hankali ya ce yana Kuma shafa kan Mnasura "Ki natsu Mana, Wana mafarki kikai wanda ya firgitaki haka?."
Mansura goge hawayan da ya fara zubar Mata ta yi ta ce. "Yaya Abba na yi mafarkin Ina sanye da kayan prisoner hannuna an samin min handcuff."
Abba shiru ya yi yana bin Mansura da kallo dan shima irin mafarkin ya yi.
Mansura ko ta dage sai kuka take, Abba hannun Mansura ya kama ya kaita har toilet kafin ya dawo ya ce "Ki yi Alwallah yanzu za a Kira Sallah ki samu raka'atanal fijir."
Bayan Mansura ta fito ta yi raka' a tanal fijiri, Abba ya jamusu limanci suka taka sallar subihi.... ✍🏻
Littafin ABBANA na kudi ne, 400 ne kafin in gama free pages daga zarar na kammala 500 my number 08063830828
Free pages ya kusa karewa.
Fadila Sani Bakori ce
⭐ ABBANA ⭐
🔔📚
*JARUMAI WRITER'S ASSOCIATION📚*
Domin samun littafin ABBANA daga farko 👇🏻Follow the ABBANA channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaYZGsNEFeXsr1CKQl3r
P 39-40
Bayan sun idar da sallar Abba kallan Mansura ya yi da ta yi tagumi, Abba cire ma Mansura tagumin ya yi ya ce "Mansura dole za ki shiga Islamiyar da mama take zuwa, bazai yuwu a rika barinki ke kadai ba, yanzu bacin mun kwana tare da haka zaki Kari ihunki har ki farka, sannan ki rika salati ba ihu ba kar in kara jin kin farka barci kina ihu haka kamar ba musulma ba."
Mansura dai Kai kawai take tada ma Abba amma gabadaya damuwar mafarkin nan ba karamin tashin hankali ya sata ba.
Abba hannun Mansura ya kama ya ce "Mu je mu koma barci kafin 7."
Abba na rike da hannun Mansura suka hau kan bed din Mansurar, Wanda ita gabadaya tsantsar damuwa tasa bin Abba kawai take ta zama kamar butun butumi. Abba bayan sun kunta da Mansura da tashin hankalin da damuwar halin da take ciki ya sa gaba daya kusan a rabin jikin Abba take amma damuwa da furgicin da take ciki bai bata damar ankarar da ita ba. Wanda yana yin kwanciyar da Mansura ta yi ajikin Abba sai ya taka muhimmiyar rawa ga Abba, Wanda ya ja hankalin Abba zuwa ga Mansura. A cikin sanyayyar Safiyar nan Abba ya kusancin Mansura, bayan mai faruwa ta faru barci ya kwashesu baki dayansu Wanda bugun da mahaifiyar Abba take ma su ne ya tadasu daga barcin da suke yi. Abba furgigi ya tashi da alamar bayyanar tsoro a tare da shi, dan yasan mahaifiyarsa tana buga ma Mansura kofa ne jin shiru Bata tashi ba. Abba wayarsa ya jawo Koda ya duba 8:30 AM, Abba kallan Mansura ya yi da itama daga gani a tsorace take da yanayin.
Mahaifiyar Abba Kara bugawa ta yi tana cewa "Mansura, lafiyarki kuwa yau dinnan."
Abba nuni ya yi ma Mansura da ta je ta bude ma mahaifiyarsa kofa.
Mansura tashi ta yi tana ciccije baki, tana rike kanta dake ciwo sosai har bata gani ta nufi kofar.
Abba Kuma ledar da ya shigo da ita ya dauka da wayarsa da takalminsa da sauri ya yi bathroom din Mansura dasu.
Mansura na rike da kanta taje ta bude ma mahaifiyar Abba kofa. Mahaifiyar Abba bin Mansura ta yi da kallo ganin yadda Mansura ke rike da kanta. Mahaifiyar Abba dakin tashigo da sauri tana kamo Mansura ganin kamar tana layi zata fadi. Mahaifiyar Abba na rike da Mansura har suka karasa kan bed din Mansura. Kwantar da Mansura mahaifiyar Abba ta yi ta ce "Haba ni dama tun da na ga har 8 baki fito ba nasan kullum kina shigowa da asuba nasan yau ba lafiya, ga Abba ma yau sammakon fita ya yi ko shigowa wajena baiyi ba, amma bari in dakko wayata in kirasa ya zo ya duba ki, yau zuwa Islamiya ma ai bai ganni ba bari in je in Kira wayarsa in fada mai."
Mansura dai bata ce komai ba mahaifiyar Abba ta juya ta fita, bedroom dinta ta je ta Kira wayar Abba, yana dagawa ta sanar da shi ya zo yanzu Mansura babu lafiya.
Abba da baisan yadda zai yi ya fita bedroom din Mansura ba, gashi yana ji tana cewa yau babu zuwa Islamiya ma'ana zata yi jinyar Mansura kenan, Abba dabara ta fado mai ya ce "Mama, gani kusa da gida babu mota ma na fita ki je chamist din Auwal ki bashi wayar zan fada masa abin da zai baki daga na zo sai an mita allura kawai."
Mahaifiyar Abba na kashe wayar ta zura hijab dinta ta ta fita daga gidan, Abba na jin fitarta ya fito da sauri ya nufi bangaransa.
Da yake chamist din babu nisa sosai bayan layinsu ne, tana zuwa ta Kira Abba ta ba Auwal wayar, Abba magungunan da Mansura take bukata ya fadi ma Auwal ya ba mahaifiyarsa kafin ya kashe wayarsa.
Mansura tarasa dalilin rikicewarta akan maganar ankon bikin Abba da mahaifiyar Abba ta yi.
Gaba daya wunin yau haka Mansura ta yi sa wani iri, ga damuwar auran da Abba daya dora Mata ga Kuma maganar auransa dake gabatowa.
Abba bayan magariba ya dawo gidan ya nufi bangaran mahaifiyarsa, yau Abba ya dage sai ziba yake ma mahaifiyarsa, mahaifiyar Abba kallan Abba ta yi tana murmushi ta ce "Abba wannan fara'a haka, fada min wana albishir din akai ma?." Abba dariya ya yi yana kallan mahaifiyarsa ya ce "Mama Wallahi haka na tsinci kaina nima cikin farin ciki." Tom Allah ya daurar da shi, ya maganar lefan Aisha." Kai Abba ya sosa dan yama manta da maganar laife ya ce "Mama akwai wata Mata a asibitinmu sanarta kenan hada lefi, ita ta hadama Aminu abokina, zan mata magana gobe."Bana son shiririta kaga saura kwana 33 yau bikin, ya kamata ace ka gama hada komai."
Abba sun jima suna fira da mahaifiyarsa kafin ya fita ya nufi bangaransa, wanka Abba ya shiga, bayan ya fito ya shirya cikin wasu k'ananan kaya masu kyau ya dauki key din motarsa ya fita, baidade sosai ba ya dawo. Abba rufe motarsa ya yi ya fita rike da leda ahanunsa ya nufi bangaran mahaifiyarsa yana addu'ar Allah ya sa bata falon. Abba na zuwa ya tura kofar falon rufe ya jita alamun ansa Mata key, Abba Mansura ya Kira a waya da tundazu take tsimayinsa, ta ji an daura auran nasu ko a'a.
Hakan ya sa Mansura na ganin kiran Abba ta daga. Abba cikin kasa da murya ya ce "Zo ki bude min kofar falo, amma fa ki yi a hankali Kar mama ta ji." Abba na fadin haka ya kashe wayarsa.
Mansura lallabawa ta yi a hankali ta bude kofar falon kamar yadda Abba ya naima. Tana budewa Abba ya maida kofar ya rufe, Mansura magana za ta yi ganin Abba ya rufe kofar amma sai ya yi Mata nuna da hannu akan su shiga ciki."
Mansura na biye da Abba har bedroom dinta. Abba zama ya yi gefan bed din Mansura. Mansura Kuma kanta a kasa daga gani dai tana jira ne daga Abban.
Abba gyaran murya ya yi kafin ya ce "Mansura Kinga yadda kaddarar auranmu mukuma ta kasance ko? Dazu bayan na dawo dake gida na koma malam ya yi jagoranci aka Daura Mana aure bayan fitowa daga massalaci bayan sallar azahar. Ga sadakinki." Abba ya ciro kudi masu yawa daga cikin ajjihunsa ya aje a cinyar Mansura ya ce "Dubu dari da biyu ne kamar yadda na biya na Aisha, ina fatan za ki ci gaba da rufa asirin auranmu har ranar da Allah zai da mama ta amince da auranmu?."
Mansura dago idanunta ta yi da suka cika da hawaye ta kalli Abba, amma bata ce komai ba, ta maida kanta kasa.
Abba cikin sanyi ya ce "Mansura kuka baya maganin komai, duk da soyayyarki ita ta fara zama silar kulla wannan auran namu, amma abu na biyu har da fatan waraka daga zubar hawayanki na kulla Mana wannan auran Mansura."
Mansura fashewa ta yi da kuka jin abinda Abba ya ce ta ce tana kuka "Yaya Abba, hawaye ba za su taba gushewa daga fuskataba har ranar da zan yi bankwana da rayuwa, na aikata kuskure mafi muni a rayuwata, na aikata kuskure Yaya Abba." Mansura ta yi maganar cikin tsantsar kuka.
Abba kallan Mansura ya yi da ya kasa hanata daina kukanta cikin sanyi da rauni ya ce "Wana kuskure ki aikata Mansura? Fada min me kika aikata?."
Mansura kuka take sosai wanda Abba bai taba ganin ta yi irinsa ba, Abba bai hanata ba sai da ya ji tana yi da karfi gudin Kar mahaifiyarsa ta jiyo ya sa Abba ya matso kusa da Mansura ya kwantar da kanta kan kafadarsa yana shafa bayanta, shi kansa ya kasa magana. Sun dauki shawan lokaci a haka. Sauke ajiyar zuciyar Mansura ya ji wanda ya tabbatar mai da ta yi barci, Abba dago kan Mansura ya yi da mamaki yaga barci take, hakan ya sa Abba ya matsar da Mansurar tsakiyar gadon ya kwantar da ita a hankali yana tsoran ta tashi.
Abba bin ledar da ya shigo da ita ya yi da kallo ta kaza da Yoghurt ya mamanta da ita gashi wadda ya siyo mawa din ta yi barci.
Abba tashi ya yi ya shiga toilet din Mansura kafin ya zo ya kwanta gefan Mansurar Yana tofe su da addu'a.
4:00AM Abba ya farka rike da kansa saboda wani mummunin mafarkin da ya yi, Abba sauka ya yi daga kan gadon ya je ya doro Alwallah ya yi nafila da naiman tsari akan mafarkin da ya yi, Abba nanan zaune kan abin sallah yana lazimi Mansura ma ta farka a firgice tana ihu tana Kiran "Abbana."
Abba da sauri ya je ya rirrike Mansura Yana tofa mata addu'a ganin yadda ta firgice har yanzu Kuma Bata bar Kiran "Abbana." ba din da take yi.
Abba rungume Mansura ya yi ajikinsa yana shafa kanta Yana Kuma tofa Mata addu'a.
Mansura jinta jikin mutum da ta yi ya sa ta dawo natsuwarta, dago Kai ta yi suka hada ido da Abba. Mansura zaro ido ta yi tana ƙoƙarin tashi daga jikin Abba .
Abba a hankali ya ce yana Kuma shafa kan Mnasura "Ki natsu Mana, Wana mafarki kikai wanda ya firgitaki haka?."
Mansura goge hawayan da ya fara zubar Mata ta yi ta ce. "Yaya Abba na yi mafarkin Ina sanye da kayan prisoner hannuna an samin min handcuff."
Abba shiru ya yi yana bin Mansura da kallo dan shima irin mafarkin ya yi.
Mansura ko ta dage sai kuka take, Abba hannun Mansura ya kama ya kaita har toilet kafin ya dawo ya ce "Ki yi Alwallah yanzu za a Kira Sallah ki samu raka'atanal fijir."
Bayan Mansura ta fito ta yi raka' a tanal fijiri, Abba ya jamusu limanci suka taka sallar subihi.... ✍🏻
Littafin ABBANA na kudi ne, 400 ne kafin in gama free pages daga zarar na kammala 500 my number 08063830828
Free pages ya kusa karewa.
Fadila Sani Bakori ce
⭐ ABBANA ⭐
🔔📚
*JARUMAI WRITER'S ASSOCIATION📚*
Domin samun littafin ABBANA daga farko 👇🏻Follow the ABBANA channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaYZGsNEFeXsr1CKQl3r
P 39-40
Bayan sun idar da sallar Abba kallan Mansura ya yi da ta yi tagumi, Abba cire ma Mansura tagumin ya yi ya ce "Mansura dole za ki shiga Islamiyar da mama take zuwa, bazai yuwu a rika barinki ke kadai ba, yanzu bacin mun kwana tare da haka zaki Kari ihunki har ki farka, sannan ki rika salati ba ihu ba kar in kara jin kin farka barci kina ihu haka kamar ba musulma ba."
Mansura dai Kai kawai take tada ma Abba amma gabadaya damuwar mafarkin nan ba karamin tashin hankali ya sata ba.
Abba hannun Mansura ya kama ya ce "Mu je mu koma barci kafin 7."
Abba na rike da hannun Mansura suka hau kan bed din Mansurar, Wanda ita gabadaya tsantsar damuwa tasa bin Abba kawai take ta zama kamar butun butumi. Abba bayan sun kunta da Mansura da tashin hankalin da damuwar halin da take ciki ya sa gaba daya kusan a rabin jikin Abba take amma damuwa da furgicin da take ciki bai bata damar ankarar da ita ba. Wanda yana yin kwanciyar da Mansura ta yi ajikin Abba sai ya taka muhimmiyar rawa ga Abba, Wanda ya ja hankalin Abba zuwa ga Mansura. A cikin sanyayyar Safiyar nan Abba ya kusancin Mansura, bayan mai faruwa ta faru barci ya kwashesu baki dayansu Wanda bugun da mahaifiyar Abba take ma su ne ya tadasu daga barcin da suke yi. Abba furgigi ya tashi da alamar bayyanar tsoro a tare da shi, dan yasan mahaifiyarsa tana buga ma Mansura kofa ne jin shiru Bata tashi ba. Abba wayarsa ya jawo Koda ya duba 8:30 AM, Abba kallan Mansura ya yi da itama daga gani a tsorace take da yanayin.
Mahaifiyar Abba Kara bugawa ta yi tana cewa "Mansura, lafiyarki kuwa yau dinnan."
Abba nuni ya yi ma Mansura da ta je ta bude ma mahaifiyarsa kofa.
Mansura tashi ta yi tana ciccije baki, tana rike kanta dake ciwo sosai har bata gani ta nufi kofar.
Abba Kuma ledar da ya shigo da ita ya dauka da wayarsa da takalminsa da sauri ya yi bathroom din Mansura dasu.
Mansura na rike da kanta taje ta bude ma mahaifiyar Abba kofa. Mahaifiyar Abba bin Mansura ta yi da kallo ganin yadda Mansura ke rike da kanta. Mahaifiyar Abba dakin tashigo da sauri tana kamo Mansura ganin kamar tana layi zata fadi. Mahaifiyar Abba na rike da Mansura har suka karasa kan bed din Mansura. Kwantar da Mansura mahaifiyar Abba ta yi ta ce "Haba ni dama tun da na ga har 8 baki fito ba nasan kullum kina shigowa da asuba nasan yau ba lafiya, ga Abba ma yau sammakon fita ya yi ko shigowa wajena baiyi ba, amma bari in dakko wayata in kirasa ya zo ya duba ki, yau zuwa Islamiya ma ai bai ganni ba bari in je in Kira wayarsa in fada mai."
Mansura dai bata ce komai ba mahaifiyar Abba ta juya ta fita, bedroom dinta ta je ta Kira wayar Abba, yana dagawa ta sanar da shi ya zo yanzu Mansura babu lafiya.
Abba da baisan yadda zai yi ya fita bedroom din Mansura ba, gashi yana ji tana cewa yau babu zuwa Islamiya ma'ana zata yi jinyar Mansura kenan, Abba dabara ta fado mai ya ce "Mama, gani kusa da gida babu mota ma na fita ki je chamist din Auwal ki bashi wayar zan fada masa abin da zai baki daga na zo sai an mita allura kawai."
Mahaifiyar Abba na kashe wayar ta zura hijab dinta ta ta fita daga gidan, Abba na jin fitarta ya fito da sauri ya nufi bangaransa.
Da yake chamist din babu nisa sosai bayan layinsu ne, tana zuwa ta Kira Abba ta ba Auwal wayar, Abba magungunan da Mansura take bukata ya fadi ma Auwal ya ba mahaifiyarsa kafin ya kashe wayarsa.