Sashe 11
Abbana Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Abba mika mata maganin hannunshi ya yi da ruwan ya ce "Amsa ki sha."
Mansura kallan Abba ta yi, irin kallan ka tausaya min. Abba babu alamar wasa tare dashi ya Kuma maimata "Amsa ki sha na ce."
Mansura amsa ta yi tana goge hawayanta. Abba ruwan ya mika Mata ya ce "Watsa duka maganin a bakinki."
Mansura watsa duka maganin ta yi, take ta fara kararin amai zata dawo da maganin. Abba tashi ya yi ya daga kanta ya kalli sama, sannan ya amshi ruwan ya tsiyaya mata a baki. Ya ce "Hadiye shi." Ya fadi maganar yana girgiza kanta. Mansura hadiyewa ta yi ba ta shirya ba.
Abba sai da ya tabbatar ta hadiye kafin ya saki kanta.
Mansura nishi ta fara irin na yaran da akai ma dure.
Abba ruwan Allurar ya hada ya kamo hannun Mansura, take hannun Mansura ya kama rawa. Abba Amina ya sa ta rike mai hannun Mansura ya yi Mata allurar, take Mansura ta kama kuka. Amina murza mata hannun ta kama tana cewa "Sannu dear, yi hakuri."
Abba maganin ya mika ma Amina ya ce "Gashi Allah ya sa lokacin shan maganin ya kara yi bata Sha ba, dukkanku ku biyun za ku yi min bayanin dalilin da ba ta sha ba."
Abba na fahin haka ya fita. Wajan mahaifiyarshi ya koma suna fira. Mahaifiyar Abba cikin hirar tasu neka ta ce "Abba Kai kadai ne dana Namiji da nake kalla in ji dadi, kana min duk abin da na ce, sai dai har yanzu ka kasa cika muradina daya tal aduniya. Ba ni da burin da ya wuce Abba kamar in ga ka yi aure, sai yaushe ne za ka yi aure Abba? Yaushe za ka cika burina da na mahaifinka da har ya bar duniya bashi da buri kamar ya ga auranka, tom Allah bai nufa ba, baka yi ba, gashi har yana gaf da cika shekara biyar, har yanzu shiru babu ma wata alamar da kake nuna wa za ka yi aure."
Shiru Abba ya yi kafin ya ce "Ki yi hakuri mama har yanzu ban samu wadda ta kwanta min bane."
Shiru mahaifiyar Abba ta yi tana nazarin maganar da za ta fada ma Abba. Ta jima kafin ta ce "Abbana na yi maka matar aure wadda nake fatan in sha Allah ba za ka yi danasanin zama da yarinyar ba a yadda na fahimceta."
Abba kallan mahaifiyarshi ya yi cikin rauni, dan duk ba ya jin zabin mahaifiyar tashi zai mai Amma Kuma duk da haka baya jin zai iya bijire ma umarninta. Hakan ya sa ya ce "Mama tun kafin in ganta na aminta da zabin naki." Ma Sha Allah , Allah ya yi maka albarka Abbana, da Alama dai ka gaji mai sunan naka, ba kowa bace na zaba, yarinyar ..... ✍🏻
Fadila Sani Bakori ce.
⭐ABBANA⭐
🔔📚
*JARUMAI WRITER'S ASSOCIATION📚*
Damin samun littafin ABBANA daga faro Follow the ABBANA channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaYZGsNEFeXsr1CKQl3r
P 13-14
Malamarmu Aisha na zaba, yanzu haka maganar da nake yi maka har na yi ma mahaifiyarta magana ma, kuma ta amsa min ta ce ka je ka ganta. Sanin ba za ka yi min musu ba ya sa sai da na fara sanar da mahaifiyarta kafin Kai."
Abba Kai ya daga yana kallan mahaifiyarsa ya ce "Mama, in dai ta yi miki Allah ko ban ganta ba ya wadatar, amma duk da haka ki ban address din gidan nasu zan je har gidan."
Mahaifiyar Abba sosai ta ji dadin yadda dan nata ya aminta da zabin ta cikin sauki. Cikin jin dadi mahaifiyar Abba taita zindimo masa albarka tana cewa "Abbana, in sha Allah za ka yi alfahari da wannan zabin nawa. Allah ya yi maka albarka, Allah ya baka duk abin da kake nema duniya da kuma lahira, Allah ya jikan mahaifinka, ya saka masa da alkairi bisa kyakkywar turbar da ya dora min Kai."
Abba sosai ya ji dadin addu'ar mahaifiyar tasa, hakan ya sa cikin jin dadi ya ce "Ameen mamana."
Abba sun jima suna hira da mahaifiyarsa kafin ya yi mata sallama ya koma sight dinsa.
Washegari, Amina da wuri ta tashi ta yi duk abin da za ta yi kafin ta fita. Kallan Mansura ta yi dake ta tsattsakar indomie dake gabanta. Amina dakko maganin Mansura ta yi ta mika mata ta ce "Dear ga maganinki kisha."
Mansura baki ta turo ta ce "Allah bakina fa har ya fara dacin magungunan nan, ni dai gaskiya ba zan sha ba." Amina ido ta zaro ta ce "Ba za ki shaba, baki ji abin da Yaya Abba ya ce ba ne jiya, ni dai dan Allah ki rufa min asiri ki Sha, Wallahi ya zo ya ga baki sha ba har nima ba gyaleni zai yi ba, kina ji dai a gabanki ya ce in mun isa karki Sha, ni dai ki rufa min asiri ki dauka ki sha."
Mansura hannun Amina ta kamo, kamar za ta yi kuka ta ce,"Amina, zan fa babbare sai in zubar kin ga ai ba zai gane ban Sha ba" Uhmmm, Wallahi babu ruwana, idan fa zazzabin ya dawo miki? Yaya Abba da shegan bin diddigi in je ya gano ya ci ubana kila gara ma ke yana ganin bakuwace ya rabu da ke."
Amina kamar za ta yi kuka ta ce "Yanzu ba zaki tausaya min ba?."
Amina ma cikin son fahimtar da Mansura ta ce "Mansura ke ba ki san halin yaya Abba bane, ni dai kawai ki sha dan Allah."
Mansura Kuma kallan Amina ta yi kwalla na taruwar mata ta ce "Amai fa nake ji." Mansura ki sha in Allah ya yadda ba zaki yi ba." Mansura rufe idonta ta yi ta watsa maganin bakinta ta bi da ruwa da sauri."
Yunkurin amai ta fara, Amina da sauri ta fara bubbuga bayanta. Suna a haka Abba ya shigo yi mata allurarta.
Amina gaida Abba ta yi tana mai ci gaba da bubbuga bayan Mansura da har yanzu dafe take da kirji ba ta daina yunkurin amai ba.
Abba kallan Amina ya yi ya ce "Lafiya me ya sa ta yunkurin amana." Yaya Abba daga shan magani." Abba wata farar kwaya ya ciro a ajjihunsa ya mika ma Amina ya ca bata ta tsotsa."
Amina mika ma Mansura ta yi, Mansura ganin magani ne yi ta yi kamar ta je fashi a bakinta taki sha, ta rufeshi a hannunta.
Abba ledar magungunan Abba ya dakko ya hada allurar, Mansura take ta fara yarfe hannu. Abba kallan Amina ya yi ya ce "Reke min hannun yadda ba zai yi rawa ba."
Amina rike hannun Mansura ta yi sosai, Abba daidai zai tsira ma Mansura allurar ta fuske hannunta, by mistake Abba ya caka ma Amina a hannu. Wani uban ihu Amina ta fasa, dan sosai allurar ta shigeta.
Abba cikin bacin rai ya daga hannu ya wanke Mansura da mari. Mansura gigicewa ta yi, dan tun da take ba a taba marinta ba sai yau. Rike wajan ta yi tana murzawa tana kuka.
Mahaifiyar Mansura da tun ihun Amina ta shigo dakin da saurinta har tana tuntube, jin kukan mutum biyu lokaci guda.
Abba kuma daidai ya juya zai fita, suka ci karo da mahaifiyarsa. Mahaifiyar Abba kallan tuhuma take ma Abba, ganin Mansura dafe da kunci tana kuka, ga Kuma Amina rike da hannu itama tana kuka.
Mahaifiyar Abba cikin tausasa murya ta ce "Abbana, ya haka Kuma?." Nan Abba ya kwashe duk abin da ya faru ya labarta mata.
"Allah dai ya kyauta, ni ban ga abin tsoro a Allura ba, duk da ta jijiyar nan na da zafi, amma ya za a yi inda duk zafinta ba takai ciwan ba."
Abba kallan Amina ya yi da har yanzu take dafe da hannun tana kuka, ya daka Mata wata uwar tsawa ya ce"Ba za ki yi ma mutane shiru ba." Abba ya fadi maganar yana kamo hannunta yana ganin inda ya caka mata allurar, sosai ya caketa. Abba murza mata wajan ya yi ya ce "Ki je motana akwai maganin zugi ki sha."
Mansura ko Abba na daka ma Amina tsawa ta yi shiru, tana zare ido.
Abba kallan Amina ya yi ya maka mata wata uwar harara kafin ya ce "Anjima idan na dawo ki zo in miki allurar, dan na gama biyoki nan."
Yana fadin haka ya juya ya tafi.
Mahaifiyar Amina hannun Mansura ta kamo tana liliyawa, kafin ta mai da kallanta ga Mansura ta ce "Shi ya sa masu iya magana suka ce idan ka ga zama ya yi karko wai hali ne ya zo daya. Yanzu me ya acikin Allura Mansura, to Wallahi ki natsu da kyau ki ji Abba ba sauki garesa ba, a haka ma dan har yanzu yana miki kallan bakuwa ne, dan da Amina ce da Kinga yadda zai yi da ita yau a gidan nan. Allura Kuma daga gobe dama an gama inda ya ce min ta kwana uku ce, Kuma kin ji abin da ya ce baya Kara zuwa nan yi miki, daga ya dawo kin ji muryarsa a falo sai ki samesa ya yi Miki, ko Kuma Amina ta rika rakaki bangaransa ya yi miki acan, idan kin natsu har ya gama miki tom,. Idan Kuma baki natsu ba tom babu ruwana, kin ga dai tun yana raga miki sai da kika kuresa."
Mansura dai bata ce komai ba, mahaifiyar Amina ta gama fadanta ta fita.
Mansura kallan Abba ta yi, irin kallan ka tausaya min. Abba babu alamar wasa tare dashi ya Kuma maimata "Amsa ki sha na ce."
Mansura amsa ta yi tana goge hawayanta. Abba ruwan ya mika Mata ya ce "Watsa duka maganin a bakinki."
Mansura watsa duka maganin ta yi, take ta fara kararin amai zata dawo da maganin. Abba tashi ya yi ya daga kanta ya kalli sama, sannan ya amshi ruwan ya tsiyaya mata a baki. Ya ce "Hadiye shi." Ya fadi maganar yana girgiza kanta. Mansura hadiyewa ta yi ba ta shirya ba.
Abba sai da ya tabbatar ta hadiye kafin ya saki kanta.
Mansura nishi ta fara irin na yaran da akai ma dure.
Abba ruwan Allurar ya hada ya kamo hannun Mansura, take hannun Mansura ya kama rawa. Abba Amina ya sa ta rike mai hannun Mansura ya yi Mata allurar, take Mansura ta kama kuka. Amina murza mata hannun ta kama tana cewa "Sannu dear, yi hakuri."
Abba maganin ya mika ma Amina ya ce "Gashi Allah ya sa lokacin shan maganin ya kara yi bata Sha ba, dukkanku ku biyun za ku yi min bayanin dalilin da ba ta sha ba."
Abba na fahin haka ya fita. Wajan mahaifiyarshi ya koma suna fira. Mahaifiyar Abba cikin hirar tasu neka ta ce "Abba Kai kadai ne dana Namiji da nake kalla in ji dadi, kana min duk abin da na ce, sai dai har yanzu ka kasa cika muradina daya tal aduniya. Ba ni da burin da ya wuce Abba kamar in ga ka yi aure, sai yaushe ne za ka yi aure Abba? Yaushe za ka cika burina da na mahaifinka da har ya bar duniya bashi da buri kamar ya ga auranka, tom Allah bai nufa ba, baka yi ba, gashi har yana gaf da cika shekara biyar, har yanzu shiru babu ma wata alamar da kake nuna wa za ka yi aure."
Shiru Abba ya yi kafin ya ce "Ki yi hakuri mama har yanzu ban samu wadda ta kwanta min bane."
Shiru mahaifiyar Abba ta yi tana nazarin maganar da za ta fada ma Abba. Ta jima kafin ta ce "Abbana na yi maka matar aure wadda nake fatan in sha Allah ba za ka yi danasanin zama da yarinyar ba a yadda na fahimceta."
Abba kallan mahaifiyarshi ya yi cikin rauni, dan duk ba ya jin zabin mahaifiyar tashi zai mai Amma Kuma duk da haka baya jin zai iya bijire ma umarninta. Hakan ya sa ya ce "Mama tun kafin in ganta na aminta da zabin naki." Ma Sha Allah , Allah ya yi maka albarka Abbana, da Alama dai ka gaji mai sunan naka, ba kowa bace na zaba, yarinyar ..... ✍🏻
Fadila Sani Bakori ce.
⭐ABBANA⭐
🔔📚
*JARUMAI WRITER'S ASSOCIATION📚*
Damin samun littafin ABBANA daga faro Follow the ABBANA channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaYZGsNEFeXsr1CKQl3r
P 13-14
Malamarmu Aisha na zaba, yanzu haka maganar da nake yi maka har na yi ma mahaifiyarta magana ma, kuma ta amsa min ta ce ka je ka ganta. Sanin ba za ka yi min musu ba ya sa sai da na fara sanar da mahaifiyarta kafin Kai."
Abba Kai ya daga yana kallan mahaifiyarsa ya ce "Mama, in dai ta yi miki Allah ko ban ganta ba ya wadatar, amma duk da haka ki ban address din gidan nasu zan je har gidan."
Mahaifiyar Abba sosai ta ji dadin yadda dan nata ya aminta da zabin ta cikin sauki. Cikin jin dadi mahaifiyar Abba taita zindimo masa albarka tana cewa "Abbana, in sha Allah za ka yi alfahari da wannan zabin nawa. Allah ya yi maka albarka, Allah ya baka duk abin da kake nema duniya da kuma lahira, Allah ya jikan mahaifinka, ya saka masa da alkairi bisa kyakkywar turbar da ya dora min Kai."
Abba sosai ya ji dadin addu'ar mahaifiyar tasa, hakan ya sa cikin jin dadi ya ce "Ameen mamana."
Abba sun jima suna hira da mahaifiyarsa kafin ya yi mata sallama ya koma sight dinsa.
Washegari, Amina da wuri ta tashi ta yi duk abin da za ta yi kafin ta fita. Kallan Mansura ta yi dake ta tsattsakar indomie dake gabanta. Amina dakko maganin Mansura ta yi ta mika mata ta ce "Dear ga maganinki kisha."
Mansura baki ta turo ta ce "Allah bakina fa har ya fara dacin magungunan nan, ni dai gaskiya ba zan sha ba." Amina ido ta zaro ta ce "Ba za ki shaba, baki ji abin da Yaya Abba ya ce ba ne jiya, ni dai dan Allah ki rufa min asiri ki Sha, Wallahi ya zo ya ga baki sha ba har nima ba gyaleni zai yi ba, kina ji dai a gabanki ya ce in mun isa karki Sha, ni dai ki rufa min asiri ki dauka ki sha."
Mansura hannun Amina ta kamo, kamar za ta yi kuka ta ce,"Amina, zan fa babbare sai in zubar kin ga ai ba zai gane ban Sha ba" Uhmmm, Wallahi babu ruwana, idan fa zazzabin ya dawo miki? Yaya Abba da shegan bin diddigi in je ya gano ya ci ubana kila gara ma ke yana ganin bakuwace ya rabu da ke."
Amina kamar za ta yi kuka ta ce "Yanzu ba zaki tausaya min ba?."
Amina ma cikin son fahimtar da Mansura ta ce "Mansura ke ba ki san halin yaya Abba bane, ni dai kawai ki sha dan Allah."
Mansura Kuma kallan Amina ta yi kwalla na taruwar mata ta ce "Amai fa nake ji." Mansura ki sha in Allah ya yadda ba zaki yi ba." Mansura rufe idonta ta yi ta watsa maganin bakinta ta bi da ruwa da sauri."
Yunkurin amai ta fara, Amina da sauri ta fara bubbuga bayanta. Suna a haka Abba ya shigo yi mata allurarta.
Amina gaida Abba ta yi tana mai ci gaba da bubbuga bayan Mansura da har yanzu dafe take da kirji ba ta daina yunkurin amai ba.
Abba kallan Amina ya yi ya ce "Lafiya me ya sa ta yunkurin amana." Yaya Abba daga shan magani." Abba wata farar kwaya ya ciro a ajjihunsa ya mika ma Amina ya ca bata ta tsotsa."
Amina mika ma Mansura ta yi, Mansura ganin magani ne yi ta yi kamar ta je fashi a bakinta taki sha, ta rufeshi a hannunta.
Abba ledar magungunan Abba ya dakko ya hada allurar, Mansura take ta fara yarfe hannu. Abba kallan Amina ya yi ya ce "Reke min hannun yadda ba zai yi rawa ba."
Amina rike hannun Mansura ta yi sosai, Abba daidai zai tsira ma Mansura allurar ta fuske hannunta, by mistake Abba ya caka ma Amina a hannu. Wani uban ihu Amina ta fasa, dan sosai allurar ta shigeta.
Abba cikin bacin rai ya daga hannu ya wanke Mansura da mari. Mansura gigicewa ta yi, dan tun da take ba a taba marinta ba sai yau. Rike wajan ta yi tana murzawa tana kuka.
Mahaifiyar Mansura da tun ihun Amina ta shigo dakin da saurinta har tana tuntube, jin kukan mutum biyu lokaci guda.
Abba kuma daidai ya juya zai fita, suka ci karo da mahaifiyarsa. Mahaifiyar Abba kallan tuhuma take ma Abba, ganin Mansura dafe da kunci tana kuka, ga Kuma Amina rike da hannu itama tana kuka.
Mahaifiyar Abba cikin tausasa murya ta ce "Abbana, ya haka Kuma?." Nan Abba ya kwashe duk abin da ya faru ya labarta mata.
"Allah dai ya kyauta, ni ban ga abin tsoro a Allura ba, duk da ta jijiyar nan na da zafi, amma ya za a yi inda duk zafinta ba takai ciwan ba."
Abba kallan Amina ya yi da har yanzu take dafe da hannun tana kuka, ya daka Mata wata uwar tsawa ya ce"Ba za ki yi ma mutane shiru ba." Abba ya fadi maganar yana kamo hannunta yana ganin inda ya caka mata allurar, sosai ya caketa. Abba murza mata wajan ya yi ya ce "Ki je motana akwai maganin zugi ki sha."
Mansura ko Abba na daka ma Amina tsawa ta yi shiru, tana zare ido.
Abba kallan Amina ya yi ya maka mata wata uwar harara kafin ya ce "Anjima idan na dawo ki zo in miki allurar, dan na gama biyoki nan."
Yana fadin haka ya juya ya tafi.
Mahaifiyar Amina hannun Mansura ta kamo tana liliyawa, kafin ta mai da kallanta ga Mansura ta ce "Shi ya sa masu iya magana suka ce idan ka ga zama ya yi karko wai hali ne ya zo daya. Yanzu me ya acikin Allura Mansura, to Wallahi ki natsu da kyau ki ji Abba ba sauki garesa ba, a haka ma dan har yanzu yana miki kallan bakuwa ne, dan da Amina ce da Kinga yadda zai yi da ita yau a gidan nan. Allura Kuma daga gobe dama an gama inda ya ce min ta kwana uku ce, Kuma kin ji abin da ya ce baya Kara zuwa nan yi miki, daga ya dawo kin ji muryarsa a falo sai ki samesa ya yi Miki, ko Kuma Amina ta rika rakaki bangaransa ya yi miki acan, idan kin natsu har ya gama miki tom,. Idan Kuma baki natsu ba tom babu ruwana, kin ga dai tun yana raga miki sai da kika kuresa."
Mansura dai bata ce komai ba, mahaifiyar Amina ta gama fadanta ta fita.