Sashe 31
Abbana Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Mansura ido ta fara zarewa jin Kiran da mahaifiyar Abba take Mata. Abba cire hannunsa ya yi daga bakin Mansura ya je ya dauke takalminsa ya yi ma Mansura nuni da ta je ta bude ma mahaifiyarsa kofa da har yanzu take Kiran sunan Mansura tana buga kofar, shi kuma ya shiga bathroom din Mansura ya boye.
Mansura tashi ta yi ta je ta bude kofar tana mutsika idanu alamun daga barci ta tashi.
Mahaifiyar Abba kallan Mansura ta yi ta ce "Mansura me ya sa kike kwanciya baki ci abinci ba? Yanzu na shiga kitchen na ga jollop din da na yi biki ci ba, maza ki je ki dibo ki ci."
Mansura Kai ta girgiza ta ce "Mama na koshi ne fa."
Mahaifiyar Amina kofar ta ja ma Mansura ta ce "Shi kenan sai da safe."
Mansura ajiyar zuciya ta sauke kafin ta koma inda take ta zauna. Abba na jin tafiyar mahaifiyarsa ya fito. Mansura kallan Abba ta yi ta yi dariya ganin yadda yake zare ido kamar wanda ya yi karya asirinsa ya tonu.
Abba hararar Mansura ya yi bauce komai ba ya juya ya fita da sauri yana sauke ajiyar zuciya.
Haka rayuwa ta ci gaba da tafiya tsakanin Mansura da Abba, Abba bai sake mata maganar auran da ya naimi su yi ba, haka Kuma bai Kara tambayarta ba akan ahalinta kamar yadda ya yi mata alkawari.
Bangaran Aisha Abba ya yi ƙoƙarin shirya tsakaninsu gudin karta Kuma cewa ta hakura dashi.
Mansura ko kullum cikin waya suke, dan yanzu sai su raba dare suna waya ko chart.
Yanzu haka saura wata daya auran Aisha da Abba, inda soyayyarsa da Mansura yanzu ta yi karfi sosai, dan ita kanta Mansura duk yadda take shashshare Abba yanzu ta daina, idan bai kirata bama har rasa nazuwarta take, sannan abinda Abba ya lura dashi yanzu shigowarsa rayuwar Mansura kamar ya rage mata kunci, ya rabu da ganinta tana kuka kamar yadda take yi da, duk da har yanzu lokuta da dama tana yin kuka amma ba kamar da ba.
Yanzu Haka Abba zaune yake suna fira da Mansura a falon mahaifiyarsa da yake tana islamiya, Abba kallan Mansura ya yi ya ce "Man's kin yi shiru gashi lokaci sai gabatowa yake, na ce ki yi min list na abubuwan da kike bukata wanda zaki yi hidimar bikin Aisha dashi."
Mansura dagowa ta yi tana kallan Abba da idanunta da suka cika da hawaye. Abba kai ya girgiza ma Mansura ya ce "Bana so, me ye Kuma abin kuka anan."
Mansura goge hawayanta ta yi kafin ta ce "Yaya Abba narasa dalili bana son auranka da Aisha, baka ji ba yadda nake ji duk lokacin da ka yi min maganar."
Abba ya dade yana kallan Mansura kafin ya ce "Kina so in fasa auranta ne?." Kai Mansura ta daga ma Abba.
Abba murmushi ya yi ya ce "Shi kenan, gobe idan Mama ta tafi Islamiya zaki rakani wani waje kafin ta dawo."
Mansura dai batace komai, Abba gudin Kar mahaifiyarsa ta dawo ta iskesu tare da Mansura tashi ya yi ya koma wajan aiki. Da yake yanzu Haka yake yi su samu su yi hira da Mansura idan mahaifiyarsa ta tafi Islamiya shi Kuma sai ya zo susha hirarsu.
Washagari kamar yadda Abba yake yi bayan mahaifiyarsa ta tafi Islamiya Abba ya Kira Mansura a waya ya shaida mata ta samesa a waje. Bayan Mansura ta fito Abba fita ya yi ya daga cikin motasa ya rufe get din gidansu kafin ya ja motar suka tafi.
Mansura kallan Abba ta yi ta ce "Yaya Abba Ina zamu." Abba bai tankama Mansura ba saida ya yi parking daidai kofar wani gidan almajirai, ya kalli Mansura ya ce "Mansura na yi iya bakin ƙoƙarina ganin na samomana hanyar da zamu cimma burinmu amma na kasa, hakan ya sa naga wannan hanyar ita kadaice mafitarmu."
Mansura kallan Abba ta yi cikin sanyi ta ce "Yaya Abba ban gane me kake cewa ba, wata hanyar ce mafitarmu?."
Abba fita ya yi daga motar yana kallan Mansura ya ce "Muje zaki fahimta yanzu."
Mansura na biye da Abba har wajan wannan almajiran, Abba tambayar daya daga cikin almajiran ya yi ya ce "Kai Malam na nan?." Eh yanzu ya shiga gida." Kai Abba ya jinjina ya ce "Yauwa yi min sallama dashi."
Abba nanan tsaye shida Mansura Malam ya fito. Da fara'arsa ya ce "Usman Kai ne, ku karaso ciki."
Malam har cikin falonsa ya kaisu Abba, bayan sun Kara gaisawa ne Malam ya kalli Mansura ya ce "Usman wannan ce Yarinyar?." Abba Kai ya jinjina ya ce "Eh itace Malam." Malam maida kallansa ga Mansura ya yi ya ce "Yarinya ya sunanki?." Mansura kanta kasa ta ce "Mansura."
Kai malamin ya jinjina ya ce "Ma sha Allah, Mansura ya sunan mahaifinki?." Take idanun Mansura ya juya jin tambayar da malam ya yi Mata, malam lura da halin da Mansura ta shiga ya ce "A'a yan Mata daure kinji sunan mahaifinki kawai zaki fadamin daganan shi kenan."
Mansura cikin rawar murya ta ce "Kabiru." Ta fadi sunan kamar an fusgoshi daga bakinta.
"Ma Sha Allah, Mansura da fatan kina son Usman Kuma kin aminta in miki jagoranci anjima za'a daura auranki dashi kamar yadda ya bukata."
Mansura da tsananin mamaki take kallan Abba Wanda shima ita yake kallo. Mansura kuka ta fashe dashi tana tashi da sauri zata fita. Abba da sauri ya kamo hijab din Mansura yana girgiza Mata Kai.
Malam kallan Mansura ya yi ya ce "Koma ki zauna kinji." Mansura komawa ta yi ta zauna.
Malam cikin hikima ya fara yima Mansura bayani kamar haka "Mansura, Usman ya sanar dani duk abin dake faruwa, abinda zaiyi miki gatane sosai a rayuwarki a matsayin da kike yanzu babu abinda yafi da cewa dake kamar aure, Mansura wannan wata ni'imace Allah ya yi miki karki bujire ma ni'imar Allah Mansura, ki dauki haka a matsayin zanan kaddararki, ko wana dan adama zaki ga da yadda aure yake zuwa masa, dan haka ki amshi ta yin Usman kin ji."
Mansura dai kanta kasa bata ce komai ba har yanzu kuka take, dan bata ganin aure ya dace da ita a rayuwarta.
Malam jin Mansura ba ta ce komai ba ya ce "Mansura, kin amince in zama waliyinki a daura auranki da Usman?."
Mansura kasa magana ta yi hakan ya sa ta daga ma Malam kai, ta tashi da sauri ta fita.
Malam kallan Abba ya yi ya ce "Usman, ka yi jahadi Allah ya saka maka da alkairi, amma da alama akwai wani boyayan al''amari game da yarinyar nan, ka yi hakuri watarana zaka San komai game da ita.
Abba godiya ya yi ma Malam sosai kafin ya ce "Malam yanzu maganar sadaki ita zanba?." Eh Mana Usman ita zaka ba." Abba godiya sosai ya yi ma Malam kafin ya tafi ya sanar da shi zai dawo anjima.
Abba a mota ya samu Mansura ta tusa kanta tsakankanin kafafunta tana kuka. Abba cikin sanyi ya ce "Mansura bakya son auran ne ki sanar dani ba zan miki dole ba."
Mansura kai ta dago tana kallan Abba, kafin cikin kuka ta ce "Yaya Abba me ya sa ka zabi mu yi auran sirri?."
Ajiyar zuciya Abba ya sauke ya ce "Mansura, na yi ma mama maganar Ina so in aureki taki amince min, ta ce dole sai in naga ahalinki kafin idan ba haka ba bazata yadda da auranmu ba, kin ji dalilin da ya sa na naimi mu yi auran sirri."
Mansura kallan Abba ta yi ta ce "Ranar da mama ta sani fa?." Bama zata taba Sani ba, sannan idanma ta sani zata yi hakuri dole."
Mansura shiru ta yi bata Kara cewa komai ba, Abba ya tada motar suka tafi da sauri gudin Kar mama ta dawo.
Bayan sun shiga gida Abba kallan Mansura ya yi ya ce "Nawa zan baki sadaki?." Mansura rufe idanunta ta yi bata yi magana ba.
Abba murmushi ya yi kafin ya ciro kudi ya Mika ma Mansura ya ce "Gashi two hundred thousands ne, amma tsadarki ta ninninka haka, dan ke kin wuce a biya sadakinki da naira saidai saifa, Ina fatan za ki min alfarma ki amshi nairata." Mansura dai kanta kasa batace komai ba. Abba agogon hannunsa ya kalla ganin mahaifiyarsa na gaf da dawowa ya sa ya kalli Mansura ya ce "Zan tafi mama ta kusa dawowa, nan da 1 hour zan zama angon man's." Abba ya fadi maganar yana tafiya dan mahaifiyarsa zata iya dawowa a kowana lokaci.
Mansura zama ta yi bayan tafiyar Abba tana tunanin rayuwarta, ta rasa halin da take ciki farin ciki ko akasin haka ta rasa, amma tana jinta kamar wadda bata da laka a jiki, gaba daya jikinta ya yi sanyi. Mansura na nan zaune cikin wannan yanayin mahaifiyar Abba ta yi sallama ta shigo gidan.
Mahaifiyar Abba kallan Mansura ta yi damamaki ganin hijab a jikinta ga Kuma ta kalminta da ta gani kofar falon. Mahaifiyar Abba da mamaki ta ce "Mansura unguwa kika jene na ganki da hijab ga takalmi kofar falo da na gani?."
Mansura ido ta fara rabawa ta ce "A'a mama sanyi nake ji na sanya hijab na fita Ina zazzagayawa harabar gida dan kar in kwanta."
Mahaifiyar Abba murmushi ta yi ta ce "Da'alama dai 'yata ta fara zama jaruma." Mahaifiyar Abba ta fadi maganar tana zama. Bayan ta zauna kallan Mansura ta yi tana dubawa wayarta ta ce "Mansura zo ki gani, ankon bikin Abba da yan iskamiyarmu suka fidda, ni sai na ga kamar wanna tafi kyau?."
Mansura da kallo tabi mahaifiyar Abba.
Mahaifiyar Abba damamaki ta kalli Mansura ganin bata taso ba, hankalinta ma gaba daya ba akanta yake ba ta ce "Mansura lafiyarki kuwa?." Firgigi Mansura ta juyo tana kallan mahaifiyar Abba.
Mahaifiyar Abba shiru ta yi tana kallan Mansura da mamaki ta ce "Mansura lafiyarki kuwa? Tunanin me kike haka?."
Mansura kasa ta yi da kanta batace komai ba.
Mahaifiyar Abba bata sake bin takan Mansura ba ta tafi ta barta nan zaune tana cewa "Allah yaye miki wannan tunane-tunanan Mansura, kina yarinyarki karama zaki maida kanki shohowa tsabar sama rai damuwa da kika yi."
Mansura tashi ta yi ta je ta bude kofar tana mutsika idanu alamun daga barci ta tashi.
Mahaifiyar Abba kallan Mansura ta yi ta ce "Mansura me ya sa kike kwanciya baki ci abinci ba? Yanzu na shiga kitchen na ga jollop din da na yi biki ci ba, maza ki je ki dibo ki ci."
Mansura Kai ta girgiza ta ce "Mama na koshi ne fa."
Mahaifiyar Amina kofar ta ja ma Mansura ta ce "Shi kenan sai da safe."
Mansura ajiyar zuciya ta sauke kafin ta koma inda take ta zauna. Abba na jin tafiyar mahaifiyarsa ya fito. Mansura kallan Abba ta yi ta yi dariya ganin yadda yake zare ido kamar wanda ya yi karya asirinsa ya tonu.
Abba hararar Mansura ya yi bauce komai ba ya juya ya fita da sauri yana sauke ajiyar zuciya.
Haka rayuwa ta ci gaba da tafiya tsakanin Mansura da Abba, Abba bai sake mata maganar auran da ya naimi su yi ba, haka Kuma bai Kara tambayarta ba akan ahalinta kamar yadda ya yi mata alkawari.
Bangaran Aisha Abba ya yi ƙoƙarin shirya tsakaninsu gudin karta Kuma cewa ta hakura dashi.
Mansura ko kullum cikin waya suke, dan yanzu sai su raba dare suna waya ko chart.
Yanzu haka saura wata daya auran Aisha da Abba, inda soyayyarsa da Mansura yanzu ta yi karfi sosai, dan ita kanta Mansura duk yadda take shashshare Abba yanzu ta daina, idan bai kirata bama har rasa nazuwarta take, sannan abinda Abba ya lura dashi yanzu shigowarsa rayuwar Mansura kamar ya rage mata kunci, ya rabu da ganinta tana kuka kamar yadda take yi da, duk da har yanzu lokuta da dama tana yin kuka amma ba kamar da ba.
Yanzu Haka Abba zaune yake suna fira da Mansura a falon mahaifiyarsa da yake tana islamiya, Abba kallan Mansura ya yi ya ce "Man's kin yi shiru gashi lokaci sai gabatowa yake, na ce ki yi min list na abubuwan da kike bukata wanda zaki yi hidimar bikin Aisha dashi."
Mansura dagowa ta yi tana kallan Abba da idanunta da suka cika da hawaye. Abba kai ya girgiza ma Mansura ya ce "Bana so, me ye Kuma abin kuka anan."
Mansura goge hawayanta ta yi kafin ta ce "Yaya Abba narasa dalili bana son auranka da Aisha, baka ji ba yadda nake ji duk lokacin da ka yi min maganar."
Abba ya dade yana kallan Mansura kafin ya ce "Kina so in fasa auranta ne?." Kai Mansura ta daga ma Abba.
Abba murmushi ya yi ya ce "Shi kenan, gobe idan Mama ta tafi Islamiya zaki rakani wani waje kafin ta dawo."
Mansura dai batace komai, Abba gudin Kar mahaifiyarsa ta dawo ta iskesu tare da Mansura tashi ya yi ya koma wajan aiki. Da yake yanzu Haka yake yi su samu su yi hira da Mansura idan mahaifiyarsa ta tafi Islamiya shi Kuma sai ya zo susha hirarsu.
Washagari kamar yadda Abba yake yi bayan mahaifiyarsa ta tafi Islamiya Abba ya Kira Mansura a waya ya shaida mata ta samesa a waje. Bayan Mansura ta fito Abba fita ya yi ya daga cikin motasa ya rufe get din gidansu kafin ya ja motar suka tafi.
Mansura kallan Abba ta yi ta ce "Yaya Abba Ina zamu." Abba bai tankama Mansura ba saida ya yi parking daidai kofar wani gidan almajirai, ya kalli Mansura ya ce "Mansura na yi iya bakin ƙoƙarina ganin na samomana hanyar da zamu cimma burinmu amma na kasa, hakan ya sa naga wannan hanyar ita kadaice mafitarmu."
Mansura kallan Abba ta yi cikin sanyi ta ce "Yaya Abba ban gane me kake cewa ba, wata hanyar ce mafitarmu?."
Abba fita ya yi daga motar yana kallan Mansura ya ce "Muje zaki fahimta yanzu."
Mansura na biye da Abba har wajan wannan almajiran, Abba tambayar daya daga cikin almajiran ya yi ya ce "Kai Malam na nan?." Eh yanzu ya shiga gida." Kai Abba ya jinjina ya ce "Yauwa yi min sallama dashi."
Abba nanan tsaye shida Mansura Malam ya fito. Da fara'arsa ya ce "Usman Kai ne, ku karaso ciki."
Malam har cikin falonsa ya kaisu Abba, bayan sun Kara gaisawa ne Malam ya kalli Mansura ya ce "Usman wannan ce Yarinyar?." Abba Kai ya jinjina ya ce "Eh itace Malam." Malam maida kallansa ga Mansura ya yi ya ce "Yarinya ya sunanki?." Mansura kanta kasa ta ce "Mansura."
Kai malamin ya jinjina ya ce "Ma sha Allah, Mansura ya sunan mahaifinki?." Take idanun Mansura ya juya jin tambayar da malam ya yi Mata, malam lura da halin da Mansura ta shiga ya ce "A'a yan Mata daure kinji sunan mahaifinki kawai zaki fadamin daganan shi kenan."
Mansura cikin rawar murya ta ce "Kabiru." Ta fadi sunan kamar an fusgoshi daga bakinta.
"Ma Sha Allah, Mansura da fatan kina son Usman Kuma kin aminta in miki jagoranci anjima za'a daura auranki dashi kamar yadda ya bukata."
Mansura da tsananin mamaki take kallan Abba Wanda shima ita yake kallo. Mansura kuka ta fashe dashi tana tashi da sauri zata fita. Abba da sauri ya kamo hijab din Mansura yana girgiza Mata Kai.
Malam kallan Mansura ya yi ya ce "Koma ki zauna kinji." Mansura komawa ta yi ta zauna.
Malam cikin hikima ya fara yima Mansura bayani kamar haka "Mansura, Usman ya sanar dani duk abin dake faruwa, abinda zaiyi miki gatane sosai a rayuwarki a matsayin da kike yanzu babu abinda yafi da cewa dake kamar aure, Mansura wannan wata ni'imace Allah ya yi miki karki bujire ma ni'imar Allah Mansura, ki dauki haka a matsayin zanan kaddararki, ko wana dan adama zaki ga da yadda aure yake zuwa masa, dan haka ki amshi ta yin Usman kin ji."
Mansura dai kanta kasa bata ce komai ba har yanzu kuka take, dan bata ganin aure ya dace da ita a rayuwarta.
Malam jin Mansura ba ta ce komai ba ya ce "Mansura, kin amince in zama waliyinki a daura auranki da Usman?."
Mansura kasa magana ta yi hakan ya sa ta daga ma Malam kai, ta tashi da sauri ta fita.
Malam kallan Abba ya yi ya ce "Usman, ka yi jahadi Allah ya saka maka da alkairi, amma da alama akwai wani boyayan al''amari game da yarinyar nan, ka yi hakuri watarana zaka San komai game da ita.
Abba godiya ya yi ma Malam sosai kafin ya ce "Malam yanzu maganar sadaki ita zanba?." Eh Mana Usman ita zaka ba." Abba godiya sosai ya yi ma Malam kafin ya tafi ya sanar da shi zai dawo anjima.
Abba a mota ya samu Mansura ta tusa kanta tsakankanin kafafunta tana kuka. Abba cikin sanyi ya ce "Mansura bakya son auran ne ki sanar dani ba zan miki dole ba."
Mansura kai ta dago tana kallan Abba, kafin cikin kuka ta ce "Yaya Abba me ya sa ka zabi mu yi auran sirri?."
Ajiyar zuciya Abba ya sauke ya ce "Mansura, na yi ma mama maganar Ina so in aureki taki amince min, ta ce dole sai in naga ahalinki kafin idan ba haka ba bazata yadda da auranmu ba, kin ji dalilin da ya sa na naimi mu yi auran sirri."
Mansura kallan Abba ta yi ta ce "Ranar da mama ta sani fa?." Bama zata taba Sani ba, sannan idanma ta sani zata yi hakuri dole."
Mansura shiru ta yi bata Kara cewa komai ba, Abba ya tada motar suka tafi da sauri gudin Kar mama ta dawo.
Bayan sun shiga gida Abba kallan Mansura ya yi ya ce "Nawa zan baki sadaki?." Mansura rufe idanunta ta yi bata yi magana ba.
Abba murmushi ya yi kafin ya ciro kudi ya Mika ma Mansura ya ce "Gashi two hundred thousands ne, amma tsadarki ta ninninka haka, dan ke kin wuce a biya sadakinki da naira saidai saifa, Ina fatan za ki min alfarma ki amshi nairata." Mansura dai kanta kasa batace komai ba. Abba agogon hannunsa ya kalla ganin mahaifiyarsa na gaf da dawowa ya sa ya kalli Mansura ya ce "Zan tafi mama ta kusa dawowa, nan da 1 hour zan zama angon man's." Abba ya fadi maganar yana tafiya dan mahaifiyarsa zata iya dawowa a kowana lokaci.
Mansura zama ta yi bayan tafiyar Abba tana tunanin rayuwarta, ta rasa halin da take ciki farin ciki ko akasin haka ta rasa, amma tana jinta kamar wadda bata da laka a jiki, gaba daya jikinta ya yi sanyi. Mansura na nan zaune cikin wannan yanayin mahaifiyar Abba ta yi sallama ta shigo gidan.
Mahaifiyar Abba kallan Mansura ta yi damamaki ganin hijab a jikinta ga Kuma ta kalminta da ta gani kofar falon. Mahaifiyar Abba da mamaki ta ce "Mansura unguwa kika jene na ganki da hijab ga takalmi kofar falo da na gani?."
Mansura ido ta fara rabawa ta ce "A'a mama sanyi nake ji na sanya hijab na fita Ina zazzagayawa harabar gida dan kar in kwanta."
Mahaifiyar Abba murmushi ta yi ta ce "Da'alama dai 'yata ta fara zama jaruma." Mahaifiyar Abba ta fadi maganar tana zama. Bayan ta zauna kallan Mansura ta yi tana dubawa wayarta ta ce "Mansura zo ki gani, ankon bikin Abba da yan iskamiyarmu suka fidda, ni sai na ga kamar wanna tafi kyau?."
Mansura da kallo tabi mahaifiyar Abba.
Mahaifiyar Abba damamaki ta kalli Mansura ganin bata taso ba, hankalinta ma gaba daya ba akanta yake ba ta ce "Mansura lafiyarki kuwa?." Firgigi Mansura ta juyo tana kallan mahaifiyar Abba.
Mahaifiyar Abba shiru ta yi tana kallan Mansura da mamaki ta ce "Mansura lafiyarki kuwa? Tunanin me kike haka?."
Mansura kasa ta yi da kanta batace komai ba.
Mahaifiyar Abba bata sake bin takan Mansura ba ta tafi ta barta nan zaune tana cewa "Allah yaye miki wannan tunane-tunanan Mansura, kina yarinyarki karama zaki maida kanki shohowa tsabar sama rai damuwa da kika yi."