Sashe 12
Abbana Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Amina na fita ta tafi wajan aikinta, mahaifiyar Amina ma ta tafi Islamaiya, ya rage gidan Amina ita kadai, abin da ya faru take ya tuna mata da mahaifinta mai ji da ita, Wanda baya Mata gyara akan duk abin da za ta yi, duk abin da ta yi daidai ne, amma yau ita ake Mata har ana mata faɗa, akan abin da ita bata ga laifi bane.
Mansura kuka ta yi sosai, tana Kiran "Abbana! Wayyo Abbana!!." Kuka take sosai, wanda har sai da ta ji kanta ya fara ciwo kafin ta yi shiru. Abin da Abba ya yi mata Kuma ta barshi dan baya son zamanta gidan ne ya sa ya yi Mata hakan amma aganinta me ta yi mai da zai mareta ,dan ita bata ga abin duka ba, har ana mata tsawa haka. Allah sarki gata kenan, haka dan gata Wanda ba a kwabamawa yake, idan ya je gidan masu kwaba, sai ya ga kamar ba a sonsa ne a gidan ya sa ake kwabame.
Mansura na nan kwance, Sallah kadai ke tada ta, har mahaifiyar Amina ta dawo daga Islamiya. Koda ta dawo ba ta bi ta Mansura ba. Kitchen ta shiga ta Samar masu abin da za su ci.
Mansura na nan kwance har yanzu ba ta bar zubar da hawaye ba Amina har ta dawo. Amina ko da ta shigo bedroom din nasu, kallan Mansura ta yi jin ba ta tanka Mata ba, Amina ta ce "My dear, na yi laifi ne kin ganni kin kauda Kai."
Abin mamaki Mansura kawai sai ta fashe da kuka.
Amina cikin tashin hankali tahau kan bed din tana kamo Mansura ta ce "Mansura, jikin ne, ki yi shiru dan Allah ki fada min?." Amina ta idasa maganar kamar za ta yi kuka. Mansura cikin kuka ta ce "Ba Yaya Abbanku bane ya maran, Kuma mama ba ta yi masa fada ba, ni ta yi ma fada ma. Ni tafiya Zan yi in bar muku gidanku."
Amina cikin tashin hankali, jin Mansura za ta tafi, ta rasa dalili tana matukar kaunar Mansura a ranta, hakan ya sa cikin tashin hankali ta ce "Wayyo dear dan Allah karki tafi, Wallahi Yaya Abba haka yake, ko nima baki ji ba yadda yake min fada, dan Allah ki yi hakuri Yaya Abba ba zai Kara dukanki ba." Mansura da har yanzu kuka take, dan har idanta ya canza kamanni ta ce "Tom ki ce ya ban hakuri, in ba haka ba Wallahi ni gara in tafi."
Amina da kuka itama ba wuya yake Mata ba, fita ta yi daga bedroom din ta nufi falo fa gudu tana kuka. Tana zuwa ta fada kan mahaifiyarta dake zaune tana kuka. Mahaifiyar Amina kamo Amina ta yi tana cewa "Subahanallahi, Amina me ya faru Kuma?." Mama, Mansura ta ce tafiya za ta yi ba zata zauna ba, dan Allah mu je ki bata hakuri, ni dai Wallahi ina sonta bana so ta tafi." Amina ta idasa maganar cikin kuka. Mahaifiyar Amina ganin yadda Amina ke kuka buga Mata bayanta ta fara tana cewa "Shi kenan, Amina ki natsu ki fada min Mana, me ya sa za ta tafi?." Amina goge hawayanta ta yi ta ce "Yaya Abba ne dazu ya kama marinta, dan zai yi mata allura ta goce, Kuma kema mama kika yi ta Mata fada, ni dai Mama ki yi ma Yaya Abba magana dan Allah ya bata hakuri karta tafi."
Mahaifiyar Amina al'ajabi ya sa ta kasa cewa komai. Bata taba tunanin sangartar Mansura takai haka ba, sai yau. Mamakin kalar shagwabawar da aka yi ma Mansura take, wadda ba ta san daidai ba kamar ta haka,. A iya shekarun yarinyar yanzu ai ya kamata ace ta san daidai ta san ba daidai ba.
Amina Kuma jin mahaifiyarta ta yi shiru ya sa ta ce "Mama, dan Allah, kin ga marainiya ce, mu tausaya mata."
Mahaifiyar Abba kallan Amina ta yi ta ce "Shi kenan, Zan ma Abban magana in ya dawo."
Mahaifiyar Amina fadi haka ne dan Amina ta rabu da ita.
Yau ma kamar jiya Abba ya dawo. Yana zaune suna fira da mahaifiyarsa, Amina ta shigo falon.
Bayan ta yi ma Abba barka da dawowa zama ta yi ta yi shiru, tana sauraran ta ji Abba ya ce ta Kira Mansura ya bata hakuri ta ji shiru. Amina, kallan mahaifiyarta ta yi ta ce "Mama, kin fada masa." Ke baki da baki ne da ba zaki fada masa da kanki ba?."
Amina baki ta turo. Abba Kuma aje wayar hannunsa ya yi yana kallan Amina ya ce "Me kike son fada min, da ba za ki iya ba sai mama ce zata fada mi? Fada min ina jinki?." Abba ya ce yana kallan Amina.
Amina wasa da yatsun hannunta ta fara, da alama dai kamar maganar na naiman yi mata nauyin fada.
Abba dai bai kuma tambayarta ba, amma ya mai da kallansa ga Amina, irin kallan ke nake saurare.
Amina cikin kame-kame ta ce
"Yaya Abba Marin da ka yi ma Mansura dazu ne take ta kuka har yanzu, ta ce tafiya za ta yi indai baka bata hakuri ba. Kuma Wallahi Yaya Abba baka ga fuskarta ba."
Amina har ta Kai maganarta, daga Abba har mahaifiyarsa Amina kawai suke.
Abba dan ya kauda mamakinsa, kallan Amina ya yi ya ce "Ita tace ni sai na bata hakurin marin da na yi Mata?."
"Wallahi Yaya Abba baka ga fuskarta ba."
Abba hararar Amina ya yi ya ce "Tambayar da na yi miki kenan? Na ce ita ta ce sai na bata hakuri.?." Eh, Yaya Abba dan Allah ka bata."
Abba shiru ya yi yama rasa abin da zaice, kila shi ya sa ya kauda maganar ya ce "Ya jikin nata? Zazzabin ya dawo?." A'a, baidawowa ba. Amma ta ce min tunda ka mareta kanta ke ciwo."
Shiru Abba ya yi, kafin ya ce "Kira min ita, ta zo da ledar maganin."
Mansura tashi ta yi ta nufi sight dinsu, Kwance ta iske Mansura kamar yadda ta barta. Amina dafa Mansura ta yi da har yanzu hawaye bai bar fita a idonta ba ta ce "Dear ki yi hakuri haka nan dan Allah, na yi ma Yaya Abba magana yana falo ya ce ki zo."
Amina hannu ta mika ma Mansura ta tashi, da yake tun safe taki cin komai hakan ya sa bata da karfin jiki sosai.
Mansura na bin Amina suka isa har falon.
Mansura zama ta yi kusa da Amina.
Amina kallan Abba ta yi dake dannawa waya da alama kamar bai san sun shigo ba, Amina ta ce "Yaya Abba ga Mansurar."
Abba Kai ya dago ya saukesu akan Mansurar. Abba ko ba a fada mai ba yasan ta ci kuka dan ga idanunta nan sun yi ja. Abba cikin kasa da murya kamar dole akai mai ya yi maganar ya ce "Lafiya me akai miki kike kuka?."
Mansura goge hawayan da ya zibomata ta yi ta ce "Ba Kai bane dazu ban yi maka komai ba kamaran, Kuma har yanzu kunnena ciwo yake."
Abba Kai ya dago sosai ya kalleta, ya rasa abin dama zai ce mata, ya dade yana kallanta kafin ya ce a hankali kamar ance dole sai ya bata hakurin ya ce "Sorry."
Mansura dai kanta kasa bata ce komai ba, Kuma Bata fasa zubar da hawaynta ba, dan ta raina yadda ya bata hakurin.
Mahaifiyar Abba kallan Mansura ta yi ganin har yanzu tana zubar da hawaye ta ce ,
"Tom ki yi hakuri ya isa sai ki bar kukan haka nan ko?."
Abba hannu ya mika ma Amina alamun ta bashi magungunan Mansurar. Mansura Mika masa ta yi. Amina ta Mika masa magungunan ta yi. Abba lura da Mansura iya gaskiyarta take tsoran allurar ya sa bai bi takan Kuma yi mata allurar ba, ya hada allurar da maganin ya tusa a ajjihunsa.
Mansura ko murmushin farin ciki ta yi, ganin Abba ya tusa ledar magungunan cikin aljihunsa, haka ya nuna ba zai Kuma yi Mata ba kenan, hakan ya sa Mansura cikin jin dadin yau ba za a yi mata allura ba ta tashi za ta tafi. Amina kallanta ta yi, ta ce "Mansura, Abinci fa?." Nakoshi." Mansura ta ce ta juya ta tafi.
Amina tashi ta yi ta bi bayan Mansura, ta ji dalilin da ya sa ba zata ci abinci ba bayan tun safe rabonta da abinci.
Mansura kuka ta yi sosai, tana Kiran "Abbana! Wayyo Abbana!!." Kuka take sosai, wanda har sai da ta ji kanta ya fara ciwo kafin ta yi shiru. Abin da Abba ya yi mata Kuma ta barshi dan baya son zamanta gidan ne ya sa ya yi Mata hakan amma aganinta me ta yi mai da zai mareta ,dan ita bata ga abin duka ba, har ana mata tsawa haka. Allah sarki gata kenan, haka dan gata Wanda ba a kwabamawa yake, idan ya je gidan masu kwaba, sai ya ga kamar ba a sonsa ne a gidan ya sa ake kwabame.
Mansura na nan kwance, Sallah kadai ke tada ta, har mahaifiyar Amina ta dawo daga Islamiya. Koda ta dawo ba ta bi ta Mansura ba. Kitchen ta shiga ta Samar masu abin da za su ci.
Mansura na nan kwance har yanzu ba ta bar zubar da hawaye ba Amina har ta dawo. Amina ko da ta shigo bedroom din nasu, kallan Mansura ta yi jin ba ta tanka Mata ba, Amina ta ce "My dear, na yi laifi ne kin ganni kin kauda Kai."
Abin mamaki Mansura kawai sai ta fashe da kuka.
Amina cikin tashin hankali tahau kan bed din tana kamo Mansura ta ce "Mansura, jikin ne, ki yi shiru dan Allah ki fada min?." Amina ta idasa maganar kamar za ta yi kuka. Mansura cikin kuka ta ce "Ba Yaya Abbanku bane ya maran, Kuma mama ba ta yi masa fada ba, ni ta yi ma fada ma. Ni tafiya Zan yi in bar muku gidanku."
Amina cikin tashin hankali, jin Mansura za ta tafi, ta rasa dalili tana matukar kaunar Mansura a ranta, hakan ya sa cikin tashin hankali ta ce "Wayyo dear dan Allah karki tafi, Wallahi Yaya Abba haka yake, ko nima baki ji ba yadda yake min fada, dan Allah ki yi hakuri Yaya Abba ba zai Kara dukanki ba." Mansura da har yanzu kuka take, dan har idanta ya canza kamanni ta ce "Tom ki ce ya ban hakuri, in ba haka ba Wallahi ni gara in tafi."
Amina da kuka itama ba wuya yake Mata ba, fita ta yi daga bedroom din ta nufi falo fa gudu tana kuka. Tana zuwa ta fada kan mahaifiyarta dake zaune tana kuka. Mahaifiyar Amina kamo Amina ta yi tana cewa "Subahanallahi, Amina me ya faru Kuma?." Mama, Mansura ta ce tafiya za ta yi ba zata zauna ba, dan Allah mu je ki bata hakuri, ni dai Wallahi ina sonta bana so ta tafi." Amina ta idasa maganar cikin kuka. Mahaifiyar Amina ganin yadda Amina ke kuka buga Mata bayanta ta fara tana cewa "Shi kenan, Amina ki natsu ki fada min Mana, me ya sa za ta tafi?." Amina goge hawayanta ta yi ta ce "Yaya Abba ne dazu ya kama marinta, dan zai yi mata allura ta goce, Kuma kema mama kika yi ta Mata fada, ni dai Mama ki yi ma Yaya Abba magana dan Allah ya bata hakuri karta tafi."
Mahaifiyar Amina al'ajabi ya sa ta kasa cewa komai. Bata taba tunanin sangartar Mansura takai haka ba, sai yau. Mamakin kalar shagwabawar da aka yi ma Mansura take, wadda ba ta san daidai ba kamar ta haka,. A iya shekarun yarinyar yanzu ai ya kamata ace ta san daidai ta san ba daidai ba.
Amina Kuma jin mahaifiyarta ta yi shiru ya sa ta ce "Mama, dan Allah, kin ga marainiya ce, mu tausaya mata."
Mahaifiyar Abba kallan Amina ta yi ta ce "Shi kenan, Zan ma Abban magana in ya dawo."
Mahaifiyar Amina fadi haka ne dan Amina ta rabu da ita.
Yau ma kamar jiya Abba ya dawo. Yana zaune suna fira da mahaifiyarsa, Amina ta shigo falon.
Bayan ta yi ma Abba barka da dawowa zama ta yi ta yi shiru, tana sauraran ta ji Abba ya ce ta Kira Mansura ya bata hakuri ta ji shiru. Amina, kallan mahaifiyarta ta yi ta ce "Mama, kin fada masa." Ke baki da baki ne da ba zaki fada masa da kanki ba?."
Amina baki ta turo. Abba Kuma aje wayar hannunsa ya yi yana kallan Amina ya ce "Me kike son fada min, da ba za ki iya ba sai mama ce zata fada mi? Fada min ina jinki?." Abba ya ce yana kallan Amina.
Amina wasa da yatsun hannunta ta fara, da alama dai kamar maganar na naiman yi mata nauyin fada.
Abba dai bai kuma tambayarta ba, amma ya mai da kallansa ga Amina, irin kallan ke nake saurare.
Amina cikin kame-kame ta ce
"Yaya Abba Marin da ka yi ma Mansura dazu ne take ta kuka har yanzu, ta ce tafiya za ta yi indai baka bata hakuri ba. Kuma Wallahi Yaya Abba baka ga fuskarta ba."
Amina har ta Kai maganarta, daga Abba har mahaifiyarsa Amina kawai suke.
Abba dan ya kauda mamakinsa, kallan Amina ya yi ya ce "Ita tace ni sai na bata hakurin marin da na yi Mata?."
"Wallahi Yaya Abba baka ga fuskarta ba."
Abba hararar Amina ya yi ya ce "Tambayar da na yi miki kenan? Na ce ita ta ce sai na bata hakuri.?." Eh, Yaya Abba dan Allah ka bata."
Abba shiru ya yi yama rasa abin da zaice, kila shi ya sa ya kauda maganar ya ce "Ya jikin nata? Zazzabin ya dawo?." A'a, baidawowa ba. Amma ta ce min tunda ka mareta kanta ke ciwo."
Shiru Abba ya yi, kafin ya ce "Kira min ita, ta zo da ledar maganin."
Mansura tashi ta yi ta nufi sight dinsu, Kwance ta iske Mansura kamar yadda ta barta. Amina dafa Mansura ta yi da har yanzu hawaye bai bar fita a idonta ba ta ce "Dear ki yi hakuri haka nan dan Allah, na yi ma Yaya Abba magana yana falo ya ce ki zo."
Amina hannu ta mika ma Mansura ta tashi, da yake tun safe taki cin komai hakan ya sa bata da karfin jiki sosai.
Mansura na bin Amina suka isa har falon.
Mansura zama ta yi kusa da Amina.
Amina kallan Abba ta yi dake dannawa waya da alama kamar bai san sun shigo ba, Amina ta ce "Yaya Abba ga Mansurar."
Abba Kai ya dago ya saukesu akan Mansurar. Abba ko ba a fada mai ba yasan ta ci kuka dan ga idanunta nan sun yi ja. Abba cikin kasa da murya kamar dole akai mai ya yi maganar ya ce "Lafiya me akai miki kike kuka?."
Mansura goge hawayan da ya zibomata ta yi ta ce "Ba Kai bane dazu ban yi maka komai ba kamaran, Kuma har yanzu kunnena ciwo yake."
Abba Kai ya dago sosai ya kalleta, ya rasa abin dama zai ce mata, ya dade yana kallanta kafin ya ce a hankali kamar ance dole sai ya bata hakurin ya ce "Sorry."
Mansura dai kanta kasa bata ce komai ba, Kuma Bata fasa zubar da hawaynta ba, dan ta raina yadda ya bata hakurin.
Mahaifiyar Abba kallan Mansura ta yi ganin har yanzu tana zubar da hawaye ta ce ,
"Tom ki yi hakuri ya isa sai ki bar kukan haka nan ko?."
Abba hannu ya mika ma Amina alamun ta bashi magungunan Mansurar. Mansura Mika masa ta yi. Amina ta Mika masa magungunan ta yi. Abba lura da Mansura iya gaskiyarta take tsoran allurar ya sa bai bi takan Kuma yi mata allurar ba, ya hada allurar da maganin ya tusa a ajjihunsa.
Mansura ko murmushin farin ciki ta yi, ganin Abba ya tusa ledar magungunan cikin aljihunsa, haka ya nuna ba zai Kuma yi Mata ba kenan, hakan ya sa Mansura cikin jin dadin yau ba za a yi mata allura ba ta tashi za ta tafi. Amina kallanta ta yi, ta ce "Mansura, Abinci fa?." Nakoshi." Mansura ta ce ta juya ta tafi.
Amina tashi ta yi ta bi bayan Mansura, ta ji dalilin da ya sa ba zata ci abinci ba bayan tun safe rabonta da abinci.