Sashe 14
Abbana Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Amina kwance ta iske Mansura tana kuka, ta tusa kanta tsakankanin cinyoyinta tana kuka. Amina cikin damuwa ta ce "Mansura wai ke yaushe zaki daina kuka ne? Baki gajiya da kuka ? Shi kenan ba damar ki kasance ke kadai sai kuka. Yanzu yi hakuri dan Allah ki fada min meye?." Mansura dagowa ta yi tana kallan Amina, ta ce "Idan kika yi aure dawa zan zauna, Kuma bansan Ina zani ba, nan da wata uku za ki yi aure ki barni. Wallahi ba zan iya jure abin da ke raina ba babu ke, kashe kaina zan yi in huta, da azabar kuncin da furgicin da nake sha a raye."
Amina da idonta da ya cika da kwalla take kallan Mansura jin kalamanta. Amina ta dade tana kallan Mansura kafin ta ce "Mansura ki huta da kuncin da furgicin da kike sha a raye kika ce, kuma kika furta kalmar za ki kashe kanki, duk da na yi alƙawarin ba zan sake tambayarki akan abin da baki son asani ba, hakan ba zai sa in janye daga gareki ba, dan Allah Mansura ki bar irin kalaman nan, kin manta na yi miki alkawari zan yi ma Yaya Abba magana a d'aga har sai sanda kika samu muji kafin a hada a yi gabadaya?."
Kai Mansura ta girgiza ta ce "A'a ni dai karki fada ma kowa Kar a hada auran, ni Babu wani miji da Allah zai fito min da shi, ni bazan taba yin aure ba.."
Amina rasa abin da zata ce ma Mansura ta yi hakan ya sa ta yi shiru tana lallashin Mansurar, a haka dai har barci ya kwace Amina.
Bangaran gidan su Aisha, mahaifiyar Aisha Koda ta tambayi Aisha yadda suka yi da bakonta, Aisha ba ta gayama mata gaskiyar yadda suka yi da Abba ba, ce ma mahaifiyarta ta yi sun aminta da junansu.
Aisha duk da ba taga alamar Abba zai kirata a waya ba, amma tuk da haka daga wayarta ta yi ringing sai ta dauka ko shine, sai ta duba taka daga akasin hakan. Aisha wayata ta dakko ta tura ma Abba da sako kamar haka. "Ina fatan ka kaje gida lafiya."
Bangaran Abba ko Koda ya ga sakon tsaki ya yi.
Aisha irin matannan ce masu shishshige, hakan ya sa tana jin mahaifiyarta ta ce mahaifiyar Abba ta sanar ba za ta zo Islamiya ba kwana biyu saboda kanwar Abba ta haihu. Aisha kallan mahaifiyarta ta yi ta ce "Mama ni ko Ina son zuwa sunan." Aisha ta fada tana kallan mahaifiyarta ta ji abin da za ta ce.
Mahaifiyar Aisha shiru ta yi, kafin ta ce "Shi kenan bari in sanar da Aishar." Da yake Aisha sunan mahaifiyar Abba gareta.
Mahaifiyar Aisha Kiran mahaifiyar Abba ta yi ta sanar da ita ta Aisha za ta je masu suna.
Mahaifiyar Abba ko da murnarta ta ce "Shi kenan, Zan ba Amina number Aishar sai su tafi tare."
Mahaifiyar Abba bangaransu Amina ta shiga bayan ta gama wayar, zama ta yi tana cewa" Amina, gobe da yaushe ne za ku gidan sunan? Aisha wadda yayanku zai aura tana so za ta je na ce sai ku je tare." Amina ta shi ta yi da murnarta ta ce "Wayyo Mama ban numberta." Amina ta idasa maganar tana dakko wayarta.
Mahaifiyar Amina number Aisha ta sama Amina ta mika mata ta fita. Amina da yake mai son mutane ce take ta doka ma Aisha Kira, sun jima suna waya kafin Amina ta yi mata sallama da sunan sai sun hadu gobe.
Bangaran Aisha Kuma duk wata fargaba dake damunta game da Abba duk sai ta ji babu ita, dan kiran Amina sai ya Kuma tabbatar mata da auranta da Abba kamar yadda take fata. Hakan ya sa take ta dakko wayarta ta fara rubuta ma Abba text message kamar haka. "Assalamu alaikum mosoyin zuciyata, Ina fatan kana cikin koshin lafiya da nishadi."
Abba Koda ya ga sakon Aishar tsaki ya yi ya maida wayarsa ya aje.
Washegari, Amina da wuri ta tashi suka yi shirin tafiya gidan suna. Jin Aisha shiru kiranta ta yi ta sanar Mata sun shirya ita suke jira. Aisha ta ki Kiran Amina ne dama dan ta ga ko sun damu da ita, ana haka ko kiran Amina ya shigo wayarta ta sanar Mata ita suke jira.
Aisha simple makeup ta yi, ta zura hijb dinta doge har kasa tare da nikabi ta rufe fuskarta. Sallama ta yi ma mahaifiyarta dan ta bata address din gidan surukan nata.
Amina suna nan zaune Aisha ta yi sallama ta shigo gidan. Amina da kallo ta bita dan bata gane itace Aishar ba, mahaifiyar Amina da yake tana falon kallan Aisha ta yi tana murmushi ta ce "Amina ga Aishar nan ta karaso.
Amina da gudu ta ruga ta rungume Aisha, a haka suka karaso har falon. Aisha cikin girmamawa ta gaida surukarta.
Amina kallan Mansura ta yi tana mamakin halinta ganin ko inda Aisha take bata kalla ba, Amina dafa Mansura ta ce "Dear mu je ko?." Mansura tashi ta yi suka tafi. Bayan sun fita gidan Aisha ta kalli Mansura ta ce "Ina kwana sister." Lafiya." Mansura ta ce mata ta dauke kai. Amina da mamaki ta kalli Mansura amma Kuma sai ba ta ce mata komai ba.
Napep suka hau har gidan sunan, Aisha da Amina sai firarsu suke Mansura dai ba ta sa masu baki ba. Amina cikin hirarne ta ce "Aunty amaryar yayanmu Abba, ni fa na gaji da kawaici ki bude mana fuska mu ganki."
Murmushi Aisha ta yi ta ce "Ki bari sai mun je gidan sunanko ba a nan a titi ba." Amina bude baki ta yi ta ce "Tom mu da muka sa gyale sai Yaya kenan?." Dariya Aisha ta yi ta ce "Ku kunsaba fita haka, nima na saba fita a haka." Haka dai suka ci gaba da hirarsu har suka Kai gidansunan, ban da Mansura da bata tanka masu ba, dama Kuma ita ba ma'abociyar magana ba ce.
Ko a gidan sunan Mansura fita waje ta yi dan duk sai taji ta takura kasan cewar yawan jama'a da hayaniya, hakan ya sa ta fita waje ta zauna.
A cikin gidan kuma Amina sai naiman Mansura ta ke, Aisha ce ta kalleta ta ce "Anya kuwa ba fita ta yi ba." Wajan suka duba inda suka iske Mansura zaune ta yi tagumi, daga ganinta ta yi nisa sosai a duniyar tunani. Amina dafa Mansura ta yi ta ce "Mansura lafiya kika fito waje kika zauna anata hutuna?."
Mansura dako jajayan idanunta ta yi ta ce "Ni gida Zan tafi."
Amina da mamaki ta ce "Gida Kuma Mansura, baki ga na zo Mana da kayan canzawa ba ? A nan fa zamu kwana." Ni dai gida zan tafi." Mansura ta sake maimaitawa Kamar za ta yi kuka.
Aisha tsugunnawa ta yi ta dafa Mansura ta ce "Sister, dan Allah idan wani abun akai miki ki yi hakuri ya za ayi kun zo suna daniyar kwana Kuma ku tafi gida, ko mama ma in taga Kun koma gida suna baiwatse ba ai ba zata ji dadi ba."
Mansura ture hannun Aisha ta yi dake kan kafadarta ta ce "Da allacan malama ki sakan za ki zo ki kama dafa ni da katsamin hannunki."
Amina da Mansura ta gama kaita bango cikin fushi ta ce "Haba Mansura wai meye kike yi haka ne? Matar da Yaya Abba zai aura kike in gijewa dan ta fada miki gaskiya."
Mansura da babu abin da tasani ban da ririta, yana daya daga cikin abin da ya sa ta saki jiki da Amina har itama take mata kallan masoyiyartace, amma ganin yanzu ta dake tana mata faɗa akan Aisha sai ta ji ranta ya bace har ta fara daukar ko Amina ta gaji da ita ne. Mansura cikin goge hawayan da ya fara zubar Mata ta ce "Na ingijeta din." Amina kama hannun Aisha ta yi suka tafi suka bar Mansura nan tsaye. Mansura fashewa ta yi da kuka. Mansura ta dade tana kuka kafin ta samu napep ta tafi gidansu Amina. Mansura kallan mai napep din ta yi bayan ya sauketa ta ce "Dan Allah ka yi hakuri ban da kudi."
Wani mugun ashar ya mulmulo ya danna ma Mansura ya ce "Wallahi ko ubawan waye ya tsaya miki sai kin ban kudina zaki bar wajan nan."
Mansura da kwatakwata ba ta da wuyar kuka fashewa da kuka ta yi ganin wai yau itace za a rike akan k'ananan kudi. Gashi lokacin duhu ya fara yi ana ta sallar magariba, ana cikin haka sai ga Abba ya dawo Sallah zai shiga gidan. Abba damamaki ya tsaya jin kuka mace shi Kuma Mai napep din ya dage sai cewa yake "Wallahi ko kukan jini za ki yi sai kin biyani kudina, ubanwa ya ce ki hau min keke baki da kudi."
Abba karasawa ya yi wajan ba dan ya san dawa ake fadan ba.
Da mamaki Abba ya bi Mansura da kallo, ta dage sai uban kuka take ci. Abba tsawa ya yi ma mai napep din ya ce "Ba kada da ankali ne da zaka riketa akan k'ananan kudi, sakarta."
Da yake mai napep din irin yan tashar nan ne ya ce " Yo rankashidade aban kudina mana aga in ban saketa ba." Sakarta. "Nawa ne kudin naka?." Dubu biyu ce."
Abba kudin ya ba ma mai napep din, sannan ya kalli Mansura ya ce "Ina Aminar fa?." Tana can." Mansura ta ce tana goge hawayanta. Abba juyawa ya yi ya yi cikin gidan Mansura ta bi shi a baya.
Amina da idonta da ya cika da kwalla take kallan Mansura jin kalamanta. Amina ta dade tana kallan Mansura kafin ta ce "Mansura ki huta da kuncin da furgicin da kike sha a raye kika ce, kuma kika furta kalmar za ki kashe kanki, duk da na yi alƙawarin ba zan sake tambayarki akan abin da baki son asani ba, hakan ba zai sa in janye daga gareki ba, dan Allah Mansura ki bar irin kalaman nan, kin manta na yi miki alkawari zan yi ma Yaya Abba magana a d'aga har sai sanda kika samu muji kafin a hada a yi gabadaya?."
Kai Mansura ta girgiza ta ce "A'a ni dai karki fada ma kowa Kar a hada auran, ni Babu wani miji da Allah zai fito min da shi, ni bazan taba yin aure ba.."
Amina rasa abin da zata ce ma Mansura ta yi hakan ya sa ta yi shiru tana lallashin Mansurar, a haka dai har barci ya kwace Amina.
Bangaran gidan su Aisha, mahaifiyar Aisha Koda ta tambayi Aisha yadda suka yi da bakonta, Aisha ba ta gayama mata gaskiyar yadda suka yi da Abba ba, ce ma mahaifiyarta ta yi sun aminta da junansu.
Aisha duk da ba taga alamar Abba zai kirata a waya ba, amma tuk da haka daga wayarta ta yi ringing sai ta dauka ko shine, sai ta duba taka daga akasin hakan. Aisha wayata ta dakko ta tura ma Abba da sako kamar haka. "Ina fatan ka kaje gida lafiya."
Bangaran Abba ko Koda ya ga sakon tsaki ya yi.
Aisha irin matannan ce masu shishshige, hakan ya sa tana jin mahaifiyarta ta ce mahaifiyar Abba ta sanar ba za ta zo Islamiya ba kwana biyu saboda kanwar Abba ta haihu. Aisha kallan mahaifiyarta ta yi ta ce "Mama ni ko Ina son zuwa sunan." Aisha ta fada tana kallan mahaifiyarta ta ji abin da za ta ce.
Mahaifiyar Aisha shiru ta yi, kafin ta ce "Shi kenan bari in sanar da Aishar." Da yake Aisha sunan mahaifiyar Abba gareta.
Mahaifiyar Aisha Kiran mahaifiyar Abba ta yi ta sanar da ita ta Aisha za ta je masu suna.
Mahaifiyar Abba ko da murnarta ta ce "Shi kenan, Zan ba Amina number Aishar sai su tafi tare."
Mahaifiyar Abba bangaransu Amina ta shiga bayan ta gama wayar, zama ta yi tana cewa" Amina, gobe da yaushe ne za ku gidan sunan? Aisha wadda yayanku zai aura tana so za ta je na ce sai ku je tare." Amina ta shi ta yi da murnarta ta ce "Wayyo Mama ban numberta." Amina ta idasa maganar tana dakko wayarta.
Mahaifiyar Amina number Aisha ta sama Amina ta mika mata ta fita. Amina da yake mai son mutane ce take ta doka ma Aisha Kira, sun jima suna waya kafin Amina ta yi mata sallama da sunan sai sun hadu gobe.
Bangaran Aisha Kuma duk wata fargaba dake damunta game da Abba duk sai ta ji babu ita, dan kiran Amina sai ya Kuma tabbatar mata da auranta da Abba kamar yadda take fata. Hakan ya sa take ta dakko wayarta ta fara rubuta ma Abba text message kamar haka. "Assalamu alaikum mosoyin zuciyata, Ina fatan kana cikin koshin lafiya da nishadi."
Abba Koda ya ga sakon Aishar tsaki ya yi ya maida wayarsa ya aje.
Washegari, Amina da wuri ta tashi suka yi shirin tafiya gidan suna. Jin Aisha shiru kiranta ta yi ta sanar Mata sun shirya ita suke jira. Aisha ta ki Kiran Amina ne dama dan ta ga ko sun damu da ita, ana haka ko kiran Amina ya shigo wayarta ta sanar Mata ita suke jira.
Aisha simple makeup ta yi, ta zura hijb dinta doge har kasa tare da nikabi ta rufe fuskarta. Sallama ta yi ma mahaifiyarta dan ta bata address din gidan surukan nata.
Amina suna nan zaune Aisha ta yi sallama ta shigo gidan. Amina da kallo ta bita dan bata gane itace Aishar ba, mahaifiyar Amina da yake tana falon kallan Aisha ta yi tana murmushi ta ce "Amina ga Aishar nan ta karaso.
Amina da gudu ta ruga ta rungume Aisha, a haka suka karaso har falon. Aisha cikin girmamawa ta gaida surukarta.
Amina kallan Mansura ta yi tana mamakin halinta ganin ko inda Aisha take bata kalla ba, Amina dafa Mansura ta ce "Dear mu je ko?." Mansura tashi ta yi suka tafi. Bayan sun fita gidan Aisha ta kalli Mansura ta ce "Ina kwana sister." Lafiya." Mansura ta ce mata ta dauke kai. Amina da mamaki ta kalli Mansura amma Kuma sai ba ta ce mata komai ba.
Napep suka hau har gidan sunan, Aisha da Amina sai firarsu suke Mansura dai ba ta sa masu baki ba. Amina cikin hirarne ta ce "Aunty amaryar yayanmu Abba, ni fa na gaji da kawaici ki bude mana fuska mu ganki."
Murmushi Aisha ta yi ta ce "Ki bari sai mun je gidan sunanko ba a nan a titi ba." Amina bude baki ta yi ta ce "Tom mu da muka sa gyale sai Yaya kenan?." Dariya Aisha ta yi ta ce "Ku kunsaba fita haka, nima na saba fita a haka." Haka dai suka ci gaba da hirarsu har suka Kai gidansunan, ban da Mansura da bata tanka masu ba, dama Kuma ita ba ma'abociyar magana ba ce.
Ko a gidan sunan Mansura fita waje ta yi dan duk sai taji ta takura kasan cewar yawan jama'a da hayaniya, hakan ya sa ta fita waje ta zauna.
A cikin gidan kuma Amina sai naiman Mansura ta ke, Aisha ce ta kalleta ta ce "Anya kuwa ba fita ta yi ba." Wajan suka duba inda suka iske Mansura zaune ta yi tagumi, daga ganinta ta yi nisa sosai a duniyar tunani. Amina dafa Mansura ta yi ta ce "Mansura lafiya kika fito waje kika zauna anata hutuna?."
Mansura dako jajayan idanunta ta yi ta ce "Ni gida Zan tafi."
Amina da mamaki ta ce "Gida Kuma Mansura, baki ga na zo Mana da kayan canzawa ba ? A nan fa zamu kwana." Ni dai gida zan tafi." Mansura ta sake maimaitawa Kamar za ta yi kuka.
Aisha tsugunnawa ta yi ta dafa Mansura ta ce "Sister, dan Allah idan wani abun akai miki ki yi hakuri ya za ayi kun zo suna daniyar kwana Kuma ku tafi gida, ko mama ma in taga Kun koma gida suna baiwatse ba ai ba zata ji dadi ba."
Mansura ture hannun Aisha ta yi dake kan kafadarta ta ce "Da allacan malama ki sakan za ki zo ki kama dafa ni da katsamin hannunki."
Amina da Mansura ta gama kaita bango cikin fushi ta ce "Haba Mansura wai meye kike yi haka ne? Matar da Yaya Abba zai aura kike in gijewa dan ta fada miki gaskiya."
Mansura da babu abin da tasani ban da ririta, yana daya daga cikin abin da ya sa ta saki jiki da Amina har itama take mata kallan masoyiyartace, amma ganin yanzu ta dake tana mata faɗa akan Aisha sai ta ji ranta ya bace har ta fara daukar ko Amina ta gaji da ita ne. Mansura cikin goge hawayan da ya fara zubar Mata ta ce "Na ingijeta din." Amina kama hannun Aisha ta yi suka tafi suka bar Mansura nan tsaye. Mansura fashewa ta yi da kuka. Mansura ta dade tana kuka kafin ta samu napep ta tafi gidansu Amina. Mansura kallan mai napep din ta yi bayan ya sauketa ta ce "Dan Allah ka yi hakuri ban da kudi."
Wani mugun ashar ya mulmulo ya danna ma Mansura ya ce "Wallahi ko ubawan waye ya tsaya miki sai kin ban kudina zaki bar wajan nan."
Mansura da kwatakwata ba ta da wuyar kuka fashewa da kuka ta yi ganin wai yau itace za a rike akan k'ananan kudi. Gashi lokacin duhu ya fara yi ana ta sallar magariba, ana cikin haka sai ga Abba ya dawo Sallah zai shiga gidan. Abba damamaki ya tsaya jin kuka mace shi Kuma Mai napep din ya dage sai cewa yake "Wallahi ko kukan jini za ki yi sai kin biyani kudina, ubanwa ya ce ki hau min keke baki da kudi."
Abba karasawa ya yi wajan ba dan ya san dawa ake fadan ba.
Da mamaki Abba ya bi Mansura da kallo, ta dage sai uban kuka take ci. Abba tsawa ya yi ma mai napep din ya ce "Ba kada da ankali ne da zaka riketa akan k'ananan kudi, sakarta."
Da yake mai napep din irin yan tashar nan ne ya ce " Yo rankashidade aban kudina mana aga in ban saketa ba." Sakarta. "Nawa ne kudin naka?." Dubu biyu ce."
Abba kudin ya ba ma mai napep din, sannan ya kalli Mansura ya ce "Ina Aminar fa?." Tana can." Mansura ta ce tana goge hawayanta. Abba juyawa ya yi ya yi cikin gidan Mansura ta bi shi a baya.