← Book details Ta Daban Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 11 OF 37

Sashe 11

Ta Daban Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read

Slowly ta shiga buɗe idanunta da taji sun mata nauyi loƙaci guda, ɗan lumshesu ta sake yi tana ƙoƙarin saita kanta dan koda wasa batai tunanin zerewa motar ba. Wata ƙatuwar Ajiyar zuciya ta sauƙe me nauyi. Tana ambatar sunan ALLAH cikin rai da ruhinta. ★ Ɓangaren Sheikh juraij kuwa a natse ya sanya kansa cikin ƙaton parlour'n gidan, da gwaggo Haleemah wacce ta kasance kaka a gareshi ya fara cin karo. Gwaggo Haleemah yaya ce ga Ama kuma ita kaɗai take da ita ƴar uwa anan kusa idan ka cire dangin su dake saudia. "Aaaahhh lale marabu da babban angona, Juraij yau kuma kaine da kanka?, Kodai ɓatan hanya kayi Ni Ko nace banda wajen zaman masu ɓatan hanyar?" Tay maganar da murmushi kwance saman fuskarta. Zama yay daga saman 1str ɗin dake kusanta. Zamansa babu daɗewa kamar an cillota Samha ta shigo cikin parlour'n zaram tamkar ana tunkuɗota.
Samha ƴa ce ga Surayya ƙanwa ga Annie kenan wacce kuma suke ƙoƙarin haɗa aurentane kuma da juraij ɗin, sedai sam yarinyan bata da kamun kai amma su basa ganin hakan babban burinsu kawai auren ya haɗu. Se data ta shigo kuma cikin mugun bariki da kisisina ta wani sinne kanta ƙasa tana furta. "Laaaah dama uncle kaine? To sannu da zuwa Bara a kawo maka juice" da hannu ya mata halaman bai buƙata. Dan faɗa fuska tayi tare da duban gwaggo Haleemah tana furta, "Gaskiya gwaggo ki ma Uncle juh magana! Shikenan yazo shi kullum ba zai ci abincin mu ba inda Ni ce na ce zan kawo mishi"
Dan murmushi irin nasu na manya gwaggo Haleemah ta yi tana furta "Yo in banda abin kima Samha kwana nawa ya rage miki, ku ce kan kita masa girkin kalan wanda yake so, kuma dai kinsan juraij bai fiye son komai a sake ba, amma idan da gake se shi ne seki ta lallaɓa kayanki ko" ta ƙarishe maganan da Murmushin nan ɗauke saman fuskarta. Dariya ta saki tana rufe idonta wai ita ala nan dole an bata kunya.Daga haka ta shige dayan parlour'n dake kusa da wannan ɗin shi kuwa a natse yaja fruits ɗin dake gaban gwaggo'n apple ya ɗauka ya ɗan ci kaɗan. Bayan bata saƙon da yay ya miƙe da shirin tafiya. Suraj ne ya shigo parlour'n da yake shima jika ne ga gwaggo Haleemah'n. Gefensa ɗan wani matashin saurayi ne suna tafe gwanin birgewa. "Ahhhh yau wa nake gani kamar babban malami" ya fadi a washe hakwaronsa farare tasss waje, Bai bi ta kan iya shegen da suraj ɗin ya soma mashi ba yana bama matashin hannun suyi masabaha. Don ya san idan ya biye ma suraj ɗin babu ruwansa kunya ne kawai ze bashi.
Ita kuwa gwaggo Haleemah bin bayan Samha tay, zama tay gefenta suka soma fira cikin dabara gwaggo take dan son lurar da Samha'n kan lamarin Sheikh juraij ɗin da ake shirin aura masa dap. Sedai maganan bawai tama ko fita bane iyaka yasu ya sune suke ƙusƙus dinsu tsakani. Sosai firan da gwaggo take mata akan juraij ɗin ke mata daɗi da sanyata nishaɗi

♡
Rasss gabanta ya mugun buga mata don ganin drector Muhsin Aliey Yahaya tsaye da wasu yara wanda kana kallon su kwanyarka zata Hasko maka cewan ƴan daba ne. Sedai shanye tsoron nata bayyanuwa tay tana karasa fitowa a motar nata kai tsaye ba tare data kalla inda yake ba ta shigewanta inda zasu gabatar da shooting film ɗin ta na. ★TAURARUWA♡

Film ne da take son yin cleaning up nashi Kan yadda waɗanda taurarinsa suke Haskawa a cikin duniyar suke wulaƙanta mabiya dama masoyansa. Tana shiga hall ɗin Hotels din da za'a gudanar da shot ɗin suka dauki sowa da ihun ƙiran sunanta.

Kanta ta É—auke daga kallon Moh Ameern Saif daya kafeta da ido. Nan aka soma gudanar da shirin cike da birgewa.

Ba itane ta sama kanta ba se wajajen 5:40 pm. A matuƙar gajiye lilis ta fito daga cikin hall ɗin tana jin matuƙar haushin kanta na kin tahowa da ko gurds ɗaya da batay ba. Jingina da jikin Railer'n dake gaban hall ɗin tay idanunta lumshe. Ko dinner gaza yi tayi haka har wata actress me suna Khadija Yobe ta fito itama ta sameta.
"Meesherh lafiyan ki kuwa?"
"Hummm kedai Khadijah kyaleni wllh duk a gajiye nake jima nake kamar bazan iya driving É—in nan bane ma wllh"

"Me zai hana idan har babu damuwa na miƙaƙi gidan" ɗan numfashi ta fesar tana furta "No ba ma se kin hawal da kanki ba na kira ayrah amoh nace ta biyo ta nan ta tafi dani"
"Kuma kina ganin har loƙaci bazai ƙure miki ba kanta ƙara so?" Khadijah yoben ta tambaye ta ko kafin ma ta bata amsar sega wata arniyar farar Roy *R* Rayce nan na danno Kanta cikin Hotels ɗin.
Har gab dasu motar ta ƙaraso kafin a natse aka soma yin kasa da glass na motar, wani kalan zaro fararen idanuwanta woje tay don ganin..............

To ai Shikenan muma semu gimtse 👌

*BY AMMEY LAYLERH*

Chat mee view
My phone
07085041758
Or
08104493215

Don son magana dani AMMEY LAYLERH chart Mee or call a wannan No É—in 08104493215

Masu neman *MIKIYA* ma har yanzun ƙofarku a buɗe take har yanzu yana nan akan farashin sa na ₦ 500 ban ƙara ba kamar yacce na ce a baya.

https://whatsapp.com/channel/0029Vb4EHwq6LwHgpTokZA3D

༺༻

*༺♡𝕋𝔸 𝘿𝘼𝙱𝔸𝑵☆༻*

_𝘚𝚙ҽcⅈɑʟ _
♡
𝙈𝙖𝙧𝙮𝙖𝙢 𝙉a𝙨𝙚𝙚𝙧 ɱⅈ𝔯𝔯ɑһ

_𝘼𝙈𝙈𝙀𝙔 𝙇𝘼𝙔𝙇𝙀𝙍𝙃_

𝙋a𝙜𝙚

9&10

✯ *🌠 JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION💫*
(J.W.A)
https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v

_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️*

*𝙄 𝘿𝙀𝘿𝙄𝘾𝘼𝙏𝙀𝘿 𝙏𝙊 𝙂𝙊𝙑𝙀𝙍𝙉𝙈𝙀𝙉𝙏 𝙂𝙄𝙍𝙇 𝙐𝙉𝙄𝙏𝙔 𝙎𝙀𝘾𝙊𝙉𝘿𝘼𝙍𝙔 𝙎𝘾𝙃𝙊𝙊𝙇 𝙈𝘼𝙇𝘼𝙈 𝙈𝘼𝘿𝙊𝙍𝙄 𝙋𝙈𝘽 001*

♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡
Chapter 11 · 0% Book details