← Book details Sarauniyar Kyau Takun Farko Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 57 OF 96

Sashe 57

Sarauniyar Kyau Takun Farko Complete Hausa Novel · about 8 min read

A hankali sannan cikin kashe murya ta ce "Mister Mai Kyau, please idan bazan takura ka ba, zaga iya ragemin hanya izuwa gidan Uncle Riyaz a domin na amso wani saƙo wajen matar sa Auntie Ramlat kuwa?."

Murmushi ya yi ke nan dai zai sama dama na ganin hasken Ranshi.🥳

"Okay babu damuwa shiga ki kira ƙannin naki, mu tafi tare."

Da wani irin mugun sauri ta kalleshi bakinta har wani rawa yake wurin faÉ—in

"Mene are You kidding me?."

Ta sauke ajiyar zuciya tana kuma danne abin da yake caccakar zuciyarta, cikin É—an sanyin murya ta ce

"Alright it's okay. Bari kawai na shiga na kira su, sai mu tafi taren."

Tayi maganar a É—an daburce sannan ta bar wurin cikin sauri sauri ta shige cikin gida.

AFT£R F£W MINUT£S

Su uku suka fito a tare Rafi'at Rafiq Rayyan, sai Haleesat Rashid Rayyan, sai kuma wata kyakyawar matashiyar budurwa wacca ba za ta kaisu a shekaru ba, Rafi'at da budurwar a tare sai Haleesat tana bin bayansu hannunta janye da wani madaidaicin Akwati.

Dukkansu suna sanye cikin shiga kala É—aya wato Arabian gown white color mai adon flowers coffee color, sai ma yafi coffee color da suka yi rolling kansu dashi.
Ƙari sawa wurin shi sukayi yana jingine da Motarsa yanzu kuma waya yake yi da alama abin da ya shafi harkokin kasuwancin sa ne.

Rafi'at babu abin da take saƙawa cikin Ranta fa ce duk yadda zata yi Haleesat Rashid Rayyan karta shiga cikin Motar Abubakar Mai Kyau, dan kuwa ba shi kanshi ba hatta da abin da ya shafeshi bata ƙaunar Haleesat ta raɓa.

𝗞𝗵𝗮𝗱𝗲𝗲𝗷𝗮𝗿𝘁𝗵 𝗦𝗮𝗯𝗶'𝘂 𝗬𝗮𝗵𝘆𝗮𝗵

𝗪𝗿𝗶𝘁𝗲𝗿 𝗢𝗳

Ŝ̬Â̬R̬̂Â̬Û̬N̬̂Î̬Ŷ̬Â̬R̬̂ K̬̂Ŷ̬Â̬Û̬
fιяѕт ѕтєρ

Ganin ya kammala wayar da yake yi ne, yasa cikin washe fuska ta ce dashi "Barka dai Mister mai kyau 2days Fatan kana lafiya?."

Murmushi ya yi cike da jindaÉ—in jin muryar ta na rashin dalili ya amsa ma ta da
"I'm very Normal, Fatan kema hakan, Ina Ƴan uku na?."

Murmushi Haleesat Rashid Rayyan tayi ta ce
"Oh Ƴan uku suna gidansu. Yanzu haka can zamu wuce ai."
"Okay harna ƙosa a ƙarisa domin kuwa nayi kewar Rashin jin su sosai."

Abubakar ya yi maganar cike da zoyala da nishaÉ—i kamar ba shike tamke fuska É—azu ba.

Kallon É—ayar budurwar dake tsaye gefe ya yi Yana faÉ—in
"Barkan ki ƙanwar mu kina lafiya?."

ÆŠan sosa kai budurwar tayi cike kunyar bata gaisheshi ba, sai shi ya gaisheta, ta amsa da
"Lafiya qalau Mister Mai Kyau, Fatan kaima hakan?."

Tayi maganar ne a Yayin da suka shiga Motar sa ita da Haleesat Rashid Rayyan a baya, sai Rafi'at a gaba, sai kuma shi bayan ya amsa ma ta sannan ya tada motar suka bar gidan.

A hanya a tsakanin Haleesat Rashid Rayyan da Abubakar Mai Kyau sai kuma wannan Budurwa mai suna Sailuba ne ake taɓa fira.

Yayin da gefe guda kuwa Rafi'at ta mayar da kanta tana kallon hanya amma can ƙasan ranta ji take kamar ta harbe Haleesat Rashid Rayyan kowa ma ya huta, daurewa kawai takeyi tana kuma ba kanta haƙuri, sai dai ta yanke a ranta suna komawa gida zata sama Dadynsu Alhaji Rafiq Rayyan da maganar Auren ta da Abubakar, kuma batason ya wuce sati biyu.

A haka har suka ƙariso gidan Uncle Riyaz! gaba ɗaya fitowa suka yi bayan ya yi parking a ƙofar gate na gidan.

Haleesat Rashid Rayyan da Sailuba suka yi gaba ita kuma Rafi'at ta tsaya suka yi sallama da Abubakar sannan ita ma tabi bayan su, shi kuma Yaja motar sa ya yi gida.

Haka abin dai ya ci gaba da tafiya kullum Abubakar sai yace gidan su Rafi'at fira, amma fa bawai dan ya yi fira da ita ba a'a.

Sai dai idan yaje ya saka ta kira masa Haleesat Rashid Rayyan suyi ta fira abin su, ita kuma a barta da kwasan Haushi.

Haleesat tun tana jin kunya harta ware sai abin ya zama idan zai zo ita take masa girki na musamman domin kuwa ita qwararriya ce ta fanin, shi kuwa haka zai ware ya kwashi gara.

Ana cikin hakan kuma aka saka Ranar Auren Rafi'at Rafiq Rayyan da Abubakar Mai Kyau, sati biyu a Ranar Rafi'at tayi kwanan farin ciki sosai, dan jinta take kamar wata amaryarsa ma.🤣

Shi kuwa ta ɓangaren Abubakar ba zai ce yana farin ciki da wannan Aure ba, haka zalika ba zai ce baya Farin ciki ba, abin dai ba yabo balle kuma wani Abu wai shi fallasa.

Haka Rayuwar ta ci gaba da wucewa ta ko wani ɓangare shiri suke, abin babu kama hannun yaro ta can Jigawa State ɓangarensu Hajiya Harirah ma duk shirya shiryen bikin Abu lele suke😘

Mutanen Lagos, France, Mai Duguri, Adamawa States harda ma mutanen Birnin London su Sagir da matarsa duk sun ƙariso, gaba ɗaya sun taho da matayen su haka su Zuwaira, Sakeenah, Jawaheer, Jummai.
Sai shirin bikin Abubakar Mai Kyau suke yi dama abu harka na masu Naira, ko da ba wani lokaci aka saka ba.
Abuja City nan ma dai shirin biki sukeyi amarya Rafi'at saboda tsananin farin ciki sai da ta zuba Ruwan sanyi a ƙasa tasha🤔.

https://whatsapp.com/channel/0029VaEZtE15a2429vfcpf20

*💋💋𝑆𝐴𝑅𝐴𝑈𝑁𝐼𝑌𝐴𝑅 𝐾𝑌𝐴𝑈💋💋*

*👑𝑇ℎ𝑒 𝐺𝑙𝑎𝑚 𝑄𝑢𝑒𝑒𝑛👑*

*𝑊𝑟𝑖𝑡𝑖𝑛𝑔 & 𝑆𝑡𝑜𝑟𝑦 𝐵𝑦*

*𝐾ℎ𝑎𝑑𝑒𝑒𝑗𝑎𝑟𝑡ℎ 𝑆𝑎𝑏𝑖`𝑢 𝑌𝑎ℎ𝑦𝑎ℎ*

{♥︎𝑇ℎ𝑒 𝑁𝑎𝑖𝑛𝑎𝑟ℎ 𝑘𝑑♥︎}

💘*𝘓𝘈𝘍𝘈𝘡𝘐 𝘞𝘙𝘐𝘛𝘛𝘌𝘙𝘚 𝘈𝘚𝘚𝘖𝘊𝘐𝘈𝘛𝘐𝘖𝘕*💘🤙

<><><><><><><><><><><><><><<><><><><><><><>>

Page *53&54*

____*

Tun ana saura kwanaki takwas a ɗaura Auren, Abubakar ya dena zuwa gidansu Rafi'at domin kuwa bai ga amfanin zuwan nashi ba, ita ma dai Rafi'at ta wani ɓangaren jindaɗinta ne hakan, tunda dai wata magana zata dena shiga tsakanin shi da Haleesat Rashid Rayyan.

Rayuwa ta ci gaba lulawa kwanaki suna raguwa a kullum kwanan duniya lokaci daÉ—a ja yake yi domin shi baya jira sai dai a jira shi.

_____*

"An É—aura Auren Abubakar Sadeeq Sameer LamiÉ—o da zankaÉ—eÉ—iyar Amaryarsa Rafi'atu Rafiq Rayyan akan sadaki mafi daraja da cancanta lakadan ba Ajalan ba.'

Wannan maganar da wani maroƙi yake yi yana ƙarawa, ita ce ta dura a kunen Haleesat Rashid Rayyan tamkar Saukar Aradu.

Dafe kanta dake faman sara ma ta tamkar zai rabe gida biyu tayi da duka hannayenta babu abin da take furtawa a bakinta fa ce kalmar.

"Inna-lilahi-wa-inna-illahir-raji'un. Alhuma-la-sahla-illa_ma-ja'altahu-sahlan,wa-anta-taj'alu-l-hzana-idha-shi'ta-sahlan.

Ya Allah! Babu wani abu mai sauƙi sai abin da ka sanya shi ya zama mai sauƙi, kuma kai kana sanya tsanani idan ka so ya zama sauƙi.''

Haka kawai take iya furtawa a bakinta zubewa a ƙasa tayi tsakiyar Bedroom ɗin.
Wai meke shirin faruwa da ita ne?. wannan wata kalar makauniyar kaddara ce, ta rasa wanda zata so sai Saurayin Yayarta, a halin yanzu kuma miji a gareta...

"Kai! Kai!! Ya Allah! Allah na tuba, wannan wata kalar makauniyar soyayya ce?."😭

Ta furta a fili cikin matsanancin kuka, baiwar Allah gaba É—aya tabi ta fita a hayyacin ta, komai abin mutum ya ganta cikin halin da take ciki sai ya tausaya mata.

Ta daɗe a wurin tana gurzar kuka kamar ranta zai fita. Kafin daga baya jin an fara knocking bedroom ɗin, yasa ta miƙe tsaye da kyar, ta shiga bathroom wanka tayi sannan ta fito zuwa lokacin kumburar da idanunta suka yi, sun ɗan ragu ba laifi.

Cikin kayanta na Anko ita ma ta shirya tsaf, sannan tayi kwalliya sama sama ba domin ya ƙara ma ta kyau ba sai dan ya rufe kumburin idanunta.

Ɓangaren da Amarya da ƙawaye da Ƴan uwa suke ta wuce kai tsaye.

Ita ma aka ci gaba da shagalin biki da ita, amma gaba É—aya jikinta a sanyaye Yake.
{Allah sarki macen fah ke nan, komai tana iya shanyewa, tana iya sadaukar da farin cikin ta akan farin cikin wani mutum daban, zaka samu a koda yaushe fuskarta a washe take da fara'a, amma kuma can ƙasan zuciyarta ita kaɗai tasan abin da takeji. Mata na gari Allah ya ƙara ɗaukaka ku, sannan kuma Allah yasa kuci ribar haƙuri duniya da lahira Ameen}...🙏

Zuwa ƙarfe huɗu da rabi na marece, masu ɗaukar Amarya suka zo domin sai an fara kaita Jigawa State wurin dangin ango, sannan bayan kwana uku zuwa lokacin sun gama shagulgulan biki da na al-ada.
Sai a dawo da ita danƙareran gidan mijinta wanda Abubakar ya gina anan Abuja.

Tayi sallama da Ƴan uwa da Abokan arziki, sannan suka kaita wajen Dadynsu ya ma ta nasihar da ko wani uba na gari yake yiwa ɗiyarsa kafin a wuce da ita ɗakin miji.

Sannan aka fito da ita, suka shishshiga motoci aka nufa Jigawa State.
Amma har lokacin da aka fita da ita daga gate na gidansu ko gudan hawaye babu a idanunta.🌚

*JIGAWA_STATE_NIGERIA_*

Sun isa Jigawa State da Amarya Rafi'at wuraren ƙarfe takwas da rabi na dare, dangin Amarya sun sama tarba na mutun tawa da dajara a wurin dangin ango manyan mutane.

Haka ma sauran kwanaki uku da suka yi suna ganin yadda aka sha shagulgulan biki dana al-ada. Lafiya aka watse sannan kuma a rana ta huÉ—u aka juya da Amarya Abuja izuwa gidan mijinta abin alfarin ko wata matar kirki.

Sun isa Abuja City wuraren ƙarfe biyar na yammaci da yake ba fitowar wuri suka yi ba.

Da isarsu tanƙameman gidan Abubakar Mai Kyau, kai tsaye aka wuce da amarya ɗakinta bayan ansa tayi addu'a kafin shigarta cikin gidan, haka ma da zasu shiga ɗakin sai da tayi addu'a, kana ta saka kyawawan ƙafafunta na dama wa'danda suka sha jan lalle ta shiga cikin haɗaɗɗen Bedroom nata a gidan mijinta Abubakar Mai Kyau.

Zuwa ƙarfe tara na dare kowa da kowa an watse, an barta ita kaɗai domin kuwa ba ango ba labarinsa.
Ganin haka yasa bata wani damu ba a nata tunanin tunda dai an É—aura aure tofa anyi mai wuyan, bathroom ta shiga tayi wanka haÉ—e da É—auro alwala.

Sannan ta fito ta shimfiÉ—a darduma a wajen da aka tanadar domin yin sallah, sannan tayi magarib da isha'i waÉ—anda bata samu tayi ba tunÉ—azu.

Shiru shiru dai Amarya Rafi'at Rafiq Rayyan tana jiran ƙarisowar angonta Abubakar Mai Kyau har wajajen ƙarfe sha ɗaya na dare, amma shiru kakeji ba ango ba labarin sa kamar yaro yaci shirwa.

Harta fara gyan gyaɗi tajiyo ƙarar mota, alamun ƙarisowar angonta Abubakar Mai Kyau. Abin ƙaunar ta.
Chapter 57 · 0% Book details