← Book details Sarauniyar Kyau Takun Farko Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 54 OF 96

Sashe 54

Sarauniyar Kyau Takun Farko Complete Hausa Novel · about 8 min read

Murmushi kawai AL_HAJI SAMEER LAMIÆŠO. Yakeyi ganin yadda family É—inshi suke cike da farin ciki, ga haÉ—in kai, wannan ya nuna mishi kenan ko da bayan ranshi Ahalinshi ba zasu tarwatse da rashin zumunci ba.

Kallon matan shi dake zagaye gefan shi ya yi yana kuma sakin murmushin nishaɗi can cikin zuciyar shi kuwa tasbihi yake yana kuma godiya ga Allah da ya azurtashi da wannan kyakyawan Ahali abin kwantance fa ɗin Birnin Jigawa State dama ƙasa Nigeria baki ɗaya hadda ƙasashen waje.😘

*SARAUNIYAR KYAU*💓

_(The Glam Queen)_ 👑

```Takun Farko```

Story & Written By:

*_The Nainarh KD_*

____________________________________________👑

*THE ONGOING BOOK'S*

1. *SONKI NE ƘADDARA TA*

MALLAKAR
FATIMA ABDULLAHI
_Batool Kamba_

2. *ZAN JIRA KA*

MALLAKAR
A'ISHA ALƘALI
_Mrs Aysib_

___________________________________________👑

Page*49&50*

Sameen dai ganin Sagir ba kyaleshi zayyi ba, yasa shi É—a ga hannu alamar surrender.

Ganin haka yasa Sagir ya koma tsakiyar palon ya zauna yana faÉ—in

"Amma Yah Sameen nagode sosai dan kuwa idan ka faÉ—a bansan ina zankai kunya ba Allah kuwa "

Ya yi maganar yana dariya sosai, shima dai Sameen dariyar yakeyi.

"Wai wannan wata kalar magana ce, da ba'a so muji ne?."

Cewar Zuwaira cikin murmushi, "Kedai bari, wata ƙila ba gaskiya a lamarin tunda kikaga yaƙi bari a faɗamana muji."

Jummai ta amshe zancen ita ma fuskar ta washe da farin ciki.

Abubakar ne yace "Tunda dai ba'a so muji shikenan mun haƙura, idan tayi wari maji ai."

Haka suka ci gaba da fira cikin fahimtar juna da maɗaukakiyar ƙaunar junansu, can wajajen magarib mazajensu Jawaheer suka zo suka ɗaukesu suka koma gida bayan sun shiga ciki an gaggaisa.

_____👑

Rayuwa ta ci-gaba da tafiya tana lulawa da mutane cikin Æ´an watanni da suka gabata, komai ya daidaita Abubakar ya koma Abuja da zama, domin kuwa a can yake kula da companies na AL_HAJI SAMEER LAMIÆŠO.

A yayin da shi kuma Yusuf ya wuce Borno State shima ya fara gudanar da.
S.L__ GROUP OF COMPANIES dake can BORNO STATE.

Shima Sameen ya yi nashi gurin Lagos yana gudanar da aikin na shi Likitanci a Babban Asibitin ƙasa dake Birnin Lagos.

Tuni aka saka ranar bikin Sagir da kyakyawar shi Suwaiba sakamakon yadda ya qwazzaba shi fa aure yake Buƙata, harda kwanciya rashin lafiya na ƙarya, duk dan saboda ah farko AL_HAJI SAMEER LAMIƊO Yaƙi Yarda, haka dole ba yarda aka saka ranar bikin nashi da Suwaiban shi, wacca ta kasance ɗiya ga Alhaji Saleh Sama'ila a Birnin Kano ta Dabo koda me kazo anfika Aha, wanda take cikin AREWA cin Nigeria yankin Africa.

Sameen shima da zankaÉ—eÉ—iyar shi Sadeeyah wacca ta kasance Æ´ar Gombe State ce ita, sai Yusuf da tashi gwanar Yusra Æ´ar asalin Kaduna State garin governor, mazauniyar Borno State.

Kaf cikin su Abubakar ne kawai bandashi a auren, shima dai lokacin da aka zaunar dashi ana tambayar shi ko yanada tashi gwanar, sai cewa ya yi bai isa Aure ba ai.🤣

A lokacin dariya AL_HAJI SAMEER da Æ´an uwanshi maza biyu dake wurin sukayi, sannan Alhaji Yahya da yake Yaya a gurin AL_HAJI SAMEER LAMIÆŠO.

Yace "Abubakar kenan ai shi Aure da kake ganin shi lokaci ne dashi, idan lokacin ya yi kai da kanka zaka nememu, amma tunda yanzu kace baka isa auran ba, mu zamu baka lokaci nanda watanni biyar, ka ga lokacin ya yi daidai da Auren su Yusufa wata biyu da yi kenan, tunda wata uku aka saka, lokacinzamu sameka da magana idan lokacin ya yi kace mana baka samu ba. Ka yarda mu aura maka ko wacece?."

Murmushi Abubakar ya yi sannan cike da girmamawa Yace "Na amince Alhaji sannan ina godiya."

Murmushin manya kawai sukayi sannan aka ƙulla Deal.

Rayuwa ta ci-gaba tafiya yayin da kullum kwanan duniya lokaci yake kuma raguwa, wanda hakan ke ƙara ƙarfin imani ga masu shi.

A can ɓangaren kuma hakan ya yi daidai da saura sati biyu, bikin mutane uku daga Babban Ahali yara ga shahararren mutumin da duniya ke damawa dashi AL_HAJI SAMEER LAMIƊO Jigawa State.

Gaba ɗaya ɓangarori biyun shiri suke ba kama hannun yaro, ba ga dangin amare ba, haka zalika baga dangin angwaye ba, shirin shan shagalin biki ake sosai waɗannan suna nunawa waɗancan wane ku ta fannin mutunta juna da nuna abin Alkhairi ga juna.

Lokaci naja sosai har aka wayi gari a ranar wata laraba, an ɗaura Auren Sagir Samir Lamiɗo, da zankaɗeɗiyar amaryarsa Suwaiba Saleh Sama'ila a Birnin Kano ƙarfe sha ɗaya na safe, Auren da ya sama hallartar duban jama'a na fa ɗin Nigeria dama wajenta.

Sai kuma Sameen Samir Lamiɗo, shima da tashi gwanar a Babban masallacin jumma'a na Birnin Gombe State, misalin ƙarfe biyu da rabi na rana.

Sannan Yusuf Samir Lamiɗo, shima a Kaduna State ƙofar gidan mahaifin amaryar sa Yusra, Alhaji Nazir Sani Sidi, misalin ƙarfe huɗu da rabi na yamma aka ɗaura Auren.

Daganan kuma Æ´an É—aurin Aure da kuma matan da sukazo tare, aka wuce da amarya Yusra Jigawa State wurin dangin ango, kafin daga baya ita da angonta su wuce Borno State wurin da yake zaune.

Sun isa Jigawa State can cikin dare wajajen ƙarfe sha ɗaya, dan haka ba'a tsaya jiran komai ba, aka musu tarba na ban girma sannan aka saukesu a masauki ɓangarena musamman.

Washe gari da ta kama Alhamis sannan kuma ranar cikan biki, aka tashi da sabon shagali wanda aka nuna ainihin al'adar mutan garin, ansha shagulgulan biki sosai kuma jama'a da dangin amare sun ƙayatu matuƙa.
Sai da aka kwashe kwanaki uku ana shan shagulgulan biki sannan komai ya lafa.

Zuwa rana ta biyar da bikin, gaba É—aya jama'a sun watse gida ya rage daga amare da angwayen su sai kuma surukai iyayen angwaye.

Zuwa dare bayan isha'i Alhaji Samir LamiÉ—o, da matan shi Hajiya Harirah da Dr_Raheemah da kuma da Hajiya Zuwairiya.

Gaba ɗaya suna zazzaune a ƙaton palon gidan, wanda ya gaji haɗuwa yasha kayan more rayuwa kala kala abin ba'a magana sai wanda ya gani.

Sai ga Yusuf ya shigo amaryar shi na take mishi baya, fuskar ta lulluɓe da lufaya mai shigen kayan jikinta, wuri suka samu daga can gefe a ƙasa, suka zazzauna, sai ga Sameen shima da tashi amaryar sanye cikin shiga kala ɗaya suke, ita himar ne dogo har ƙasa a jikinta, wuri suma suka samu suka zazzauna Sameen kusa da Yusuf yayin da da amaryar shi ta zauna kusa da Yusra matar Yusuf suma suka gaggaisa dasu Hajiya Zuwairiya.

Can sai ga Auta Sagir da kyakyawar amaryar sa Suwaiba suma sun shigo bakinsu ɗauke da sallama cikin shiga iri ɗaya, suka shigo sai faman baza ƙamshi da gyalli irinna amare sabbin suke.🥰

Kusa da Alhaji Samir Lamiɗo Sagir ya ƙarisa ya zauna, ganin hakan yasa Suwaiba ita ma ta ƙarisa wajen su Sadeeyah ta zauna tana Suna sakarwa juna murmushin yaƙe na rashin sabo.

Buɗe taro akayi da addu'a sannan AL_HAJI SAMEER da matansa suka shiga jero nasihohi akan zaman Aure da ladan dake ciki, muddin za'a daure ayi haƙuri to akwai riba a gaba, domin shi Aure akwai farin ciki a ciki sannan kuma akwai akasin hakan, daga ƙarshe dai aka kuma rufe taro da addu'o'i sannan aka sallami kowa.

WASH£ GARI

Gaba É—aya amare da angwaye duk suka watse yayin da Yusuf ya yi Borno State da matar shi.

Sameen kuma ya yi Lagos da nashi matar, su kuma Sagir da Suwaiba amarya sai wajen ƙarfe shida na yamma sannan suka bi jirgi izuwa London domin su a can ɗin zasu ƙarishe karatun su.

Gida ya rage daga Abubakar wanda shi sai zuwa gobe zai wuce Abuja, sai kuma sauran jama'ar ciki suma dai su Zuwaira, Jawaheer, Jummai, Sakeenah waÉ—anda sukazo rakiya ga angwaye sai zuwa dare duk suka koma gidajen su cike da kewar Æ´an uwansu.

*AURE KENAN*

*WASH£ GARI*

Shima Abubakar mai kyau 😁

Yabi jirgin Safe izuwa Babban Birnin Nigeria Abuja City.

Da isarsa Abuja ya ɗaura da harkokinsa daga inda ya tsaya, sam baya ma saka maganar Aure a ranshi, domin kuwa ba shine a gabanshi ba, a halin yanzu Babban abin da ke gabanshi, shine gudanar da Aikin shi cikin nasara da kuma kyautatawa na ƙasa dashi.

_*
Rayuwa ta ci-gaba da tafiya tana lulawa da mutane cikin sauri sauri lokaci ke wucewa.

Har aka kwashe tsawon watanni biyar gaba, cikin lokacin harkoki sun ƙara buɗewa Abubakar Mai Kyau ta ko'ina kuɗaɗe shigowa suke yi gare shi, dama kuma akwai su waɗanda ba'asan a dadi ba ma, sunan Abubakar Mai Kyau ba iyaka family da Abokan shi waɗanda suka saka mishi sunan ya tsaya ba, a'a sunan Abubakar Mai Kyau ya zagaye gaba ɗaya ƙasa, harma da wajen ta.

Abubakar Mai Kyau shi sam yama manta da wata Agreement dake a tsakanin shi dasu Alhaji Yahya akan batun Aure, gaba É—aya yafi mayar da hankalinshi akan gina gobenshi.

Wata Ranar Saturday da ta kasance weekend yana kwance saman 3sieter a dake ƙaton palon shi, yana tunanin yanayin Rayuwa ya yi nisa sosai.

Yaji ƙarar ringtone na wayar shi dake saman center table, cike da kasalar da baisan ta miye ba, ya miƙa hannun shi na dama ya ɗauki wayar, ba tare da ya duba mai kiran ba, domin kuwa idanun shi a rufe suke ruf ya yi picking call din, Sannan ya yi sallama a kasalance.

Bai san lokacin da ya miƙe daga zaune ba, ƴan sauran baccin da yakeji da kasala, gaba ɗaya ya nemesu ya rasa.

Cikin tsananin girmamawa da ladabi yake gaisar da mahaifin shi da ya kira wayar. Tamkar yana a gaban shi, cike da ladabi ya amsa da
"To Abbhee Insha Allah nanda gobe ina hanya."

Yana faÉ—an hakan sukayi sallama ya kashe wayar.

Aje wayar ya yi gefe sannan ya yi tsuru, yana tunanin abin da zaisa mahaifinsa ya mishi irin wannan kiran na gaggawa, Amma duk iya tunanin shi bai hasaso komai ba, dan haka miƙewa ya yi ya koma Bedroom tun a lokacin ya fara shirya shirye domin zuwa gobe ya wuce Jigawa State.

__WASHE GARI

JIGAWA STATE__

Ƙarfe ɗaya na rana tayi mishi a ƙofar gate na gidansu, horn driver ya yi, gate man ya wangale gate sannan slowly jerin motocin suka shiga cikin gidan.
Chapter 54 · 0% Book details