Sashe 59
Indo Sarƙa Complete Hausa Novel · about 8 min read
Hajiya Safiya ta kalli Indo dake cen a zaune kusa da mahaifiyarta ta ce, "Ya me shari'a bani da wani dalili face ƙyashi, hassada da baƙin ciki da suka ruɗeni. Kasancewar mun taso gari ɗaya kuma unguwa ɗaya da Safna, sai ya kasance makarantarmu ɗaya kuma ajinmu ɗaya da ita. Safna tana da ƙwazo da ƙoƙari yadda har makarantar mu ya kasance ansan da ita, kafin zuwanta duk ajinmu dama na girmesu dan haka gabaɗaya sai suke tsorona, duk abinda na faɗa basa iya ƙetarewa kuma duk abinda na gani agunka nace ina so zan karɓa baka isa ka tanka ba. Kwatsam sai aka kawo Safna ajinmu, tun daga zuwanta na fara nuna halina akanta amma sai taƙi amince da shi, saboda bata da tsoro ko kaɗan kuma girmana baisa ta ji shakkuna ba. Ganin haka yasa sauran ƴan ajinmu suka fara daina tsorona, daga baya ma sai gabaɗaya ƴan ajinmu suka rainani, tun daga lokacin tsanarta ta ɗarsu a zuciyata. Sai kuma ƙoƙarin da take da shi duk lokacin da akayi jarrabawa ita take zuwa ta ɗaya, ni kuma kusan nice ta ƙarshe ta biyun ƙarshen aji. Wata rana munyi faɗa da ita, dan kuwa ni na takali faɗan kawai sai ta mun gorin ƙoƙari nikuwa na lakaɗa mata duka, aikuwa tana guduwa ta samu ƴan ajinmu suka fara yi minj waƙar Safiyya ganɗama daƙiƙiya, tun daga ranar sunana yayi fice a makarantarmu, har ta kai ta kawo idan bakace Ganɗama babu wanda zai ganeni. Sai na koma mujiya a cikin makarantar kowa tsokanata yake yi, ana haka har Yayana ya zo ya sanar da shugan makarantar, daga ranar ne na ɗan samu sasaauci. Ana cikin haka sai su Safna suka dawo nan layinmu gida biyu ne kawai ya rabamu da su, a lokacin kuma muna shekarar mu ta ƙarshe a sakandire. A lokacin ina tare da saurayina Sulaiman yana ƙyalla ido da ya ganta, ya daina zuwa gurina dana matsa masa da tambaya ya kwatanta mun ita, tare da cewa ya faɗa tarkon ƙaunarta. Ba ƙaramin tashin hankali na shiga a lokacin ba, amma sai mahaifiya ta tausheni tare da nusar dani wataƙila dama ba mijin aurena bane.
Wata rana da yamma na fita naci karo da Safna tana zance da Khalil, tunda na ƙyalla ido akanshi naji duk duniya babu wanda nake ƙauna kamar shi, a ranar dashi na kwana a raina ko baccin kirki banyi ba, tunani na dinga yi yadda zan samu na samu koda lambarsa ce amma na kasa. Sai dabara ta faɗo mun akan na ƙulla ƙwawance da Safna ko na samu ta saki jiki dani na samu lambarsa a gurinta. Shiryawa nayi naje gidansu na sameta muka gaisa fuskarta ba walwala, kasancewar kowa yasan ba shiri muke da Safna, sunkuyar da kai ƙasa nayi na nemi alfarma da mu aje wannan rashin jituwar da muke gefe ɗaya mu cigaba da rayuwa kamar kowa, amsa mun tayi daga haka na fara nuna soyayyata ga Safna a fili wanda a zuciyata ba haka bane, ita kanta Safna da farko ƙin sakin jiki tayi da ni, sai daga baya ta saki jikinta muka cigaba da ƙawancenmu gwanin sha'awa..." Alƙali ne ya ƙatse Hajiya Safiya sannan lauyoyi suka cigaba da fafatawa, daga ƙarshe Alƙali ya ɗaga shari'ar zuwa goma ga watan gaba, sati biyar kafin komawarsu.Hajiya Safiya da su Hadari aka tasa ƙeyarsu gidan yari, haka kotun ta tashi mutane na Allah wadai da hali irin na Hajiya Safiya.
A yau ne su Indo suka zana jarrabawarsu ta ƙarshe, murna gurinta tare da sauran ɗalibai ba'a magana. Kuma tun safiyar ranar Yaseer ya tura mata saƙwanni kala-kala na soyyaya, kuma a ranar ne ya da Daddynsa abinda ke tsakaninsa da Indo, Daddy ba ƙaramin farinciki yayi ba, a take kuma ya kira ƴan Mahaifin Indo ya sanar dashi, shima ba ƙaramin daɗi yaji ba nan take ya kira sauran ƴan uwansa ya sanar dasu.
_UMMOU ASLAM BINT ADAM_😉
[02/10, 19:30] Omu Aslam Bint AdamâœðŸ¼: *FIRST CLASS WRITERS ASSO*☀ï¸
*{Home of qualities and trusted writer's of The nation}*
https://www.facebook.com/groups/856755331683130/?ref=share
*INDO SARƘA*🤸ðŸ¼â€â™€ï¸
*BY*
*AMEERA ADAM*
*FOLLOW ME @WATTPAD*
_*AmeeraAdam60*_
GARGAÆŠI BAN YARDA WANI YA SAUYA MUN LITTAFIN NAN TA KOWACCE SIGA BA BATARE DA IZININA BA.
_*WANNAN LITTAFIN GABA ÆŠAYA SADAUKARWA NE GA DUK MAI SUNA AISHA😉🥱 NAMESAKE WHERE ARE UðŸ¤*_
_SHARARRIYAR MARUCIYAR NAN MAI LITTAFIN *SO KO WAHALA* TA ƘARA DAWO MUKU DA WANI ZAZZAFAN LITTAFI MAI SUNA *ƳAR HIZBA* BAZANCE KOMAI AMMA KUNSAN SALON LABARINTA DABAN YAKE, MASOYA KU GARZAYO KAR A BAKU LABARI._
*Alhamdulillah masu buƙatar sabon littafina 🧕ƳAR HIZBA🧕 da zai zo bayan sallah zasu iya biyan kuɗin karatunsu tun yanzu, normal group #200, vip 300, special 400. Za'a tura kuɗin ta wannan Accoun No. ɗin 2083460164 Abubakar Abdullahi Usman Zenith Bank ko a turo katin Waya na MTN ta wannan number 07038826617 ta wannan number za a turo shaida, ta nan za a tuntuɓeni don neman ƙarin bayani.*
89&90
Kwamishina gyaran murya ya yi ya ce, "Alhaji dan Allah ka saurareni ka bamu haɗin kai, dan sun faɗi haka bashi zai nuna cewar da gasken hakan bane. Bincike shi zaiyi aikinsa mu tabbatar da me gaskiya, mara gaskiya mu miƙashi Kotu..." a hassale Yaya Haruna ya ce, "Kana zargin Iyalina a matsayin mai laifi kuma ka ce na kwantar da hankalina, sam ni ban yadda da wannan maganar ba. Kai Mhusin tashi mu tafi." Muhsin da tun da yaji sunan mahaifiyarsa a ciki yake muzurai, yana harare-harare ya miƙe ya bi bayan mahaifinsa. Har ya kusa zuwa ƙofa Kwamishina ya ce, "Alhaji karka manta ita hukuma tana amfani da hujja ne, zan turo yara su binciki matarka, ba ma ita ba ko da kai ne bincike ya biyo ta ka kanka ina fatan zaku bamu haɗin kai." Yaya Haruna ji yayi kamar anwatsa masa ruwan zafi, saboda masifa jikinsa har rawa yake ya juyo ya ce, "Na amince idan kuka same ni ko iyalina da laifi duk hukuncin da ya dace kuyi mun, idan kuma yaran nan ƙazafi sukayi mata wallahi sai ɗauki mataki." ya juya fuuu ya bar ofis ɗin Alhaji Khalil na ƙwala masa kira, amma ko waige baiyi ba.
Kwamishina murnushi ya yi ya ce, "Alhaji karka damu, idan da sabo mun saba da ganin irin haka harma fiye da haka. Ka ƙyaleshi na ɗan lokaci zai sakko kasan ko waye aka gaya masa irin haka, zai shiga irin wannan yanayi amma ka bari bincike shi zai fayyace mana komai." Alhaji Khalil ya ce, "Yallaɓai ina tsoron kar wannan dalilin ya wargaza farincikin dangina, wallahi ina matuƙar ƙaunar ƴan uwana banasan zumuncinmu ya ruguje." Kwamishina ya ce, "Abokina sai fa ankauda ƴan uwantaka da sanayya, idan ba haka ba za'ayi kitso da kwarkwata." ajiyar zuciya Alhaji Khalil ya yi ya ce, "Haka ne Abokina, Allah ya iya mana" Kwamishina ya ce, "Amin, zan tura yarana su gayyato mana Hajiya Safiya, kuma zamu tsaurara bincike akai" tattaunawa suka ƙarayi sannan suka yi sallama da Kwamishina ya wuce gida.
Lokacin da yaje gida ya sanarwa da Aunty Safna maganar da su Hadari suka faɗa, jikinta ne ya yi sanyi cikin kuka ta ce, "Ni kuwa me nayi wa Safiya da zata aika haka agareni? Me na tsare mata a rayuwa?" Lallashinta ya dinga yi har ya samu ya lallasheta, ta daina kuka sannan ya kira sauran ƴan uwansa ya sanar da su halin da ake ciki. A cen gidan Alhaji Haruna ƴan sanda tuni sukayi dirar ɗango, da gaske suke yasa Alhaji Haruna ya ce zai ɗauki matarsa ya kai ta da kansa. Hajiya Safiya banda muzurai babu abin da take yi. Hankalinta bai ƙara tashi ba sai da suka ƙarasa tayi tozali da su Hadari, ana tambayar Hadari ya tabbatar da ita, har da lambar wayarta ya shaida musu a wayarta da kwangilar da ta basu, daga ƙarshe ya nuna musu alert ɗin kuɗin da tayi musu wanda ga sunanta nan, ɓaro-ɓaro da lambar bankinta. Lokacin da abin yake faruwa Fahad da Alhaji Khalil sun koma headquater, a gabansu duk yake faruwa.
Alhaji Haruna ne ya buga mata tsawa jin antamabaye tayi shiru. kamar munafuka haka ta fara raba idanu tana motsa baki amma ta kasa magana, a hassale ya miƙe kamar zai doke ya ce, "Wai ba magana nake miki ba? Kece kika basu umarnin kashe Humaira?" girgiza kai tayi ta ce, "A'a ƙarya suke mini" Hadari yayi karaf ya ce, "Ke lallai matar nan ni zakiyiwa latsi, wallahi ko kwalba haka ta ganni ta ƙyale a iya sharri" Kwamishina ya ce, "Idan ba ke bace, ya akayi kikayi musu alert?" tsugunnawa Hajiya Safiya tayi ta ce, "Dan Allah Alhaji ku gafarceni wallahi sharrin sheɗan ne..." kafin ta rufe baki Alhaji Haruna ya ɗauke ta da mari ya ce, "Keda Sheɗan ɗin na ɗura muku ashar, kisa akashe mun ƴar ƙanina ki ce sharrin sheɗan ne?" da sauri Alhaji Khalil ya riƙe ɗan uwansa yana bashi haƙuri, Yaya Haruna banda huci babu abinda yake yi, cikin huci ya ce. "Wallahi sai an hukuntaki annamimiya makira" Muhsin da ke gefe haushin mahaifiyarsa ne yaji ya kamashi, wani irin kallo yake jifanta da shi mai wuyar musaltuwa.
Da ƙyar Kwamishina ya sallami Alhaji Khalil tare da ƴan uwansa, lokacin da zai tafi ya kalli Mahaifiyar su Lubna ya ce, "Kuma wallahi ni da ke har abada kije na sake ki saki uku" Hajiya Safiya rushewa tayi da kuka amma ko waigenta baiyi ba, Fahad banda harara babu abinda yake wurga mata.
Daga nan Headquater kai tsaye kotun Addinin musulunci aka miƙa su Hadari da Hajiya Safiya, Yaya Haruna da kanshi ya ɗauki lauyan masu ƙara. ya yinda Hajiya Safiya ta ɗauki lauyanta, su kuwa su Hadari basu da lauya dan haka Alƙali yace sai dai su kare kansu.
Wata rana da yamma na fita naci karo da Safna tana zance da Khalil, tunda na ƙyalla ido akanshi naji duk duniya babu wanda nake ƙauna kamar shi, a ranar dashi na kwana a raina ko baccin kirki banyi ba, tunani na dinga yi yadda zan samu na samu koda lambarsa ce amma na kasa. Sai dabara ta faɗo mun akan na ƙulla ƙwawance da Safna ko na samu ta saki jiki dani na samu lambarsa a gurinta. Shiryawa nayi naje gidansu na sameta muka gaisa fuskarta ba walwala, kasancewar kowa yasan ba shiri muke da Safna, sunkuyar da kai ƙasa nayi na nemi alfarma da mu aje wannan rashin jituwar da muke gefe ɗaya mu cigaba da rayuwa kamar kowa, amsa mun tayi daga haka na fara nuna soyayyata ga Safna a fili wanda a zuciyata ba haka bane, ita kanta Safna da farko ƙin sakin jiki tayi da ni, sai daga baya ta saki jikinta muka cigaba da ƙawancenmu gwanin sha'awa..." Alƙali ne ya ƙatse Hajiya Safiya sannan lauyoyi suka cigaba da fafatawa, daga ƙarshe Alƙali ya ɗaga shari'ar zuwa goma ga watan gaba, sati biyar kafin komawarsu.Hajiya Safiya da su Hadari aka tasa ƙeyarsu gidan yari, haka kotun ta tashi mutane na Allah wadai da hali irin na Hajiya Safiya.
A yau ne su Indo suka zana jarrabawarsu ta ƙarshe, murna gurinta tare da sauran ɗalibai ba'a magana. Kuma tun safiyar ranar Yaseer ya tura mata saƙwanni kala-kala na soyyaya, kuma a ranar ne ya da Daddynsa abinda ke tsakaninsa da Indo, Daddy ba ƙaramin farinciki yayi ba, a take kuma ya kira ƴan Mahaifin Indo ya sanar dashi, shima ba ƙaramin daɗi yaji ba nan take ya kira sauran ƴan uwansa ya sanar dasu.
_UMMOU ASLAM BINT ADAM_😉
[02/10, 19:30] Omu Aslam Bint AdamâœðŸ¼: *FIRST CLASS WRITERS ASSO*☀ï¸
*{Home of qualities and trusted writer's of The nation}*
https://www.facebook.com/groups/856755331683130/?ref=share
*INDO SARƘA*🤸ðŸ¼â€â™€ï¸
*BY*
*AMEERA ADAM*
*FOLLOW ME @WATTPAD*
_*AmeeraAdam60*_
GARGAÆŠI BAN YARDA WANI YA SAUYA MUN LITTAFIN NAN TA KOWACCE SIGA BA BATARE DA IZININA BA.
_*WANNAN LITTAFIN GABA ÆŠAYA SADAUKARWA NE GA DUK MAI SUNA AISHA😉🥱 NAMESAKE WHERE ARE UðŸ¤*_
_SHARARRIYAR MARUCIYAR NAN MAI LITTAFIN *SO KO WAHALA* TA ƘARA DAWO MUKU DA WANI ZAZZAFAN LITTAFI MAI SUNA *ƳAR HIZBA* BAZANCE KOMAI AMMA KUNSAN SALON LABARINTA DABAN YAKE, MASOYA KU GARZAYO KAR A BAKU LABARI._
*Alhamdulillah masu buƙatar sabon littafina 🧕ƳAR HIZBA🧕 da zai zo bayan sallah zasu iya biyan kuɗin karatunsu tun yanzu, normal group #200, vip 300, special 400. Za'a tura kuɗin ta wannan Accoun No. ɗin 2083460164 Abubakar Abdullahi Usman Zenith Bank ko a turo katin Waya na MTN ta wannan number 07038826617 ta wannan number za a turo shaida, ta nan za a tuntuɓeni don neman ƙarin bayani.*
89&90
Kwamishina gyaran murya ya yi ya ce, "Alhaji dan Allah ka saurareni ka bamu haɗin kai, dan sun faɗi haka bashi zai nuna cewar da gasken hakan bane. Bincike shi zaiyi aikinsa mu tabbatar da me gaskiya, mara gaskiya mu miƙashi Kotu..." a hassale Yaya Haruna ya ce, "Kana zargin Iyalina a matsayin mai laifi kuma ka ce na kwantar da hankalina, sam ni ban yadda da wannan maganar ba. Kai Mhusin tashi mu tafi." Muhsin da tun da yaji sunan mahaifiyarsa a ciki yake muzurai, yana harare-harare ya miƙe ya bi bayan mahaifinsa. Har ya kusa zuwa ƙofa Kwamishina ya ce, "Alhaji karka manta ita hukuma tana amfani da hujja ne, zan turo yara su binciki matarka, ba ma ita ba ko da kai ne bincike ya biyo ta ka kanka ina fatan zaku bamu haɗin kai." Yaya Haruna ji yayi kamar anwatsa masa ruwan zafi, saboda masifa jikinsa har rawa yake ya juyo ya ce, "Na amince idan kuka same ni ko iyalina da laifi duk hukuncin da ya dace kuyi mun, idan kuma yaran nan ƙazafi sukayi mata wallahi sai ɗauki mataki." ya juya fuuu ya bar ofis ɗin Alhaji Khalil na ƙwala masa kira, amma ko waige baiyi ba.
Kwamishina murnushi ya yi ya ce, "Alhaji karka damu, idan da sabo mun saba da ganin irin haka harma fiye da haka. Ka ƙyaleshi na ɗan lokaci zai sakko kasan ko waye aka gaya masa irin haka, zai shiga irin wannan yanayi amma ka bari bincike shi zai fayyace mana komai." Alhaji Khalil ya ce, "Yallaɓai ina tsoron kar wannan dalilin ya wargaza farincikin dangina, wallahi ina matuƙar ƙaunar ƴan uwana banasan zumuncinmu ya ruguje." Kwamishina ya ce, "Abokina sai fa ankauda ƴan uwantaka da sanayya, idan ba haka ba za'ayi kitso da kwarkwata." ajiyar zuciya Alhaji Khalil ya yi ya ce, "Haka ne Abokina, Allah ya iya mana" Kwamishina ya ce, "Amin, zan tura yarana su gayyato mana Hajiya Safiya, kuma zamu tsaurara bincike akai" tattaunawa suka ƙarayi sannan suka yi sallama da Kwamishina ya wuce gida.
Lokacin da yaje gida ya sanarwa da Aunty Safna maganar da su Hadari suka faɗa, jikinta ne ya yi sanyi cikin kuka ta ce, "Ni kuwa me nayi wa Safiya da zata aika haka agareni? Me na tsare mata a rayuwa?" Lallashinta ya dinga yi har ya samu ya lallasheta, ta daina kuka sannan ya kira sauran ƴan uwansa ya sanar da su halin da ake ciki. A cen gidan Alhaji Haruna ƴan sanda tuni sukayi dirar ɗango, da gaske suke yasa Alhaji Haruna ya ce zai ɗauki matarsa ya kai ta da kansa. Hajiya Safiya banda muzurai babu abin da take yi. Hankalinta bai ƙara tashi ba sai da suka ƙarasa tayi tozali da su Hadari, ana tambayar Hadari ya tabbatar da ita, har da lambar wayarta ya shaida musu a wayarta da kwangilar da ta basu, daga ƙarshe ya nuna musu alert ɗin kuɗin da tayi musu wanda ga sunanta nan, ɓaro-ɓaro da lambar bankinta. Lokacin da abin yake faruwa Fahad da Alhaji Khalil sun koma headquater, a gabansu duk yake faruwa.
Alhaji Haruna ne ya buga mata tsawa jin antamabaye tayi shiru. kamar munafuka haka ta fara raba idanu tana motsa baki amma ta kasa magana, a hassale ya miƙe kamar zai doke ya ce, "Wai ba magana nake miki ba? Kece kika basu umarnin kashe Humaira?" girgiza kai tayi ta ce, "A'a ƙarya suke mini" Hadari yayi karaf ya ce, "Ke lallai matar nan ni zakiyiwa latsi, wallahi ko kwalba haka ta ganni ta ƙyale a iya sharri" Kwamishina ya ce, "Idan ba ke bace, ya akayi kikayi musu alert?" tsugunnawa Hajiya Safiya tayi ta ce, "Dan Allah Alhaji ku gafarceni wallahi sharrin sheɗan ne..." kafin ta rufe baki Alhaji Haruna ya ɗauke ta da mari ya ce, "Keda Sheɗan ɗin na ɗura muku ashar, kisa akashe mun ƴar ƙanina ki ce sharrin sheɗan ne?" da sauri Alhaji Khalil ya riƙe ɗan uwansa yana bashi haƙuri, Yaya Haruna banda huci babu abinda yake yi, cikin huci ya ce. "Wallahi sai an hukuntaki annamimiya makira" Muhsin da ke gefe haushin mahaifiyarsa ne yaji ya kamashi, wani irin kallo yake jifanta da shi mai wuyar musaltuwa.
Da ƙyar Kwamishina ya sallami Alhaji Khalil tare da ƴan uwansa, lokacin da zai tafi ya kalli Mahaifiyar su Lubna ya ce, "Kuma wallahi ni da ke har abada kije na sake ki saki uku" Hajiya Safiya rushewa tayi da kuka amma ko waigenta baiyi ba, Fahad banda harara babu abinda yake wurga mata.
Daga nan Headquater kai tsaye kotun Addinin musulunci aka miƙa su Hadari da Hajiya Safiya, Yaya Haruna da kanshi ya ɗauki lauyan masu ƙara. ya yinda Hajiya Safiya ta ɗauki lauyanta, su kuwa su Hadari basu da lauya dan haka Alƙali yace sai dai su kare kansu.